Kanin Ajali
Chapter 6 of 34
daga rana mai kaman ta yau.
Kada inji kada in kara ganin ka tsaya min da jika na bani ba irin gidan ku a zuri,ana har duniya ta kare mai na gaba yaci balle na baya ya lasa.
Yanzu ba sai gobe ba gidan ku zanje in ma iyayyen ka iyayyaka dakai cikin zuria ta ke kuma wuce mu tafi mufuka banza da wofi kawai.
Ta juya tare da fasa zuwa unguwar da zata tana gaba tana zagina Ainau da muke tare ta biyo ni ta juyo tace kul kika biyo mu sai na saba maki rai.
Duk munafuncin nan kece mai kulla shi keda hafsa na sani ba yau ba kar nake kallon ku dama irin ranan nan nake jira gare ku.
Banda lalacewa mai ya hada ki da wanan zurian marasa mutunci da tarbiya dama barewa bata gudu danta yai rarafe ai.
Har muka kai gida tana saman bakin ta gurin fitina da tonon asiri wanda a lokacin ina jin kamar in magare ta ta bayan da nake binta don haushi.
Lungin mu muna shiga take kwalawa maman mu kira ta fito da saurin don da jin kiran bana alheri bane an tabota ko wani abu ya faru.
Mama na fitowa take fadin yanzu saude da sanin ki yar nan ke wanan iya shegen a gari haka yaron nan dana rabata dashi ashe suna tare har yanzu.
Cikin mamaki mama tace umma wani yaro kuma tace dan gidan babbako mana shegen yaron nan mai son karyan tsiya.
Karamin yaro ya dauki karya irin na ubanshi ya sawa kanshi tun yanzu gata nan can na tsura su wurin gidan wanzan sun labe suna zance da ita.
Zance umma mama ta fadi a cikin mamaki tana mayar da kallon ta gurin da nake tsaye na sada kaina kasa da sauri don kunya da tsoron dake raina a lokacin.
Ta juya tana fadin yanzu gidan su nayi gurin iyayyen shi ai mashi kashedi akan jikata bani ba irin zurian su a cikin kayana su sun sani dama.
Umma kiyi hakkuri zan mata fada basai kinje ba muryan baba yusha,u dake dakin matar shi ne ya fito don jin abinda umma ke fadi.
Tace kaidai barin je don da zafi zafi ake buga karfe kada yazo ya bata muna yarinya bamu sani ba don ba mutanen kwarai bane ka sani.
Ya sake fadin umma yi hakkuri don mutuncin dake tsakanin mu dasu kinga duk gida ne nine ya kamata inje in tsawata mai tunda maganan mazane ai.
Tace to shike nan tunda kace zaka amma duk na sake ganin haka ya zama dole in fada ma ubanki don yasan abinda kike zuwa nan kinayi.
Da sauri nace don Allah umma kiyi hakkuri ba zan sake ba ko yanzu karatu ya tsayar dani ina koya masu shine kika samay mu tare a wurin ta daka min wani uwar harara sai da nasha jinin jikina don kallon da tayi min.
Tsorona Allah tsorona ta fada ma mahaifin mu nasan dukan tsiya zansha kuma ya hanani zuwa gida idan mun tashi zuwa.
Ranan duka nane mahaifiyata bata yi ba don ta nuna min iya bacin ranta itama sosai sai da na bata hakkuri sosai ta kyale ni sai dai ba wani sakin fuska a tsakanin mu.
Haka har dare na nemi wuri na kwanta ba tare da naci abincin dare ba ranan ina tunane kala kala wanda duk haushin kakata umma nake ji a raina tunda itace ta hadani da mahaifiyata take wanan fushin dani haka.
Ranan dai haka yazo min ba dadi tun wanan ranan ban kara fita ko ina ba koda yaushe ina gida da mahaifitya idan na fita sai dai idan naje wani lungu na gidan namu ne.
Jamilu yabi duk hanyan da zaibi yaga mun hadu dashi amma abin ya gagara don kullun ina gida tare da mama da kanne na haka yasa yake turo min sako daga wurin su hafsa.
Ban iya amsa mai don ina son in kiyayye kamar yadda mahaifiyata tayi mun kashedi a kanshi sosai na dauka kuma a raina.
Anyi haka da sati biyu ne muka kai ma baba kabiru ziyara a local govenment din mu inda yake zaune da iyalin shi da matar shi ma,aikaciyar asibiti.
Mun ji dadin zuwa wanan ziyaran don irin yadda baba kabiru yake nuna muna kulawanshi akan mu sosai wanda nina san mahaifin iya mu iyalin shi ne ya sani zai iya nuna muna hakan.
