Showing 225001 words to 228000 words out of 299981 words

Chapter 76 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17617

gaskiya ta kwasa ta fada mata tanaji ance har da,saki ya,shiga tace dawa Allah ya hada ta,bada Umma ba nan suka yo gidan syka,dinga tonon asiri tdakanin su da Umma duniya tana jin su,,,


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON HAKA CIN AMANA NE,,,,

Alhamdullahi don yanzu abubuwa duk sun daidaita a,gidan mu an yiwa gidan kwasarima sosai ya koma kamar na,zamani,
Daga sana,an kai kaya company sai kums ya juya ga harkan noma ya raba hannun don dama shi ma,nomine baida da halin yi ne,
A yanzu noma Hamza keyi sosai ba kama hannun yaro dayake Allah ya albarka ci al,amarin shin tun noman farko sai alamarin ya daga sosai,
Yana noma masara dawa da,wake sai fadamun noman shimkafa da,su rake daya bude,
Nan ya fara,samun yaran aiki masu bin shi su ma su samu daga cikin su har Yahaya dan gidan mama Atika,,
Jidda,tana da, shekara daya na samu wani ciki a lokacin wanan cikin yazo min da,banbanci akan na Jidda din,,
Don ni kaina ban san dashi ba sai dai ina yawan alolayi kwanakin nan ga yawan tashin zuciyan dake damu na,sosai duk abinda naci sai na amaye shi tas mama ce tace dana ci na,saka dan namijin goro guntu a bakina ko ainihin goro ko dan dabino,
Ranan Hamza ya,dawo daga tafiya ya sayo kan sa yace a gyara da taimakon mama na,samu na kamala aikin naman, nai muna tuwon farar shimkafa, yai fari tas ga kamshin kayan yaji dake tashi daga cikin miyan,
Kowa yasan idan Hamza yai tafiya yadawo ba karamin dadi muke ci ba a gidan hakan yasa kowa dawowa gida a ranan,
Suna zaune kowa na kwasan gara agaban shi har shi uban aikin Hamza ya na gida tare da yan uwan shi ana hira, gwanin ban sha,awa, don Asmau zatayi aure badadewa ba, insha Allahu,
Ina tsaye sai aiyuka na nake ta faman yi ni ban zauna cin abincin ba tare dasu,
Gurin mama nazo ina cewa mama akwai sauran goron ne a wurin ki don ina son zan danci abinci,
Mama tace Eh akwai shi Aisha ai bazan yarda yanzu in rabu dashi ba duk da ni ina kokarin na daina cin shi sai gashi kuma watan cin shi ya kama a gidan mu,
Da sauri Umma ta dago kaina tana min kallon tantancewa don ta tabbatar da maganan mama,
Sukuma sauran basu fahinci may mama take nufi da zancen ta sai cewa Jibrin yayi a,a mama watan cin goro yakama mu kuma aini ban son goro sam wallahi,
Mamatace ai inkai baka son ci dan ka ko yar ka na so don in ba goron taci ba yanzu data sha ko ruwa ne zaka ga, sai ta amaye shi tas,
Sai lokacin suka fahinci zancen mama sai sukayo min ido caaa akaina lokacin ina kokari bude ledan goron da mama ta miko min,.
Ke madam kice min kin samu kujine har yafara gubda ruwa ban sani ba ni, inji Asmau take zolaya na,
Yar sheri kawai nace kema kwana,nawane kin gunda naki mu ga nashi kalan,
Hamza don jin dadi sai murmushi kawai yake daga inda yake zaune wani irin dadi ya kumay shi don shi sam bai kawo zazzabin daren da nakeyi wai ciki bane don cewa nake maleria ne ke damuna,
Kai wasu matan dai akwai su da bakar jaraban tsiya ace ko yaye yaro baka yi sai ka dauki wani ciki ka halaka dan ka da hannun ka,,
Take ran Hamza ya ba ci ya daure fuskan shi da da yake murmushi dashi don sam baiji dadin zancen Umma ba,
To ai haraban yana gurin dana shi da ya kasa barin ta ta yaye ya lalabata ya dura mata wani cikin batai yaye ba,
Ita Aisha maye nata aciki banda wahalan da take fama da ita ace ko ruwa kasha yana kasa,
Inajin haka na juya zuwa kofana don nasan yanzu zancen su zai iya rikidewa don fadin gaskiya,
Haba yaya wanan magana aibai dace aji shi a bakinki ba gaskiya abin farin ciki yasamu kuma zaki cewa yarinyar mutane jaraba ne da ita,
Da can baya da bata samu cikin da wuru ba ai gaba kuka sata da zuguba a gidan nan bata da shakat taki hauhuwa,
Yanzun kuma Allah ya kawo cikin da,wuri zakice wai tafaye jaraba dan adam dai ba,a iyashi wallahi mutum yakama girman shi mana wanan halin gaskiya ki sake fmdin yarinyar nan wallahi bata da makusa a gidan nan duk abinda akai mata komai dacin shi shaye shi takeyi ba acewa ga abokin fadan ta,
Hamza da ranshi ya gama baci mikewa yayi bayan ya daurayen hannun shi daruwan wanke hannun dana tanadar masu, yabar gurin ranshi a bace fita yayi yabar gidan zuciyar shi tana mashi kuna,
Umma tace taufa ai tunda na taba yar gwal din ku yanzu zanji zance iri iri
Ba haka bane wallahi shi babba ya rike girman shi ga yaro don kada yaro ya raina shi,
Ida waccan mara kunyar ce Sadiya aida yanzu ta baki amsa daidai dake balle kema bazaki ko fara ba,
Da alama duk yaran basuji dadin maganan Umma ba sai shiru sukayi kowa yagama cin abincin shi ya bar gurin
Sai mamace ta zo kofana bayan sungama take cewa kin ko iya cin abincin Aisha ?
Nace wallahi mama na kasa cin sai dai dan kunu zan dama nasha tace a,a ina Hamza din yake yadan samo maki ko hura ne tunda dazun ma kunun naga kinsha da rana,
Muryan shine daga bayan ta yake cewa mama tunda bataci kuma bata da lafiya su Sa,ade su dinga girkawa mana har ta ji sauki gada wahalan yai mata yawa kai aiki a,wahalce kuma ka kare baka lasaba,,
Nace ai zan iya cine dai kawai ban iyayi kidai huta kwana biyu inji hamza har kiji sauki,
Bari nafita na samo maki furan mai dan sanyi ko zaki iya sha,

