Showing 24001 words to 27000 words out of 299981 words
ni da ummi dama sauran wanda ke dakin
Dayar matar tace ai shi mutum duk bai wuce kaddaran ubangijin shi don haka sai muyi mata fatan alheri ga sabuwan rayuwan da zata,shiga a yanzu,
Ki tashi kije ki roki sauran matan gidan gafaran zama muyi haraman kaiki tun dare baiyi ba,,
Dakin mama Saude muka fara shiga kamar bazata amsa muna ba sai can tace ku iso mana,
Muka shiga da sallama a,bakunan mu muna gaisheta tare da mata yaya,gida,
Daya,daga cikin gwagwanina ta ce mata tau uwargida ga yar ki nan mun kawo maki ita kunyi sallama yau zata tafi dakin ta insha Allahu,
Mama Saude tace "Ya ta kikace fa aida yata ce da bazata wanan gidan fakiran ba,
To kiyi hakkuri don Allah duk abinda tai maki ki yafe mata akwai kurciya a tare da ita,
Mama Saude tace ai mu gamu gani shine namu kawai,
To Allah ya kyauta inji gwago na dake kokarin tashi tsaye,,
Sai da na dan yi jin nace mama don Allah ki yafe mi duk laifin da naii maki,
Allah dai yakai lafiya aini baki min komai ba yar Agwai,, kanki kikaiwa,
Mubar dakinta muka nufi dakin Atika amm sai muka samay ta a waje take cewa mu tsaya daga wajen ma yayi ai,
Tace yar Agwai sai ayi hakkuri daduk irin yanayin da za,a gani a gidan Hamza don ko sai rarita yasan da zatayi yoyo,
An nufi dani gurin malam Mudi wanda shigowan shi gidan ke nan a lokacin,
Mun shiga turakar shi yana zaune yana kokarin cin abinci Atika tana tsaye daga kan shi tana kokarin mika mai ruwa,
Baba yai muna sannu da zuwa tare da,bamu guri don mu zauna daga dan nesa kadan,
Baba yace Aisha yau Allah yayi aure zai raba mu dake, zai rabaki da uwar ki da yan uwan ki ko ?
Baba yace aure kenan sha kan yaro duk da,ba nesa zakiyi damu ba amma shi al,amarin aure yana da matukar yawa da a,rayuwa,
Baba yace Aisha yau Allah yayi rayuwar ki zata koma a cikin wasu jama,an dabaki saba zama dasu ba, a baya,
Aisha kamar yadda na fada maki a baya aure sunna ne maikarfi,
Wanda yatara wajibai masu yawa a gare shi sosai ,
Nan Baba ya kara nanata min yadda mukayi ranan da na umurci yai fitar kunya dani akan Kubura,
Baba yace Aisha dake da mijin ki ku kasance masu matsakaiciyar rayuwa kamar yadda nasan halin kowanin ku,
Halaiyar ku danasan ku dashi indan har kunci gaba dashi zaku kasance acikin jin dadin rayuwan zaman takewa,
Yace yau Aisha abinda kikai min yasa na tuna da wani Hadisi na na mazon Allah inda yake cewa,
1 Mutane zasu so abin halitta su manta da,wanda yayi su,
2 mutane zasu rayuwan su har su manta da makomar su,
3zasu mallakar manya manyan gidaje su mance da kabarin su,
4mutane zasu zabi aikata zunubi su manta da yawan tuba (gafara)
5 mutane zaso dukiya su manta da hissabi,,
Baba yace yau Aisha kin gwada min cewa kedin diiyace a duniya kin nuna min cewa mahaifan ki sunyi sa,an haihuwan ki a,duniya,
Yadda kika iya fitar da mutumin da kikewa ksllon uba a gare ki alhalin wanan mutumin yai sakaci da damar da Allah ya,bashi na kasancewa uba agare ki tun farko,
Sai kawai baba yasa kuka yana cewa Aisha yadda kika fitarni kunyan duniya Ubangiji Allah ya albarkaci auren ki yabaki zuri,aa masu albarka duniiya da lahira,
Itama Aishan kukane ya kubce mata inda ,suka bar gidan a cikin hawaye,
Yan uwanane kawai suka rakani gidan miji sai yan tsiraru daga matan uguwa masu son ganin kwam,
Dakafa muka taka don ba nisa sosai da gidan Mama Rahana da mu,
Ina rike da hannub kaunar mahaifna da mahaifiyana, muna kai kofan shiga gidan su Hanza sukace min dakata daga nan sai mukaja mukai tsaye,
Yayin da gwago na,tadan rankafo daidai kunnena ta rada min da cewa nac bissimillahi A,uzu bikkalamatillahi tamat min sherin mahallak, 3,
Takara cewa kiyi bissimillah kija suratul Iklas kafa uku hagu da daman ki sai ki shiga da kafan dama Allah ya sa albarka a rayuwar auren ki,
Kamar yadda gwagona ta umurce ni da nayi hakan nayi don ita din malamar addinice a kauyen mu,
Inda ina tafiya bakina yana lailaha,illah hasbunallahi wani,imal wakil,,
Kofar shiga dakin da aka gyara a matsayin nawa muka dan ja runga muka tsaya gwagona ta kara furta nin kiyi bissimillah ki kara jan Iklas kafa uku ki shiga da kafar dama,
