Showing 231001 words to 234000 words out of 299981 words

Chapter 78 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17672

yake sayen kayan a gurin su,
Daga wanan sana,an sai kuma yafara sana an sayar da kayan maganin amfanin gona na zamani dake sa shuka saurin fitowa da wurin,
Ai fa anan kasuwa ta barko mashi balle yan kauyen da yake sana,a dasu don ko basu da kudi zai iya basu idan sun samu su biya shi,
Tuni sunan shi ya fara fice a gurin kanan manoma masu karamin karfi dake bukatan taimako
Hakan bai hana Hamz zama tare da abokan shi na kuryciya da,suke zaman majalissan su dasu
In har tana a gari a tare dasu yake zama suna harkokin su kamar baya ayi raha,ayi zolaya,da,wasa da,dariya, a tare,

Yanzu in akwai wani matsala a,tare dani bai wuce irin yadda yan mata da zawarori suke kawo wa Hamza hari ba har gida sukan biyu shi wani lokaci suce ace wani mutum yana mashi sallama sai yafita zaiga mace ce ke mashi sallama ashe,
Tun ban sani ba har na fara daukan hannun don zanji yana waya a cikin wani yanayi hakan kan sa na fahinci da mace ne yake waya,
Tun ina boye bacin raina har takai na fara nuna mashi a fili cewa nasan may yakeyi,
Don daya fara irin wayan nan nakan ja tsaki na tashi nafita daga dakin,
Gashi cikin jiki ya tsufa sosai don har yafito daga jikina,
Sai dai duk kulawan da ya dace miji yaiwa matar shi ina samu dags gareshi wanan matsalar dai ta neman mata ne ke hada mu fada dashi
Ko shi fadan ba,wai can ba nakance ni dai wallahi ina tsoron a kwaso min cuta ina zaman zamana a halakani,
Sai dai yayi dariya yace kada Allah ya nufeni da aikata zina, a rayuwana don da ina yi da tun akan Lima zan fara zina,
Namiji ai ba abin yarda bane tun da,ba,tare da kai nake yawo ba dariya yakan min yace ki yarda da,mijinki Aisha mijinki ba mazinaci bane,
A cikin ikon Allah har cikina yakai watan haihuwan shi a lokacin komai da ya dace asays na haihuwa Hamza ya,saya min, ya aje yakan ce shi ba mazaunin gida bane don haka ya saya kada na haihu baya gida,
Jidda tun da mama,ta,yaye ta a gurin ta take har yanzu bata dawo da ita gurina ba acewan mama,wai naji da cikin dake a jikina,
Kamar wancan haihuwan wanan ma haka yazo min da sauki duk da na kira wata mai aiki asibiti ta dubani a tare da ita na haihu na,sambado katuwar jaririya,ta,
Sai faman ihu take ta,tsalawa don sanar da,mutane cewa ta iso wanan duniyar tamu ta maliki,yumindeen,
Mutanen gida suna jin kukan baby suka san cewa an haihu sai murna sukeyi da farin ciki,
Sai da nurse din taga,min komai sannan ta bude kofan a lokacin duk kowa na tsaye cirko cirko sun matsu su ji cewa, may na haifa,
Nurse tafito tana cire safan hannun ta tanacewa mama barka mama kin samu kishiya katuwa sai fari kamar yar turawa,
Daga inda Umma take tace kuma dai Allah ya,sauwaka,
Nan su mama,suka hau murna aka shiga aikin jego tare da aikawa mutane cewa na sauka lafiya,
Kafin wani lokaci gida ya fara cika da yan uwa da abokan arziki suna zuwa taya mu murnan samun karuwa da akayi,
Umma kan kamar ba haihuwa akai mata ba don fuskan ta a daure yake,
Ibrahim ya buga ma Hamza waya yake fada mai an haihu ya kara samun baby girl cikin murnan shi da nuna jin dadin shi ga dan uwan shi,
Shima hamza yai matukar murna da farinciki nan ya bugowa Umma waya yana fada mata barka,
Yace Umma ashe an haihu bayana yanzu ibrahim ya bugo yake fada min Aisha ta sauka lafiya,
Umma tace eh takara haiho abinda ta saba haihuwa maka mace kuma,
Umma aikin samu takwara ance yariyar babba da ita kuma gata fara itama kamar gwagona,
Cikin nuna gundura da zancen shi tace idan kazo ai zaka gan ta ko,
Yai murmushi yace to Allah ya dawo dani lafiy ainan da kwana biyu ko uku zan dawo insha Allahu,
Allah ya kawoka lafiya tace cikin matsuwa,su gama wayan dashi,
Don wani irin haushin shi take jin an haifa mashi mace karo na biyu shine shi harda nuna farincikin shi haka tace sha,sha bai san ciwon kan shiba,
Murna,sosai yakeyi sai bugawa mutanen shi waya yakeyi yana,sanar dasu cewa ya samu karuwa an haifa mashi baby girl,
Kamar yadda yace kwana biyu haka din da kwana biyu sai gashi ya dawo daga tafiyan cikin murnan shi,
Bayan sun gaisa da Umma yai mata barka da samun karuwan da akayi afili ya mikewa zuwa diban baby shi,
Ya samay ni a zaune na zuba ruwan zafi a cup sai turiri yake ina son insha
Nai mashi sannu dazuwa yayin da shikuma yake min barka da sauka lafiya tare da tambayana ban jin komai da zuwa yanzu a jikina ko,
Yarinyar dake kwance saman gado ya dauka tare da dan kura mata ido har wani lokaci nan ya,fara mata adduoi irin yadda addini yace aiwa jaririn da yazo duniya yana cewa mamana Allah ya raya muna ke ta farkin addinin musilunci,
Zara da tazo taga yadda Umma take muna take cewa haba dai Umma abinda kikeyi fa gaskiya,bai dace ba idan yar ki ce yaya zakiyi,
Bafa Aisha ce kebawa kan ta,wanan haihuwan diya matan da takeyi ba
Yanzu dai tunda banda dama na nuna damuwa sai ku sa ta haifi namiji ku gani,
Ai da macen da,na mijin duk shiryuwan su yana a gurin Allah mu fatan mu Allah ya,sa masu albarka zarah ta bata amsa da hakan,
Ranan suna yarinya taci sunan Umma Rabi, sai umma kecewa nibda,baku saka mata,suna,na ba da sunan hafsi kuka sa mata ai da yafi,
Hamza yace sai na kara samun wata in saka,mata sunan mama ai nan gaba,
Au ashe kai sakaraine ban sani ba yanzu har kana fatan akara haifo maka macen kuma ?
Yace Umma aini dama ina son haihuwan diya mace a,rayuwana
Ai ko ka samu don gashi nan ana,ta sambado maka su sai kashi ai maka,su dozin don wanan uwar diya mata din naga tana da niyar yin hakan ai,
Murmushi yayi ka wai sai dai zancen yai matukarci mashi zuciya don bai san may Umma take nufi ba da wanan akidar nata,
Ni dai kamar yadda kowa yace na share umma da akidar ta hakanne nayi na bar kula da abinda take muna,
Hamza iya yakasa yake da yaran shi gasu gwanin ban sha,awa dasu kamar diyan larabawa don kyau,
Harkokin shi sai ci gaba sukeyi don yanzu komai ya,kan kama arziki Allah ya,ba,ahi a lokacin kurciyan shi

