Sarautar Mata

Chapter 75 of 94

yasa yan gidan mu samu daman ci gaba da zancen su suna mai cigaba da gulmana ni da mijina da uwarshi, da,ta hana rayuwana,shakat,
Ina shiga dakin Umma,na,samu wa yan nan yan matan suna shirin fita,daga dakin Umma sai faman godiya,take zabga masu godiya take ta faman yi,,
Gani tafe kai tsaye dakin fuska na,sai sheki yaki yi yasa suka, dan kauce min don ba,alamar zan kauce masu,
Nake cewa Umma ance wai na bada kudin da,za,a sayo wasu labulaiyya Umma suna jin murya sai suka dan kara tsuke fuskan su,
Suna fita daga gidan dayan tace tirka shi ashe akwai aiki a gaban ki ja Biba wanan matar ta Hamza ban taba zaton haka take ba wallahi,
Hmm bari kedai Amina wallahi narasa gano wani abin makusa a jikin yar iskan yarinyar nan,
Ashe ma karamar yarinya ce haka sharaf wanan ai kin,gimay mata nisa ba kusa ba,
Ashe shiyasa yake min wani gani gani yasan abinda ya aje a gidan shi amma dai komai tsiyar ta sai na shiga gidan nan wallahi ko,
Zaki ko sha kallo don wanan yarinyar da nake gani akwai shegen wayo gare ta, ba karami ba jifa tun bata masan ko mu suwaye ba irin maganan da takeyi,
Ni ko sai nake gani kamar ta gane komu su waye don kin da zamu fita ko kallo bamu ishe ta ba fa,
Wanan dole na,sake shiri a kan ta don akwai aiki gaskiya sosai saboda naga kamar ta dan waye,
Mu dai yi bincike a kan ta don mu san ko wacece ita ,
Wai wanan ce ake cewa matar hadi ce ba wai soyayya sukayi da ita ba ya aure ta,
Haka dai suna tafiya suna zance a kaina dakuma gidan namu har suka kai gida suke shedawa Uwar su cewa sun ga matar hamza a gidan da suka tafi,
Nikan ranan na jigarartu sosai don mun sha fama da jama,a anyi taro lafiya an kuma watse lafiya,
Sai dare Hamza ya samu ya shigo gidan don jama,a sun watse sai yan garin su Umma da suka zo mata buki ne a gidan,
Tun shigowan shi gidan yake kokarin kallon fuskana sai dai ya kasa fahin ta na ,
Ban tsaya ta kan shi ba kamar yadda na saba na gama kimtsawa na haye gado abina tare da yar diyata wace tayi wayo ko sosai yanzu,
Jin motsin shi danayi a,bayana yasani kara lafewa saman gadon wai make faru dake ne yau nagan ki haka Rangida ?
