Showing 27001 words to 30000 words out of 299981 words
dakina,,
Ina,zaune tare dasu a,daki ne Gwagona take kara min nasiha irin wanda iyayye kewa diyan su,
Hawaye ne ki tsiyayo min a idanuwa na, gwago tace, kamar yadda na fada maki jiya yau sji din ne,rayuwa takai a,wani guri kuma na,daban,
Yanzu halinki mai kyau ne kadai zai maki jagora a zamantakewar ki da,su,
Kada kiyi sakaci da ibadan ki hakkuri da kuma kunya,
Idan harkin iya tsare wa yan nan tau kingama tsara rayuwar ki ke nan,
Sister din Ummi dake daga gefe tana gyara,min kaya,tace a,kuma hada da tsabta,
Don kin san mazan yanzu mai tsabta suke yayi idan mace tace ita yar son jiki ne zaki ga komai nata sai a,slow,
Gwago na tace min karbi wanan a cikin dabara na karba kamar mai rada tace wanan farin gorar naso nabaki tunjiya, kisha duk dai ko yanzu bai baci ba,
Amma anso kafin miji ya,shigo gurin ka kadan goga kadan a goshin ka zuwa kirjin ki da,marar ki,
Abin kurciya sai cewa nayi ai baishigo dakin ba tun jiya, har suna hads baki a tare da mama hanne,
Gurin cewa to a ina yakwana shi ?
ke nan ke kadai kika kwana, ?
Nace tare da Asmau kaunar shi mama tace mu kwana tare
Sai naga sun dan kalli junar sai kuma suka,ce lalai da akwai matsala amma Allah ya gyara kawai kiyi ta hakkuri kinji,
Tafiyan yan uwa na Umma ta,shiga kasafin kayan cicin da aka kawo mata,
Sai muryan ta kake ji yana tashi sama ita da yarsn ta da masu shigowa don ganin amarya,
Tun tafiyan yan uwa ina zaune a dakina nayi tagumi sai famsn tuna ne inda matsalar da naji suna kira zai shigo min,
Shigowan Hamza sau biyu gida baiga giccin Aisha ba a tsakar gidan, yana son shiga ya duba yana tsoron idon Umman shi,
Ganin hankalin Umma yana gurin kayan dake gaban ta ya sashi dan satan shiga gurin da nake,
Ina zaune a kasa saman tabar roban da aka shinfida a kasan dakin wanda su Gwago suka tashi a saman shi,
Ban san da shigowasar ba sai ganin shi nayi a tsaye yana cewa
Aisha ke kadaine a dakin abinda yasani saurin dan dago kaina ke nan sai kuma nai saurin dukar da kaina,a kasa,
Ya matso inda nake a zaune ya dan tsuguna gap dani kadan yana cewa kin kuwa karya Aisha, ?
A cikin natsuwa da kulawa yake tambayan nawa, ?
Na dan dago kaina a hankali nake cewa eh na karya yaya,
Hmmm naji yana cewa kiyi duk abinda Umma take so don ku daidaita da ita,
Cikin sauri na dago kai na dan kalle shi yayin da idanuwa na,da,basu raina hawaye har sun ciko ko,
Yace idan har kin kiyaye abinda take so to zaki ji dadin zama da ita sosai,
Don tafi da son duk abinda tacewa mutum to mutum ya to kawai shine zaman lafiya
Yace don haka Aisha kamar yadda na,sanki da hali irin na kirki don Allah ki cigaba dz halinki da hakkuri,
Duk abinda ta hane ki ko umurce ki dayi ki yishiba lokaci don bata son mussu da tauri kai nace tau a hankali,
Nasan baki saba da yadda muke karyawa ba,agidan nan da irin cimar da muke yi amma ina rokon ki daki daure ki ci ko yayane don samun salama kawai,
Muna ciki haka mukaji muryan yaro yana cewa wai ana sallama da Hamza a waje,
Umma tace ai yana nan shagon ka barshi a ciki yaron ya kara fadi cewa baya shago yashigo ciki yanzu
Take naga rudewa a idanun shi kaman wanda yayi wani iri laifi maigirma duk dan rude a hankali yadaga labulen dakin yai waje simi simi dashi yana cewa gani nan ai yanzu nashigo gida,
Banga giccin yarinyar nan bane tundazi shine na dubata don naga ko lafiya take,
Wani uwar harara Umma ta sakar mai sai ya sadda kan shi kasa da sauri tace baka dai jin magana ke nan ko ?