Wata rana suna irin wanan zaman majalissan sai ga wasu yan mata,sun shawo kwaliyan su da alaman wani wuri na muhinmin zasu,
Ganin gungun matasa maza yasa su dan canza takon tafiyan su cikin sallo da yanga irin na matasan yan mata, zamani,
Har sun dan gwauta su kadan yayin da idanuwan mazan yake a kan yan matan masu tafiya,
A,a Habiba yai ko gaisuwa babune daya daga cikin abokan hiran su hamza yake cewa yan matan tajuyo cikin yauki da yanga tana cewa kai, Abdul wallahi na fada maka kabar kirana da habiban nan ko muyi tsiya,
Dariya yasa yana cewa ai tunda kinci sunan tsohuwa ni dashi zan dinga kiran ka don ban san wani Biba can,
Ashe tobashiyar Abdul ne yarinyar don haka,suke wanan wasan shi da ita idan sun hadu,
Hamza ya kura mata ido yana nazarin abubuwa da dama akan yarinyar,
Bayan tafiyan su Hamza kece wa Abdul wanan yarinyar fa yar wani gidane
Abdul ya dan kalleshi da mamaki yace zi tobashiya tace nan yake fada mashi irin yadda alakar su yake da,yarinyar,,,,,




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[6/28, 4:11 AM] اختي خفصة: IDDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON YIN HAKA CIN AMANA NE,,,,,