Ran gida ai suna can maka a waje nikan ai yar gadin gida ce ko ince yar aikin gida,
Kuma dai duk may yakawo wanan zancen kuma haka yau,
Nace matan banzan ka da ka turo buki don ai min dariya mana,
Katuro sune dama don su zo su ganin ko kuwa ni fa ban hanaka sha,aninka ba yaya amma cin fuska ne ban so,
Su tsaya a matsayin su kada su shiga gonata bazata iya bari idan ka kwaso ta tazo ba, don bata da kunya shine za su muna har gida wai sunzo ma buki,
Kuma don a,wullakantani kamar yadda kake son nuna masu shine Umma zatace wai sai ni zanyi services din su,
Murmushi naji yayi yace akan zuwan su Biba ne kike wanan cika kina batsewa Humaira,
Yaushe kika fara kishi hakane wai ban sani ba nace kasan ni, ba mace bace ko ince ba mutum nake ba,
Tau idan kin yarda wallahi ni ban ma,san da zuwan su ba asali ma har sai da sukazo suka koma ne tai min text cewa tazo taga beautiful wife dina da yara na,
Nace dama ai shi ya kawo ta kuma tagani tunda wanan ne kawai daman da take dashi na shigowa gidan nan,
Ni yanzu wanan zance bai gaba don haka ki sawa ranki sanyi don ni wata Biba can bata a gabana,
Daga haka ya mike ya,zagaya ta bayan mu ya kwanta ban bita kanshi don tukaki nake ji a cikin raina a lokacim ina ga ya fahinci hakane ya kyale ni,

****** ********* ******
Ina zaune a falona bayan bukin Asmau da kamar wata daya, Hamza dake fitowa daga kuryan daki a cikin shirin shi nafita,
Na,dago idona kalle shi nake cewa yaya dama yau iba son zuwa gidan Antu Hindatu ne na,dubo su,
A take ya tsuke fuskan shi yana cewa wai l loop yawan yi zuwa gidan Hindatune, kullun fitan ki ke zuwa gurin hindatu ne,
Nace kullun har da,yaushe yaya rabon da nafita fa tun bukin Asmau da akayi a gidan nan,
Ko wanan ma ai dalili ne zai kaini don nai mata ban gajiyan zuwa muna bukin da tayi
Ni dai ban son kina masu zariya a gida har aga kamar wani abu kike yawan zuwa yi,
Nace in ba dalili ba yaya may zai kaini ni gidan wa nake zuwa,a garin nan banda gidan mu sai ko nata,
Fusace yace min baki zuwa nace Aisha don ban son yawan fitan nan ni gaskiya, yafita a hasale ya barni nan cikin mamakin shi,
Ban daga a gurin ba,sai na fara tuhumar ko dsi da wani abune a kasa yasa ya hanani zuwa gurin ta,
Jin ya tayar da motar shi ya tafi baya gidan yasa na dauko wayana na kira Hindatun,
Mun gaisa da ita take ce min kwana biyu haka shiru Aisha ba ko waya,
Nace wallahi yanzun haka dashirin zuwa gidan ki a jikina amma kuma mai gidan ya hana ni fita ko ina wai ni ke nan kullun zuwa gurin ki,
Murmushi naji tayi tana cewa kyaleshi Aisha tsoron kada kizo guri na ki samu labarin shi shine ya hana,shi barin ki kizo,
Ashe bai isa ba tunda yana jin tsoron a fada maki abinda yake yi a gari,,
Wani irin damm naji kirji yaba da nace ke nan a kwai wata akasa ko anty tace kyaleshi ai nai mashi tas ranan da yazo gidan nan,
Anty may ke faruwa ne wai don ni wallahi har hankalina ya tashi sosai wallahi,
Tace ke ba wani zance bane zancen yar iskan nan ne da ta lake mashi da kaman sun rabu dashi amma yanzu sai gashi sun dawo sun kara dinkewa kuma har ranan nagashi da ita a mota,
Kin san bani bada bashine nadaga waya na kirashi shine yake ce min zai zo gida gurina ya samay ni,
Nashiga Ukku anty badai Biban nan ba tace wallahi ita kuwa Aisha
Ni banga abinda Hamza yagani ga wanan mace mai tsowa kamar hannun lema ba
