Kanin Ajali
Chapter 7 of 34
dalilin saurin ginan da yakeyi don ya samu kafin buki su tare da sabuwar amarya a ciki da yake mama mace ce mai hakkuri duk wanan abin bata yarda ta tada hankalin ta ba akan auren da zai kara din.
Duk dako abin yana taba mata zuciya sosai sai take ganin kamar don yanzu ya samu ne yake son ya kara mata kishiya kamar yadda wasu maza da yawa keyiwa mace.
Don wasu mazan sai su wahala da mace da zaran samu da yalwa yazo masu wanan matar da aka wahala da ita ta zama banza a gare su.
A lokacin zasu fara neman wata wace zasu ji dadin rayuwa a morewa juna ke ko kin zama yar bi sai yadda akayi dake duk da tasan mahaifin mu yana kokari ta fannin kyautata ma iyalin shi din.
Sai da fargaban ta shine bata san sauyin da hakan zai kawo a tsakanin su ba don anyi sau dayawa tana ganin yadda matar gida take komawa sai anyi dace da wace ta san Allah ake zaman lafiya yanzu.
Duk wanan zancen auren da baba keda niyar karawa ba wanda ya sani a cikin yan uwan shi don haka bayan ya hada laifen shi ne.
Yayi shirin zuwa gida don ya sanarwa umma da yan uwanshi zancen auren da yake son ya kara din nan bada jimawa ba.
Umma ta nuna mai rashin jin dadin ta duk ko da yawan fitinan ta da mahaifiyar mu din anan kan umma ta nuna ma mahaifiyar mu gata don tas tayiwa mahaifin mu din.
Sai da ya fadakar da ita abinda yake nufi da auren da yake son ya kara din sannan hankalin umma ya kwanta tayiwa mama nasiha ta kwantar da hankalinta indai tana raye bazata bari a cuta mata ba insha Allahu.
Da haka hankalin mahaifiyar mu ya dan kara kwantawa don umma din data tsaya mata kan zancen tasan abinda ta fada haka yake don diyanta basu fi karfinta har lokacin.
Da haka muka juyo muka dawo sai dai wanan tafiyan banji dasin shi ba don a cikin kwana biyu kawai da mukaje mukayi a gidan.
Gashi ban samu ganin Jamil ba lokacin yana makaranta suna jerabawan karshe na fita secondry school ke nan
Nikan damu da halin da nakan ga mahaifiyar mu a ciki na damuwa wanda nima yakan sani in damu a lokacin har nakan yi tunanen ko laifi mahaifiyar mu tayi mashi da zai kara aure kuma.
Ranan dai sai da yakai na tambaye ta ko laifi mukayi wa baba zai kara aure mama ta dago ta kalle ni raci gaba da ninke kayan wankin da mukayi na kwaso muna a waje.
Tace ba laifi mukai mashi ba ra,ayin shine kawai haka yanzu yaga lokaci yayi da zai kara ne don haka kibar wanan tunanen don ba naki bane a yanzu.
Nan dai mukaci gaba da harkokin mu irin na yara ba tare dana kara bi ta kanta ba kuma, sai dai duk a cikin kwanakin haka nake ganin ta bata walwala idan na tambaye ta sai tace min ba komai.
Na gama girkin rana tana daki na samay ta ina fada mata kai kawai ta gyada min har na juya zan tafi na juyo ina fadin in debo maki ne mama ?
Tace bari idan na fito zanci kidai dibarwa kannen ki suci na amsa mata da to, na fice daga dakin ina kiran kanne na su zo suci abincin.
Bayan na zuba masu ne sai sumaiya ta dawo tana fadin wai na zuba mata miya kadan sai ta kara nace ba zata kara ba.
Muna cikin rikici da ita sai ga mahaifiyar mu fito daga daki tana fadin wai yaya haka ne mai ke faruwa daku ne wai ?
A hasale nake mayar mata da abinda ke faruwa tsakanin mu kallo na tayi tana fadin yar kabiru ki zama mai hakkuri da kannen ki mana.
Ki kara mata mana maye a ciki idan kin kara mata miyan ba akwai sauran miyan a cikin tukunyar ba, kara mata don Allah.
Bayan na kara mata miyan na dawo na zauna ina hasalan dariyan da kaunan nawa take min muryan mamane yasa na dago kai ina kallon ta.
Don cewa tayi keda zaki zama uwar su wata rana tun yanzu, kina nuna masu haka yaushe zasu girmama ki nan gaba kin riga da kin bari sun raina ki ko.
