Showing 279001 words to 282000 words out of 299981 words

Chapter 94 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17686

a bace sai ya hago shi zaune a saman abin sallah ya hada kai da gwiwan shi wuri guda alaman yana cikin damuwa a lokacin,
Da kyat hamza ya dago kai ya kalli Ibrahim din a cikin wani yanayi mai ban tausayi,
Yace da kyat ya iya bude bakin shi Ibrahim may naiwa Umma take son kashe ni sai kawai ga hawaye shar a idanuwan shi suna saukowa, sharrrr,
Ganin haka yasa jikin Ibrahim yai sanyi yace mai akayi tare da samun guri ya kai zaune,
Nan Hamza ya labarta mashi komai yadda,duk sukayi da Biba abinda tafada mashi
Innallilahi kawai Ibrahim ke nanatawa yace wanan abin kunya ina zamu kaishi haka yaya may yasamu umamane wai haka,
Kai kai Amma Umma ta bamu kunya,wallahi gaskiya ni bazan iya zama a gida daya da Umma ba da matana wallahi gara naje na samu haya yafi mun,
Hamza yace shawaran da nakeyi kenan nima na kwashe iyalina daga garin nan nkoma can nesa inda bata ganin mu balle wani abu ya kara shiga tsakanin mu irin haka,.
Shiru sukayi kowa da abinda yake tunane a ran shi wanda zai fishe shi,
Ibrahim ne ya kawar da shirun da,cewa yanzu Yaya, yaya kake ganin za,ayi magana fa zamuyi wa Umma tasan mun gane abinda take aiwatarwa,
Yace Ibrahim may zance wa Umma ni har kunya hada ido da ita nakeyi wallahi ko don ban san may nai mata ba,
Kabari gobe zan kira Zarah da Asamau mu hadu a gida sai ai maganan,




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU DON HAKA CIN AMANA NE,,,,,