Magana antu keyi amma ni hankali baya,a,gare ta,ina can ina tunanen cewa wacce nagani baka,doguwa daga cikin su itace ke nan Biba din,
Sai ji nayi tana cewa kai kibar namiji kawai Aisha sai kiga sun kwaso abinda ko kwatan na gida bai kama ba,
Wanda ke da mace kamar ki a gidan shine wai ya tafi kallon wata Biba can maikama da siffan samudawan dauri,
Anty ni na,rasa may wanan mutimin yake tayiwa aure haka don banga abinda na,ragashi dashi ta fannin rayuwa,
Amma kuma yake fita waje yana hangen wasu da ba,su kai ko kwatana,ba,
Tace ai garama ya,auro maki waccd bata kaiki ba din yafi ace tafiki da,wani abu, ke namiji sai kiga kamar idon shi a,rufe yake neman wata,macen,
Ni dai yanzu nasan cewa bawai kina,gazawa da bukatan shi bane kawai dai shi mutum ne mai ra,ayin wanan auren,
Wanda idan kin duba,mu diyan hausawa dama mun gaji irin wanan rayuwan tun kakan ni da iyayye,
Da,wuya kiga dan bahaushe ya tabbata,da mace daya a,rayuwan sai kin samay su da irin aure auren nan wanda zance maki a jinin mu hausawa abin yake,
Don kin ga da,ace ana gadon abin ne da Hamza bai yi ta,wanan halin aure auren ba da kurciyar shi don ance mahaifin shi bai taba auren wata ba bayan Umma,
Don haka don Allah dai kiyi hakkuri ki barshi da halin shi yaje yai ta,aure auren shi tunda ke bai rage ki da komai ba na rayuwa,
Ba dai komai akewa kishi ba sai jijiyar namiji ko tau ai ajikin shi yake ba,a jikin ki ba shi ya sani da bakin auren don shi zai fadi ai ance jiki magayi,
Halin mutum mai kosar dashi, shi da,ya jajibo shi ne zai gasu kina zaune zaki ji shi da ita in har kinyi hakkuri,
Ko murai kada ki wahalan tayar da hankalin ki a,banza don ba bari zaiyi ba idan yai niyya,
Ke da ki kula da kanki da tarbiyan diyan ki, sa mashi ido kawai don ko shiru magana ne Aisha,
A sanyayye nace naji Anty nagode insha Allahu yadda kikace hakan zan yi don baki tabani shawaran da bai min dadi ba a rayuna,
Munyi sallama da ita tana ta kwantar min da hankali ina ce mata babu komai insha Allahu,

****** ********* ******
Kamar ban san komai ba haka na daure na dake da zancen a cikin zuciya na sai dan lalaba kaina nakeyi kada na kasa,
Ya gama ginan gidan sbi komai ya,saka acikin gidan sai kace wani palace ,
Sai da wata matsala da,takunno kai a kan zancen komawa gidan shine,
Umma tace sai ta koma tare da mu amma kuma shi Hamza din ya ce gaskiya ba zai so takoma can ba abar masu gida ba kowa sai su Ibrahim kawai ta daiyi hakkuri ta zauna dasu idan sunyi aure sai ta,dawo gurin shi din,
Da kyat aka samu su liman dasu Baba suka shawo kanta harta yarda amma da sharadin idan taso zata dinga zuwa ta kwana biyu a gurin mú ta dawo, nama dai badon yaso ba yarda,da hakan,
Don haka ranan laraba da zamu tare a,gidan tare da ita muka koma sai da tai mu Sati biyu tadawo gida badon ranta yaso ba,
Ko shi Ibrahim ne yazo ya,sata gaba sai da ya dauke ta suka tafi tare da shi,
Aka barni ni da yarana sai a gidan sai mai gadi don a lokacin shi yana gurin tafiya da kyat Umma tabar mu Sa,ade ta taya ni kwana kafin ya dawo tunda,ban saba da gidan ba,
Ranan da ya dawo da dare ya,mayar da,Sa,ade gida akabarmu daga mu sai yan yaran mu biyu a gidan,
Bayan ya,dawo daga gurin kai Sa,ade ne ina zaune a falon yaran sun gaji da,wasa,sunyi barci a gefe na ya,shigo gidan cikin shigar kanan kaya,