Ki dinga binsu a hankali ki dauki girman ki gare su sai kiga sun koma jin tsoron ki suna daukan maganan ki da muhinmanci sosai ba raini a tsakanin ku.
Nace nagode mama tace ba komai don Allah ki koyi hakkuri da yan uwanki don watan watarana kece dai babban su.
Ta juya gurin da sumaiya ke cin abinci ta fara mata fada mai kamar nasiha ita ma ta nuna mata amfanin girmama na gaba gare ka.
Ba tare da taci abincin ba ta mike don kiran sallah da ake zata je tayi sallah a lokacin na sake fadin mama abincin fa kada yai sanyi kuma ?
Ta juyo a cikin yanayin rashin jin dadi tana fadin barin idar da sallah zan fito inci ta shige daki na bita da kallon tausayawa don na fara fahintar bata da lafiya ne.
Sai dai tana daurewa kada mu fahinci halin da take ciki a lokacin abin yarinta sai ban mai da hankalina ba ga alamarin.
Wasa wasa har yakai mama ga kwanciya asibiti ashe ciki ta samu yake mata wasa bai zauna ba shine take wanan wahalan haka.
Ta sha jiki sosai da kyat ta sha wanan karon jikin bai gama warke mata ba na koma makaranta don jerabawan mu da ya fito sai dai na koma ba a dade ba don na dan jima ban koma ba akao hutu muka dawo gida .
Abinda ya ban mamaki shine tunda na koma ba wanda ya lekoni a gidan mu har dan visting din da mahaifina yakan kawo mun na bazara wanan karon ba wanda ya leko ni .
Sai dai ina shiga gida na samu tashin hankali don na samu mahaifiyata a cikin jin jiki sosai har yafi wanda tayi da farko wahala hankalin mahaifina yana a tashe shine dalilin rashin ganin shi da banyi ba.
Wanan halin da mahaifiyar mu take ciki ya tayar muna da hankali sosai duk da yara kanana ne mu amma mun san mahaifiyar mu tana cikin wani hali mai muni a lokacin.
Nafi kowa shiga tashin hankali a cikin mu don nafi sauran wayau don nice tunda na dawo na koma jinyar mama din don da makwabta da abokan arzikine ke jinyar ta.
Dawowana sai komai ya dawo kaina nice girki nice kula da mahaifiyar mu din ga laluran kanne na wani lokaci nice maiyi masu wani abin.
Da mahaifin mu yaga abin ba sauki sai na Allah dole ya buga waya yana sheda ma baba kabiru halin da mahaifiyata take ciki.
Kwana biyu sai ga baba kabiru da umma da daya daga cikin matan shi sun iso garin hankalin su ya tashi sosai ganin yadda mama ta koma a dan kankanin lokacin.
Sunyi jinyar ta a cikin ikon Allah zuwan su ta dan samu sauki sosai ta dan warke haka yasa na fara shirin komawa makaranta don an koma da dadewa .
Saboda ciwon mama yasa ni ban koma ba do baba yaje ya daukan min permition a makaranta don kada aga na makara da yawa saboda suna daukan mataki sosai.
Bayan tafiyana da sati daya Allah ya karbi ran mama ta tafi da cikin dake jikin ta su umma sun ga tashi hankali don mahaifin mu ya birkice masu shima gaba daya don mutuwan ya taba shi sosai.
Abin mamaki a ranan ne kuma mahaifiyar Jamil ta rasu a can gida sai waya suka samu Allah yayi mata rasuwa itama da yammacin ranan a gida don ita ma tayi dan jiya sai dai ba a sa ran rashinta ba don zazzabi ne tayi na dan kwanaki yazo da ajali.
Ina school ban san wainar da ake toyawa a gida don nasa ran mama taji sauki har su umma kila sun koma gida a lokacin.
Ashe mama bata duniya ta tafi gurin da ba a dawo sai rabon a hadu gobe kiyama idan da rabon haduwa din gare mu Allah yasa mu cika dakyau da imanin ubangijin mu a ran mu Amin.
Nasan wanan shafin zai taba zukatan makaranta da dama don akwai zafi irin wanan mutuwan ka rasa mahaifiya a lokacin da kafi kowa bukatan ta a duniya.
Mama ta tafi tabar baba da nauyin rikon iyalin data bari shine kalman da mahaifin mu ke fada ko wani lokaci yana kuka da hawayen shi na rashinta a tare damu.
Har sunje gida anyi zaman makoki sun kwana biyu a gida suka dawo duk banda labari saboda makaranta da ya boyeni a lokacin.
Mahaifina ya kawo min ziyar sai dai duk da karancin shekaruna naga sauyi a tare dashi don ya ramay yayi baki sosai babu walwala a tare dashi.