Don ba damuwa yayi shi da nasu iyalin ba sam don ina yawan jin mama na mashi wanan korafin sosai idan dan abu ya hada su a gaban mu.
Hakan bai sa ya canza halin shi sai ma cewan da yake shi ba haka nashi tsarin yake ba don kowa nasa yasani a yanzu idan bai muna tanadi ba wayake so yayi muna.
Ire iten wanan maganan dai yana hadasu lokaci da dama don nasha jin suna wanan maganan wasa wasa sai da muka share kusan wata daya a gurin baba kabiru.
Da zamu koma ma mahaifin mu shi yayowa waya kan ya samu a mota a dauki shata a dawo damu har abuja sai da muka koma gida mukai sallama da mutanen gida inda na dan samu kebewa a sace da jamil mukai sallama.
Inda ya nuna min shifa da gaske yake maganan shi don haka in rike alkawarin mu idan munje can ni dai dariya nayi kawai ba tare dana nuna mashi wani alaman na yarda ba ko ban yarda da maganan shi ba.
Wanan karon mun fi dauko kaya fiye da kullun idan zamu dawo wanda duk yawanci abin daga wurin baba kabiru ne ya fito don yin tsaraba dashi ga kayan daya dinka muna masu kyau dukkan mu har mahaifiyar mu.
Mun sauka abuja lafiya sai washe gari ne mama ke nuna mashi kayan da dawainiyar da baba kabiru din yayi damu a wurin shi.
Sai kallon kayan baba yayi yana fadin aiko kabiru yayi kokari sai dai idan yana hakan ai ba zai tara komai ba da mamaki mama ke kallin shi don jin furicin mahaifin mu din ta kasa hakkuri sai da tace mai.
Wai kai wani irin mutum ne haka dan uwanka yai ma iyalinka abu haka na yabawa babu godiya sai wani magana can da bai dace ba haka , ?
Murmushi kawai yayi tare da fadin ai dama idan zancen kabiru ne baki son a fadi a gaban ki ni gani nayi bai abinda ya dace a kanshi yasa na fadi wanan maganan.
Ban dade ba na koma makaranta sai babane ya kaini da kansa don hutun dana kara yayi yawa bisa ga dokan makarantar mu sai da kyat suka karbe ni ma.
A cikin wanan shekaran ne baba kabiru yakai mahaifiyar su saudiya ta sauke farali don itace ta fara kaiwa kafin shi ya tafi ya sauke nasa.
Idan da son samu ne mahaifi yana da halin da zai kaita saudiya din sai dai baiyi dabaran hakan ba har Allah yaba baba kabiru ikon kaita ta sauke faralin.
Muna ta daukin zamu je mu ganeta don muna dauka idan mutum yaje saudiya yana wani canzawa ne idan ya dawo.
Ashe abin ba haka yake ba a fili ta aiko muna da tsaraban mu ta hannun wani mutumin garin mu daya gane gidan mu yake shigowa Abuja yin sana,an shi.
Munyi murna sosai da ganin tsaraban zuwan da mahaifin mu yayi gaida umma ne yayi shawaran sayen fili don yai gina a garin da baba kabiru yake don nan ne local govenment din mu.
Bai dawo ba sai da yaga komai ya kan kama na ginan ya dawo yabar baba kabiru da sauran aikin ginan gidan yadda yake son a tsara mashi ginan gidan.
Akan ginan ne baba kabiru ya shigo Abuja wurin mahaifina munyi murna da ganin shi sai dai haduwan su baida dadi don bai koma ba sai da suka samu sabani sosai akan ginan da mahaifin mu.
Don yace shi bai gane kan ginan ba don ba haka akai mashi lissafin komai ba kafin ya dawo wanan maganan ne ya tunzura baba kabiru din yai fushi ya fada ma mahaifin bakaken maganganu shima.
Sai dai kafin ya dawo sai da mama tasan yadda tayi ta shirya tsakanin su dashi har ya hakkura ya karbi aikin akan zaici gaba da kula mashi da aikin a can.
Washe gari ya juya ya koma sai da yai muna alheri sosai kafin ya tafi din muna ta murna da hakan shiyasa muke son zuwan shi ga kifi da sauran abin marmari dayazo muna dashi na tsaraba.
Hutun mu ya kare na koma makaranta cike da kewan yan uwana dana bari a gida don sune abokan hiran nawa a gida tunda ba kawaye nakeyi ba ni.
Karatuna ba wani matsala don baba yana alfahari dani sosai don bani cin na kasa da uku duk hutu don hakane ma nake samun kyauta daga gurin mahaifin namu.
