Kanin Ajali
Chapter 27 of 34
zancen gaskiya bane su ko gidan su maryam bata zuwa har ta bar gari.
Haka yasa ni naji sanyi a raina har na basar da zancen don dama na kulla zan barsu har abada idan zancen ya zama gaskiya sai na samu ba haka zancen yake ba.
Ashe sun boye min ne gaskiya ne dasu akai duk wani kulle kullen tafiyan ita maryam din.
Ba dadi da dadi akoma sana,ata ta kayan mata ina kuma dan yin sana,an yara madara aya da sauran su a gida yara na shigowa suna saye.
Sai da ya share wata hudu kafin kacar yayo min sakon dubu biyar mu sai abincin da zamuci.
Jifa dubu biyar mai zai min nida yara da duk sun isa cin abinci yanzu haka na hakkura na karbi kudin muka sai dan abin bukatan mu dashi.
A cikin hakan da muke ne na samu na dan sai tufafin dana dinka nida yarana karo na farko a rayuwana ke nan koshi bashi naci ina bada dan abin daya samu a hankali.
Wanan yasa har ina da shiga jama, a yanzu tunda ina da dan nashiga mutane din da ko bukin dangi ya tashi duk yadda muke da mutum ba zai ganni ba.
A cikin hakan kanwata suka zo ganin gida karo na farko tun tafiyan su kano da mijin ta da ya dauke ta suka tafi.
Sai dai ba wanda yaji dadin gani yadda duk ta ramay ta kalmashe da gani itama dai zaman ana dai yin shine hakana.
Sai dai ita tana da zurfin ciki sosai don bata fadawa kowa halin da take ciki a gidan ta duk da yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba gun mutane.
Bata fada ba amma an fahinci hakan a gareta do a san halin da take ciki ba mai dadi bane don ba jiki mai kyau ba suturan kware a gareta sai dai ta dan darani ga hakan .
Don tana dana canzawa gaskiya sosai sai dai ba wani na birgewa ba ne sosai hakan da za a gani asan miji yana kulla da ita .
Abi mamaki shine duk mazaje namu sai kiba suke mulkawa a jikin su muko muna rama kamar ana diban mu kullun.
Don ko shi mijin nata yadda nawa yayi kiba haka shima ya mulka kiban shi ga mota har ya saye na hawa da fara aikin shi .
Shikan zaka gane shi ka gane da birni ne sosai ga wayewa a fuskan shi sai itace ta zama wata yar kunju da ita.
Sai da muka samu kebewa ne da ita nake tambayan ta halin da suke ciki da mijin nata sai take fada min komai.
Babu dai dadi sai dai ta dan dara nine kadan wurin samun walwala amma shima kusan mayau dari ne mijin nata don bai bari ta rike komai a hannun ta karshe kuma yace ba kudin kamar na Jamil dina.
Kuka mukayi sosai muna ba juna magana kn halim da maza suka jefa mu a ciki sai da mu kayi sai da muka gaji muka ba kan mu hakku.
Nace ta boye wanan zancen kada ta bari kowa yaji halin da take ciki a gidan ta tace ai ba zata iya fadi ba ko don anty .
Tunda tun farko saida ta fada muna haka zasuyi muna bamu ji ba yanzu wa zamu tun kara da zancen.
Duk da mun boye sai da anty ta gane muna a cikin wani hali tundai summaiya din don dai ni idan da sabo sun saba da nawa matsalan ko.
Tare muka shigo gidan da kanwata bayan mun gaisa anty ke fadin anya Summaiya kina cikin dadin rai kuwa ?
Dariya tayi na anty kawai tare da tambayan may ta gani halan tace yanayin ki ya nuna akwai abinda ke damun zuciyar ki gaskiya.
Bata samu wani amsa kwarai ba ta bar zancen aka dauko wani hira sai dai hankalinta bai kwanta da ita ba.
Don yawan kallon kanwar tawa da take yi akai akai yasa duk muka tsargu da zama tare da ita.
Karshe tashi mukayi zuwa dakin yan matan gidan muka zauna ana hira mun kai har yamma a gidan kafin mu koma gidajen mu.
A hanya muke maganan abinda yafaru tsakamin mu da anty har muka kai gidan mu muna magana daya akan matsalolin mu.
Bayan kwana biyu ban san inda taji zance a gari ba wanda ni ma dake garin ban sani ba sai ita da tazo daga baya.
Sai gata min hankali tashe tana tambayana wai Jamil wani gari yace min yake ?
