Sarautar Mata

Chapter 76 of 94

ke kadai ba ,
To ai Umma ke kadai kika zauna a gidan Baba don may wai kike son aiwa Aisha kishiyace tana zaman lafiya da mijin ta,
Anshi naka taiwa Jibrin dakuwa da hannun ta tace ai da na zauna ni daya ban samu wuri irin haka ba,
Kai Umma fadi gaskiya don dai kowa yasan da,baban mu na,da rai yana da,wadatan shi sai dai aga abu a gurin ki,
To kai sai ka zauna da mace daya in ka tashi auren amma,shikan sai ya kara wata gidan nan takara daga kai tana bin gidan da kallo,
Kaina ya daure da,wanan irin kiyayyan na Umma a kaina ni dai abin wani lokaci yana damuna sosai don ban san,
Da dare muna daki dashi ina zaune a bakin mirror ina gyara jikina yake cewa cikin dan jan tsuki,.
Wai ni ban san wanan abin na Umma da bazata iya zama da yar uwan ta da yara a gida
Nidai ban tanka mashi ba sai yake kwata kwata na fahinci Umma bata son zaman lafiya na wallahi,
Don bata fahinci irin yadda rayuwan yanzu yake ba da take wani matsawa wai nai aure aure ba sai mutum ya,shirya yin shi ba zai yi, ya,sake jan wani tsakin yana juyawa,
Yace ita gashi taci nata rayuwan ba wanda ya damay su da zaman ta ita daya ,
Jin nayi shiru yasa shi juyowa inda nake yana cewa yaya ina magana kin kyaleni kin san ban son ina magana ai min shiru ko
Niyi dan murmushi tare da,mikewa daga inda nake ina cewa kayi hakkuri ka bar wanan magana yaya,
Don kasan ni ban da baki magana akan kan wanan zancen tun da ni ake son kawai kishiya,
Saboda zamana a gidan nan ni kadai ya kai wa Umma ko ina shine yasa take son ka kawo wata wace zamu zauna tare muci arziki da ita don ni yai min yawa ni kadai,
Yai murmushi don ya fahinci raina yana a bace akan maganan Umma don hakan ne nai shiru,
Yace naji amma ai ko na kara auren in da Umma ce bazaman lafiya zasuyi da wata din ba,
Kamar nace hakane mana don Umma kishi take da matan ka,,
Na hawo gadon tare da dan fara matsa mashi kafan shi a hankali har na,soma yi mashi abubuwan da na san sun fiye mishi wanan magana muhinmanci a yanzu,
Tun sanda Mama ta dawo gidan namu da sunan yi muna kwana biyu ban samu wani cikakken natsuwa ba kuma,
Zaman lafiya da kwanciyar hankali sun min karanci saboda a kullun Umma zancen ta shine ita dai ni gida yai muna girma ni da "ya"yana burin ta bai wuce taga raina ya baci ko an dagula min lissafi nayi bakin rai,
Gashi duk yadda zata sa yaya ya bata rai a kaina sai Umma ta kirkiro shi,
Gashi idan hiranta ya tashi takan ta yaba irin rayuwan da tayi da nata mijin da irin yadda tasha gaban yan uwan shi da kowa da yake tare dashi,
Shekarun ta yana karuwa mugun halinta yana kara baiyyana a fili,
Shi kuma Hamza sai Umma bata kusa yakan yi korafi akan halinta na takura min yakan yi kokarin kwantar min da hankali akan halin ta, yace wai girma ne ke sata yin hakan,
Gashi wanan zuwan taki tafiya gida tace ita bama san ranan tafiyan ta ba,
In anyi maganan tabar yara agida sai tace aida uwar su ta barsu har Sa,adatu sai da ta dawo gidan da zama,
Wata rana nai muna sakwara da miyar taushe da naman rago sai da taci takoshi tana santi,
