Showing 222001 words to 225000 words out of 299981 words

Chapter 75 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17655

daga kurmi inda yake kai sanaan shi, Umma ta tare shi da zancen cewa ya dawo da Sadiya hakana dakin shi,
Sai yake cewa Umma ko Sadiya zata dawo dakin ta ba yanzu ba don yanzu wallahi kinga hankalina yafi kwantawa sosai,
Don ko tafiya nayi banda wani farga ba akan komai hankalina akwance don nasan banu wani fitina a gida,
Umma tace ai dama hakana zakace tunda ai maka agumo kasha ka taune ka hade,
Bai fahinci may Umma take nufi da zancen ta ba sai yake cewa agumo kuma namay fa wayai min,
Tace yar lelen ka mana da,baka son ai zancen ta agidan nan Aisha ni dama wanan yarinyar tun farko ban yarda da ita ba,wallahi don nasan cewa duk irin sherin uwayen ta sai tafisu iya,
Dubi gidan malam mudi uwar ta, sai kaga kamar itace ake cuta nan kuwa itace ke cutan sauran,
Umma ina kuma wanan zancen yafito haka abakin ki babu ko dadin ji Aisha ce kuma zatai min wani asiri can,
Kai may kasani dama banda hauka ga abu afilin Allah ai ni ban damu da yarda ka ba tunda dama ba yardan zakayi ba,
Ina dai maka gargadi da kakausar murya kayi mazaka dawo da,Sadiya dakin ta zaman gidan ya isa hakana,
Idan kuma kaki wallahi za,ajimu a gidan nan da ksi don zan dauki mataki ta inda bakai tsanmani ba,
Cikin mamaki Hamza yace yanzu Umma akan nadawo da Sadiya har kike min wanan kalamin, ?
Sadiya fa dakika sani ce ba wata ba agidan nan tace eh ita din kuwa,
An susuta ka duk kawani birkice wa mutane, a lokaci guda akan wanan mai fari kamar zabaya din,
Wallahi Umma ina mamaki don ni har yanzu nakasa fahintar abinda Aisha take maki a gidan nan ,
Ai bazaka fahinta ba tunda ka makance a kanta sai kace wata yar gwal can,
Umma nifa sani da Aisha a gidan nan ban taba gani kojin cewa tai maki wani abin assha ba,
Mutane da yawa suna magana acikin abokaina cewa nai sa,ar mata don suna min korafin yadda matsaloli yake tasowa a tsakanin, gidajen su,
Musan man irin rikicin da ake samu tsakanin matan su da iyayyen su a lokacin ni nakan yi mamakin yadda matarka zata ta wa mahaifiyar ka,rashin mutunci,
Ashe nima hakan zai faru a kaina sai gashi shigowan Sadiya gidan nan duk abinda suke fadi akan iyalinsu nata yashanye nasu,
Koma dai may ye kadawo da ita dakin ta don itama matarka ce tana da hakki a kan ka ta karashe maganar gami da cewa nadai fada maka ranka zai baci idan kaki abinda na fada ma,
Maganan Umma bai sa shi dawo da,Sadiya ba a,wanan lokacin, sai da ta,kara kusan wasu sati biyun yai tafiya sau biyu a lokacin, ya dawo,

****** ********* ******
Ana gobe Sadiya zata dawo gidan ya ke ce gobe wanan zata dawo nake gani,
Kamar ban san wa yake nufi ba sai nake cewa wake nan fa,?