Cikin washe baki nake fadin yana abuja ai kila ma ya dawo kafin ku koma don yace kwanan nan zai leko gida.
Ke kin yarda da cewan shi a Abuja yake zaune ne ta tambayane cikin son jin abinda zance mata din.
Nace can yake don haka yace min da zai tafi sai naga tayi shiru taja bakin ta batai wani dadewa ba tace zata koma gida.
Nace tun yanzu zaki koma barin dan dafa muna wani abu muci mana, kai ta girgiza min tare da fadin ita zata tafi.
Don a gidan mahaifan mijin ta suka sauka don sun sake gidan da suke haya da farko.
Rakiya nayi mata har ta samu abin hawa da zai kaita gida sai dai ina dawowa tunanen maganan ta ya hanani sukuni a raina.
Da kyat na basar da maganan cikin zuciyana don kaina ya kulle da tambayan da tai min din wanda ban san dalilin ta na min wanan tambayan ba haka kan jamil din.
Maganan yaso ya tsaya min a rai ko washe gari, sai dai na basar da zancen don ban san dalilin ta na tambayana ba dai.
Yan tsunmakaran ta da na yaranta ta debo ta bamu mu kara duk da banda su hakana na amsa sai dai na raina kayan .
Har fada mata nayi yanzun ke wanan raggadudan zaki bamu don Allah tace ai itama bata da wadattacen kaya da zata bamu wanda yafi wanan din.
Bayan kwana biyu suka fara shiri komawa kano har lokacin Jamil bai dawo ba sai ana jibi zasu koma ne ya dira a garin.
Abin mamaki ga wanda yaje nema ana sa ran zai dawo da abin arziki baje baje sai dai shi Jamil sabani haka na gani a gare shi.
Don daga shi sai yar jakkar tafiya irin ta maza ya dawo garin babu komai a tare dashi.
Sai na dauka kudi ya riko ya dawo dasu gidan don wahalan daukan kayan da zaiyi daga can .
Sai dai har aka kwana aka wuni banji wani abu daga guri shi ba sai kwasan barcin da yake faman yi tun da yadawo a gida bai fita ba.
Abinci lafiyayye na hada mai har da ciwo bashin kayan miya a makwabatar mu na hada mai abincin.
Ya tashi daga barci ya nemi ruwan wanka nakai mai da soso da sabulu ya fito lokacin na gama abinci sai da ya shirya idan ya gama zai fita.
Yar karamar yar mu ce tazo wurin shi tana fadin baba mai ka sawo muna can da zaka dawo shafa kan yarinyar yayi yana fadin..
Ka dai ba kinga babanki ya iso gida lafiya ba mamana da yanzu yan fashi sun kashe maki baba a ganya ai.
Cikin faduwan gabx nace yan fashi kuma ban ya shiga rabtabo min karyan da ya shirya mi duk nabi na rude.
Hankalina ya tashi yadda yake bamu labarin a cikin tashin hankali nan nayi muna barka da arziki da Allah ya tsirar muna dashi daga hannun yan fashi basu kashe shiba ko su illanta shi.
Yana ganin karyan shi ya kamani yace zai tafi gidan mahaifan shi ya gaida su ya fada masu arzikin daya auna a hanya.
Nace tunda dai rayuwan ka ya tsira ai mun gode ma Allah arziki kuma idan da rabon muyi mayi a gaba ai.
Yaji dadin magana na yace wai da Allah yasa yazo gida da kudin nan da mun warke wallahi mun fita daga talaucin don ya samo kudi sosai acan.
Nace ba rabon mu mare masu bane Allah ya kawo hakan nan nayi ta kwantar mai da hankali da dadden magana har ya samu ya fita daga gidan.
Yana fita na nima na fita wurin yan hayan mu ina fada masu suyi min barka da arziki yan fashi Jamil ya hadu dasu a hanya sun kwace mai komai nasa da zai dawo.
A gabana sun min jaje sosai da Allah ya kare gaba kuna sai dai ina basa baya sukace wawiya ya tsarata ta yarda.
Nan dai suka zauna suna gulmana a gurin suna zagina kan irin watauna gurin miji daya tsara ni sai in yarda da karyan shi.
Yinin rana duk wanda na gani sai ba bashi labarin mijina ya auna arziki da yan fashi a hanyar shi na dawowa gida.
Komai basu barshi dashi rayuwan shi kawai ya tsira dashi a gurin su wasu suna yarda wasu kuma suna mn kallon shasha ban sani ba.
Da yamma yar uwata tazo nake fada mata abinda ya faru da jamil din a hanya.