Zuwa yamma sai cikin ta ya rude tafara haraswa da kewayawa da dan ta yazo yana tambayan abinda taci sai cewa tayi nice naja matashi nasan bata son doya amma nai muna sakwara taci shi ya jawo mata rudewan ciki,
Wata kila tafadi hakane don yai cikina da masifa sai yake cewa to ke umma da baki so ai sai kiwa Humaira magana ta sake maki wani abinci,
Tace wane ni nasata canza min abinci tace nazo gidan ta na saka tagaba da fitina kadai san halin yaran yanzu,
Juyawa yayi inda nake zaune yana ce min may yasa baki girka mata nata daban ba Humaira yanzu gashi kin ja mata matsala irin haka,
Raina yai matukar baci ya gama fadan shi ya fita ita kuma ta,shige daki da yar ta ina jin su suna dariya,
Daki na,shiga ranan sai da nai kuka mai isata ina hadiyan zuciya ni kadai sai yarana dake kallon yadda nake kuka,
Ibrahim ne yashigo gidan yaga bani falo yai ta kwada min kira sai da na fito sama sama nake gaida shi kallo daya yai min yafahinci nayi kuka
Yace yau kuwa lafiya Aisha cikin muryan da ya dashe min don kuka na furta mai babu komai yaya Ibrahim,
Yace Umma ko nasan dama hakkuri kikeyi da ita har ma,shi mijjn naki nasan baida yadda zaiyi ne amma insha Allahu yau takai karshe don gida zasu kwana wallahi,
Fita yayi don ban ma tsan manin ya shiga gurin ta ba inda take,
Dan wani lokaci sai gashi ya dawo ya shiga gurin ta yana cewa yazo daukan tane su koma gida don mama bata da lafiya gida ya koma shiru,
Kin zuwa tayi sai da Ibrahim din yace mata idan bata bishi sun koma gida ba zai fadawa Baba lawal tasan zafin Baba lawal don haka bashiri suka fito ya kwashe su sai gida,
Sai dare ya dawo gidan yake tambayan ina Umma nace sun tafi yaya Ibrahim ya, zo ya dauke ta, yace sai Ibrahim don shi kadai zai iya sata gaba ta koma gida,
Wanan dalilai danake lisafawa maki akan umma sai suka sa aurena ya zamo auren da a daidai lokacin da mutane ke ganin ina jin dadi da farin cikin shi sabod nasarorin da zahiri ya nuna ina ciki,
Nikuma da nake a cikin matsalolin nasan yanzu nake zaman aure da fuskantar kalubalin rayuwan aure daga uwar mijina,
Sai duk da halin da nake ciki ban taba yarda wani ya fahinci ina cikin wani halin rayuwan aure ba,
Iyayyena ne idan na,fada masu hakkuri su kan bani suce dama duk wata mace mai aure tana tare da kalubalin aure don haka inyi ta hakkuri kawai don rashi hakuri ga rayuwan aure a yanzu shike kawo yawan mutuwan aure,
Dadin abin kawai ina samun sauki a gurin mijina da yan uwan shi,

****** ********* ******
Har lokacin tafiyan su gabas yazo ranan da aka,fada mata tare muka tafi da Hamza don yafads mata zancen tafiyan su din,
Tai murna tayi farin ciki sai kuma daga karshe tai mashi adduan tare da,cewa Allah yasa badi kuma ya kai mata zarah da Asmau,
Yace Umma bakice Humaira ba sai ki kawo zancen Zarah da,Asmau kuma ,
Yanzun dai na gane ba zancen yan uwanka kakeyi ba sai na matar ka duk tabi ta shanye ka akowa,
Haba Umma kada fa ki manta da hakkurin da humaira tayi a gidan nan shine fa ake gani kamar ta shaye nine,
Ni dai shiru kawai nayi ina zaune waje da Mama muna hiran mu muna jin zancen su,
Mama tace kada ki damu da zancen ta Aisha ya ci ace yanzu kin saba da halin uwar ku don kishi take da ke haikan,