Matsalata daya da baba yawan ce mun banda wayo da yakeyi ko yaushe alhalin niko naga ina da wayau ai amma daga baba har mama abinda suke ce min ke nan danayi dan abu kadan yanzu zansha fada sosai a gurin su.
Umma tazo ta kwana biyu a gurin mu lokacin na dawo gida na samay ta haka muka zauna a cikin tsangwama irin nata .
Tsangwaman ta akainane da kanina baffa da yanzu ya tasa bai son zaman gida ko yaushe suna kwasa da baba akan fitan da yakeyi waje.
Haka yasa itama zuwan ta ta karbe korafin da ta fita yanzu zata haushi da masifa ta bal,balleshi da masifa wai idan ya fita wanan garin da babu kai ba a gane gabas din shi don yawa.
Ranan tare da da kanne na muka je bukin wani birthday sai ba a fara program din da wuri ba har muka kai dare muna can wurin wasan.
Mahaifin mu ya dawo gida ya samu bamu nan nan ya hau mahaifiyar mu da fada don birthday din dan kawar tane muka je dan da kyat ya yarda mu tafi don umma ta saka baki yasa ya yarda muje din.
Ya fita ya bimu a can ya samay mu ana sallaman mu don komawa gida sai gashi tun a gaban mai bukin ya fara bal,balan mu da fada tana bashi hakkuri.
A mota ma mun shs fada sosai a furin shi inda duk laifin ani ya dora min don nice babba a cikin mu muna shigowa gidan umma ce ta tare ni da wani fadan kuma again har yafi na baba ma fadan nata.
A cikin fadan take fadin da wanan wautar har kike son wanan yaron mai shegen wayau din da son banza da sauri baba yake tambayan ta wani yaro kuma umma.
Ita hadiza din har take soyayya ban sani ba ni wai ma wani yaro ne take so din tace rabu da yar nema mara wayau kawai bata san sherin mutanen garin nan bane.
Allah ya rufa muna asiri ya rabaku dasu kike son wanan dan banzan yaeon ya hure maki kunne wa yanda ke cikin garin ma mai suka zama har yanzu.
Wani kallo nayi mata ta watso min dakuwa da hannun ta na noke kaina da sauri tace don na zage shi zaki min kallon banza ko ke gaki issasa ko ?
Baba ya sake tambayan wani yaro ne wai take magana a kanshi tace bar yar nema ai na balbale ta babanta yushau kuma yaje yai mai iyaka da ita har gidan su.
Don ubanshi yazo ya ban hakkuri har gida don yasan halina sarai ba kyalesu zanyi ba wurin mahaifiyana ya juya yana mata kallon tuhuma.
Tayi saurin fadin ga umma nan ka tambaye ta idan da masaniyana haka ya faru din ta yi saurin kare kanta daga masifan shi.
Kutawa yayi ya shige daki na koma na rakube a guri daya ina ganin kamar zai dauki matakine a kaina ranan.
Umma duk abinta Allah yayi ta mace mai rikon ibada sosai dama ance mutum dan tara ne bai cika goma ba gata da yawan saka ma diyan ta albarka.
Bata da sakaci da ibadan ta don ko yaushe a cikin lazimi take tana zikiri da sauran abin ibada daya dace mutum yayi a ganuwan shekaran shi ta karshe.
Tun wanan ranan nake dari dari da mahaifina don ban san irin matakin da zai dauka a kaina kan maganan daya ji daga bakin umma din ba.
Sai dai shiru har hutun mu ya kare muka koma makaranta na barsu a gida daya kaini tun a mota yake min fada mai kama da nasiha akan in mayar da hankalina ga karatuna sosai.
Idan na gama zai kaini inyi kararun likita nan gaba kada in sa wasa in bata kurciyana ga banza har sai da nayi hawaye ba tare da ya sani ba.
Lokacin vistinga da yayi ina saka idon zuwan yan gidan mu sai naga sabanin hakan sai babane yazo shi kadai wai sun tafi gida su.
Banji dadin hakan ba amma sai na dake ina addu,an Allah ya dawo dasu lafiya ba karamin sayayya baba yai min ba a lokacin.
Nasan duk cikin tsigar lalashine yasa yai min sayayya haka mai yawa bai jima a gurina ba ya wuce sai dana koma hostel ne nayi kukan tafiyan da sukayi wanan karon ba tare dani ba gida don ban san lokacin da zan tafi ba kuma.
Mun dan jima wanan karon don candy da zamuyi na jinor waec sai da muka gama na dawo gida da kaina don yanzu ina da wayo na zan iya kai kaina gida da school din.