Yace Sadiya nake nufi nace Allah ya kai mu kawai a takaice,
Sai dai ina son idan ta,dawo kada ki biye mata kuna fitina duk da dai nasan cewa yanzu tashiga hankalin ta ai dan zaman da tayi a gida,
Sai kuma zancen gwagona ban son kina yawan wanan kunyan dakike yi a kan ta ya kamata ki saka ido akan ta ga kowa a gidan nan banda mama,
Maganan da ya,daure min kai ke nan don ya tafi ya barni da mamaki da tunane akan zancen,
Ke nan har Umma yake nufi na,sa ido akan ta kan jikanta jinin ta lalai akwai wani abu a kasa,
Hmmm ikon Allah wai Umma da kanta take zuba,ruwa a randan ruwan Sadiya ta share mata kofa da kayan ta aka,wanke,
Ni ko ajikina don duk da raina ya,baci amma ko a jiki ban nuna nawani damu ba don nasan muje zuwa mai hali baya barin halin sa,
Ta dawo da wani ladabi da wani dan yin wanka da gaye ni dama wanan bawai sai ranan da nake da girki ba nake abina kullun dagani har diyata tsab zaka samay mu a gidan,
Ba wani shiri har yanzu a tsakanin mu don kishiyace balle dani ta dawo a ranta sosai,
In har ina da matsala a zamana gidan yanzu to tsakani na da Umma ce da ta sakani a gaba da fada kamar karamar yarinya,
Kiri kiri take fitowa fili ta nuna bata so na ko kadan kuma Jidda tankar ba jikan ta ba,
Sai yarinyar taita kuka Umma naji ko Sadiya babu mai karban min ita idan ina aiki ga Jidda da,yawan kuka,
Umma kance wai yawan tsegumin uwarta ne duk tabiyo yarinya kamar gyare a guri kuwa,
Sai in mama Hafsi tana gida ne nakan dan samu sauki a gurinta ta karban min ita nai aiyukana hankali kwance,
Sunyi ta kokarin cusawa Hamza ra,ayi musgunawa a kaina amma sam bai taba dauka ba,,
An dan samu saukin fitina yanzu saboda irin sharuddan da Hamza din ya kidanya mata kafin ya,yarda ta dawo gidan,
Dole badon Allah ba ta sauya halin ta zuwa na zaman lumana da kowa har kusan wata,daya,ba wanda yaji muryan ta da kowa a gidan,
Wata rana bayan ya,dawo daga tafiyan shi da kwana biyu nice da girki na idar nai mashi komai yadda na,saba ya shigo don cin abinci yake ce min A
Aisha ya kamata na fara rage maki kudin ki tunda yanzu ina dan samun riba sosai a kai,
Nace haba dai yaya idan ka bani su yanzu may zanyi dasu tunda ba,wani sana,a nake mai kwari ba duk rushewa kudin zasuyi,
Kabarsu kawai a gurin ka kana juyawa zaifi na karbe su su lalace, a hannu ni ban sai komai ba kai baka more ba,
Nikan ai Alhamdullahi na more masu sosai wallahi don dasu na samu nawa, nace to Allah ya kara masu albarka yace amin uwar gidan Hamza
Dariya kalman ta bani wai uwargidan Hamza nace kalman taimin girma yar karama dani
Yace to Allah ya baki ko zaki ki karbane yanzu wata ta karbe ke sai ki koma matar Hamza ko don dai kuma ban yarda ace amaryan Hamza,
Abinda yasa mu dariya ke nan har akejin sautin muryan mu daga wajen tsakar gida,
Wanan abu ashe ya batawa Sadiya da Ummu dake waje zaune saman tabarma daya rai suka daga ido suka kalli junan su,
Umma tace ana can ana mashi karuwanci shiko sai kwasan dariya yakeyi yaga guri,
Sadiya ta,wani yamutse fuska tana cewa ai wanan yarinyar Umma ta iya makirci kamar karuwa,
Ni maganin su zanyi dukkan su don ban dukan shashanci a mayar min da yaro kamar rakumi da,akala,
Sadiya,ta,cije leben ta cikin jin zafi da kunan rai don ita in akwai abinta taki jini aduniya,bayan mutuwan to Aisha ce,
Daidai lokacin Hamza yafito dakina da murmushi a fuskan shi yana kokarin sa takalman shi dake kofan daki,
Wani wawan harara gaba daya,suka bishi dashi alokacin nima nafito da kayan da yaci abinci don a dauraye,
Cikin tsigar son fitina Sadiya tace aikin banza wai cusa kai inda ba,a kaunan ka,
Ban bi ta nasu ba nabi bayan shi ina cewa, kada ka manta da zancen sayen permpers din Jidda fa yaya,
Yace ai saboda shima zan fita yanzu don kada na manta ban sayo mata ba har dare yayi,
Ina wuta su sakani a lokacin kafin nagama wanke wanke ina jin dan kuskus din su koda zan shiga daki har su bar gurin kowa ya shige dakin shi,
Nace a raina Umma kan anyi girman atta wallahi da matar danki kuma kike gulman kishiya Allah ya kyauta,
Washegari da safe ya shiga dakin don ya gayar da Umma,sai take cewa babana yanzu dai naga kamar gaba daya baka fafin kan ka a gurin Aisha sai abinda tace,