Sai cewa naji tayi kai amma Jamil din nan bai ma ko iya karya ba wallahi da wani irin kallo mamaki na dago kai ina kallo ta.
Ban bari ta karasa maganan ta ba na hauta da fada harda zagi inda nake shiga ba nan nake fita ba don raina ya baci sosai da kalamin ta.
Tace Allah baki hakkuri anty nima rigima na ya kaini fafin haka ai ta mike tare da fadin zata karasa gidan baba kabiru tayi masu sallama.
Ko kallon arziki bata samu ba a gurin balle a dawo lafiya yadda muka saba yi idan tazo gurina sai mu dade muna zuba hira dasu.
Ba yar uwata ba a lokacin duk wanda yayi gigin tara ta ya fada min wanan magana wanke mai shi zanyi tas don idona da rufe.
Sai kuma yadda na yarda da Jamil ya sa ban iya gano illar shi ta ko ina aka fito da zancen sukan shi a gabana.
Don haka kowa yaja bakin shi yayi shiru tunda ban bari a fadi har wasu na zuwa gida yi min jaja suna muna barka da arziki.
Niko sai rabbata masu labarin yadda abin ya faru nakeyi kamar a gaba hakan ya faru yadda nake bada labarin kamar yadda ya fada min.
Kwana biyu muka fara dan ciye dan kudin dake hannu na ina dan juyawa ya fara karewa sai kama kama ya rage munayi.
Gadai miji yaje nema amma haka ya dawo muna hannu rabbana babu ko ledan burudi ya dawo muna gida.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Ya gama yaudaran shi na yan fashi sun tare shi a hanya sun kwace komai ni kuma na gaji na sake yanzu.
Baifi wata daya ba yace zai koma ya nade ya juya zuwa inda ya fito naci gaba da rayuwana a yadda na saba a baya.
Ba wayan shi ba sako tunda ya tafi don haka fadi tashi ya taso ma rayuwana don nema wa kaina abinda zamu ci.
Tunda ba zancen sutura bane yanzu gare ni sai dai na abinda zamu ci wa cikin mu kullun shine abin yi gare ni.
Ina kallo yan uwa ba zuwa buki ni ba hali inje don ko nace zan tafi babu abinda zan sa a jiki babu wanda zan kai gudu mawa a guri bukin.
Haka yasa na daina duk wani hurda da ya uwa na yanzu sai zagina ban so zumunci ban shiga dangi ga dai magana nan kala kala a kaina ba dadi anayi.
Ni kuma ni nasan abinda nake ciki da miji na ba wai a cikin dadin rai nake ba gashi ya raba ni da kowa daga cikin yan uwana.
Babu mau zuwa gurina da sunan zumunci kamar yadda nima ban zuwa gidajen nasu da sunan yin zumuci.
Wahala yakai min wahala dole na nufi gidan mu dan samun mafita a kaina bayan an gama saurare na.
Anty tace to hadiza ke ce da abin haushi duk abinda akai maku a baya baku gani ba an taimaka maki kin kwashe kin bashi.
An maki fada kin kwashe kin fada mashi abinda kowa ya fada maki gamay yana kallon kowa a hankade don kin gama zubarwa yan uwanki da mutunci a gaban shi.
Ina zaune ina hawaye banda bakin magana don duk abinda take fadi haka akayi babu karya a cikin shi.
Muryan ta ne ya katse ni tana fadin ko yanzu aka taimaka maki kara bashi zakiyi don dawowa zaiyi ya lalabe ki ya kwashe abinda kika tara.
Da sauri nace aa wallahi anty ai yanzu nayi wayau wallahi, tsuki taja bata bari naci gaba ba take fadin.
Dama duk wanda ya danki na miji a matsiyin uba itako zata mutu maraya a duniya.
Don namiji bai da tabbas baka daukan amana ka mikawa namiji hundred pacent kun nuna dan uwan mahaifin ku ya cuce ku yana cin amanan ku kan dan abinda aka bar maku a duniya.
Idon ku ya rufe mazajen ku sun maku huduban shedan kun haye kunyibwa kowa cin mutunci duk mu nan kuna muna kallon mayaudaran ku .
Abinda aka baku muke so muci daga gare ku hakan yasa kuka jaye daga wuri mu dama sun shirya hakan ne do su samu kafan yaudaran ku ba tare da kowa ya saka maku ido ba.
Don ku zauna daga ku sai su suci karen su babu babbaka ko gashi sun kuma ci tunda wawaye kuke.