Nace mama ai babu komai halin Umma na hassada a kaina,ba bakona bane, yanzu,
Mun kai wani lokaci a gidan muka fito zuwa gida sai da ya,tayar da mota yake cewa, kai ni wallahi idan Umma tai wani abin har mamaki take bani,
Na fahinci nine Umma bataso da alheri ba,wani ba taya zatace wai nakai Zarah ko Asmau makka gaki,
Idan ma nai haka ai ita mai min fada ne sosai da tana kaunana da alheri da bata sani hanyan da Allah zai tambaye ni, ba kan cin amana,
Banyi magana ba sai ma kallon titi da na mayar da hankalina a kai tare da dan wasa da hannun yarinya na da nakeyi ina dan mata wasa,

A haka har zancen tafiyan su gabas yataso in da ya sai muna komai da yasan zamu bukata a bayan shi,
Sa,adatu zata dawo gidan mu ta zauna wai sabo da tsaro don Umma tace wai mama bata zama a gida da rana,
Rashin zaman mama da har take fita zuwa kujiba kujiban ta gurin nema kudi don saboda yawan fitinan Umma na da take mata kamar karamar yarinya,
Duk da Hamza ya hana mama yin wanan sana,an amma bata bari ba tafi bukatan ta fita zuwa neman nakan ta gashi kuma abin ya karbe ta sosai,
Dawowan Sa,a datu gidan mu ya kawo muna matsloli da dama a zaman ta gurina,
Don kullun sai tafita wai tana zuwa gurin yan uwan ta yini,
Idan kuma tana gida sai dai ta mike kafa tana kallo ko kwanon da taci abinci bata iya kawarwa sai dai ni mai shi na dauke da kaina,
Sai kuma fita hiran da takegi a kofan gida da dare har wani lokaci mai tsawo nai mata magana amma tai banza dani,
Gashi yarana duk da kanana ne basu da shakat a gurin ta dan abu kadan ta kai masu duka ko zagi,
Wanan bai damay ni ba don nasan diyan tane tana da iko akan su don kaunar mahaifin su ne,
Ranan da tana kallo mimi tazo inda remote yake ta dauka tana daddannawa ta juyo ta kwashe ta da mari sai da yarinyar ta gigice da zafin marin,
Nace haba Sa,a datu may mimi ta sani da zaki mata wanan irin dukan haka yarinya ce ko anjima karawa zatayi,
Tace min ko zaki hana na duke tane zaki gwada min ke ce kika haife ta ko,
Ko don nazo gidan ubansu kike son kiyi min wullakanci dama nima wallahi ban so zuwa wanan zaman ba duk yayane yaja min zuwa nan,
Don dama nasan bason mu kikeyi da dan uwan mu ba kinfi son abarki ke da diyan ki ku mahe gida ku kadai sai abinda ranki yaso,
Nace don nai maki magana akan dukan mimi shine kike kokarin fada min abindake zuciyar ki dani,
Sau nawa kike dukan su ban maki magana ba kona yau naga dukan yai tsanani ne bai dace da karamin yaro ba,
Tace mai da wukar ki a kube Aisha na daina shiga harkan yaran ki har da naki ma na daina,
Nace to dayafi nono fari wallahi
Tun daga ranan ta daina shiga harkan mu ta daina yi min magana ko gaisuwa bamuyi da ita,
Sai nice ma nake kokari kawar da gaba a tsakanin mu nakan dan yi mata magana ta amsa,min a lalace,
Ko shigowa zatayi gidan bata sallama haka ma idan zata fita bata ce min uffan,
Naga zata zubar muna da mutunci a guwa yawan fitan ta da zama a kofan gida har wani lokaci yasani daukan mataki a kan ta,
Nai mata magana akan ta daina,wuce karfe goman dare bata dawo ba,