****** ********* ******
Cikin dare ne yake ce min Aisha ban son ki saka zancen Umma a ranki don bake take muzantawa ba ni dan ta takewa,
Don yau ko dabba na dauko na aje agida a matsayi mata dole ne taso ki don ni balle keda tasan kowa naki take maki haka,
Yace yanzu ina dadin wanan maganan da tayi maki a baina kowa ina ko a banza muka samay shi bata halal ba ita mai rikewa ne,
Murmushi nayi nace ai fada take min cewa kada mu cutawa Jidda bawai wani abu bane can,
Hmmm kawai yace tare da fadin Allah dai ya kyauta wanan abubuwan nadaga cikin abinda yasa nake sin yi gina,mubar gidan nan duk dako muna da filin da,zan iya yin gina acikin gidan mu amma gara na matsa nisa da ita don samun saukin ki,
Ban ce uffan ba don nasan bacin raine amma,ai uwa uwa ce duk abinda zatayi dole muyi hakkuri da halin ta don a rabu lafiya da ita,
Kamar yadda ya,fada dole na bar wasu aiyukan gida don na,samu dan hutun kwana biyu,
Ina zaune a dakina wanda yanzu an mayar min dashi ciki da falo, ina shayar da Jidda mama hafsi ta,shigo dakin ta samay ni,
Ina ganin ta zauna nasan cewa tana da magana da ni ke nan don haka na mayar da hankali a gare ta,
Mama take cewa Aisha ya kamata a cire wanan yarinyar a,nono hakana don kada ta sha ciki da yawa, dama na bari ne har dan kara sha,sai mu cireta,yanzun kuma nagama duk shirin da nakeyi akan cire ta din,
Don kinga tun kwanaki yaya tana ta zancen a cire ta duk wullakancin da take maki akan kina,shayar da yarinya da ciki ina gani,
Na dago idanuwa na,da,sukai ja sun dan tara ruwa don gap nake da hawaye su zubo min nace,
Ni Umma may ye laifina akancikin nan tunda bani naba kaina ba da Umma take cewa wai samun guri yasani daukan ciki ban yaye yarinya ba don na cika gida da "ya"ya na,
Yanzu in kuma na yaye yatinyar nan a lokacin wani abu ya,samayta cewa kuma zatayi da gangan nayi shi don na kashe mata jika,
Mama tace bar zancen ai na fada mata cewa nice na ce abarta kada a yayye ta a lokacin,
Yanzu dai bar zancen a hannu na zan samu ita yaya nai mata bayanin cewa za a cireta a nono kinga tafiyan da Hamza din zaiyi kafin yadawo tabar nonon ,
Nace a hankali tau mama, duk yadda kikace haka din za,ayi sai a fada min idan an tashi nacire ta,
Mama tafita da ga dakin ta koma dakin ta nadan kallin yarinyar dake manne a,jikina tana zukar nonon ta nace a fili Jidda Allah yaraya ki yasa wanan nonon da kikasha mai amfanine a gare ki,
Da daren ranan mama,tanajin shigowan shi tafito ta samay shi a dakin Umma suna gaisawa, dashi sai take cewa cikin kallon Umma
Za,a cire Hauwa,u a nono ranan laraba in Allah ya kaimu,
Umma tace ai na zaci baza,a yayye taba sai ranan da ta haihu tunda itace sarkin son diya tana son ta tai mata ciki da nonon ta a baki,
Haba yaya yarinyar nan fa ta riga da tasha ciki ko to don may za,ai mata saurin yayye a lokacin batayi kwari ba ta tsuge da gudawa da lalururin iri irí
Hamza dake zaune yana jin su yace tau mama yanzu da may damay za,a sayo mata na yayyen,