Gaba dayan su suna zaune a kofan dakin umma fuskokin su duk babu walwala a cikin shi, don fuskokin mazan a murtuk suke sunfi na matan daurewa,
Shi suke jira, a gurin don haka ne ba wanda yai magana sai shiru a taron
Ya shigo gwiwa ba karfi yana gaida Mama hafsi dake zaune daga gefe daya cikin dan damuwa ita ma,
A daure ya juya gefen Umma yana cewa ina kwana, bai ce mata yaya jiki ba don ta kwana a,wahalce, saboda sukan kwalabe sun sa jikin ta yin tsami da ciwo,
Bayan ya samu guri ya zaune ne mama hafsi ce tafara magana da cewa tau yaya nasan zakiyi mamaki matuka don ganin mu anan baki dayan mu a lokaci guda,
Gaskiya mun taru a nan ne a matsayin mu na jininki diyan ki dani yar uwar haihuwan ki damuke muke nan dama a gurin uwar mu,
Gaskiya gaskiya yaya abinda kikayi yasa zukatan mu a cikin rudani da tashin hankali don zan iya ce maki kusan duk wanda yaji abinda ya faru daren jiya baiyi barci da dadi ba,
Umma tace ina ko zaiyi barcin dadi wanan mara kunyar yarinyar ta hanani lafiya,
Mama hafsi tace kika dai hana kanki yaya yanzu don Allah yaya ina ke ina zuwa gurin matar danki da zance ku hada kai kuyi wa dan ki dan cikin ki asiri da wata bare sabba can mara mutunci irin habiba,
Umma,bata,fahinci inda maganan mam ya dosa ba sai cewa tayi haba hafsi aini da farko na zaci yar azikine sai daga baya na,fahinci ba yar goyo ba ce ita,
Ashe zancen ta gaskiya ne ke nan kin samay akan wasu zantutukan marasa dadin ji ga mai sauraren su,,
Kamar yaya basu da dadin ji kuma may tace na fada mata,
Zance akan Aisha da,yaran ta harshi dan naki Hamza da kikai mata,
Umm tace ai ba wani sabon zance bane in har tace na fada mata wani abu akan Aisha ina dai magan gudane, yadda Aisha ta mayar min da yaro tun shigowar ta cikin mu may na fahinta a kan shi,
Innalillahi Hamza ya maimaita tare da rintse idanuwan shi cikin kunan rai,
Asmau ta fashe da kuka tace amma Umma wallahi, kin cuce mu kin bata,muna suna ace mahaifiyar ka ce za,a hada kai da ita a cuci iyalinka,
Jibrin yace Umma kin gama damu cikin gatin nan yanzu ashe duk abinda Biba tafadi da gaske ne,
May yayan mu ya rage ki dashi, har kikai mai wanan irin sakaiyan haka a,rayuwan shi,
Umma jikokin ki jinin ki zakice a salwanta masu rayuwan su haba Umma su wa muke gani yanzu muji dadi a rayuwan mu inba diyan da yayan mu ya haifa muna ba
Sune kuma ke da kanki kike neman halaka masu rayuwan su, su salwance don kawai kina kin uwar su,
Kai banfa fahinci maganan kaba may kake fada min ne haka koda nake adawa da Aisha ai ban hada da diyan taba itace dai bani son irin rayuwan ta a raina,
Wani irin rayuwa ne gare ta a duniyan nan wani irin biyayyane Aisha ba tai muna a gidan nan,
Mata nawa kika sa shi ya aura amma duk babu na gari yan mata nawa kika sa shi nema amma duk a kareta a tsiyace dake,
Yau har takai kece maiba da maganin da za,a yiwa jikokin ki jinin ki Umma Ibrahim ke fadi cikin kunan rai,
Tace cikin mamaki magani kuma wani irin magani kake magana wai,
Zarah tace wanda kika kaiwa Biba ta ba yayan mu ita kuma taki karba har yakawo maku matsala haka,
Magani wani irin magani kuke magana akaine wai ban gane ba fa,
Mama tace yaya kin ba habiba magani ta zubawa yaron nan ga abincin shi shine taki karba har ya kawo maku matsala, haka,
Innallilahi Umma tace ni magani fa kikace ni zanba wanan mara mutuncin yarinyar magani akan may,
In magani ne ai sai dai nayi wa kaina ba na ba,wata tai min ba,
Kuka yaran suka fara yi gaba dayan su in ka debe Hamza wanda kan shi yake a dafe don takai,
Cikin kuka Zarah tace Umma kin gama damu wallahi kin muna mugun tabo da zamu zama abin kwatance a garin nan,
Ace uwar mu don mugun hali har dan ta take son a kashe mata duk da Umma na jin jikin ciwon da ke damun ta bai hana ta kwashe Zarah da mari ba,
Mikewa Hamza yayi yana cewa na riga da na gama yanke hukunci zanbar garin nan da iyalina gaba daya, mu koma can nesa da ku don kawaucewa fitina,ya fadin haka ya bar dakin ran shi a bace
Gaba daya,sai hankalin su ya tashi suna cewa Umma kinga abin kunyan da kika jawo muna,
Ba wani abinda yanzu zamu iya yi don abin yayi muni gaskiya, don hakan da yayi shine daidai tunda baki kaunan shi da iyalin shi, inji Ibrahim shima mikewa yayi yabi bayan dan uwan shi,
Umma ta na gani haka sai ta fashe da kuka tana cewa wanan yarinyar ta cuce ni wallahi don bamu taba wanan zancen da ita ba,
Tiryan tiryan mama take fada mata,duk yadda Biba ta fada masu kara,sautin kuka Umma takara ta shiga kwashe wa Biba albarka da tsinuwa,