Dan abinda zata,sayawa yarta don amfanin kanta shine sai kai za,a matsawa kasayo ita may ye amfanin sana,an nata datakeyi kullun a gidan nan,
Cikin mamaki yadago kai ya kallo Uwar yace yanzu Umma kuma banibda halin da zan saiwa "ya ta abu sai najira uwarta ta saya mata,
Ai na fahinci Aisha da "yarta kake wa nema duniyan nan don sune kawai a gaban ka bayan su baka damu da damuwar kowa ba,
Hmmm Umma ke nan yanzu abin dari da hamsi dana,sayowa Jidda shine kuma abin magana,
Hakkin waye sayan kanyan yarinyar banawa ba ko sai na barta Allah ya kamani da,alhakin su a kaina,
Aisha abinta bai rufe mata ido ba idan ma ban sayo ba nasan zata sayewa kanta,
Jekaita masu facali da kudin idan sun kare ai sai mu zauna mu zurawa kofa ido gaba,dayan mu,
Subbahanallahi Umma mai yai zafi haka har da zancen karewan kudi akan abin naira dari da hamsi,
Asalima fa kudin yariyar na na,gado na karba nake juyawa a hannuna ba,wanda yaji kuma kin sani amma baki magana ba a hakan sai don nai wa Gwagona lalura dashi don ta fito daga tsatsan Aisha zai zama abin magana,
Kai kada ka,fada min maganan banza don kaga wuyanka yai kauri ya isa yanka wallahi yanzu zan bata maka rai a gidan nan,
Allah ya huci zuciyar ki Umma amma gaskiya kuma bazan yarda hakkin yarinya ya hau kaina ba,
Idan kudin zai zama na gori ne ai sai ka mayar mata da abinta bashi ke nan ba,
Bai ce mata uffan ba sai dai ya mike cike da mamakin Umma a ranshi yafito ran shi bace daga dakin,
Hamza idan kafita ka,sayo min sabulun wanki da omo don zanyi wanki ne,
Ai ba ke ce ke sani saye ba idan na,tashi kuma ma yau kwana nawa da na,sayo maku sabulu ke ina naki suke,
Ta amsa a yatsune da cewa nayi wanki dashi mana ya kare inji Sadiya dake tsaye daga kofan ta cikin murde fuska
Dama halinta ne duk ranan da yake dakina fuskan ta babu annuri ko kadan kamar zatayi ihu,
Yace wanan ba gaskiya bane don kafin nai tafiya na,sayo su agidan nan,
Ai kaji irin ta yanzu ka sayo mata abu ka tsaya kana mata tambayoyi kamar tsohon dan sanda,
Amma da,wanine yace ka,sayo mai jikin ka har rawa yakeyi gurin sauri kada rai ya baci,
Daga inda nake ina jin su murmushi kawai nayi don nasan inda zancen su ya nufa,
Nace Allah gani gare ka kai min tsari acikin wanan mutanen daka hadani zama dasu,
Fita yayi batare da ya tsaya jin kalaman Umma ba don suna mashi zafi a rai sosai,
Har zuwa yamma bai dawo gidan ba sai bayan la,asar lis yashigo da alama ma daga kauye yake gurin sana,anshi,
Idan kagan shi bakacewa ma ya taba bako ko yasan biro don yai futu futu dashi already dama ruwan wankan shi yana saman murhu ina jiran yadawo yai wanka,
Da,sallaman shi ya shigo a lokacin duk kowa yana waje har da Umma da mama da ta dawo daga gurin neman kudin ta, ta baza kayan da ta sayo tana daurayewa, na gwanjo duk ta sayo sai ta zabawa Jidda masu kyau tace na saka mata,
Yana gaisawa da iyayyen nashi yake wasa da Jidda dake hannun mama,daga gefe daya,
Hamza ina Sabulun da nace ka sayo man din tun da safe nake jira ka kawo min,
Ban sayo ba yace mata a takaice,
Oho don ni ba mowar ka bace yasa baka,sayo min ba da,watace da yanzu ka,sawo ko tun dazun,
Ai kin gama zance tunda kince da,
Kai amma Sadiya baki da dabi a daga dawowan mutum babu ko sannu sai kice wai ya,ina,sakon ki halan kin aike shine,
Mama hafsi ke maganan nan cikin bacin rai don Allah ku dinga tausayawa mazajen ku mana ba a rayuwa haka gaskiya,
Mama ki kyale ni don ba maganan ki bane wanan ,
Idan baka,sayo min kabani kudina sai na,saye ko,
Ta tsiyan naki yau tashi ke nan dai Allah ya kyauta inji mama tamike tana kokari dauka yarinyar dage gefen ta,
Na fito dauke da,jug din ruwa a hannuna ina mika mashi Sadiya taci gaba dacewa sai a dinga yiwa mutum banbanci ana gani baza ai magana ba,
Haba ki bi sannu mana ai dole ya,sayo maki inji Umma take lalashinta,
Ruwan ya karba yakafa kai yasha sai da yai rabin jug din yamiko min tare da cewa,
Kai min ruwa na watsa kafin naci abinci duk a gajiye nake,
Har lokacin Sadiya tana bakar magana ya shiga daki zuwa can yafito da kudi a hannun shi yace,
Sadiya wai nawa ne kudin naki shin ?