Hakan na kara karantawa tace shiga da kafar dama da,addu,an da duk kika iya domin Allah maji rokon bayin sa ne,
Duk abinda yazo min daga fannin addu,a haka nauta jero su har asma,u husna saida na jero su,
Nai mamaki kwarai yadda naga an gyara min daki a tallakance dai dan ban zaci haka ba sam,
Aka zaunar dani a saman gado shima,da,addua abakina yayin da nadanyi kamar minti goma a zaune sai suke cewa na mike zuwa dakin uwar miji,
Mun samu Umma Rabi da dan taron jama,an ta a dakinta tana zaune a saman katifan dake a cikin dakin ta,
Duk da bata da miji amma kafanta yasha kumshi yana sheki, ta dan yi kwalliya itama,
Yaranta duk suna a cikin dakin azaune suma tare da mahaifiyar su,
Daya daga cikin iyayyena take cewa tau yadai ga yar ki mun kawo maki Allah ya baku hakkurin zama a tsakanin ku,
Dayar gwagona tace sai anyi hakkuri da yaran yanzu don Allah aita tsawata mata akan abinda tayi ba,daidai ba,
Umma Rabi tace ai da na kowa balle Aisha ai dama diyatace, Allah ya bamu hakkurin zama da su,
Mijinta yaron kirkine baida matsalar rayuwa duk inda na ajeshi anan yake tsawa inaa fataan zaki bamu hadin kai muyi zaman lafiiya a gidan nan ,
Kina da kannen miji don haka sai kinyi hakkurin zama dasu don a zaunna lafiya,
Bamu jima adakin ba suka ce na taso mukoma dakina,
Muna shiga naji kauna mahaifiyana tace tau Aisha tun yanzu na,fara hango hakkuri a gare ki,
Din wanan sarrakuwar taki da alamar irin matan nan ne masu goyon bayan diyan su akan komai,
Don kiji tun a gaban mu tana yabon danta da kanta bata bari hallinsa ya nuna ba,
Don haka nasan kina da kirki kiyi hakkuri kinji gaduk irin abinda kika gani daga gare ta ki kawar da idon ki akan abinda take da diyan ta a gidan nan don ku zauna lafiya kinji,
Hawaye ne masu zafi suka zubo min ina kokarin dan share su da habar hijjab din dake a fuska na,
Na ji mama Rahana tana cewa nasan tunda baki da nisa da Fatima yan gidan su ma zasu dinga shigowa don yin lecture ki don haka ki zama mai boye sirin ki ga kowa, kadaa naji wani zance a waje akan zaman ki gidan nan,
Tsabta, yinayi bari na bari shine zaman aure harki ji daga baya ana fadar ai wance ta samu miji ko ta samu gida,
Daga karshe wanan gwagon tawa tace masu salli, allanabiyull karem suka karba da sallallahu alaihim wasallam,
Nataita jero adduoin nemamin zaman lafiya da kariya daga duk wani sheri na kalubalin rayuwa,
Sukai min sallama sukace su zasu tafi sai da,safe kafin su tafi zasu shigo mu kara sallama,
Har,sun tafii mamana,Rahana tadan dawo daga baya tana ce min ki yi duk abubuwan dana koya maki a gida
Na,amsa a hankali dacewa tau mama sai na saka kuka haka inaji ina gani suka tafi suka barni a,sabuwar rayuwa a wani gidan,
****** ********** ******
Kubura yanzi ita da,sabon saurayin da tayi mai suna Alhaji Nura dinke suke cif da shi don akan shi duk ta kore mane manta na farko shike masu ruwan kudi suna bushashan su ita da mahaifiyar ta,
Yan uguwa suna kallon ikon Allah don har kofan gida zai zo ya,dauketa su fita yakuma dawo da ita,
Duk a gaban idon Hamza wanda shagon shi yake kallon kofan gidan nasu,
Tsakani Hamza da ita yanzu ko gaisuwa babu sai ma yar harara da take yawan watso mai idan sun hada ido,
Malam Mudi tun yana ji har yagani da idon shi ranan yai masu masifa sosai ita da uwar ta
Yace yaba sati biyu in har aurenta yake son yi to ta fada mai ya fito ya wanke ta yahuta don shi bazai aje yarinya haka a gida ba,suna gwada sa,a da uwar ta,
Hakan yasa ta fadawa Alhaji Nura sakon Baba din da farko yaso ya,doje mata amma kuma ko may ya tuna sai yake ce mata, zai zo yaga mahaifin nata akan zancen,
Zuwan Alhaji Nura gurin Baba ya,saka mahaifiyana a,wani sabon kuncin bakin ciki a gidan mu don irin gori da habaicin da suke mata,
Amma mama Rahana taba Ummi shawaran cewa tayi tankar bata fahince su ba,
Ta zage ta shige cikin su tanuna farin cikin takoda kuwa,suna basar wanne taa nuna tafisu farin ciki da hakan