****** ********* ******
Ina zaune a dakina abin duniya yakai min ko ina a,rayuwa na na rasa inda zan sa kaina shawaran karshe dana yanke wa kaina shine na hakkura na bar mata dan ta kawai,
Ance in so cutane hakkuri magani ne don haka na shiga hada kaya tun wuri na bar gidan har yaran ita ta dade bata kashe su ba in nafita,
Ibrahim ne ya kawo shi gida don ya kasa jan motan da kan shi Madina da yake tana da wayo sai tashiga kuka ganin Madina na kuka yasa itama Jidda yin ku,
Sun samu yaran suna kuka ya ke ce mazu cikin kasa laliyar murya may yafaru sai Madina take cewa Antyna tace zamu tafi gida yau tabar su,
Jidda har da tagwaye ta dakin ya fada ranshi a bace ya samu ina gyara kayan sawana a cikin akwatina na ya na min kallon mamaki yake cewa,
May nene haka wai Aisha ban kale shi ba sai aikin hada kayana nakeyi kawai inda nake ya karaso ya karbi kayan dake a hannu na yake cewa,
Nace wai maynene haka Humaira may kike shirin yine wai please ?
Na dago idanuwana da sukai ja ina cewa, kabarni kawai yaya in tafi don banga amfanin zamana a gidan nan ba,
Tun ina ni daya Umma bata kaunan zamana da kai har yanzu da na tara iyali su ma kiyayyan nawa ya shafe su,
Don Allah yaya ka sakeni kowa ya huta in dai na bar gidan ina shike nan zance ya kare ke nan ko sai a,auro masu kirki da mutunci diyan masu arziki ka zauna dasu,
Ni kike fadawa haka Aisha nace cikin zafin rai dole na fadi don dai nice ba,a so ko zanbar gidan ka zauna da wa yanda ake son ka zauna din,
Ibrahim ya shigo dakin yana kalkon mu yake cewa maman Jidda may nene haka kuma,
Nace gidan mu zan tafi yaya Ibrahim don shine kawai mafita a wanan zancen,
Bakin jini na har ya shafi diyan da na haifa daku a gidan nan, haka yaran nan may suka sani a duniya da za,ace a illanta man su haka,
Yaya Ibrahim may naiwa Umma ne haka a duniya takini taki jini na da ita,
Yace yanzun dai ki kwantar da hsnkalin ki don Allah wanan zancen ai baikai haka ba, kuma ma idan kinyi haka bakiyi wa mijin ki adalci ba inda akafito,
Ki fa san duk dadewan nan yana bayanki bai yarda ya biyewa Um a ba a cuta maki,
Don may ke zaki yanke maku dan yen hukunci haka ne wai,
Nace gaskiya ni bazan zauna ba nidaine ba,a so ko tsu zan bar gidan akawo wanda ake so su zauna ba shike nan ba,
Ibrahim.ka barta in haka take ganin shine daidai, ban son kuma hukuncin da take so ba bayan wanan nan dana dauka,
Barin garin nan ga baki daya daku shi nake ganin mafita a gareni don nima ba zan tsaya nan ba a cuta min haka,
Idan aka nakasa min yara aini aka nakasa ba wani ba a duniyan nan,
Nace ba sai kabar gari ba a kaina ka bari ni na tafi don ko mun bar gari ai still auren ka na a kaina,
Don haka abin ba zai kare ba ke nan amma idan na tafi kaga kowa ya huta shi ke nan,
Ba inda zaki inji yaya ibrahim wallahi ke da barin gidan nan Aisha sai mutuwa,
Halin Umma ne kuma sabo yau a gareki ko kuwa wani irin fitina ne na Umma baki sani ba Aisha,
Nace amma ba irin wanan ba yaya gaskiya don wanan yai muni da yawa sosai,
Kafin aiwa yaran illa a kuka dani gara kawai na bar gidan shine mafita, mai sauki,
Juyawa Hamza yayi yabar dakin nan ya barni da Ibrahim yana ta faman yi min nasiha dakin shi ya shige ya rufo kofa da karfi yafada,saman gadon shi,
Fita yaya Ibrahim yayi sai gidan mama, Rahana ya fada mata ya juya zuwa gurin Ummina yai sa,a Baba Mudi yana gidan shima ya fada mai,
Sin samu na gama hada kayana ina zaune a bakin gadona ina ba hussaini nono, don shi sarkin tsotsone,
Ganin su kawai nayi don kusan lokaci daya suka iso gidan gaba dayan su,
Kalkon bacin rai suke min don ranan harda Baba sai da ya shigo dakina, nan suka fara yi min fada wai banda hankaline nake shirin yankewa kaina danyen hukunci haka,
Cikin kuka na zanyana masu duk abinda ya faru gaba dayan su suma hankalin su ta shi yayi Baba Mudi yace eh lalai kina da gaskiyan ki Aisha,
Abar mata gidan da diyanta shi yafi sauki don muddin ba,a girgizata ba na gane Rabi bata shiga hankalin ta,
Tare da su muka bar gidan sai dai Baba yace dole na tafi da yan jariraina da basu ko kai sati biyu ba da haihuwa,
Nan muka bar su Jidda da Mimi yaran na ta wani irin kuka da gurjji,
Kukan su ne yafito da Hamza daki yaga dakina a kulle alaman na tafi ke nan,
Ya ja yaran zuwa dakin shi yana lalashin su har ya samu sukai shiru,
Yakai wani lokaci dasu a dakin shi Biba ko tana dakin ta sai addu,a take Allah yasa na tafi ke nan kar na dawo gidan don duk abin da akeyi tana jin komai,
Sai zuwa magariba yafito daga dakin yaga haske a dakin Biba din rai bace ya nufi dakin cikin daga labule yake cewa ke Habiba fito ki tafi gidan ku ke ma sai na nemay ki daga haka yabar dakin,
Sai kuma ya juyo yana ce mata,na fada maki ki tafi don in na dawo na samay ki wallahi yau ranki sai ya baci a gidan nan,
Ta kalleshi fuska ba tsoro tace akan wani dalili zan bar gidan don matarka ta tafi zakace nima sai na tafi,
To bari kaji don wallahi babu inda zan tafi tunda ba laifi nai maka ba daga tai mako sai kari ya koma, ciwo,
Yace zaki ko sha mamakina yau wallahi ya juya yafita zuwa sallah don ya dawo kafin yaran su tashi,