Nasan ko waye jamil fiye da sanin ku na karanci wanan yaron tun yana karami nasa ko shi waye bake yake so ba hadiza tun farko abinku yake so.
Ya kuma ci yanzu ma abinda baki sani ba shine ni zuciyana bai kwanta da wanan tafiyan daya ce yayi ba na zuwa wai neman kudi.
Kaina na dago da sauri ina kallon ta da mamaki don ina tsoron kalamin anty don kamar mai baki take da wuya ta fadi bai faru ba.
Da sauri na tare ta ina fadin wallahi anty yana abuja abokin shi ma da suke can tare ya fada muna tare suke.
Na tare na hanata magana sai naga tayi murmushi tare da mikewa ta dauko dubu biyar tace shi zata iya bani a yanzu inyi hakkuri.
Idan baba ya dawa zata fada mai halin da ake ciki don a samu abinda aka taimaka min dashi din ina kuka nayi mata godiya na koma gida.
Ga dai anty tana nuna muna tankar ita ta haife mu amma mu har lokacin son mazajen mu ya rufe muna ido.
Bamu yarda su sakamu a hanya da zaran an dauko zancen mazajen namu yanzun ne zamu nuna bacin ran mu gun mutum.
Dama ita kadai ce mai fada muna gaskiya mu kyale ta itama din dai bata da zuciyane irin abinda muke mata tana shanyewa.
Nayi iya bakin kokarina i bar fada mai zancen yan uwana akanshi sai dai dadin hira bai bari na daina ba do ban sani sanda za kwashe in fada mashi komai.
Ba laifi baba ya dawo sai ga sako abinci harda kudi da sauran tarkace an kawo min naji dadin wanan sako don an samu banda komai a gidan dama.
Ranan da naje godiya a gurin baba na samu anty ta dawo daga aiki take ce min hadiza zuciyana yana ban mijin ki yana tare da wanan matar daya musuluntar har yanzu.
Ina dariya nace Anty ita da take nan jahar shi da yake abuja zaune ba tare suke ba gaskiya tace to Allah yasa .
Ban dade ba na bar gidan don raina ya baci da zancen sosai sai hakkuri na shanye har zuwa lokacin da ya dawo garin.
Wanan karon ba laifin irin yadda yake yi tun a waya yasa nasa zai dawo muna da abin arziki irin tambayan yara shi tsaraba da suke so ba kamar wancan karon ba da ya dawo da karya yan fashi.
Na san da zuwa shi don haka nayi kwalliya kamar yadda mata keyi idan mijin su yayi tafiya zai dawo gida.
Irin su kitso kumshi da gyaran daki da gida duk nayi shi kafin ya dawo daga tafiyan.
A cikin dare ya sauka muna don haka ba kowa ne yasa da zuwan shi garin ba irin yadda ya shigo muna ana shigo da katon ghana most go yasa ni jin dadi a raina.
Ga doya da manja da yashigo dashi duk da ba wani mai yawa bane sosai hakan dai yayi min dadi sai da nakai mai ruwa yayi wanka kafin ya bude jakkar bayan ya gama cin abinci.
Kowan mu ya samu tsaraba dagani har yaran dadi ya kashe ni nan nake fadin dama ance mahakurci mawadaci da ace na dauki zuga da yanzu nine a ciki.
Da sauri ya tambaya zuga akan may sai nayi shiru ban iya fada mai komai ba don na fara hankali da halin shi.
Yanzu idan na furta mai sai ya sani a gaba dole na fada mai wanda ya fadi maganan yasa nayi shiru da bakina don ban son ince anty ce ke hasashe ba can yaje ba wai.
Dadi dadi muke sai dadi muke ci kwana biyu har yan haya suna gulma idan ya kwanta bai tashi tun barcin dare sai karfe daya ko biyu na rana.
Babu zancen sallah ga al,amarin shi don ko nayi mai magana ma bai sallah don haka na kawo ido na saka mai.
Idan yayi wanka suna da wani daba a unguwar dake kallon titi ana suke zama har dare na dauka tafiyan da yayi ya sa ya canza rayuwan shi ne akan yawon banza.
Ashe abin ba haka bane kudine baida ya kawo hakan ya dawo ya lafe min a gida niko ina ganin yadawo da kudade masu yawa yadda naga yana muna tunda neman kudi yaje.
Ashe ban sani ba adashe yayi da albashin shi ya dan tara yadawo dasu yana muna karyan yaje nema a nan ba gaskiya bane.