Hakan ko akayi don duk da nuna matan da suke basu ra,ayinta a cikin su tana nuna zakewar ta a zancen Kubura din don dai a zauna lafiya kawai, ,
Ance idan kana son shanmatar uwa to karike dan ta ganin haka a sannu sannu har mama saude tadan fara rage tsangwamar da takewa Ummi da yarran ta suka dan koma daidai sai dai sama sama don na ciki na ciki,
Sai dai su su a ganin cewa ai dai nagaba yai gaba don sun tserewa Ummi din da komai tun da yar ta a gidan wahala take rayuwan ta ai,
Su ko zasu tafi inda kowa nasu zai huta har su shafa ma,wani arziki,
Arziki kan ana gwadawa kubura din shi don yanzu har takai bata iya cin abincin gidan mahaifin nata sai dai a sayo mata ko ta girka abinda ran ta yake son ci taci,
****** ********** ******
Bayan fitar iyayyena daga dakin ina zaune ni kadai a dakin ba wanda ya leko dakin,
Sai dai ina jin hayaniyar mutanen gidan daga dakin su acan naji Zarah tana masu sai da safe inda tadan leko dakin nawa tashigo da yar fara,ar ts tana cewa,
Tau amaryan mu ni zan tafi sai da safe nasan cewa ba lalai bane Alhaji ya barii na fito gobe amma insha Allahu idan an kwana biyu zan shigo na duba ku,,
Ga amanan yayana nan nabar maki kin san yayana salihin mutun ne idan munga ya canza ke ce,
Damm naji don zance mama Hanne ne ya fado min a rai na cewa sai nayi taka tsantsan don su da alamar nasu suka sani,
A hankali na dan bude baki nace Anty Zarah sai anjima nagode a gaida gida ,
Tace ke waya fada maki cewa ni antyn ki ce yanzu ai kin zama matar yayana don haka ni kaunarki ce,
Nace cikin dan jin kunya ainima yayanane ko kin mata cewa ni din kaunar ku ce,
Tadan dafani tace hakane Aisha Allah yabaku hakkurin zama kinji sai kiyi hakkuri da kowa a gidan nan,
Tai min sallah ma ta,tafi na kara komawa ni kadai a cikin dakin, bakowa a tare dani,
Sai zuwa dare ina zaune a gefen dan gadon katakona mai cin mutum biyu wanda yasha shimfida da zannuwan gado,
Naji Asma,u ta,shigo dakin tana rataye da hijjab din ta da wani zani take cewa Umma tace wai nazo na taya ki kwana,
Cikin dan murmushi da,sakin fuska na ke ce mata, to ga wuri ki kwanta don haka na mike tare da jawo kofan dakin nadan rage kayan jikina na,dauki butana wanda yake cike da ruwa nafita zuwa babdakin gidan don nasan dashi,
Nai sarki saidai naga an dan gyara bandaki ba kamar yadda na,san shi ba,
Ina tsugune na,fara alwala naga shigowan Hamza gidan dauke da,wani bakin leda bag karama a hannun shi,
Ganin nice naje alwala a tsanake yadan sashi shan jinin jikin shi kamar zai min magana ssai mukaji muryan Umma Rabi tana cewa kai Hamza zo nan,
Ya juya zuwa gurinta nidaii nai alwalana nashige daki na rufo abina inda na tada sallah,
Nakai wani lokaci a gurin da nai sallah a zaune ina jero addu,io neman tsari daga Allah ga,wanan sabuwar rayuwan da na,fara fuskan ta a,sabon mazauni na,
Na koma can dan nesa kadan da Asmau na kwata inda ina jinta sai nasarin ta take hankali kwance abinta,
Washegari asabar na tashi don kiraye kirayen sallah da,akeyi na, dauro alawala ,
Ana,sallamay sallah nafito na,gyara tsakar gidan nan gaba,dayan shi don dama nasan kan gidan,
Har ban daki na tsabtace muna koda gari zai haska ko ina na gidan na gyara tsab har zuwa lokacin banji Umma Rabi tafito daga dakin ta ba,
Na nufi gurin da,suke ahe icce na debo na hassa wuta a murfu tare da dora ruwan zafi duk da ban san may za a girka a matsayin abin karya kumallo ba,,
Na hada kwanuka zan wanke sai dai babu clean din da zan wake a fili,
A lokacin naji motsin Umma ta bude kofan ta abinda yadan sani sauri dan dago kaina ke nan na nufi kofan nata don in gaishe ta,
Yayin da take bin gidan da kallon mamakin yadda na gyara shi haka tun da farar safiya,
Sai idon ta ya sauka a murhu naji tana cewa ke Aisha wanan irin icce da kika zumbuda a murhu ai yau kawai zaki kashe muna dan jarin namu damuke maneji dashi,
Hamza ne yashigo gida a lokacin inaga daga masallaci yake don naga casbaha a hannun shi,
Inda murhun yake yake kallon sai naji yace Umma sai naga kamar kwara biyar ne tasa kawai,
Kaina na,sada a kasa inda naji Umma tace tau mara kunya zaka hana na nuna mata yadda ake tattali ke nan ko ?