Tun daga wanan ranan alaka ta kullu a tsakanin shi da Biba, soyayya suke mai karfi a tsakanin su, irin ta saurayi da budurwa,
Ranan da na fara tsintar maganan ba karamin tashin hankali mukayi da hamza amma si yake gwada min shi ba,wai zancen serious bane kawai dai lokaci ne
Don shi, da wasa ya dauki zancen a gurin don haka in zan daina hauka na dai don shi bai ma da lokacin wanan,
Ba wai na yarda da zancen shi bane kawai dai na hakkurane don kada wani yaji mu yace ina da matukar kishi,
Amma abin yana ci min rai sosai don sai nakan ji su suna hira cikin nuna so da shaukin junan su,
Da abin ya damay ni sai na samu anty hindatu da zancen don ta samo min mafita akan matsalar,
Tambayoyi tafara yi min akan ko dai ina da matsalane a gurin kwanciya da Hamza,
Kunya na kawar nace mata ban tsanmani ba gaskiya don duk yanayin da nake nakan daure da bukatar shi a kaina,
Tace kuma duk kin tabbatar da,cewa kina bin duk wani sallo na kwanciya,ki tafiyar dashi don kin san fa,shi namiji yafi son ana juya shi a kan gado,
Duk abinda zakiyi in ba kece mai shafar shi sai shi kadaine zakibarwa yana ainkin shi akwai matsala a hakan,
Nake cewa,gaskiya ina da dan raganci a wanan fanin don wani lokaci shi kadai ke aiwatar sa kwanciyan mu,
Kinga matsalar ki ta,farko ke nan Aisha indon kice daya bukace ki zaki yarda kawai ba tare da kin ba da taki gudun mawar ba ke ma,dole ki dinga samun matsala dashi gaskiya,
Don haka ki tabbatar da duk lokacin da zaku kwanta kamar gasar gamsar da junan ku zakuyi bawai ki barshi ya kida yaraya ba shi kadai, don haka nasa wani namijin hangen nesa,duk kowani namiji yana da sha,awar mace tana shafar sa aduk lokacin da,suka kasance tare,
Nace a hankali zan gyara hakan Anty tace da kin kyautawa kanki inkinyi hakan,
Idan yai tafiya ko ya,shiga gari sau nawa kike kiran shi Aisha ?
Nace gaskiya ban faye damuwa dana kirashi ba anty gara mashi yakan kirani kila safe da yamma kafin mu kwanta,
Matsala Aisha matsala wallahi,
Wa yafada maki mazan yanzu ana masu haka ai in fada maki idan bakira ba a yini tau sau biyar ke nan,
Ke ko kazan gidan ku tai koto ce mashi, aikuwa yanzu kazan nan tai min abu kaza na gyara mata kaza,
Wayan kiran namiji a waya yana da matukar amfani Aisha shakuwa, so, da kauna yana kara shigane ta haka a tsakanin ku,
Ke baki da abin fadi ce mashi kawai yallabai ya rana ya kake, ko kaci abinci kuwa, don hakan zai sa ya san cewa kin damu dashi matuka,
Idan yana gari kuma hakan ma ya kasance ki kuma dinga shiga kina fita kina kwalliyan ki,
Idan yana gida a tare dake kina kokarin dan manna jikin shi a naki kina dan jan shi da hira koda akan harkan sana,an shi,
Sanu sanu sai kiga kin zama abokiyar shawaran shi don ko wani abu zaiyi sai ya kira ki ya nemi shawaran ki,
Nasan matsalar ki Aisha shine uwar mijin ki zakice kina jin kunyan idon mutanen gidan ku,.
Wallahi ki gyagije ki zama abin, kallo a gurin su don farautawa mijinki rai don samun ci gaban rayuwan ki
Hakama fanin girkin ki tunda yanzu kuna da,wadata atare da ku ki dage ki koyi girki masu ma,ana kikuma fahinci wani irin nau,in abinci yafi bukata namu na gargajiya ko na modern one,
Gyaran gida dakin ki da kuma yaran ki harshi kanshi maigidan ki tabbatar kina kula da hakan,
Nasan kina da biyayya ga iyayyen shi da uan uwan shi to sai ki kara ki gwada mai kin ma fishi kaunan su,
Abinda bai so ki ki wanan aban kema har cikin ranki,
Haka abinda yake so gwada mashi kinfishi son abin kema don yana so amma banda kishiya, fa sai muka dara duk ni da ita,
Tace a in kin gwada kin son kishiya ai sai yakaro maki uku lokaci guda,
Balle ma ba kishirya ce ba a so ba yanzu halinta don duk wace zata shigo da gurin take shigowa ko ta fitar dake ko ta nakasa ki dake da babu duk daya a gun miji,
Shiyasa kikaga mata yanzu sun jajirce akan kishi don gudun komawa baya a,rayuwa,
Hakan ma kawai idan kin gwada zamu iya fahintar wasu abubuwa daga gare shi don a haka zamu gane inda kike da,weakness a,gareshi,
Don zaki matukar ganin canji a gareshi a lokaci guda zai sake maki gaba daya,
Nan dai taita kawo min musalai irin yadda ya dace mace ta bullowa mijin ta gurin kama kafan shi da daure zuciyar shi baki daya,

