Showing 276001 words to 279000 words out of 299981 words
mu sheda masu don su shirya tunda duk yawancin kaddarorin shi an sayar dasu don su aganin su baya raye ya mutu,
Nace yanzu kan yadda yaya yake fada min ai, bai ko kawo zancen wanan a ranshi, tace amma ai hakkin shi ne dole su bashi nace tau sai dai in Allah yakawo muna shi din ko,
Sai yamma muka shiga gurin Umma ta,tare mu kadaran kada ham, ba yabo ba fallasa kamar bazatai min murna ba sai take cewa ashe mahaifinki ya baiyyana,
Amma ni dai sai nake ganin kamar bashi bane kila kama daine suka gani kawai a take naji wani iri don ta nuna min hassada nasan kuma za,a shiga wani sabon kulli ke nan akan zancen,
Ba,a dade ba yaya yazo ya kwashe mu take cewa duk yaran nan ashe kai aka kaiwa dawai niya haka,
Allah dai ya kyauta don irin haka nasan watarana har uwar zasu koma gidan ka gaba daya,
Umma wai wani irin zance haka saboda Allah to wallahi bari na,fada maki gaskiya mahaifin Aisha duk fadin garin nan yanzu banga wanda ya kaishi hali ba,
Ikon Allah Allah yasa yadawo din mugani don wanda ya saba da yawon duniya ai bai tuna gida balle iyalin shi,
Mu dai mukai mata sallama muka tafi zuciya na tap da kuncin maganganun Umma sai na,shiga tunane barkatai akan zancen,ta,,
Sai washe gari na bugawa gwagona waya ina,sheda mata albishir din ganin dan uwan ta
Tace bari takaiwa liman waya don kada tani ita kadai shima na fada mashi yadda yaya yafada min yace masha Allahu Allah mungode ma in har shi baizo ba mu mu shirya mutafi kwanan nan, insha Allahu,
****** ********* ******
Allah yadawo da su Ummina lafiya su yan biyu tunda mukaje taronta sukace basu dawowa,
Daga ita har mama sunyi kyaun su saidai sunda fada don aikin hajjin da sukayi amma gaskiya jikin su yayi kyau sosai,
Zancen auren Ibrahim akeyi zai auri diyar wani dan kasuwa mutumin Jega amma a kano suke zaune da iyalin shi,
Shima Ibrahim ya hadu da itane can wurin business din shi da yake shiga kano saro kaya a nan suka hadu sundan saba da yayanta shine watarana yaje gidan su yaganta sai soyayya ya kullu a tsakanin su,
Umma tana ta murna dan ta zai auri diyar mai kudi ba irin mu ba diyan tallakawa, acewan ta
Wai harda karyan anga mahaifi gashi har yanzu ba wanda ya gan shi ke nan karya akeyi,
Niko da zancen Abbana nake kwana dashi nake tashi a raina ko yaushe, sunyi waya da hamza akan zancen zuwan shi yake cewa akwai abinda yake son yakammala kafin yashigo Nigeria,
Yanzu zancen inda Ibrahim zai sa amaryan shi akeyi Umma ta sa hamza gaba sai ya sai masu gurin da zasu zauna, ko yai maigina a gidan su,
Ga shini har zuwa lokacin ban haihu ba cikina sai wani girma yake har asibiti sai da hamza ya kaini akace lafiya lau cikin yake har ni, din, lafiya lau nake haka yasa hankalin mu kwantawa,
Ban haihu ba sai bayan sati biyu na haihu wanan karon na kasa haihuwa yadda na saba a gida saida aka kaini asibiti,
Yara maza biyu ne suka fito daga jikina kusan lokaci guda sukazo duniya batare da nai mugun wahala ba,
Mama hafsi da Anty Hindatu suna,waje nurse din take cewa ku bamu zani guda biyu musa yaran aciki,
Yara suna hada baki nurse tace eh maza biyu ta haifa ai baku san cikin tagwaye ke gare ta bane,
Wani ihu suka sa a lokaci daya suna fadin Allah mun gode ma wana albishir din dole mu baki tukwici inji mama ta bude post din ta ta dauko dubu daya taba nurse din tana godiya,
Hindatu ce tafara yiwa hamza albishir shima hamza ya kasa boye farincikin shi a fili,
Umma ce mutum na farko daya fara kira ya sheda mata na haifi tagwaye maza,