Nayi murna da na samu sun dawo gida suna ta ban labarin gida da wuraren da sukaje ina son in tambaye su labarin Jamil babu daman in tambaya don mama dake falon tare damu.
Da dare na ina shirin kwanciya baffa ya ban takarda wai inji Jamil yace ya kawo min tare da fadin bai bari kowa ya ga takardan ba ya boye min.
Naji dadi sosai ga labarin shi da yake ban yace yanzu yana final year ne a inda yake karatun shi.
Sai dana gama komai mun shige na fito da takardan na karanta gaisuwa ne tare da jaddada min irin kaunar da yake min din naji dadi sosai har cikin raina na samu wuri na boye takarda.
Duk da takardan ya dade a wurin baffa kafin in dawo gida amma bai hana shi kamshin turaren daya zuba a jikin takardan ba daya rubuta.
Na mayar da takardan abin dabe min kewa do duk dare idan zan kwanta zan dauko in karanta in mayar in nuke a inda nake adanawa kada wani ya gani a cikin iyayyena.
Haka rayuwa ya dinga gudana muna jin dadi sosai a gurin mahaifan mu don duk wani abinjin dadi suna muna shi na nuna so da kauna gare mu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:49 PM - 🤔🤔🤔: 🙆🏼♂️ KANIN AJALI 🙆🏼♂️
7️⃣
ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI DA FATAN MUN WAYI GARI LAFIYA, YAN UWANA LITTAFIN KUDI NE MUJI TSORON SHIGA HAKKIN JUNAN MU DON ALLAH.
MAI FAHINTA ZATA GANE MAI NAKE NUFI ALLAH YASA MU DACE YA KARE MU DAGA DUK WANI ABINKI DAGA SHERIN SHEDAN AMIN ALLAH TA BAMU WUNI MAI ALBARKA, , ,
Wanan dawowa gida ne danayi na samu mahaifina yana gina gida a garin abuja bayan wancan daya gina a garin mu wanda na samu yan gidan mu na ta dokin sabon gidan namu da zamu tare a ciki idan an kare ginan shi .
Yau baba bai fita aiki don haka yana gida bai fito ba tun da safe sai mama ne takan fito jefi jefi ta duba aikin da mukeyi ni da kanwana dake secondry na jeka ka dawo don ita bata je bording school ba.
Acewan mahaifin tayi karama sosai da zuwa makarantar kwana a shekaru ta gama yadda duniya ta koma yanzu babu yarda ta kowani fanni.
Sai wuraren shadaya ya fito daga dakin kwanan shi muna falo muna kallo muka shiga gaidashi da kwana yana amsa muna tare da tambayan mu dalilin rashin zuwan mu islamiya yau.
Nice na bashi amsa da fadin baba ka manta ance mu dinka uniform din makaranta idan bamu dinka ba kada muzo.
Ya juya gurin mahaifiyar mu yana fadin may yasa baki tuna min ba na manta da zancen maganan uniform din nan gaba daya hankalina yana wurin aikin nan yanzu.
Mama tace na tuna maka ai sai dai idan ka mantane amma ko shekaran jiya sai da na tuna ma ai kace kaji.
Yace yana zama saman daya daga cikin kujerun falon yau insha Allahu idan na fita zan biya in saya maku ban son zancen rashin zuwa islamiya sam.
Baffa ne yace da baba din baba idan zaka wurin ginan ka yau zakaje dani daga inda nake nace nima baba ina son zuwa inga wurun ban taba zuwa ba.
Zanje daku yace amma ba yau ba don yau ba zan leka wurin akwai inda zan tafi idan na fita abinci yaci ya gama ya fita inda na mike na kwashe kayan na kai kitchen.
Mama ne na gani zaune tayi shiru yasa na mayar da hankalina wuri ta tare da tambayanta abinda ya samay ta tace dani babu komai .
Ashe aure mahaifin mu ya tarkato zai kara don yanzu ba zai iya zama da mahaifiyar mu ita kadai ba yana ganin yana a cikin lokacin shi.
Kudi yana shigo mai ta ko ina akoda yaushe yadda mukaji labari wai wata yar uwarsu dake kaduna ne tayi mashi hanyar kanwar mijin ta zai aura.
Aure rigirigi har yakai wani lokaci a dan zaman gidan da nakeyi baba ya kwashe mu har mama sai kaduna wai su sada zumunci da matar.
Ran mama ya baci sai dai ba yadda ta iya don kalman zumunci daya fada zasuyi da yar uwarshi din yasa ta hade abinda ke ranta ta biye mashi akaje lafiya aka dawo lafiya.
Ba a dauki wani lokaci ba muka ji labarin ashe har baba ya hade lefe kudi yaba wanan yar uwar tashi ta hada mashi lefe a can.