Yace a,a wane ni kawai dai na zaci ai baki gani bane dakyau,,
Yace mata ina kwana Umma an tashi lafiya ya gajiyan baki,
Nima,sai a lokacin na tuna cewa bamu gaisa,ba,shi nazo yi ta tareni da wani magana,
Nazube kasa a gaban ta gwiwa bibiyu ina cewa acikin yar murya ta,siririya Umma ina kwana,
Tace Lafiya kalau ya kuka kwana nace cikin dan jin kunya Alhamdullahi,
Ashe har kun tashi kinyi wanan aikin haka ni barci ya kara kwasana ai ban sani ba,
Gefen da yake a tsaye nadan kalla still ina,a,tsugunne nace ina kwana yaya Hamza,
Ya amsa min a,wani yanayi da cewa lafiya ya gajiyan jama,a,
Idon Umma,Rabi kyam a kan mu kamar wacce ke,son gano wani abu a kan mu,
Nace Umma nasa ruwa ban san may za,ayi da safen nan ba,
Akwai saura kamun koko yana nan shi zamu dama, aiko,
Hamza yace ko na,turo da madara ne ku dan hada tea ko ?
A,a kada ka fara min shi ranan da babu tea din fa kariga da ka,saba mata dashi,
Na mike a,sanyaye nabar gurin ban tsaya jin may zasu ce ba,
Ina bada baya naji tana cewa kawai zaka kwashi dan jarinka a ciye bayan ko yar irin gara,din nan da ake kawo wa Ango banga an kawo muna,ba mu,
Hamza wanda ya,danjin gina jikin shi a bayan bangon dakin Umma din ya dan ce a hankali haba Umma wani gara kuma bayan kin san yadda akai wanan auren ba,shiri,
Ta,watsa mai harara tana cewa da yake basu san kunya,ba za,sy kawo muna ya hakana ,
Na dawo nake cewa tabani Omo na wanke kwanoni sai ce min tayi ai kayan basu yi wani dauda,ba na wanke hakanan kawai,
Fita naga yayi sai gashi da clean yake cewa idan na gama,saina ahe sauran a gurina lokacin Umma ta daki ita da kanin Hamza din wanda ya,fito yana shirin zuwa makaran tan boko,
Kamar yadda Imma tace kunnun na dama inda batazo ta,gani ba amma take ce min wai nadama kunu da,ruwa ruwa kuma,bai dahu ba
Yarinyar ce taahigo da robar kosai tana cewa ance a cire na dari wai a raba,abawa kowa nashi,
Na karbi ledan na kaiwa Umma kosai din na juya don na bar dakin naji tace min karbi naki kafin ki fita,
kosai ne kwara biyu tamiko min na karba gwiwa bibibyu nake mata godiya,
.
***** *********** ******
Yan uwa na,suka shigo da kayan garar da Ummi tafa min gori a kanshi ,
Shikafa garin masara, gero sai kayan miya su mangyda ,albasa, maggi gishiri, kifi da,sauran su,,
Sai kuma bahohi dakeda guguru cincin da sauran su,,
Haba nan Umma ta,shiga waahe baki tana cewa au a she kuna tafe dama ,
Nan tafara dan cewa Allah sarki wanan irin dawai niya haka yan uwa,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUN KU
👑 SARAUTAR MATA 👑
1⃣0⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
A,kofan dakin Umma Rabi aka jibge kagan gara inda suke ce mata ta karba d hakkuri don bukin yazo ba,shiri,
Su ka kaimin wanda zanyi amfani dashi a