Mutane sun sani nice dai sakaran ban sani ba lokacin nake yarda da karyan shi idan ya sharara min sai in hau in zauna
Haka yasa ni naji sanyi a raina har na basar da zancen don dama na kulla zan barsu har abada idan zancen ya zama gaskiya sai na samu ba haka zancen yake ba.
Ashe sun boye min ne gaskiya ne dasu akai duk wani kulle kullen tafiyan ita maryam din.
Ba dadi da dadi akoma sana,ata ta kayan mata ina kuma dan yin sana,an yara madara aya da sauran su a gida yara na shigowa suna saye.
Sai da ya share wata hudu kafin kacar yayo min sakon dubu biyar mu sai abincin da zamuci.
Jifa dubu biyar mai zai min nida yara da duk sun isa cin abinci yanzu haka na hakkura na karbi kudin muka sai dan abin bukatan mu dashi.
A cikin hakan da muke ne na samu na dan sai tufafin dana dinka nida yarana karo na farko a rayuwana ke nan koshi bashi naci ina bada dan abin daya samu a hankali.
Wanan yasa har ina da shiga jama, a yanzu tunda ina da dan nashiga mutane din da ko bukin dangi ya tashi duk yadda muke da mutum ba zai ganni ba.
A cikin hakan kanwata suka zo ganin gida karo na farko tun tafiyan su kano da mijin ta da ya dauke ta suka tafi.
Sai dai ba wanda yaji dadin gani yadda duk ta ramay ta kalmashe da gani itama dai zaman ana dai yin shine hakana.
Sai dai ita tana da zurfin ciki sosai don bata fadawa kowa halin da take ciki a gidan ta duk da yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba gun mutane.
Bata fada ba amma an fahinci hakan a gareta do a san halin da take ciki ba mai dadi bane don ba jiki mai kyau ba suturan kware a gareta sai dai ta dan darani ga hakan .
Don tana dana canzawa gaskiya sosai sai dai ba wani na birgewa ba ne sosai hakan da za a gani asan miji yana kulla da ita .
Abi mamaki shine duk mazaje namu sai kiba suke mulkawa a jikin su muko muna rama kamar ana diban mu kullun.
Don ko shi mijin nata yadda nawa yayi kiba haka shima ya mulka kiban shi ga mota har ya saye na hawa da fara aikin shi .
Shikan zaka gane shi ka gane da birni ne sosai ga wayewa a fuskan shi sai itace ta zama wata yar kunju da ita.
Sai da muka samu kebewa ne da ita nake tambayan ta halin da suke ciki da mijin nata sai take fada min komai.
Babu dai dadi sai dai ta dan dara nine kadan wurin samun walwala amma shima kusan mayau dari ne mijin nata don bai bari ta rike komai a hannun ta karshe kuma yace ba kudin kamar na Jamil dina.
Kuka mukayi sosai muna ba juna magana kn halim da maza suka jefa mu a ciki sai da mu kayi sai da muka gaji muka ba kan mu hakku.
Nace ta boye wanan zancen kada ta bari kowa yaji halin da take ciki a gidan ta tace ai ba zata iya fadi ba ko don anty .
Tunda tun farko saida ta fada muna haka zasuyi muna bamu ji ba yanzu wa zamu tun kara da zancen.
Duk da mun boye sai da anty ta gane muna a cikin wani hali tundai summaiya din don dai ni idan da sabo sun saba da nawa matsalan ko.
Tare muka shigo gidan da kanwata bayan mun gaisa anty ke fadin anya Summaiya kina cikin dadin rai kuwa ?
Dariya tayi na anty kawai tare da tambayan may ta gani halan tace yanayin ki ya nuna akwai abinda ke damun zuciyar ki gaskiya.
Bata samu wani amsa kwarai ba ta bar zancen aka dauko wani hira sai dai hankalinta bai kwanta da ita ba.
Don yawan kallon kanwar tawa da take yi akai akai yasa duk muka tsargu da zama tare da ita.
Karshe tashi mukayi zuwa dakin yan matan gidan muka zauna ana hira mun kai har yamma a gidan kafin mu koma gidajen mu.
A hanya muke maganan abinda yafaru tsakamin mu da anty har muka kai gidan mu muna magana daya akan matsalolin mu.
Bayan kwana biyu ban san inda taji zance a gari ba wanda ni ma dake garin ban sani ba sai ita da tazo daga baya.
Sai gata min hankali tashe tana tambayana wai Jamil wani gari yace min yake ?
Cikin washe baki nake fadin yana abuja ai kila ma ya dawo kafin ku koma don yace kwanan nan zai leko gida.