Shine
Kada inji kada in kara ganin ka tsaya min da jika na bani ba irin gidan ku a zuri,ana har duniya ta kare mai na gaba yaci balle na baya ya lasa.
Yanzu ba sai gobe ba gidan ku zanje in ma iyayyen ka iyayyaka dakai cikin zuria ta ke kuma wuce mu tafi mufuka banza da wofi kawai.
Ta juya tare da fasa zuwa unguwar da zata tana gaba tana zagina Ainau da muke tare ta biyo ni ta juyo tace kul kika biyo mu sai na saba maki rai.
Duk munafuncin nan kece mai kulla shi keda hafsa na sani ba yau ba kar nake kallon ku dama irin ranan nan nake jira gare ku.
Banda lalacewa mai ya hada ki da wanan zurian marasa mutunci da tarbiya dama barewa bata gudu danta yai rarafe ai.
Har muka kai gida tana saman bakin ta gurin fitina da tonon asiri wanda a lokacin ina jin kamar in magare ta ta bayan da nake binta don haushi.
Lungin mu muna shiga take kwalawa maman mu kira ta fito da saurin don da jin kiran bana alheri bane an tabota ko wani abu ya faru.
Mama na fitowa take fadin yanzu saude da sanin ki yar nan ke wanan iya shegen a gari haka yaron nan dana rabata dashi ashe suna tare har yanzu.
Cikin mamaki mama tace umma wani yaro kuma tace dan gidan babbako mana shegen yaron nan mai son karyan tsiya.
Karamin yaro ya dauki karya irin na ubanshi ya sawa kanshi tun yanzu gata nan can na tsura su wurin gidan wanzan sun labe suna zance da ita.
Zance umma mama ta fadi a cikin mamaki tana mayar da kallon ta gurin da nake tsaye na sada kaina kasa da sauri don kunya da tsoron dake raina a lokacin.
Ta juya tana fadin yanzu gidan su nayi gurin iyayyen shi ai mashi kashedi akan jikata bani ba irin zurian su a cikin kayana su sun sani dama.
Umma kiyi hakkuri zan mata fada basai kinje ba muryan baba yusha,u dake dakin matar shi ne ya fito don jin abinda umma ke fadi.
Tace kaidai barin je don da zafi zafi ake buga karfe kada yazo ya bata muna yarinya bamu sani ba don ba mutanen kwarai bane ka sani.
Ya sake fadin umma yi hakkuri don mutuncin dake tsakanin mu dasu kinga duk gida ne nine ya kamata inje in tsawata mai tunda maganan mazane ai.
Tace to shike nan tunda kace zaka amma duk na sake ganin haka ya zama dole in fada ma ubanki don yasan abinda kike zuwa nan kinayi.
Da sauri nace don Allah umma kiyi hakkuri ba zan sake ba ko yanzu karatu ya tsayar dani ina koya masu shine kika samay mu tare a wurin ta daka min wani uwar harara sai da nasha jinin jikina don kallon da tayi min.
Tsorona Allah tsorona ta fada ma mahaifin mu nasan dukan tsiya zansha kuma ya hanani zuwa gida idan mun tashi zuwa.
Ranan duka nane mahaifiyata bata yi ba don ta nuna min iya bacin ranta itama sosai sai da na bata hakkuri sosai ta kyale ni sai dai ba wani sakin fuska a tsakanin mu.
Haka har dare na nemi wuri na kwanta ba tare da naci abincin dare ba ranan ina tunane kala kala wanda duk haushin kakata umma nake ji a raina tunda itace ta hadani da mahaifiyata take wanan fushin dani haka.
Ranan dai haka yazo min ba dadi tun wanan ranan ban kara fita ko ina ba koda yaushe ina gida da mahaifitya idan na fita sai dai idan naje wani lungu na gidan namu ne.
Jamilu yabi duk hanyan da zaibi yaga mun hadu dashi amma abin ya gagara don kullun ina gida tare da mama da kanne na haka yasa yake turo min sako daga wurin su hafsa.
Ban iya amsa mai don ina son in kiyayye kamar yadda mahaifiyata tayi mun kashedi a kanshi sosai na dauka kuma a raina.
Anyi haka da sati biyu ne muka kai ma baba kabiru ziyara a local govenment din mu inda yake zaune da iyalin shi da matar shi ma,aikaciyar asibiti.
Mun ji dadin zuwa wanan ziyaran don irin yadda baba kabiru yake nuna muna kulawanshi akan mu sosai wanda nina san mahaifin iya mu iyalin shi ne ya sani zai iya nuna muna hakan.