Cikin farin ciki da kaguwa na tambaye shi mahaifiyar mu yace taji sauki sosai tana gaishe ni umma fa na tambaya sun koma ne baba ?
Yace umma nanan zaune gida zata kwana biyu a wurin mu kafin ta koma sai dai maman mu ta tafi gida a can zata haihu yace dani.
Ina ta murna maman mu zata haihu ya bani abinda zai bani ya tafi bai dade a gurina ba kamar yana sauri ashe kuka ne yazo mashi a lokacin.
Ina ta fadama abokaina mahaifiyata zata haihu zan gyaiyace buki suna ban address din su tare da layin wayan su idan ta haihu in fada masu.
Har akai hutu baba yazo da kanshi ya dauke ni na isa gida da murna na ko zan samu mama ta haihu a lokacin.
Sai dai ba mama a gidan sai umma da kanne na a gidan suma yanayin su ba dadi a yadda na samay su sai umma ce mai karfin halin taro na da zuwa.
Ni a zatona tunda nace umma mama har yanzu tana gida bata haihu ba naga bata dawo ba sai cewa tayi da sauran lokaci zata dade a can kafin ta dawo.
Na dauka idan ta haihy zamu tafi gida ayi bukin suna damu acan tana ganin ina murna ta shige daki tana kuka tunda nace Allah yasa mama ta haifi mace wanan karon.
Maimakon in ga murna da doki a fuskan kanne na sai bata rai danaga sunayi idan na shiga daki su biyo ni sai umma ta kwala muna kira dole mu fito daga dakin.
Ashe umma bata son su fada min halin da ake cikine sai washe garine bayan mun karya naga mahaifina bai fita aiki ba sai na dauka yana up ne aikin dare zai fita.
Kira ya kwala min ina daki ina gyara na fito da sauri yake ce min tare da nuna min wuri in zauna bayan na samu wuri na zauna ne ya kira sunana.
Na dago kai a hankali na amsa mashi da na,am baba yace magana zamuyi dake ina son ki fahince don ke musulmane ko.
Na daga mashi kai a hankali yace kin san rayuwan mu a gurin Allah yake ko nace eh baba ya ce dakyau yace kin san ko yanzu ko anjima Allah zai iya kiranmu mu koma gare shi ko ?
Sai lokacin na fara jin tashin hankali yana ziyara na don ban son ai min maganan mutuwa ko kadan sai naga umma tana share hawaye da gefen hijjab din ta.
Baba yace kin san kin wuce kin bar mahaifiyar ki bata da lafiya ko da sauri na dago ina fadin eh baba nasani yace to hadiza hakkuri zamuyi don Allah daya bamu ita ya karbi abinshi .
Baba nace da karfi sai kuma na koma fadin inna lillahi wa,inna alaihim rajiun sai naje su a gurin na somay masu ban san inda nake ba don halin da na shiga.
Sai farfadowa nayi na ganni a hannun umma tana shafa min ruwa a fuskana budan baki na nace mama da karfi tayi saurin rufe min baki da hannun ta.
Baba bai iya fadin komai ba don shima kuka yakeyi a lokacin ga kanne na da suke kuka wiwi a kaina suma.
Umma rana naga taushi a gurin ta don ita ta koma tana lalashi kamar yadda mama zatayi min ta koma min makwafin mahaifiya a gareni.
Banci ban sha don damuwan da nake ciki bazan iya fada ma mai karatu ba sai wanda ya taba shiga irin halin da nake ciki a lokacin yasan irin rayuwan dana riska a lokacin.
Baba yana lalashin mu yana nan nan damu baya son yaga ran mu ya baci ko kadan sai dai duk wanan ban gani nidai muradina mahaifiyar mu ta dawo gare mu.
Da kyat suka shawo kaina na fara dan walwala da kannena da nasiha da fada da komai hankalina ya fara kwantawa.
Sai daga bayane nake jin labarin mutuwan mahaifiyar Jamil wurin kanne na na tausaya muna sosai dani dashi don irin halin da muka riski kan mu a ciki na rashin magaifiya da mukayi.
A cikin wanan yanayi na bakin ciki ne hutun mu ya kare haka aka mayar dani school ba tare da na gama warwarewa ba.
Wanan time din na dai koma school din ne ba don zan aiwatar da komai ba na fannin karatuna haka din ne kuwa don tunanen mahaifiyata ya hananu shakat a raina.