Har da,wasu abubuwan can za,a sai wa yarinyar da bata ma damu da abinci ba,.
Sai mama take cewa haka za,a barta ko yan kwalaben magani itin na bature ba,a sai mata da,yan sauran abubuwan amfanin ta kuma tunda ba nono take sha ba,
Allah yasa a yayye lafiya inji Umma cikin dan kawar da kanta gefe daya,
Hamza bai bi ta Umma yayi sayyaya masu yawa ya shigo dasu a ledoji yana fadin ga kayan yayyen gwagona nan Allah yasa a yayye lafiya Allah ya,sa mata albarka duk wanda ke gurin ya amsa da amin,
Ranan Laraban kamar yadda mama tace tunda safe tai mata wanka ta goya ta suka fita gidan nabi su da kallo ina tausayawa yarinyar don sai naga maganan Umma gaskiyane mu mu kaiwa yarinyar laifi,
Shiko gogan ko a jikin shi sai harkokin shi yakeyi kafin ya wuce tafiyan shi sai dai, ranan da ya wuce da dare da,safe aka cire ta a nono,,
Nonuwa na sun hake sun ciko sun fara saka min zazzabi, don haka na shige dakina na kwanta don ji nake ba dadi a jikina,
Mama bata gidan sun fita tun safe da Jidda sai na koma ni kadai don dan sabon da nayi da zama da Jidda,
Ba,wanda ya damu da ya,duba lafiya sai Jibrin da yashi ina jin muryan shi nasan abinci yake ci har yagama bai ganni ba sai naji da zai fita yana cewa wai yau ina RAN GIDA take ne,
Tana ciki kasan tayi yaye yau ba fita tana kewar yar ta,
Cikin sauri naji yana ina Jidda din take ya nufo kofan dakina yana tambaya,
Yana daga labule yake fadin ran gida ashe yau an wa Jidda laifi ne, na dago ina murmushi tare da cewa, kadawo na,katako ?
Irin yadda yadda yaga yanayi yasa cewa bakijin dadi ne halan naganki wata iri haka dan murmushi na kakaro a fuskana cikin sanyin murya nace,
Wallahi sanyi nake dan ji da zazzabi shine nadan kwanta ko zai bari,
Subbahanallahi, kin sha magani kuwa?
Nace zan dai sha yace Allah ya sauwaka ashe yau diya ta tasha yaye tana ina ne wai,
Nace sun fita da mama tun safe basu dawo ba har yanzu nasan tana can tana mata rigima yau kam,
Yace jiki kina tausayin ta kika cire min ita a nono ai gaskiya yau kin wa baby na laifi sosai,
Yafita bai wani dade ba,sai gashi da leda ya sayo min maganunuwa masu yawa a ciki,
Na karba nai ta zabbaga mashi godiya yace haba ran gida dole ne fa muyi maki don ke tamuce,
Sai dai ni fa har yanzu ina binki bashin ki ce min yaya nace kaji ka dai nikuma wallahi ban yarda tunda ajin mu guda fa da kai, yace kin ji ki,,,
Maganin da ya,sayo min na,sha sai naji dan saukin jikina zazzabin ya sake ni,
Sai da yamma su mama su ka dawo yarinyar tana a bayan ta, tai barci kuma harda wanka akai mata,
A,dakin mama ta kwana sai dai ranan ba suyi barci ba don har da Umma saida tafito daga dakin ta don kukan da takeyi,
Duk kwanakin basu zama gida sai dai mama ta goya ta su fita zuwa sha,a nin su da haka har yarinyar ta dan saba tafita zancen nono,
Kwanan shidda acan yadawo nima a lokacin nagama dan zazzabin yayena na dan koma normal ko,