Don ba damuwa yayi shi da nasu iyalin ba sam don ina yawan jin mama na mashi wanan korafin sosai idan dan abu ya hada su a gaban mu.
Hakan bai sa ya canza halin shi sai ma cewan da yake shi ba haka nashi tsarin yake ba don kowa nasa yasani a yanzu idan bai muna tanadi ba wayake so yayi muna.
Ire iten wanan maganan dai yana hadasu lokaci da dama don nasha jin suna wanan maganan wasa wasa sai da muka share kusan wata daya a gurin baba kabiru.
Da zamu koma ma mahaifin mu shi yayowa waya kan ya samu a mota a dauki shata a dawo damu har abuja sai da muka koma gida mukai sallama da mutanen gida inda na dan samu kebewa a sace da jamil mukai sallama.
Inda ya nuna min shifa da gaske yake maganan shi don haka in rike alkawarin mu idan munje can ni dai dariya nayi kawai ba tare dana nuna mashi wani alaman na yarda ba ko ban yarda da maganan shi ba.
Wanan karon mun fi dauko kaya fiye da kullun idan zamu dawo wanda duk yawanci abin daga wurin baba kabiru ne ya fito don yin tsaraba dashi ga kayan daya dinka muna masu kyau dukkan mu har mahaifiyar mu.
Mun sauka abuja lafiya sai washe gari ne mama ke nuna mashi kayan da dawainiyar da baba kabiru din yayi damu a wurin shi.
Sai kallon kayan baba yayi yana fadin aiko kabiru yayi kokari sai dai idan yana hakan ai ba zai tara komai ba da mamaki mama ke kallin shi don jin furicin mahaifin mu din ta kasa hakkuri sai da tace mai.
Wai kai wani irin mutum ne haka dan uwanka yai ma iyalinka abu haka na yabawa babu godiya sai wani magana can da bai dace ba haka , ?
Murmushi kawai yayi tare da fadin ai dama idan zancen kabiru ne baki son a fadi a gaban ki ni gani nayi bai abinda ya dace a kanshi yasa na fadi wanan maganan.
Ban dade ba na koma makaranta sai babane ya kaini da kansa don hutun dana kara yayi yawa bisa ga dokan makarantar mu sai da kyat suka karbe ni ma.
A cikin wanan shekaran ne baba kabiru yakai mahaifiyar su saudiya ta sauke farali don itace ta fara kaiwa kafin shi ya tafi ya sauke nasa.
Idan da son samu ne mahaifi yana da halin da zai kaita saudiya din sai dai baiyi dabaran hakan ba har Allah yaba baba kabiru ikon kaita ta sauke faralin.
Muna ta daukin zamu je mu ganeta don muna dauka idan mutum yaje saudiya yana wani canzawa ne idan ya dawo.
Ashe abin ba haka yake ba a fili ta aiko muna da tsaraban mu ta hannun wani mutumin garin mu daya gane gidan mu yake shigowa Abuja yin sana,an shi.
Munyi murna sosai da ganin tsaraban zuwan da mahaifin mu yayi gaida umma ne yayi shawaran sayen fili don yai gina a garin da baba kabiru yake don nan ne local govenment din mu.
Bai dawo ba sai da yaga komai ya kan kama na ginan ya dawo yabar baba kabiru da sauran aikin ginan gidan yadda yake son a tsara mashi ginan gidan.
Akan ginan ne baba kabiru ya shigo Abuja wurin mahaifina munyi murna da ganin shi sai dai haduwan su baida dadi don bai koma ba sai da suka samu sabani sosai akan ginan da mahaifin mu.
Don yace shi bai gane kan ginan ba don ba haka akai mashi lissafin komai ba kafin ya dawo wanan maganan ne ya tunzura baba kabiru din yai fushi ya fada ma mahaifin bakaken maganganu shima.
Sai dai kafin ya dawo sai da mama tasan yadda tayi ta shirya tsakanin su dashi har ya hakkura ya karbi aikin akan zaici gaba da kula mashi da aikin a can.
Washe gari ya juya ya koma sai da yai muna alheri sosai kafin ya tafi din muna ta murna da hakan shiyasa muke son zuwan shi ga kifi da sauran abin marmari dayazo muna dashi na tsaraba.
Hutun mu ya kare na koma makaranta cike da kewan yan uwana dana bari a gida don sune abokan hiran nawa a gida tunda ba kawaye nakeyi ba ni.
Karatuna ba wani matsala don baba yana alfahari dani sosai don bani cin na kasa da uku duk hutu don hakane ma nake samun kyauta daga gurin mahaifin namu.