Ke kin yarda da cewan shi a Abuja yake zaune ne ta tambayane cikin son jin abinda zance mata din.
Nace can yake don haka yace min da zai tafi sai naga tayi shiru taja bakin ta batai wani dadewa ba tace zata koma gida.
Nace tun yanzu zaki koma barin dan dafa muna wani abu muci mana, kai ta girgiza min tare da fadin ita zata tafi.
Don a gidan mahaifan mijin ta suka sauka don sun sake gidan da suke haya da farko.
Rakiya nayi mata har ta samu abin hawa da zai kaita gida sai dai ina dawowa tunanen maganan ta ya hanani sukuni a raina.
Da kyat na basar da maganan cikin zuciyana don kaina ya kulle da tambayan da tai min din wanda ban san dalilin ta na min wanan tambayan ba haka kan jamil din.
Maganan yaso ya tsaya min a rai ko washe gari, sai dai na basar da zancen don ban san dalilin ta na tambayana ba dai.
Yan tsunmakaran ta da na yaranta ta debo ta bamu mu kara duk da banda su hakana na amsa sai dai na raina kayan .
Har fada mata nayi yanzun ke wanan raggadudan zaki bamu don Allah tace ai itama bata da wadattacen kaya da zata bamu wanda yafi wanan din.
Bayan kwana biyu suka fara shiri komawa kano har lokacin Jamil bai dawo ba sai ana jibi zasu koma ne ya dira a garin.
Abin mamaki ga wanda yaje nema ana sa ran zai dawo da abin arziki baje baje sai dai shi Jamil sabani haka na gani a gare shi.
Don daga shi sai yar jakkar tafiya irin ta maza ya dawo garin babu komai a tare dashi.
Sai na dauka kudi ya riko ya dawo dasu gidan don wahalan daukan kayan da zaiyi daga can .
Sai dai har aka kwana aka wuni banji wani abu daga guri shi ba sai kwasan barcin da yake faman yi tun da yadawo a gida bai fita ba.
Abinci lafiyayye na hada mai har da ciwo bashin kayan miya a makwabatar mu na hada mai abincin.
Ya tashi daga barci ya nemi ruwan wanka nakai mai da soso da sabulu ya fito lokacin na gama abinci sai da ya shirya idan ya gama zai fita.
Yar karamar yar mu ce tazo wurin shi tana fadin baba mai ka sawo muna can da zaka dawo shafa kan yarinyar yayi yana fadin..
Ka dai ba kinga babanki ya iso gida lafiya ba mamana da yanzu yan fashi sun kashe maki baba a ganya ai.
Cikin faduwan gabx nace yan fashi kuma ban ya shiga rabtabo min karyan da ya shirya mi duk nabi na rude.
Hankalina ya tashi yadda yake bamu labarin a cikin tashin hankali nan nayi muna barka da arziki da Allah ya tsirar muna dashi daga hannun yan fashi basu kashe shiba ko su illanta shi.
Yana ganin karyan shi ya kamani yace zai tafi gidan mahaifan shi ya gaida su ya fada masu arzikin daya auna a hanya.
Nace tunda dai rayuwan ka ya tsira ai mun gode ma Allah arziki kuma idan da rabon muyi mayi a gaba ai.
Yaji dadin magana na yace wai da Allah yasa yazo gida da kudin nan da mun warke wallahi mun fita daga talaucin don ya samo kudi sosai acan.
Nace ba rabon mu mare masu bane Allah ya kawo hakan nan nayi ta kwantar mai da hankali da dadden magana har ya samu ya fita daga gidan.
Yana fita na nima na fita wurin yan hayan mu ina fada masu suyi min barka da arziki yan fashi Jamil ya hadu dasu a hanya sun kwace mai komai nasa da zai dawo.
A gabana sun min jaje sosai da Allah ya kare gaba kuna sai dai ina basa baya sukace wawiya ya tsarata ta yarda.
Nan dai suka zauna suna gulmana a gurin suna zagina kan irin watauna gurin miji daya tsara ni sai in yarda da karyan shi.
Yinin rana duk wanda na gani sai ba bashi labarin mijina ya auna arziki da yan fashi a hanyar shi na dawowa gida.
Komai basu barshi dashi rayuwan shi kawai ya tsira dashi a gurin su wasu suna yarda wasu kuma suna mn kallon shasha ban sani ba.
Da yamma yar uwata tazo nake fada mata abinda ya faru da jamil din a hanya.