Umma yanzun nashiga don na dubata kawai ba wani abin ba,
Har zatai magana ko may ta tuna kuma sai tai shiru kawai ta kuta ya bishi da harara bayan shi inda yafita kofan gida gurin da ake neman shi,
Tun daga wanan lokacin ban kara ganin Yaya Hamza a dakina ba sai dai idan ya shigo naji muryan shi a tsakar gida daga nesa,
Kwana biyu ke nan ina zaune a gidan duk wani aiki nice ke yin shi batare da najira ko kuma ance ba,
Idan na dafa abinci Ummace ke rabawa da kan ta, don sai dai na dauko na kawo mata a gaban ts ta raraba,
Umma bata jin kunya ko nauyi gurin cika wa Asmau da dan ta karami Ibrahim tana cewa wai yarane, bari a zuba masu da yawa alhalin sa,ar mu guda da ita Asmau din,
Ba ruwan Yaya Hamza da al,amari na nima din haka iyakata dashi idan ya shigo nai mashi ina kwana da safe,
****** ********** ******
Kubura yanzu zancen ta da wanan Hamza din dan uguwar sabon gari ya kan kama don kowa yanzu yasan cewa shine zai aure ta,
Take mutane suka,soma magana a kan zance kowa na kawo suka daban daban,
Idon mama Saude ya rufe sai cewa take hassada ga mai rabo ai taki ne,
Don haka kowa ya cirewa yar ta ido ga,al,amarinta da mai baki da goro da mai baki da taba da mai baki da kuka duk suka kwaso zancen su sai suce wai Kubura to ita hakan ya sheta don haka zata daura kafan wando guda dasu ne,
Hakan ne yasa mutane suka ja bakin su sukai shiru suna kallon aikin karya, a cikin uguwa,
Ranan da safe babu yaron da zata aika ya sayo mata idomie a shagon hamza,
Hakan yasa ta yafa dan yalalon gyalen ta akai na just to cover ta fita zuwa sayowa,
Yun bayan cin mutuncin da taiwa Hamza wanan ne karo na farko da zasu gana,
Yana daga cikin shago yana mikawa wani yaro kayan da yasaya yaji wani irin kamshi ya daki hancin shi,
Da sauri ya juyo don yaga ko waye mai wanan kamshin haka a lokacin yayi zufa zufa dashi,
Ba,sallama ba komai tace aban idomie na dari biyu kwai guda shidda,
Cikin dan murmusawa yace a, hajiya Kubura ce barka,da,dare ta,wani ya, mutsa fuska tace ka,ban indomie nace,
Murmushi kawai yai mata inda a zuciyar shi yake jin ke jin wani radadin abinda take nunawa a kan shi,
Abinda tazo saya ya,saka mata a leda ya mika mata ta miko mai naira dubu guda ya cire kudin shi yace jeki kawai kibar shi,
Tace look malam wakake ne ma dauki kudin ka kabani canji na don ban son hada abina da abin matsiyata mutum yace ka kashe mai shago kawai,
Yai tsaye sororo yana kallon ta a cikin mamaki yace Kubura nine kuma matsiyaci yau don nace ki bar kudin ki,
Dakata malam may kake so dani ne bari na fada ma ko wanan ganin da kai min a dalili na,zo inbashi banda lokacin tsayawa harka da yaku bayi irin haka masu zubarwa mutum da daraja,
Ta fige ledan ta tawuce tana zuba mai bakaken magan ganu daga bakin ta,
Binta HAMZA yayi da kallon mamaki yadda akaiyi idanuwanta suka bude haka aa lokaci guda,
Shi bawai da manufar da take nufi yabata wanan alheri ba kawai din mutuncin da ke a,tsakani na,sarrakuta yanzu,
Ta shiga gida tana ta masifa Atika ce ke cewa may yafaru ne haka kuma,?