Na kalle shi cikin girmamawa nai mashi sannu da zuwa ledan da ya,shigo dashi nai kokarin tashi na karba sai dai akwai mimi a jikina don haka yske cewa zauna abinki na hutar dake, kada ki tayar min da uwa kin san yazu tana,fara rigiman nan nata ta hana mu shakat,
Shi kan shi ya shiga har kitchen ya dauko plate ya ciro kaza guda daga cikin ledan yazo har gabana inda nake zaune ya zauna a kasa gap da kafafuna na yake ce min bisimillah,
Naso na,dawo yaran nan basuyi barci ba don su samu suma suci shi da zafin shi amma sai wani ya tsayar dani can,
A raina nace wani ko wata kai dai kasani in kaya ne kaji dashi can,
Daga inda nake zaune yake dan miko min nama ina ci muna hira, nan yake fada min cewa yana son bana su sauke farali da Umma insha Allahu,
Nai matukar farin ciki dajin zancen shi inda yake ce ni kuma badi in Allah ya,kaimu sai na tafi na sauke, nima ban lokacin da na kaiwa kanshi dake daidai cinyata runguma,ba ina matukar farin ciki da jin zancen,
Yace min sai dai ina son kija bakinki kiyi shiru kada ki fadawa wa ko sai in har tafiyan ya,tabbata kawai za,aji dan dama ina da pasphot din Umma dashi nake son nai mata amfani na tafiyan,
Zaman mu a,sabon gida zan iya cewa wani irin zama ne da muks dade muna mafalkin shi a,ran mu don so ne da kauna tsan tsan ta muke shimfidawa a gidan,
Wanan karon nai yaye babu ciki a tare dani don haka ban samu wani tsegumi ba,a gurin Umma don tace ina son na cika maigida da "ya"ya mata



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU,IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON HAKA CIN AMANA NE YAR UWA,,,



HAMZA ne zaune a falo yana rike da waya a hannun shi magana yake akan wasu kayan da za,a shigo mashi da,su daga kwatano,
Nafito daga daki acikin shigar dagon riga ta matan Niger style din rigar yai matukar kabar jikina, tunda na shigo falon gaba daya ya mayar da hankalin shi a kaina,
Ya zuba min idanuwan shi sai kace mara gaskiya ya motsa bakin shi don yakirani sai kuma ga waya a kunnen shi da hannun yai min alamar danazo inda yake,
Kitchen zan shiga sai na juya zuwa gurin shi alama yai min da na zauna a gefen shi,
Ina zama ya dauki hannun shi guda ya rike min hannuwana yana dan murwa a hankali yana wayan shi ,
Shiru nayi daga gefen shi ina sauraren wayan da yake yi da abokin sana,ar shi,
Sai da ya gama wayan yadan sauke numfashi shi ya juyo gareni yana cewa Rangida, ashe aikin nan bai maki yawa ba ke kadai ga gyaran gida ga, luran yara ga kuma girki duk ke kadai,
Nace sai kace ba yar Umma nake ba wace tai aikin mutum kusan bakwai a gida daya har tsawon wasu shekaru sai wanan na mu kadai ne zai min yawa,
Ya ce Nop ciki daga hannun shi da juya kan shi ina bukatar ki huta yanzu tun da Allah ya hutar damu,
Don haka ki samo wata da zata tai maka maki da wanan aiki ko tsohowa ko kuma yarinya,
Murmushi nayi tare da dan kwantan da kaina a kafadar shi nace kaidaine kake ganin shi aiki amma ni aguri na wanan ai ba aiki bane,
Yace na sani amma ina son ki samo wacce zata taimaka maki da ko da gyaran gida ne ke sai a barki da dawainiya na dana yara,
Nace harda girkin ma ni ce zanyi abina da kaina don ban son wata tai maka girki bani ba,
Yace cikin lushe idanuwan shi tare da dan sunsunan wuyana nima nafi da son hakan ai amma so nake ki huta ki kula min da wanan jikin naki da kullun yake koma mawa kamar ta under age,