Sai cewa naji tayi kai amma Jamil din nan bai ma ko iya karya ba wallahi da wani irin kallo mamaki na dago kai ina kallo ta.
Ban bari ta karasa maganan ta ba na hauta da fada harda zagi inda nake shiga ba nan nake fita ba don raina ya baci sosai da kalamin ta.
Tace Allah baki hakkuri anty nima rigima na ya kaini fafin haka ai ta mike tare da fadin zata karasa gidan baba kabiru tayi masu sallama.
Ko kallon arziki bata samu ba a gurin balle a dawo lafiya yadda muka saba yi idan tazo gurina sai mu dade muna zuba hira dasu.
Ba yar uwata ba a lokacin duk wanda yayi gigin tara ta ya fada min wanan magana wanke mai shi zanyi tas don idona da rufe.
Sai kuma yadda na yarda da Jamil ya sa ban iya gano illar shi ta ko ina aka fito da zancen sukan shi a gabana.
Don haka kowa yaja bakin shi yayi shiru tunda ban bari a fadi har wasu na zuwa gida yi min jaja suna muna barka da arziki.
Niko sai rabbata masu labarin yadda abin ya faru nakeyi kamar a gaba hakan ya faru yadda nake bada labarin kamar yadda ya fada min.
Kwana biyu muka fara dan ciye dan kudin dake hannu na ina dan juyawa ya fara karewa sai kama kama ya rage munayi.
Gadai miji yaje nema amma haka ya dawo muna hannu rabbana babu ko ledan burudi ya dawo muna gida.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Ya gama yaudaran shi na yan fashi sun tare shi a hanya sun kwace komai ni kuma na gaji na sake yanzu.
Baifi wata daya ba yace zai koma ya nade ya juya zuwa inda ya fito naci gaba da rayuwana a yadda na saba a baya.
Ba wayan shi ba sako tunda ya tafi don haka fadi tashi ya taso ma rayuwana don nema wa kaina abinda zamu ci.
Tunda ba zancen sutura bane yanzu gare ni sai dai na abinda zamu ci wa cikin mu kullun shine abin yi gare ni.
Ina kallo yan uwa ba zuwa buki ni ba hali inje don ko nace zan tafi babu abinda zan sa a jiki babu wanda zan kai gudu mawa a guri bukin.
Haka yasa na daina duk wani hurda da ya uwa na yanzu sai zagina ban so zumunci ban shiga dangi ga dai magana nan kala kala a kaina ba dadi anayi.
Ni kuma ni nasan abinda nake ciki da miji na ba wai a cikin dadin rai nake ba gashi ya raba ni da kowa daga cikin yan uwana.
Babu mau zuwa gurina da sunan zumunci kamar yadda nima ban zuwa gidajen nasu da sunan yin zumuci.
Wahala yakai min wahala dole na nufi gidan mu dan samun mafita a kaina bayan an gama saurare na.
Anty tace to hadiza ke ce da abin haushi duk abinda akai maku a baya baku gani ba an taimaka maki kin kwashe kin bashi.
An maki fada kin kwashe kin fada mashi abinda kowa ya fada maki gamay yana kallon kowa a hankade don kin gama zubarwa yan uwanki da mutunci a gaban shi.
Ina zaune ina hawaye banda bakin magana don duk abinda take fadi haka akayi babu karya a cikin shi.
Muryan ta ne ya katse ni tana fadin ko yanzu aka taimaka maki kara bashi zakiyi don dawowa zaiyi ya lalabe ki ya kwashe abinda kika tara.
Da sauri nace aa wallahi anty ai yanzu nayi wayau wallahi, tsuki taja bata bari naci gaba ba take fadin.
Dama duk wanda ya danki na miji a matsiyin uba itako zata mutu maraya a duniya.
Don namiji bai da tabbas baka daukan amana ka mikawa namiji hundred pacent kun nuna dan uwan mahaifin ku ya cuce ku yana cin amanan ku kan dan abinda aka bar maku a duniya.
Idon ku ya rufe mazajen ku sun maku huduban shedan kun haye kunyibwa kowa cin mutunci duk mu nan kuna muna kallon mayaudaran ku .
Abinda aka baku muke so muci daga gare ku hakan yasa kuka jaye daga wuri mu dama sun shirya hakan ne do su samu kafan yaudaran ku ba tare da kowa ya saka maku ido ba.
Don ku zauna daga ku sai su suci karen su babu babbaka ko gashi sun kuma ci tunda wawaye kuke.
Nasan ko waye jamil fiye da sanin ku na karanci wanan yaron tun yana karami nasa ko shi waye bake yake so ba hadiza tun farko abinku yake so.