Nan tana kokarin cire dan gyalen da ta yafa a kanta take fada mata a cikin daga murya,
Wanan matsiyacin mana Hamza ke so ya kawo min rainin wayyo wai na tafi saye indomie yake ce min na bar kudin,
Nace mai anfada mai cewa ni matsiyaciya ce ko may yake nufi yatafi can shi da tallakam matar shi ya kara ya,ciyar da ita,
Don ni ba,sa,ar yin sa bace ko amfada mai ni matsiyaciya ce da zan buge a dan kayan treder shi, da bai wuce nasha ice cream da shi ba,
Ko yana zaton zai iya sayeni da wanan tarkacen banzan nashi ne har yaushe yai kudin da zai bani tsiyatsiya jiya wa yau dashi,
Masu kwadan kayan shi dai ai suna can sai suci mu gani in ci banza ne gida ma ba, a koshi ba balle akaiwa bare,
Ta shige kitchen din su tana kokari dora girki Atika tace bari na dafa maki ai baida wuya,
Daga daki Ummi tana jin su tace a hankali Allah ya kyauta Allah kaga nufin mu,
Sai daga baya mama Saude tafito take cewa ke ko hankalin shi yana a kan ki mana tunda dama cushe akai mai bawai da ra,ayin shi ba, yake auren ,
To wallahi ahir din shi dakr don baiga kin masa kama dayar masiyata ba
****** ********** ******
Rana bata karya sai dai uwar diya tai kunya yau saura Sati guda gasa duk gari inda kabi zancen wanan gwajin amfanin gona ne tako ina,
Samarin dake zaune a baki kofan shagon Hamza suna hira yau firan nasu akan zance wasan da za,ayi a garin ne,
Hamza ba ma,aboci son surutu bane yana dai sauraren su a hankali duk abinda suke fada a gurin,,
Wanan yace shi kaza zai kai wancan yace shi abukaza zasu kai a gidan su,
Acikin zuciyar shi yake cewa ni Hamza to may zan kai ?
Gashi bamu da kiwo balle nace zan kai gashi bamu da,wani abin azo a gani wanda zan iya kaiwa,
Tau Allah dai ya,rufa muna asiri kawai zan dai tafi nai kallon nima kada a bani labari,
Daga inda yake zaune Ibrahim kanin shi yafito yana fada mai mama tace yabada dari a,sayo iccen da za,a girka abinci,
Ya dan lalaba aljihun rigar sa ya ciro wata tsohuwar naira dari duk ta yage ya mika mai,
Sai zuwa wani lokaci ya dan rufe shagon ya,shiga cikin gida don yaci abinci,
Ya,samay ni a bakin kwata,ina wanki daga ind nake a duke saye da hijjab dina kamar kullun zan iya jiyo hirar su da Umma ,
Inda yake fada mata cewa gasar da akai shella a akai lokaci ya gabato don wani satine za a yi,
Umma tace Allah ya,ba mai rabo sa,a masu kudi da ma,aikata suke da abinyi ,
Shikan tallaka ai iyakar shi kallone kawai da ihu ko tafi don farinciki,
A daidai lokacin da nake shanyi kayan Umma ne dana Asma,u na wanke,
Hamza ya kasa daurewa murya kasa kasa yake cewa amma Umma wanki harda na Asmau kuma,
Umma tace tau rasa kunya anya kuwa yaron nan ida ban samaka waigi da bakace kada yarinyar nan ta taimaka min da komai a gidan nan ba,
Yace Umma ba hakana bane yariyar nan amana take a gare mu kin ga,wasu abubuwa bai kamata ace tayi ba,
Tunda sa,a guda suke da Asmau mai zai hana a raba masu aiyukan nan a tsakanin su su dinga yi tare,
Tace amma ita Aisha aure, tazo yi ba zaman gida ba don haka zaka bari tayi bautan aure ko,
Watau mama ba hakana bane mutane masu shigowa sune zasu iya fita,da zancen har ya koma a gidan su,
Umma tace yanzun dai tunda ban iya,ba shike nan zan baka matarka,sai kayi mata training da kan ka,
Umma tace dama ni da akwai dalilin da yasa nake mata hakan don ta saba,
Ranan da dare muna daki nida Asmau muna hira sai ga,Umma tazo ta tsaya daga kofa tana cewa Asmau ki dawo daki kibashi guri ya,shiga dakin matar shi,
Jin abinda Umma tace yasani jin gabana ya fadi dammm ke nan tana nufin adakina yau Hamza zai kwana,
Murya umma ce naji tana cewa Aisha ga amanar dana nan gare ki da fatan zaki kulsmin dashi yadda ya kamata kada ki manta cewa Hamza maraya ne,
Don haka ki bi min shi a sannu banda turasasa shi a ksn abinda baida halin yinshi ace sai yayi su,,
Ina jin tafiyan ta zance mama Rahana ya fado min a rai cewa kada na taba,bari miji ya,shigo dakina ya,samay shi ba gyarare ba don haka na mike a hankali na fara gyara,daga zanin gado zuwa dan shara da,sauran su duk da kuwa ance sharan dare baida kyau a musulunci,
Na,dan fesa kamshi kafin a ce a haka daki ya canza kala kamar bashi ba, ne,
Na saci jiki jin umma tana daki tana magana kamar na,siri da diyan ta na,dan kara yin wanka,
Tsab na gyara jikina abinda baku fahinta ba,shine duk hakan bada wani manufa nakeyin su ba kawai fadar da,akai min ne nake amfani dashi,bawai don zan kwana da miji bane,
Ina gamawa da,sauri na,dauko turare na na mutsuka kamar yadda gwagona tai min bayani, inyi dashi,
Kaina wanda aka yarfawa kitso na dunkule shi a cikin yar hulata dana wanke da rana, don yawan gashi da tsawo gareni
Nasaka yar rigar barcin da mama hanne tace min indinga sawa idan zamu kwanta,,
A,bakin gado na dan kwanta na,dunkule kamar wace ke tsoron wani abu,
Sai dare Hamza ya,shigo gida inda Umma tai mashi bayanin cewa ya tafi dakin matan shi yau Asmau a gunta zata kwana,
Ya shirya kamar yadda ya saba duk shi dan tallakawane ammw akwaishi da tsabtan jikin shi irin wanka wanke baki da aski,
Wankin tufafine dai bai faye samu time din yi ba,saboda ujila,
Banji shigowan shi ba saboda barcin da ya fara dibana a lokacin sai dai ji da nayi a hankali kamar ana kiran sunana,
Na mike zubur zaune daga kwancen da nake cikin dan rudewa ina fadin yaya Hamza ina wuni,
Ya amsa min da cewa tashi zaune muyi magana dake,
Ba musssu na zauna dan nesa dashi kadan kamar maijin tsoron wani abu,
Tambayqna ya farayi da cewa an yi wani abune a tsakaninki da Asmau, yau ?