Murmushi nayi ina under age inda Jidda da Mimi suka fito yace kece ke ganin haka ni kullun kamar bakece kika haife suba nake gani,
Mikewa naso yi don zuwa duba girki da na dora a gas sai yariko min hannu yana cewa ina kuma zaki muna magana nace na,dira abinci a wuta don ka,samu kaci kafin kafita don nasan in kafita sai dare,
Ya lumshe idanuwan shi yana cewa kuma gaskiya kika fada don ko nafita din ba wani abu nake ci ba sai fura da dan snacks,
A hankali nayi wata yar sanyanyar ajiyar zuciya nace nasan haka wallahi don nakan ga yadda kake cin abinci idan kadawo shiyasa ma yanzu nake kokarin tashi da wuri na girka maka,,
Bayan ya kammala cin abincin shi ne ya mike tare da dan shafan gaban rigan shi yana,fadin kin dai kusa sani katon tubi Humaira wanan irin abinci da kike tula min a gaba,
Ai nan da yan kwanaki nakara kiba ba kadan ba don dadin dakike bani,
Nace cikin murmushi kiba,ai ga,dan Africa kamar ruwa,ne don sai guda,gudane basu kiba idan sun kai age din yin kiba yanzu aikai da,sauran ka sosai,
Yace lokacin da mukai aure ana cewa dani dake duk mun yi kanana sosai yanzu gashi har mun kai ga,diya,biyu cikin ma bamu haihu ba da wuri, murmushi kawai nai mashi cikin dan jin kunya
Mikewa nayi na bishi har zuwa kofa ina mashi adawo lafiya,

****** ********** ******
Kamar yadda Umma tai alkawarin zuwa ta kwana biyu a gurin mu hakan ne kuwa don wataranan laraba da dare muna zaune a falo muna kallo sai mu kaji ana nocking din kofa,
Muryan Umma ce tana fadin ko babu kowa ne a gidan ana,sallama ba,wanda ya karba muna,
Jibrin ne yashigo ya kawo ta ya shigo yana,min raha irin yadda muka,saba dashi,
Sai Sannu da zuwa nakewa Umma na karbi kayan ta hannun shi ina ta,farin ciki da,ganin ta,
Na mata iso da firin zama ta zauna tana bin gidan da kallon yadda yasha gyara ga kamshi ta ko ina a lokacin Hamza yana dagi don bai dade da dawo ba,
Na shiga na,sheda mashi zuwan ta, ya juyo yana cewa cikin bata fuska Umma kuma da daren nan haka waya,kawo ta, nace mai Jibrin ne,
A tare muka fito dashi lokaci guda yana murmushi yake cewa Umma da daren nan kika taso ,
Tace tau tun rana nake jiran yaran nan sukawoni suna min yawo da hankali shiyasa da dan neman nan ya,shigo cin abinci yanzu na datse shi,
Ai ban ma san kana gari ba da kai zance kazo ka dauko ni, zama yayi suka fara hira da Jibrin yana mashi zancen komawa makarantan da yai mashi,
Ina can ina kokarin kawo wa Umma abinci da Jibrin sai da na aje abincin ta bude taga,may na,dafa,
Tuwon alkama nayi da miyar kubewa danye sai ta,dan bata fuska tace ki aje min kila anjima naci Jibrin yace anjima kuma umma keda yanzu kikagama cin abinci,
Nace wa Jibri kai yaya na zubo maka ne zakaci yace a koshe nake naci tuwon mama na koshi wallahi,
Abinci kike dafawa haka da yawa ke kadai a gida Aisha ?
Hamza yace ni aikin ne ma yai mata yawa ita daya nake gani shi yasa nace ta samo yar aiki ta taya,
Hummm,ummm, inji Umma yar aiki kuma kodai kayi aure ga gida da girma ace wai mace daya ce a cikin shi,
Murmushi Hamza din yai mata yace aure ba yanzu Umma don ina da,abubuwa a gaba da zan yi,
Ban tsaya jin su ba na dauki kayan abinci na,zan mayar kitchen take cewa nai maganan abinda bata so ai kaga zata gudu,
Ko bakiso sai wata tashigo gidan nan don bazaki zauna

Download complete TXT · Novel page