Sai taso ta zageni don haka na kira Ibrahim nafada mashi irin zaman da mukeyi da ita don ya,tsawata mata,
Bayan yai mata fada ya tafi tafito tana,min maganganu, rashin kunya wai dama dan tallaka bai iya samun guri ba na,samu guri shine har dasu kannen miji nake son na mulka to na tsaya iya mijina da na mallake,
Zarah nakira tazo gidan nafada mata sai bude baki zarah tayi tanacewa kai Aisha ban son kanan maganganu wanan ai sheri kike son yiwa Sa,a datu,
In har tai wani abin da ba daidai ba ki dauki mataki mana da kan ki basai kin fadawa Ibrahim ba, ki kirani mana inzo ki fada min,
Nace mata tau babu laifi suyi hakkuri amma zan dauki matakin da tace da kaina,
Tun lokacin nafahinci akwai wani sauyi a tsakani na dasu ban sani ba ashe umma ta fada masu wai na hana mijina ya kai su makka don ni ban tafi ba,
Ranan da ta fita tun safe ban sani ba,na kira yan uwan ko tana gurin su suka ce batazo ba har dare nakara kiran Zarah da Asmau sukace min bata gurin su,
Tana dawowa nai mata magana sai cewa tayi ke kin fa isheni tana magana kamar zata make ni,
Sai dai in zaki mutu ne ki mutu yar hassada kawai haka kawai ki sakani gaba da bakin lecture kamar kin aike ni,
Kuma duk tsiyar ki ba zan bar gidan ba tun da ba don ki nake a gidan ba don ba gurinki nazo ba,
Kince na daina kula diyanki nace har kema bani kulawa bana,shiga tsabgarki dana yayan
Gida kuma gidan dan uwanane sai yadda naga dama nayi dole kuma ki dafa ki bani naci koba kyaso,
Takarshe zancen ta cikin tsiwa tare dacjan wani irin uban tsaki tace banza kawai,
Na kalle ta nai murmushi kawai bayan ta,shige dakin ta,
Washegari ma nasan ba fasa fitan zatayi ba don haka na kyale ta,ko shiryo tazo ta,wuce mu zaune a falo tafita abinta,
Tana fita nabi bayan ta sai da tafice daga gidan na kalli tsohon bakaben dake muna gadi nace mashi baba cikin girmamawa,
Nace daga yau duk wanda ya, zai shigo gidan nan bayan karfe goma kowa ye kada ka bude mashi kofa idan bani nace ka bude ba ya amsa da to cikin girmamawa,
Sai sha biyu da yan mintina Sa,adatu ta dawo ta tura kofa get a,rufe yake tai kiran maigadi takafan get din wai ya bude mata gida ta shigo yace mata hajiya ta,ce kadana budewa kowa idan goma ta,wuce na dare,
Tai juyin duniya,tsohon ya bude mata amma fir yaki yana,gudun sabawa umurni na yayi laifi,
Waya ta,daga cikin daren nan takira layina naki dauka ran ta ya baci ta rasa yadda zatayi
Dole takira Zarah ta fada mata karya da,gaskiya wai na hana a bude mata gida,
Itama Zarah tai kiran wayana naki dagawa don ai tace na dauki mataki akan sherin da nakewa kaunan ta,
Gashi dare ne kuma bata son kishiyoyin ta ko mijin ta suji zancen don mijin ya taba mata magana akan Sa,ade din,
Dole badon taso ba takira Ibrahim ta fada mai abin dake faruwa agidan mu sai ko gashi a cikin daren nan yazo yasamay ta tsuru tsuru rakube a kofan get,
Kira daya yai min na fito naba maigadi Umurni da ya bude gidan suka shigo tare dashi suna shiga falo yakai mata wawan mari yana tambayan ta inda tafito a wanan lokacin,
Yai mata mugun duka ya kuma ce min nai mashi dai dai don ya tambayi maigadi yafada,mai time din da,ta,dawo,