Sannu a hankali na fara sakewa ina dan walwala a makaranta duk da ba wani yi nake kamar a baya don ba zan iya shafe rashin mahaifiya a zuciyana ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:49 PM - 🤔🤔🤔: 🙆🏼♂️ KANIN AJALI 🙆🏼♂️
8️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI DA CIKAWA DA IMANI GARE KU MASOYANA ALLAH YA SA MU FI KARFIN ZUKATAN YABA MU IKON BAUTA MASHI, BAUTA TSARKAKAKIYA ALLAHU MA AMIN YA ALLLAH 👏👏👏👏
Wanan time din haka na kare shi babu dadin rayuwa a tare dani don sam hankali baya ga karatu don tunanen mahaifiya na da yai min yawa a raina.
Na dawo gida na samu har lokacin umma tana gidan zaune da kanne na kamar kada in dawo sai umma ta tayar da hankalinta akan tana son zuwa gida ta duba su can.
Wanan abin ya daga hankalin mahaifin mu sosai da ya rasa yadda zaiyi damu gashi hutu akeyi sai ya shirya har damu zata tafi muyi hutu a can.
Da yake dogon zango ne muka fara murna zamu gida muga yan uwan mu sai dai ina gani kamar idan munje zanga mama acan a raina.
Mun zama yan matasa yanzu don haka muka fito fes damu a gurin baba kabiru muka fara yadda zango da muka iso zamu dan kwana biyu a gurin shi kafin mu karasa gida.
Matan shi suka shiga ina aka saka damu suna yi muna kokari mun fi sakewa da matar shi ta biyu a gurin ta muka sauka inda umma ta sauka gurin uwargidan shi.
Bamu da wani damuwa dan zaman sati dayan da mukayi da iyalin shi sai dawainiya yake damu yana nuna diyan dan uwan shi ne mu tankar diyan cikin shi muma muke a gurin shi.
Muka kare sati dayan mu muka wuce kauyen mu, yan uwa na ganin mu sai sharan hawaye sukeyi don tunawa da mahaifiyar mu da sukayi.
Muma dai kukan muka dauka tundai ni dake da wayau a cikin mu nafi kowa shiga tashin hankali sai da kyat da fada da komai umma ta samu na dakatar da kukan da nake yi.
Washe gari da rana muka shirya zuwa gidan kakannin mu na fanin mahaifiyar mu kai mata ziyara don muna jin dadin kasancewa da ita fiye da umma da take mahaifiyar mahaifinmu.
A can ma mun taba kukan saidai da ta rarashe mu mukai hakkuri duk firan mu na ranan kan ciwon mama ne da yadda muke maraicin ta.
Sai dare muka koma gida bayan tayi muna abinci mun ci mun dawo umma ta cika fam kan dadewan namu da mukayi a gidan kakan mu mahaifiyar maman mu din.
Ba wanda ya tanka ta muka shige dakin mahaifiyar mu inda anan muka sauka tunda muka iso don dakin umma ba fili kaya sunyi yawa.
Ina kokarin cire kayan jikina ne hafsa ta shigo tana rada min Jamil yana waje yana son ganina nace hafsa kin san ba abinda zai yuyu bane don yanzu umma ta gama muna fada munyi dare a gidan Auta don haka ake kiran kakan namu dashi.
Kije kice yayi hakkuri tunda muna nan watarana zamu hadu ai wanan ranan bamu hadu ba dashi haka ya juya ya tafi .
Ba tare da ya ganni ba sai dai banji dadin hakan ba don mun dade bamu hadu ba dashi ba zance ga ranan da muka hadu dashi last ba.
Gama shiri nayi na samu wuri na kwanta har na fara barci nake jin umma tana kwala min kira daga kofan dakin ta na amsa a sanyaye tare da mikewa zuwa wurin ta ina fadin umma gani.
Bazaku ci abinci bane har wanan lokacin baku dauka ba nace umma a koshe muke don mun ci abinci a gidan Auta kafin mu dawo gida.
Salati ta saka tare da fadin yaran nan kun iya sai da hali yanzun zuwa kukayi kuka nuna mata muna barin ku da yunwa ko may ?
Da sauri na dago ina girgiza kai tare da fadin ba hakana bane umma ba wanda ya nuna hakan a cikin mu wallahi rufa min baki munafukan banza kawai.
Gobe in Allah ya kaimu zanje gidan inji abinda yasa ta girka maku abinci a gidan ta kallon mamaki nayiwa umma din kamar ta manta da Auta ma kakan mu ne kamar yadda take kakan mu itama.
Nidai naja kafana na barta nan tana surfa muna zagi dani da kanne na akan zuwa gidan kakan mu ta uwa da mukayi muka kai dare.