Cikin sauri na dan girgiza kaina ina cewa a hankali a,a,
Shiru naji yayi sai kuma ya furzar da yar iska daga bakin shi yana cewa,
Aisha nasan cewa ke yarinyar ce mai hakkuri don haka kiyi hakkuri da irin abinda Umma tai muna,
Din ban taba ganin wanda akaiwa irin hukuncin da Umma tai min ba,
Duk da ita a ganin ta sone da kauna na ya kaita ga yi min hakan,
Ta haramta min zuwa kusa dake don wani akida nata na daban can wanda baida dalili,
Don haka nake mai kara,baki hakkuri don dan naman da yake kamar sunna na baki tun rada ya kamata na,sayo na baki Umma ta hana ta karbe,
Yanzu tashi mu fita na rakaki kiyo alwala don dare yayi ko,
Kamar yadda yace alwalan ne nayi tare da kara dan kimsawa,
Sallah ya jagorance mu mukayi nidashi inda daga baya gama adduoin mu yake umurtana da na dawo kusa dashi na zauna,
Adan takure na dan matso gab dashi na zauna a cikin jin kunya da fargaban zama a kusa da namiji haka gap da gap,
Hannuwana na Hamza ya fara rikewa yana dan wasa dasu a hankali yayin da yake fada min irin dokokin dayake son shimfida min a gidan a matsayin shi na maigidana,
Matsar da yakewa hannuwa sun fara canza,sallo don haka na dan fara kokarin bijire mashi a hakan,
Yadan jawoni zuwa gare shi inda na, zunbule ina cewa don Allah Yaya Hamza ka daina kaga hakan baida kyau haramu ne,,
Murmushi naji yayi inda yake rada,min a kunnuwana cewa ke matatace Aisha zan iya maki duk abinda naga dama, a tsakanina dake,
Cikin kokatin fahintar dani da yake ne yaga cewa ba zan tsaya yabini yadda yake so ba,
Sai kawai ya yi amfani da karfin shi kuciya ya debe shi ya amfka min yadda yaso,
Ganin irin surar dake gareni wanda a kullun yake boye a cikin hijjabin da nake dunkule kaina a cikin shi,
Kuka sosai na,dinga yi wanda ban damu da wai wani yajini ba a lokacin,
Muryan Ummace mukaji tana cewa ke kada ki hada muna kan makwabta a gida fa a cikin daren nan,
May kike nufi dama zaman ciye muna abincine kawai zakiyi ba biyan bukata,
Hamza wanda yake kokarin lalashina naga ya dafa kan shi irin idan mutum dinnan ya shiga ukku,
Takarashe fadan ta ta tafi tabar mu na inda yai ta bani hakkuri yana min nuni cewa hakan ai shine auren dama,
Har saida ya,fahinci barci ya kwashe ni yadan gyara rufe min jikina ya kwanta rigingine ya soma tunane a ranshi,
Ashe kallon da yake min da farko abin ba haka yake ba ke nan,
Duk wani abinda da namiji zai bukata agurin diya mace Allah ya,hore min shi a jikina,
Duk wani tunanen da yake kuma cewa nai karama ga abinda yske bukata sai yake gani ai na kai har na,wuce,
Washe gari Ummu ce ta bubuga muna kofa tana cewa yafito ga