Matsalata daya da baba yawan ce mun banda wayo da yakeyi ko yaushe alhalin niko naga ina da wayau ai amma daga baba har mama abinda suke ce min ke nan danayi dan abu kadan yanzu zansha fada sosai a gurin su.
Umma tazo ta kwana biyu a gurin mu lokacin na dawo gida na samay ta haka muka zauna a cikin tsangwama irin nata .
Tsangwaman ta akainane da kanina baffa da yanzu ya tasa bai son zaman gida ko yaushe suna kwasa da baba akan fitan da yakeyi waje.
Haka yasa itama zuwan ta ta karbe korafin da ta fita yanzu zata haushi da masifa ta bal,balleshi da masifa wai idan ya fita wanan garin da babu kai ba a gane gabas din shi don yawa.
Ranan tare da da kanne na muka je bukin wani birthday sai ba a fara program din da wuri ba har muka kai dare muna can wurin wasan.
Mahaifin mu ya dawo gida ya samu bamu nan nan ya hau mahaifiyar mu da fada don birthday din dan kawar tane muka je dan da kyat ya yarda mu tafi don umma ta saka baki yasa ya yarda muje din.
Ya fita ya bimu a can ya samay mu ana sallaman mu don komawa gida sai gashi tun a gaban mai bukin ya fara bal,balan mu da fada tana bashi hakkuri.
A mota ma mun shs fada sosai a furin shi inda duk laifin ani ya dora min don nice babba a cikin mu muna shigowa gidan umma ce ta tare ni da wani fadan kuma again har yafi na baba ma fadan nata.
A cikin fadan take fadin da wanan wautar har kike son wanan yaron mai shegen wayau din da son banza da sauri baba yake tambayan ta wani yaro kuma umma.
Ita hadiza din har take soyayya ban sani ba ni wai ma wani yaro ne take so din tace rabu da yar nema mara wayau kawai bata san sherin mutanen garin nan bane.
Allah ya rufa muna asiri ya rabaku dasu kike son wanan dan banzan yaeon ya hure maki kunne wa yanda ke cikin garin ma mai suka zama har yanzu.
Wani kallo nayi mata ta watso min dakuwa da hannun ta na noke kaina da sauri tace don na zage shi zaki min kallon banza ko ke gaki issasa ko ?
Baba ya sake tambayan wani yaro ne wai take magana a kanshi tace bar yar nema ai na balbale ta babanta yushau kuma yaje yai mai iyaka da ita har gidan su.
Don ubanshi yazo ya ban hakkuri har gida don yasan halina sarai ba kyalesu zanyi ba wurin mahaifiyana ya juya yana mata kallon tuhuma.
Tayi saurin fadin ga umma nan ka tambaye ta idan da masaniyana haka ya faru din ta yi saurin kare kanta daga masifan shi.
Kutawa yayi ya shige daki na koma na rakube a guri daya ina ganin kamar zai dauki matakine a kaina ranan.
Umma duk abinta Allah yayi ta mace mai rikon ibada sosai dama ance mutum dan tara ne bai cika goma ba gata da yawan saka ma diyan ta albarka.
Bata da sakaci da ibadan ta don ko yaushe a cikin lazimi take tana zikiri da sauran abin ibada daya dace mutum yayi a ganuwan shekaran shi ta karshe.
Tun wanan ranan nake dari dari da mahaifina don ban san irin matakin da zai dauka a kaina kan maganan daya ji daga bakin umma din ba.
Sai dai shiru har hutun mu ya kare muka koma makaranta na barsu a gida daya kaini tun a mota yake min fada mai kama da nasiha akan in mayar da hankalina ga karatuna sosai.
Idan na gama zai kaini inyi kararun likita nan gaba kada in sa wasa in bata kurciyana ga banza har sai da nayi hawaye ba tare da ya sani ba.
Lokacin vistinga da yayi ina saka idon zuwan yan gidan mu sai naga sabanin hakan sai babane yazo shi kadai wai sun tafi gida su.
Banji dadin hakan ba amma sai na dake ina addu,an Allah ya dawo dasu lafiya ba karamin sayayya baba yai min ba a lokacin.
Nasan duk cikin tsigar lalashine yasa yai min sayayya haka mai yawa bai jima a gurina ba ya wuce sai dana koma hostel ne nayi kukan tafiyan da sukayi wanan karon ba tare dani ba gida don ban san lokacin da zan tafi ba kuma.
Mun dan jima wanan karon don candy da zamuyi na jinor waec sai da muka gama na dawo gida da kaina don yanzu ina da wayo na zan iya kai kaina gida da school din.
Nayi murna da na samu sun dawo gida suna ta ban labarin gida da wuraren da sukaje ina son in tambaye su labarin Jamil babu daman in tambaya don mama dake falon tare damu.