Washegari tun fitowan mu dakin na gaida umma ban kara fitowa ba ina dakin mama ina aikin tunane rayuwan mun yadda muka koma abin tausayi duk
Duk dako abin yana taba mata zuciya sosai sai take ganin kamar don yanzu ya samu ne yake son ya kara mata kishiya kamar yadda wasu maza da yawa keyiwa mace.
Don wasu mazan sai su wahala da mace da zaran samu da yalwa yazo masu wanan matar da aka wahala da ita ta zama banza a gare su.
A lokacin zasu fara neman wata wace zasu ji dadin rayuwa a morewa juna ke ko kin zama yar bi sai yadda akayi dake duk da tasan mahaifin mu yana kokari ta fannin kyautata ma iyalin shi din.
Sai da fargaban ta shine bata san sauyin da hakan zai kawo a tsakanin su ba don anyi sau dayawa tana ganin yadda matar gida take komawa sai anyi dace da wace ta san Allah ake zaman lafiya yanzu.
Duk wanan zancen auren da baba keda niyar karawa ba wanda ya sani a cikin yan uwan shi don haka bayan ya hada laifen shi ne.
Yayi shirin zuwa gida don ya sanarwa umma da yan uwanshi zancen auren da yake son ya kara din nan bada jimawa ba.
Umma ta nuna mai rashin jin dadin ta duk ko da yawan fitinan ta da mahaifiyar mu din anan kan umma ta nuna ma mahaifiyar mu gata don tas tayiwa mahaifin mu din.
Sai da ya fadakar da ita abinda yake nufi da auren da yake son ya kara din sannan hankalin umma ya kwanta tayiwa mama nasiha ta kwantar da hankalinta indai tana raye bazata bari a cuta mata ba insha Allahu.
Da haka hankalin mahaifiyar mu ya dan kara kwantawa don umma din data tsaya mata kan zancen tasan abinda ta fada haka yake don diyanta basu fi karfinta har lokacin.
Da haka muka juyo muka dawo sai dai wanan tafiyan banji dasin shi ba don a cikin kwana biyu kawai da mukaje mukayi a gidan.
Gashi ban samu ganin Jamil ba lokacin yana makaranta suna jerabawan karshe na fita secondry school ke nan
Nikan damu da halin da nakan ga mahaifiyar mu a ciki na damuwa wanda nima yakan sani in damu a lokacin har nakan yi tunanen ko laifi mahaifiyar mu tayi mashi da zai kara aure kuma.
Ranan dai sai da yakai na tambaye ta ko laifi mukayi wa baba zai kara aure mama ta dago ta kalle ni raci gaba da ninke kayan wankin da mukayi na kwaso muna a waje.
Tace ba laifi mukai mashi ba ra,ayin shine kawai haka yanzu yaga lokaci yayi da zai kara ne don haka kibar wanan tunanen don ba naki bane a yanzu.
Nan dai mukaci gaba da harkokin mu irin na yara ba tare dana kara bi ta kanta ba kuma, sai dai duk a cikin kwanakin haka nake ganin ta bata walwala idan na tambaye ta sai tace min ba komai.
Na gama girkin rana tana daki na samay ta ina fada mata kai kawai ta gyada min har na juya zan tafi na juyo ina fadin in debo maki ne mama ?
Tace bari idan na fito zanci kidai dibarwa kannen ki suci na amsa mata da to, na fice daga dakin ina kiran kanne na su zo suci abincin.
Bayan na zuba masu ne sai sumaiya ta dawo tana fadin wai na zuba mata miya kadan sai ta kara nace ba zata kara ba.
Muna cikin rikici da ita sai ga mahaifiyar mu fito daga daki tana fadin wai yaya haka ne mai ke faruwa daku ne wai ?
A hasale nake mayar mata da abinda ke faruwa tsakanin mu kallo na tayi tana fadin yar kabiru ki zama mai hakkuri da kannen ki mana.
Ki kara mata mana maye a ciki idan kin kara mata miyan ba akwai sauran miyan a cikin tukunyar ba, kara mata don Allah.
Bayan na kara mata miyan na dawo na zauna ina hasalan dariyan da kaunan nawa take min muryan mamane yasa na dago kai ina kallon ta.
Don cewa tayi keda zaki zama uwar su wata rana tun yanzu, kina nuna masu haka yaushe zasu girmama ki nan gaba kin riga da kin bari sun raina ki ko.
Ki dinga binsu a hankali ki dauki girman ki gare su sai kiga sun koma jin tsoron ki suna daukan maganan ki da muhinmanci sosai ba raini a tsakanin ku.