A gidan Baba Mudi muka sauka ina shiga gida su mama saude suka gan mu harda kaya nanan suka shiga tambayan mayke faruwa ne wai haka don dai ba lafiya ba tunda basu taba ganin haka ba,
Baba Mudine yake ce masu garata dawo gida kawai don Rabi dai da kuke gani ba mutumiyar arziki bace wallahi,
Mata babu lisafi ko kada a rayuwan ta ta zauna da dan nata tunda haka take so,
Daga haka yafita ina shiga dakin Ummina na fada saman gado na kwanta su Mama Rahana da Ummina dasu mama Saude aka,shiga zancen Umma Rabi,
Sai dai suna fita suka kama gulma cewa ai ga irin ta dama an samu guri ana wa mutane sallo da daga kai ai gashi yanzu an koro ni hankalin iyayyena ya tashi suga zasu rasa gurin ci, kai kishi bala,i ne wallahi,

Mamana Rahana bata bar gidan ba sai da taga na kwantar da hankalina gashi ina jego a jikina ga yan jarirai tare dani,
Barcin da ban samu yi ba da daren jiya shi ne ya dauke ni hakan yasa ta sallama ta tafi,
Hadari a ka hada duk ina barcin ban fito ba yaran kuma Atika ta goya daya mama saude ta goya gudan,
Ummi tai min girki mai lafiya ko dana farka yana gabana take ce min na tashi nai wanka kafin dare yayi sai da nai wanka Ummi ta sani gaba tana kwantar min da hankali har sai da taga na ci abinci sosai tabar dakin,
In akwai abinda ya tsaya min a rai shine yarana da na bari gida da Biba ban san cewa itama don dole ranan tabar gidan ba ya rufe kofa daga shi sai su a gida ya cewa maigadi duk wanda yazo yace baya nan kuma ya kulle gidan ya tafi da key,
Iyayyen Biba suka dawo da ita amma sai maigadi ya fada masu yadda yace mai din,
Haka suka koma da ita gashi ya kulle wayoyin shi duk a rufe suke ba mai samun shi,
Sai dare yaiwa Ibrahim waya ya kawo masu take away da zasu ci shi da yaran,
Nan maigadi ke fada masu Biba tazo da iyayyen ta amma ya fada masu yadda yace, Ibrahim yake cewa itama bata gidan ne,
Ya kalli Ibrahim a sanyaye yace may zata zauna yi itama ai yadda saboda ita har Himaira tabar gidan nan sai ta tafi har nagama yanke hukunci tukun,
Ibrahim yakoma gida yake fada ma su mama zancen tafiya na hankakin su ya tashi suke cewa akan may zan yake hukunci tafiya nabar diyana da mijina tunda ba dani akayi ba,
Sai Ibrahim ke cewa, ai hankalina yai matukar dagawa jin da nayi ance za a salwanta min da yaran,
Tun da daren mama taso zuwa gurin yaran yake ce mata ai Hamza ya rufe gida amma ta bari da safe sai ta tafi yake fada masu ita ma Biba ya turata gidan su, ai
Duk da an fara ruwan sama amma saida mama ta shiga gidan mu don gani na,
Mama ta samay mu ni da Ummi a daki da sauran yaran bayan an gai sa take cewa may yasa nabar gidana na fito kan zancen da baikai ko ina ba ai wanan ba abinda za,ace nabar gida bane, akai,
Duk da halin kawaici irin na Ummina sai da tai magana tace haba Hafsi ai barin gidan ya zama waji bi ga Aisha don in ba gidan tabari ba wanan kiyayyan ba zai kare ba gare ta
Gara dai tabata gidan tabar mata dan ta shi yafi don abin har yakai ga shafan diyan ta Rabi ta manta cewa yaran jinin tane na har abada amma idon ta ya rufe saboda kiyayyan da takewa Aisha may yarinyar ga ta kashewa mata a duniya yai zafi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login