Da dare na ina shirin kwanciya baffa ya ban takarda wai inji Jamil yace ya kawo min tare da fadin bai bari kowa ya ga takardan ba ya boye min.
Naji dadi sosai ga labarin shi da yake ban yace yanzu yana final year ne a inda yake karatun shi.
Sai dana gama komai mun shige na fito da takardan na karanta gaisuwa ne tare da jaddada min irin kaunar da yake min din naji dadi sosai har cikin raina na samu wuri na boye takarda.
Duk da takardan ya dade a wurin baffa kafin in dawo gida amma bai hana shi kamshin turaren daya zuba a jikin takardan ba daya rubuta.
Na mayar da takardan abin dabe min kewa do duk dare idan zan kwanta zan dauko in karanta in mayar in nuke a inda nake adanawa kada wani ya gani a cikin iyayyena.
Haka rayuwa ya dinga gudana muna jin dadi sosai a gurin mahaifan mu don duk wani abinjin dadi suna muna shi na nuna so da kauna gare mu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:49 PM - 🤔🤔🤔: 🙆🏼♂️ KANIN AJALI 🙆🏼♂️
7️⃣
ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI DA FATAN MUN WAYI GARI LAFIYA, YAN UWANA LITTAFIN KUDI NE MUJI TSORON SHIGA HAKKIN JUNAN MU DON ALLAH.
MAI FAHINTA ZATA GANE MAI NAKE NUFI ALLAH YASA MU DACE YA KARE MU DAGA DUK WANI ABINKI DAGA SHERIN SHEDAN AMIN ALLAH TA BAMU WUNI MAI ALBARKA, , ,
Wanan dawowa gida ne danayi na samu mahaifina yana gina gida a garin abuja bayan wancan daya gina a garin mu wanda na samu yan gidan mu na ta dokin sabon gidan namu da zamu tare a ciki idan an kare ginan shi .
Yau baba bai fita aiki don haka yana gida bai fito ba tun da safe sai mama ne takan fito jefi jefi ta duba aikin da mukeyi ni da kanwana dake secondry na jeka ka dawo don ita bata je bording school ba.
Acewan mahaifin tayi karama sosai da zuwa makarantar kwana a shekaru ta gama yadda duniya ta koma yanzu babu yarda ta kowani fanni.
Sai wuraren shadaya ya fito daga dakin kwanan shi muna falo muna kallo muka shiga gaidashi da kwana yana amsa muna tare da tambayan mu dalilin rashin zuwan mu islamiya yau.
Nice na bashi amsa da fadin baba ka manta ance mu dinka uniform din makaranta idan bamu dinka ba kada muzo.
Ya juya gurin mahaifiyar mu yana fadin may yasa baki tuna min ba na manta da zancen maganan uniform din nan gaba daya hankalina yana wurin aikin nan yanzu.
Mama tace na tuna maka ai sai dai idan ka mantane amma ko shekaran jiya sai da na tuna ma ai kace kaji.
Yace yana zama saman daya daga cikin kujerun falon yau insha Allahu idan na fita zan biya in saya maku ban son zancen rashin zuwa islamiya sam.
Baffa ne yace da baba din baba idan zaka wurin ginan ka yau zakaje dani daga inda nake nace nima baba ina son zuwa inga wurun ban taba zuwa ba.
Zanje daku yace amma ba yau ba don yau ba zan leka wurin akwai inda zan tafi idan na fita abinci yaci ya gama ya fita inda na mike na kwashe kayan na kai kitchen.
Mama ne na gani zaune tayi shiru yasa na mayar da hankalina wuri ta tare da tambayanta abinda ya samay ta tace dani babu komai .
Ashe aure mahaifin mu ya tarkato zai kara don yanzu ba zai iya zama da mahaifiyar mu ita kadai ba yana ganin yana a cikin lokacin shi.
Kudi yana shigo mai ta ko ina akoda yaushe yadda mukaji labari wai wata yar uwarsu dake kaduna ne tayi mashi hanyar kanwar mijin ta zai aura.
Aure rigirigi har yakai wani lokaci a dan zaman gidan da nakeyi baba ya kwashe mu har mama sai kaduna wai su sada zumunci da matar.
Ran mama ya baci sai dai ba yadda ta iya don kalman zumunci daya fada zasuyi da yar uwarshi din yasa ta hade abinda ke ranta ta biye mashi akaje lafiya aka dawo lafiya.
Ba a dauki wani lokaci ba muka ji labarin ashe har baba ya hade lefe kudi yaba wanan yar uwar tashi ta hada mashi lefe a can.
Shine