Nace nagode mama tace ba komai don Allah ki koyi hakkuri da yan uwanki don watan watarana kece dai babban su.
Ta juya gurin da sumaiya ke cin abinci ta fara mata fada mai kamar nasiha ita ma ta nuna mata amfanin girmama na gaba gare ka.
Ba tare da taci abincin ba ta mike don kiran sallah da ake zata je tayi sallah a lokacin na sake fadin mama abincin fa kada yai sanyi kuma ?
Ta juyo a cikin yanayin rashin jin dadi tana fadin barin idar da sallah zan fito inci ta shige daki na bita da kallon tausayawa don na fara fahintar bata da lafiya ne.
Sai dai tana daurewa kada mu fahinci halin da take ciki a lokacin abin yarinta sai ban mai da hankalina ba ga alamarin.
Wasa wasa har yakai mama ga kwanciya asibiti ashe ciki ta samu yake mata wasa bai zauna ba shine take wanan wahalan haka.
Ta sha jiki sosai da kyat ta sha wanan karon jikin bai gama warke mata ba na koma makaranta don jerabawan mu da ya fito sai dai na koma ba a dade ba don na dan jima ban koma ba akao hutu muka dawo gida .
Abinda ya ban mamaki shine tunda na koma ba wanda ya lekoni a gidan mu har dan visting din da mahaifina yakan kawo mun na bazara wanan karon ba wanda ya leko ni .
Sai dai ina shiga gida na samu tashin hankali don na samu mahaifiyata a cikin jin jiki sosai har yafi wanda tayi da farko wahala hankalin mahaifina yana a tashe shine dalilin rashin ganin shi da banyi ba.
Wanan halin da mahaifiyar mu take ciki ya tayar muna da hankali sosai duk da yara kanana ne mu amma mun san mahaifiyar mu tana cikin wani hali mai muni a lokacin.
Nafi kowa shiga tashin hankali a cikin mu don nafi sauran wayau don nice tunda na dawo na koma jinyar mama din don da makwabta da abokan arzikine ke jinyar ta.
Dawowana sai komai ya dawo kaina nice girki nice kula da mahaifiyar mu din ga laluran kanne na wani lokaci nice maiyi masu wani abin.
Da mahaifin mu yaga abin ba sauki sai na Allah dole ya buga waya yana sheda ma baba kabiru halin da mahaifiyata take ciki.
Kwana biyu sai ga baba kabiru da umma da daya daga cikin matan shi sun iso garin hankalin su ya tashi sosai ganin yadda mama ta koma a dan kankanin lokacin.
Sunyi jinyar ta a cikin ikon Allah zuwan su ta dan samu sauki sosai ta dan warke haka yasa na fara shirin komawa makaranta don an koma da dadewa .
Saboda ciwon mama yasa ni ban koma ba do baba yaje ya daukan min permition a makaranta don kada aga na makara da yawa saboda suna daukan mataki sosai.
Bayan tafiyana da sati daya Allah ya karbi ran mama ta tafi da cikin dake jikin ta su umma sun ga tashi hankali don mahaifin mu ya birkice masu shima gaba daya don mutuwan ya taba shi sosai.
Abin mamaki a ranan ne kuma mahaifiyar Jamil ta rasu a can gida sai waya suka samu Allah yayi mata rasuwa itama da yammacin ranan a gida don ita ma tayi dan jiya sai dai ba a sa ran rashinta ba don zazzabi ne tayi na dan kwanaki yazo da ajali.
Ina school ban san wainar da ake toyawa a gida don nasa ran mama taji sauki har su umma kila sun koma gida a lokacin.
Ashe mama bata duniya ta tafi gurin da ba a dawo sai rabon a hadu gobe kiyama idan da rabon haduwa din gare mu Allah yasa mu cika dakyau da imanin ubangijin mu a ran mu Amin.
Nasan wanan shafin zai taba zukatan makaranta da dama don akwai zafi irin wanan mutuwan ka rasa mahaifiya a lokacin da kafi kowa bukatan ta a duniya.
Mama ta tafi tabar baba da nauyin rikon iyalin data bari shine kalman da mahaifin mu ke fada ko wani lokaci yana kuka da hawayen shi na rashinta a tare damu.
Har sunje gida anyi zaman makoki sun kwana biyu a gida suka dawo duk banda labari saboda makaranta da ya boyeni a lokacin.
Mahaifina ya kawo min ziyar sai dai duk da karancin shekaruna naga sauyi a tare dashi don ya ramay yayi baki sosai babu walwala a tare dashi.
Cikin farin ciki da kaguwa na tambaye shi mahaifiyar mu yace taji sauki sosai tana gaishe ni umma fa na tambaya sun koma ne baba ?