****** ********* ******
Abu na farko dana,fara gwadawa shine bugun waya, nakirashi da,safe nai mashi ina kwana bayan mun gaisa sai dan shiru,
Sai cewa yayi Humaira lafiya kuwa,
Nace may kagani sai yace a,a kawai dai na tambayane ko da wani matsala,
Ni kuma na fahinci mamakin kiran da nai mai ne yau muka gaisa bashi ya kirani ba kaman yadda muka saba,
Bayan dan wani lokaci kuma sai na kara kiran shi yadauka nake ce mai yakuke can da fatan harkoki suna tafiya daidai,
Daga inda nake a cikin waya nadan ji ya,sauke ajiyan zuciya yana cewa, Alhamdullahi Humaira gani nan ma nafito office din director,
Zuwa rana bayan munci abinci nake kara bugawa nake ce mai yayana kako ci abinci don mu gamu har mun gama cin namu,
A karshe nake cewa ga Jidda wai na gaishe ka yace bata wayan nai magana da ita,
Duk da ba magana yarinyar ta iya ba sai na manna mata waya a kunnen ta nace ga Abba yace, sweetie na sai naga yarinyar tai murmushi don jin muryan mahaifin ta,
Nan na ji wani irin tausayin kaina da yarinyar ashe na dade ina cutawa rayuwan mu ne ban sani ba,
Sai da,dare nakirashi ina ce mai ya gajiya da zirga zirga yace wallahi fa Humaira kamar kin san yau nasha zirga zirga a garin nan don ganin komai ya kammala nake ce mai to a huta lafiya,
Yace ina yaran nace ganin dai da Umma na ita ko Jidda tana gurin kakan ta,
Yace kai mai raba Jidda da mama ai sai Allah don shakuwar su tai yawa wallahi,
Nace cikin dan murmushi mamace ta sai hakan daga gare ta kasan yaro inda yaga fuska can yake,.
Yanzu fa zan iyacewa duk neman kudin mama akan Jidda ne tun ina fada har nakawo ido nasa masu,
Yace babu ruwan ki shiga tsakanin masoya kibar su suyi abin su don Jidda ta zama yar gidan mama ko nace gaskiya kan,
Mun dan yi hira akan Mimi karama dake da,shegen wayo don tasan shi sosai ko nono take sha taji muryan shi sai ta sake dashi da Ibrahim, don shi Jibrin cewa yake wai Jidda ce yar shi,
A karshe nake cewa yaya ka kula min da kan kafa kada ka dinga zama da yunwa,
Wai madam yau may ke faruwa ne haka,?
Nace may kagani yaya ?
Yace tau a daibar zancen nace kewan ka da rashin ka a kusa damune yadan fara damuna,
Yace taufa ni dan gatan Humaira da Umma ke nan don kune next to me,
Munyi sallama acikin dan barkwanci dashi bayan na kashe wayan na nisa a hankali tare da lumshe idanuwa na na ce matsala ashe a gurina take,
Allah Allah ka bani ikon gyara duk inda nake da matsala akan hakkin mijina dake kaina,
Wallahi kafin ya dawo wani dan shakuwa ne ta musan man ya shiga tsakanin mu ta,waya,
Ni kai na ko a haka nasan na samu canji ta musan man daga wani bangare ta rayuwan da nai sakaci dashi a baya amma insha Allahu da sannu zan gyara, komai na,rayuwana ta yadda zai iya jin ba wata sai ni a gaban shi dama kowa a duniyan nan,

****** ********* ******
Ranan da mukai waya yake ce min zai dawo next tomorrow ban zauna ba nai kitso na gyara dakina har wanki sai da nayi ban bar komai a fili ba,sai da na gyara har gidan mu,
Na dan zana siffan lale a hannu na da yake na iya zanen dama ban dai son yiwa kowa ne yarana nai masu kitso su ma irin ta yara mai ribbos,
Asmau wace dan kwana biyun nan muna da dan shakuwa ta musan man don har hiran saurayin ta dake dan kokarin ja baya da zancen auren su muke yi da ita ina dan bata shawaran da yadace don Umma nacewa wai ta rabu dashi don baida komai,
Dama kuma saboda shi taki aure tuntuni don yana karatu ne ita kuma ta nace sai shi zata aura,
Hiran shi da shawaran yadda zamu bullo mai da nake mata yasa ta kara manne min don ko yaushe muna dakina anan take cin abinci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login