Ya kuma ci yanzu ma abinda baki sani ba shine ni zuciyana bai kwanta da wanan tafiyan daya ce yayi ba na zuwa wai neman kudi.
Kaina na dago da sauri ina kallon ta da mamaki don ina tsoron kalamin anty don kamar mai baki take da wuya ta fadi bai faru ba.
Da sauri na tare ta ina fadin wallahi anty yana abuja abokin shi ma da suke can tare ya fada muna tare suke.
Na tare na hanata magana sai naga tayi murmushi tare da mikewa ta dauko dubu biyar tace shi zata iya bani a yanzu inyi hakkuri.
Idan baba ya dawa zata fada mai halin da ake ciki don a samu abinda aka taimaka min dashi din ina kuka nayi mata godiya na koma gida.
Ga dai anty tana nuna muna tankar ita ta haife mu amma mu har lokacin son mazajen mu ya rufe muna ido.
Bamu yarda su sakamu a hanya da zaran an dauko zancen mazajen namu yanzun ne zamu nuna bacin ran mu gun mutum.
Dama ita kadai ce mai fada muna gaskiya mu kyale ta itama din dai bata da zuciyane irin abinda muke mata tana shanyewa.
Nayi iya bakin kokarina i bar fada mai zancen yan uwana akanshi sai dai dadin hira bai bari na daina ba do ban sani sanda za kwashe in fada mashi komai.
Ba laifi baba ya dawo sai ga sako abinci harda kudi da sauran tarkace an kawo min naji dadin wanan sako don an samu banda komai a gidan dama.
Ranan da naje godiya a gurin baba na samu anty ta dawo daga aiki take ce min hadiza zuciyana yana ban mijin ki yana tare da wanan matar daya musuluntar har yanzu.
Ina dariya nace Anty ita da take nan jahar shi da yake abuja zaune ba tare suke ba gaskiya tace to Allah yasa .
Ban dade ba na bar gidan don raina ya baci da zancen sosai sai hakkuri na shanye har zuwa lokacin da ya dawo garin.
Wanan karon ba laifin irin yadda yake yi tun a waya yasa nasa zai dawo muna da abin arziki irin tambayan yara shi tsaraba da suke so ba kamar wancan karon ba da ya dawo da karya yan fashi.
Na san da zuwa shi don haka nayi kwalliya kamar yadda mata keyi idan mijin su yayi tafiya zai dawo gida.
Irin su kitso kumshi da gyaran daki da gida duk nayi shi kafin ya dawo daga tafiyan.
A cikin dare ya sauka muna don haka ba kowa ne yasa da zuwan shi garin ba irin yadda ya shigo muna ana shigo da katon ghana most go yasa ni jin dadi a raina.
Ga doya da manja da yashigo dashi duk da ba wani mai yawa bane sosai hakan dai yayi min dadi sai da nakai mai ruwa yayi wanka kafin ya bude jakkar bayan ya gama cin abinci.
Kowan mu ya samu tsaraba dagani har yaran dadi ya kashe ni nan nake fadin dama ance mahakurci mawadaci da ace na dauki zuga da yanzu nine a ciki.
Da sauri ya tambaya zuga akan may sai nayi shiru ban iya fada mai komai ba don na fara hankali da halin shi.
Yanzu idan na furta mai sai ya sani a gaba dole na fada mai wanda ya fadi maganan yasa nayi shiru da bakina don ban son ince anty ce ke hasashe ba can yaje ba wai.
Dadi dadi muke sai dadi muke ci kwana biyu har yan haya suna gulma idan ya kwanta bai tashi tun barcin dare sai karfe daya ko biyu na rana.
Babu zancen sallah ga al,amarin shi don ko nayi mai magana ma bai sallah don haka na kawo ido na saka mai.
Idan yayi wanka suna da wani daba a unguwar dake kallon titi ana suke zama har dare na dauka tafiyan da yayi ya sa ya canza rayuwan shi ne akan yawon banza.
Ashe abin ba haka bane kudine baida ya kawo hakan ya dawo ya lafe min a gida niko ina ganin yadawo da kudade masu yawa yadda naga yana muna tunda neman kudi yaje.
Ashe ban sani ba adashe yayi da albashin shi ya dan tara yadawo dasu yana muna karyan yaje nema a nan ba gaskiya bane.
Mutane sun sani nice dai sakaran ban sani ba lokacin nake yarda da karyan shi idan ya sharara min sai in hau in zauna