Yace umma nanan zaune gida zata kwana biyu a wurin mu kafin ta koma sai dai maman mu ta tafi gida a can zata haihu yace dani.
Ina ta murna maman mu zata haihu ya bani abinda zai bani ya tafi bai dade a gurina ba kamar yana sauri ashe kuka ne yazo mashi a lokacin.
Ina ta fadama abokaina mahaifiyata zata haihu zan gyaiyace buki suna ban address din su tare da layin wayan su idan ta haihu in fada masu.
Har akai hutu baba yazo da kanshi ya dauke ni na isa gida da murna na ko zan samu mama ta haihu a lokacin.
Sai dai ba mama a gidan sai umma da kanne na a gidan suma yanayin su ba dadi a yadda na samay su sai umma ce mai karfin halin taro na da zuwa.
Ni a zatona tunda nace umma mama har yanzu tana gida bata haihu ba naga bata dawo ba sai cewa tayi da sauran lokaci zata dade a can kafin ta dawo.
Na dauka idan ta haihy zamu tafi gida ayi bukin suna damu acan tana ganin ina murna ta shige daki tana kuka tunda nace Allah yasa mama ta haifi mace wanan karon.
Maimakon in ga murna da doki a fuskan kanne na sai bata rai danaga sunayi idan na shiga daki su biyo ni sai umma ta kwala muna kira dole mu fito daga dakin.
Ashe umma bata son su fada min halin da ake cikine sai washe garine bayan mun karya naga mahaifina bai fita aiki ba sai na dauka yana up ne aikin dare zai fita.
Kira ya kwala min ina daki ina gyara na fito da sauri yake ce min tare da nuna min wuri in zauna bayan na samu wuri na zauna ne ya kira sunana.
Na dago kai a hankali na amsa mashi da na,am baba yace magana zamuyi dake ina son ki fahince don ke musulmane ko.
Na daga mashi kai a hankali yace kin san rayuwan mu a gurin Allah yake ko nace eh baba ya ce dakyau yace kin san ko yanzu ko anjima Allah zai iya kiranmu mu koma gare shi ko ?
Sai lokacin na fara jin tashin hankali yana ziyara na don ban son ai min maganan mutuwa ko kadan sai naga umma tana share hawaye da gefen hijjab din ta.
Baba yace kin san kin wuce kin bar mahaifiyar ki bata da lafiya ko da sauri na dago ina fadin eh baba nasani yace to hadiza hakkuri zamuyi don Allah daya bamu ita ya karbi abinshi .
Baba nace da karfi sai kuma na koma fadin inna lillahi wa,inna alaihim rajiun sai naje su a gurin na somay masu ban san inda nake ba don halin da na shiga.
Sai farfadowa nayi na ganni a hannun umma tana shafa min ruwa a fuskana budan baki na nace mama da karfi tayi saurin rufe min baki da hannun ta.
Baba bai iya fadin komai ba don shima kuka yakeyi a lokacin ga kanne na da suke kuka wiwi a kaina suma.
Umma rana naga taushi a gurin ta don ita ta koma tana lalashi kamar yadda mama zatayi min ta koma min makwafin mahaifiya a gareni.
Banci ban sha don damuwan da nake ciki bazan iya fada ma mai karatu ba sai wanda ya taba shiga irin halin da nake ciki a lokacin yasan irin rayuwan dana riska a lokacin.
Baba yana lalashin mu yana nan nan damu baya son yaga ran mu ya baci ko kadan sai dai duk wanan ban gani nidai muradina mahaifiyar mu ta dawo gare mu.
Da kyat suka shawo kaina na fara dan walwala da kannena da nasiha da fada da komai hankalina ya fara kwantawa.
Sai daga bayane nake jin labarin mutuwan mahaifiyar Jamil wurin kanne na na tausaya muna sosai dani dashi don irin halin da muka riski kan mu a ciki na rashin magaifiya da mukayi.
A cikin wanan yanayi na bakin ciki ne hutun mu ya kare haka aka mayar dani school ba tare da na gama warwarewa ba.
Wanan time din na dai koma school din ne ba don zan aiwatar da komai ba na fannin karatuna haka din ne kuwa don tunanen mahaifiyata ya hananu shakat a raina.