Yabani hakuri tare da kara yi min nasiha akan nayi hakkuri kullun zai dinga zuwa safe darana har da,dare ya duba ta,
Tun wanan rana Sa,ade bata sake fita ba don tana tsoron Ibrahim yazo bai samay ta a gida ba yaci uban ta,
Shima Jibrin dayaji sun zo da mama sun mata tas suka kuma samu zara sukai mata cin mutunci a gidan ta,
Duk nasan maganan bai kare ba don in Umma ta dawo akwai magana amma hakan bai damay ni ba saboda nasan haka shine daidai don in wani abu ya samay ta dani za,ai kuka don may ban dauki mataki ba tun farko,,

****** ********* ******
Allah yayi matafiya sun dawo lafiya ana ta murna da farin cikin dawowan su taro na musaman nai masu sai dai shigowan dare sukai muna,
Don haka ba,a samu issashen lokacin tsayawa hira ba bamu dade ba muka shige da mijina muka bar Umma da yarta su ma adakin su din duk wanda yazo taron su ya tafi don dare yayi lokacin,
Tsab na shiryawa dawowan shi don duk wani abu da mace zatayi don taron mijin ta nasa kudina naiwa shiri wanan ranan,
Hamza sai faman santin rashina akusa dashi yakeyi yana cewa Humaira rashin ki a,wanan tafiyan yai min illa da yawa a can na,zabatun da,rashi ki a tare dani
Nace ai bautan Allah ka tafi yaya ko da atare muke ba abinda zaifaru a can ,
Yace amma in ina ganin ki abin zai min sauki sosai kara shigewa yayi a jikina yana fadin kina da,wani siri a jikin ki daba ko wace mace take dashi ba kina,sa nakanji tankar ke din kifi duk saura mata a komai,
Murmushi kawai nai mashi batare dana tanka mashi ba nasan kayan maman mujaheed ne ke aiki akan shi lokacin,
Washegari tun da,safe nafito nai masu abin karyawa tin da nakaiwa Umma nata dakin da,suke ina gaishe ta naji yadda ta amsa min yasani sanin cewa Sa,ade ta kwashi karya da gaskiya ta fada mata ko,
Sai da Hamza yai barcin shi mai isar shi sanan ya tashi yai wanka ya karya yafito don ya gaida Umma don sun dawo tana mura,
Bayan ya dawo daga dakin Umma alokacin ina kitchen ina guara gurin na,dora abincin rana don nasan ranan muna dabaki agidan,
Ina,shiga dakin na,samay shi ranshi a bace kwarai da gaske da alaman yaji maganganu iri iri a gurin Umma ,
Wanka nashiga nafito na zauna nagyara jiki shiko sai cika yake yana batsewa ya hau sosai,
Ina daura dankwali naji yana cewa, Humaira may ke faruwane bayan tafiyan mu ke da yan uwa na,
Najuyo a hankali cikin natsuwa nace mashi kaman yaya kuma ni dasu babu komai,
Yace Umma ta tareni da wani labarin da banji dadin shi dana,shiga gurin ta dazun,
Ni babu abinda ya faru tsakani dasu in ma akwaishi ka tambayi Ibrahim don shi yasan komai akan idon shi akayi,
Yace tau bari Ibrahim din yazo don ai hardashi dama a zancen,
Yaya zaki sa yaiwa yarinya mugun duka don kawai wani manufa naki na daban,
Da,sauri na dago kai na kalleshi yace idan da wani zai fada min baki son yan uwa na,su mamayni zance karya ne amma sai gashi dan tafiyan da mukayi sa,adatu kawai muka bar maki amma kinyi bakin ciki dazaman ta a gidana ,
Muryan su mama da mukaji tana cewa ina Alhajin yake ne dan nawa nagan shi Allah mun gode ma da ka dawo muna da,su

Download complete TXT · Novel page