****** ********* ******
Cikin yan watan nin da Hamza ya,fara sana,a tuni sunan Hamza ya fara shahara a gari da dan kewaye,
Don Hamza ya iya sana,a sosai da kuma tausayi a kan harkokin shi musan man da yan kauyen da yake sayen kayan a gurin su,
Daga wanan sana,an sai kuma yafara sana an sayar da kayan maganin amfanin gona na zamani dake sa shuka saurin fitowa da wurin,
Ai fa anan kasuwa ta barko mashi balle yan kauyen da yake sana,a dasu don ko basu da kudi zai iya basu idan sun samu su biya shi,
Tuni sunan shi ya fara fice a gurin kanan manoma masu karamin karfi dake bukatan taimako
Hakan bai hana Hamz zama tare da abokan shi na kuryciya da,suke zaman majalissan su dasu
In har tana a gari a tare dasu yake zama suna harkokin su kamar baya ayi raha,ayi zolaya,da,wasa da,dariya, a tare,

Yanzu in akwai wani matsala a,tare dani bai wuce irin yadda yan mata da zawarori suke kawo wa Hamza hari ba har gida sukan biyu shi wani lokaci suce ace wani mutum yana mashi sallama sai yafita zaiga mace ce ke mashi sallama ashe,
Tun ban sani ba har na fara daukan hannun don zanji yana waya a cikin wani yanayi hakan kan sa na fahinci da mace ne yake waya,
Tun ina boye bacin raina har takai na fara nuna mashi a fili cewa nasan may yakeyi,
Don daya fara irin wayan nan nakan ja tsaki na tashi nafita daga dakin,
Gashi cikin jiki ya tsufa sosai don har yafito daga jikina,
Sai dai duk kulawan da ya dace miji yaiwa matar shi ina samu dags gareshi wanan matsalar dai ta neman mata ne ke hada mu fada dashi
Ko shi fadan ba,wai can ba nakance ni dai wallahi ina tsoron a kwaso min cuta ina zaman zamana a halakani,
Sai dai yayi dariya yace kada Allah ya nufeni da aikata zina, a rayuwana don da ina yi da tun akan Lima zan fara zina,
Namiji ai ba abin yarda bane tun da,ba,tare da kai nake yawo ba dariya yakan min yace ki yarda da,mijinki Aisha mijinki ba mazinaci bane,
A cikin ikon Allah har cikina yakai watan haihuwan shi a lokacin komai da ya dace asays na haihuwa Hamza ya,saya min, ya aje yakan ce shi ba mazaunin gida bane don haka ya saya kada na haihu baya gida,
Jidda tun da mama,ta,yaye ta a gurin ta take har yanzu bata dawo da ita gurina ba acewan mama,wai naji da cikin dake a jikina,
Kamar wancan haihuwan wanan ma haka yazo min da sauki duk da na kira wata mai aiki asibiti ta dubani a tare da ita na haihu na,sambado katuwar jaririya,ta,
Sai faman ihu take ta,tsalawa don sanar da,mutane cewa ta iso wanan duniyar tamu ta maliki,yumindeen,
Mutanen gida suna jin kukan baby suka san cewa an haihu sai murna sukeyi da farin ciki,
Sai da nurse din taga,min komai sannan ta bude kofan a lokacin duk kowa na tsaye cirko cirko sun matsu su ji cewa, may na haifa,
Nurse tafito tana cire safan hannun ta tanacewa mama barka mama kin samu kishiya katuwa sai fari kamar yar turawa,
Daga inda Umma take tace kuma dai Allah ya,sauwaka,
Nan su mama,suka hau murna aka shiga aikin jego tare da aikawa mutane cewa na sauka lafiya,
Kafin wani lokaci gida ya fara cika da yan uwa da abokan arziki suna zuwa taya mu murnan samun karuwa da akayi,
Umma kan kamar ba haihuwa akai mata ba don fuskan ta a daure yake,
Ibrahim ya buga ma Hamza waya yake fada mai an haihu ya kara samun baby girl cikin murnan shi da nuna jin dadin shi ga dan uwan shi,
Shima hamza yai matukar murna da farinciki nan ya bugowa Umma waya yana fada mata barka,
Yace Umma ashe an haihu bayana yanzu ibrahim ya bugo yake fada min Aisha ta sauka lafiya,
Umma tace eh takara haiho abinda ta saba haihuwa maka mace kuma,
Umma aikin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login