Sannu a hankali na fara sakewa ina dan walwala a makaranta duk da ba wani yi nake kamar a baya don ba zan iya shafe rashin mahaifiya a zuciyana ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:49 PM - 🤔🤔🤔: 🙆🏼♂️ KANIN AJALI 🙆🏼♂️
8️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI DA CIKAWA DA IMANI GARE KU MASOYANA ALLAH YA SA MU FI KARFIN ZUKATAN YABA MU IKON BAUTA MASHI, BAUTA TSARKAKAKIYA ALLAHU MA AMIN YA ALLLAH 👏👏👏👏
Wanan time din haka na kare shi babu dadin rayuwa a tare dani don sam hankali baya ga karatu don tunanen mahaifiya na da yai min yawa a raina.
Na dawo gida na samu har lokacin umma tana gidan zaune da kanne na kamar kada in dawo sai umma ta tayar da hankalinta akan tana son zuwa gida ta duba su can.
Wanan abin ya daga hankalin mahaifin mu sosai da ya rasa yadda zaiyi damu gashi hutu akeyi sai ya shirya har damu zata tafi muyi hutu a can.
Da yake dogon zango ne muka fara murna zamu gida muga yan uwan mu sai dai ina gani kamar idan munje zanga mama acan a raina.
Mun zama yan matasa yanzu don haka muka fito fes damu a gurin baba kabiru muka fara yadda zango da muka iso zamu dan kwana biyu a gurin shi kafin mu karasa gida.
Matan shi suka shiga ina aka saka damu suna yi muna kokari mun fi sakewa da matar shi ta biyu a gurin ta muka sauka inda umma ta sauka gurin uwargidan shi.
Bamu da wani damuwa dan zaman sati dayan da mukayi da iyalin shi sai dawainiya yake damu yana nuna diyan dan uwan shi ne mu tankar diyan cikin shi muma muke a gurin shi.
Muka kare sati dayan mu muka wuce kauyen mu, yan uwa na ganin mu sai sharan hawaye sukeyi don tunawa da mahaifiyar mu da sukayi.
Muma dai kukan muka dauka tundai ni dake da wayau a cikin mu nafi kowa shiga tashin hankali sai da kyat da fada da komai umma ta samu na dakatar da kukan da nake yi.
Washe gari da rana muka shirya zuwa gidan kakannin mu na fanin mahaifiyar mu kai mata ziyara don muna jin dadin kasancewa da ita fiye da umma da take mahaifiyar mahaifinmu.
A can ma mun taba kukan saidai da ta rarashe mu mukai hakkuri duk firan mu na ranan kan ciwon mama ne da yadda muke maraicin ta.
Sai dare muka koma gida bayan tayi muna abinci mun ci mun dawo umma ta cika fam kan dadewan namu da mukayi a gidan kakan mu mahaifiyar maman mu din.
Ba wanda ya tanka ta muka shige dakin mahaifiyar mu inda anan muka sauka tunda muka iso don dakin umma ba fili kaya sunyi yawa.
Ina kokarin cire kayan jikina ne hafsa ta shigo tana rada min Jamil yana waje yana son ganina nace hafsa kin san ba abinda zai yuyu bane don yanzu umma ta gama muna fada munyi dare a gidan Auta don haka ake kiran kakan namu dashi.
Kije kice yayi hakkuri tunda muna nan watarana zamu hadu ai wanan ranan bamu hadu ba dashi haka ya juya ya tafi .
Ba tare da ya ganni ba sai dai banji dadin hakan ba don mun dade bamu hadu ba dashi ba zance ga ranan da muka hadu dashi last ba.
Gama shiri nayi na samu wuri na kwanta har na fara barci nake jin umma tana kwala min kira daga kofan dakin ta na amsa a sanyaye tare da mikewa zuwa wurin ta ina fadin umma gani.
Bazaku ci abinci bane har wanan lokacin baku dauka ba nace umma a koshe muke don mun ci abinci a gidan Auta kafin mu dawo gida.
Salati ta saka tare da fadin yaran nan kun iya sai da hali yanzun zuwa kukayi kuka nuna mata muna barin ku da yunwa ko may ?
Da sauri na dago ina girgiza kai tare da fadin ba hakana bane umma ba wanda ya nuna hakan a cikin mu wallahi rufa min baki munafukan banza kawai.
Gobe in Allah ya kaimu zanje gidan inji abinda yasa ta girka maku abinci a gidan ta kallon mamaki nayiwa umma din kamar ta manta da Auta ma kakan mu ne kamar yadda take kakan mu itama.
Nidai naja kafana na barta nan tana surfa muna zagi dani da kanne na akan zuwa gidan kakan mu ta uwa da mukayi muka kai dare.
Washegari tun fitowan mu dakin na gaida umma ban kara fitowa ba ina dakin mama ina aikin tunane rayuwan mun yadda muka koma abin tausayi duk