Ai kafi kowa sani tace tana kallon hannun shi dake rike da kudi karbi nan gasu,
Ta karba tana kirgawa cikin cewa tafi nono fari yau Allah ya kwato min abina,
Kuma wallahi idan baka sayo min ba ni ban yafe ba tunda ina da hakki a kan ka ,
Ya juyo a hasale yace baki yafe may ba hakkin may kike dashi akaina,
A,a Sadiya tunda ya baki kudi ki kuma ina zancen baki yafe ba yafito ki daina ja mashi Allah ya isa haka mana,
Mijiki ne fa kina ja mashi Allah ya isa haka kuma ,
Wanda yaji haushi ya rama mashi mana a,a ni din kuma kike nufi na rama mashi ko wa Sadiya,
Umma in ma ke din ne ai dake nake tunda in ana magana dashi duk sai ku tare ni mafa ina da iyayyen nan ba shegiya nake ba,
Yanzu don nace ki bari shine kike fa damin magana haka nidai yanzu banyi da kowan ku ba magana na ne dashi amma duk kun bi kun shige ciki zance,
To ai sai ki tayi tundake in idon ki ya rufe kowa kina takawa ki hau,
Ai in hakane kowa ma yana da, dan bana a dakin shi bani kadai bace balle a saka min baki,
Ni wallahi ban yarda da wullakanci kowa ya,sa maka baki a hanaka magana kaman kowa ba haihuwan shi akayi ba,
Har yafito daga wanka ta,zaune ta zubawa su Umma da mama kwankwami akai Umma duk nauyi da kunya ya rufe, ta,
Yanzu dai din nai magana shine ya jawo wanan zancen haka ko tace to anyi dake ne kibar ni dashi muyi mana ai ban ce kowa ya,saka min baki ba,
Ke Sadiya yace cikin wani irin murya yafito da rigar da yai niyar sawa a hannun shi,
Idanuwar shi sun kada sun yi ja yace ki tafi gidan ku na,sake ki saki daya,
Fetur ke nan tace ahayye Umma sai ki zuba ruwa kasa kisha tun da kin kai ga yadda kike so yau zan bar maki gida ga dan naki nan susu sauran mace mijin tace na bar maki sai a daura maki aure dashi dama kishiyar yar agwai kike,
Innalillahi Sadiya kina da hankali kuwa kike furta wanan kalamin da bakin ki uwar nashi zai aura,
Yace mama ki barta duk abinda tayi ai Umma ce tajawa kanta don ita tasaye,
Wanan da ba mutum ba itace Umma ta rike wai mutum don kawai kiyayyan Aisha da take ji,
Indon kankane ai da kowa Umma tana fada ba Aisha ba kawai don gashi yau takai ga yadda take so,
May nagane dama ga,wanan auren tsiya na gidan ki ba ci ba sha ba sutura sai bakar masifan tsiya da,wahala,
Garama da Allah ya kashe dan da nasamu da ku da na hada zuria da irin ku irin tsiya da masifa,
Tallakawa karshe masu cin amanan mutane kawai wallahi ni ban dana sani da mutuwar wanan bakin auren wahalan,
Macuciya tsohuwa kawai dama don ki cuce ni ki bata mani lokaci kikaje dadin baki wai na,auri danki don na kwato maki dan ki ga halaka ,
Ashe kece macuciyar ban sani ba,wallahi dake da ummana kuka cuce ni banda bakar kwazaba idan dare yayi babu abin da na karu dashi a gidan ku,
Ke kuma Aisha gaki ga gidan in dai wanan gidan ne ina zaune zanji fitowan ki don wanan muguwa bazata barki ba ita da shegun diyan ta matsiyata yan banza kawai,
Tajawo kofanta ta rufe tana tafiya tana cewa kada Allah ya,kara hadani daku ko a lahira wallahi macutan banza kawai matsiyata,
Ke tafi karyan banza karyan wofi a kwasa akai ma,wani mugun abin kuma yau dai Hamza ya huta kuma,
Hamza ne ke fadin haka cikin binta da mugun kallo
Ba don komai ya kyaleta ba,sai don yai ma,su Baba alkawarin bai kara taba jikin ta,da sunan duka,
Hamza ya juya gurin Umma yace tau Umma kin gani kin ga abinda kika kwaso wa kanki zagi da tonon asiri dai yau munji shi ,
Mazan dake kofan gida suna ganin tafito suka sa mata dari suna cewa ke nan baki barin mugun halinki Hamza ma yai kokarin zama dake bakar annoba ki zageshi ki zagi uwar shi,
Ta juya gurin su tana cewa muna fukan banza muna fukan wofi ai da ku aka hada kai aka cuce ni ban yafe maku ba,
Ta samu uwar ta da kuka karya da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login