Ta dan nuna farin cikin ta amma ba irin yadda ya zata ba a furin ta, nan yashiga bugawa mutane waya yana,sheda masu zancen haihuwana,
Kafin mu dawo gida gida ya cika da yan uwa da abokan arziki sun shigo tayamu murna zance duk yan uwan hamza suna gidan mu har mazan su sai dai banda Sa,adatu amma nasan ko ita laifin Ummane rashin zuwan ta din,
Habiba fuskan ta murtuk yake sai magana yan uwan hamza ke sakewa a tsakar gida don ta tanka,
Ba bata lokaci akaiwa yaran wanka harni na kimtsa jikina sai zolaya mutane suke suna maman biyu,
Ina dan murmusawa cikin jin dadi da farin ciki don nasan gaskiya wanan shekaran shekaran sa,a tace sosai ga mahaifina ya baiyyana ga kuma kyauta diya har biyu lokaci guda daga Allah,
Hamza ya dawo gida daga garin dayake cikin murna da farin cikin shi ya nufo dakina direct don duba mu,
Ya samu mama tana gyarawa yaro daya kwanciya tana ganin shi tafara murna tana fadin nikan ai Allah ya na sona maza biyu lokaci guda haka,
Nan tai mashi murna sosai da kumafatan albarka ga yaran sai murmushi yake yana fadin amin mama,,
Fita mama tayi daga dakin tabar ni dagani sai shi da yaran,
Daya bayan daya,yake daukan yaran yana rugumay su tare da masu addua, irin na,addinin musulunci ga yaro sabon zuwa duniya,
Tun ranan da,na haihu Hamza bai zauna ba sayo wanan sayo wancen akawo gida tun daga dangin abinci da sha da,suturun yara da,sauran abin bukata,
Koda yaushe ina daki da mutanen arzikina ban san tsiyan da Biba ke shukawa ba don a,shirye nake kan ta don nasan dama ta kulla abubuwa da yawa a ranta,.
Don ta rama abinda ya faru lokacin haihuwan ta amma sai taga duk na shanye manufarta gaba daya, duk yadda taso tarama,babu halin haka,
Suna saura kwana biyu Biba ta samu Hamza, da zancen yabata abin suna da za,a aiwatar, ya dubeta a cikin mamaki yace mata akan may zan baki su Zarah fa, ,
O ashe kasan dasu kaba ba matar ka lokacin haihuwan hausatu, yace na bayar ne don ita ta,tantanci naba don banis gari saboda ita maya tace,
Tace niko farkan ka ce ke nan ko ?
Yace gaskiya ban sani ba amma abinda kika gani wai may yasa baki son a zauna lafiya ne Biba,
Tace nice ban son a zauna lafiya ko kai da kake macuci azzalumi, idon shi suka kada sukai jawur a lokaci guda, ran shi ya baci sosai,
Yace naso ace tunda aka fara wanan sha,anin ayin agama shi lafiya dake amma naga alaman baki son hakan ke,
Yanzu kije nabaki go ahead kina iya yin duk abinda yadace kamar yadda ita Aisha tayi da kika haihu don ni kinga an min haihuwa yanzu ban son fitina da kowa,
Ni may na haifa maka kake nufi wai yace abinda kika haifa mana ko,
To wallahi baka son a zauna lafiya ke nan ai naga diya matan da aka fara haifa ma ka na ina akasaka dasu sai wanan guda dayan dana haifa maka kake nuna mata tsana da kiyayya,
Yace ciki daka mata tsawa tare da nuna mata dan yatsa,shi yace dakata, Biba kada ki fara ki sawa diya ta tsanata don ina son abina kamar yadda nake son kowani dan da,na haifa,
Halinki dai ke uwar tane bai min ba sam wallahi ban son mutun wanda baida mutunci baida tarbiya,
Tace nice banda tarbiya ke nan ko may kake nufi yace kina dashi ne dama kike ciwa manya mutunci ido rufe, zatai magana yace ki tafi
Ki tafi duk abinda yadace ki yi kiyi ai kema bukin shafe ki tunda mata ta kike, ita Humaira da kika haihu ai tsaye tayi tafitar dani a kunya,
Tace in kana son haka kabani kudi yadda ka bata
Yace kudi naba yan uwana don sun san zafina kuma zasu fitar dani kunya,
Ranta yai matukar bace zatai magana yace for god sake kibarni in huta Biba tun ban bata maki rai ba a gidan nan kinji magana ta
Ya duka kan computer shi ya barta nan a,tsaye ta dan dauki lokaci a tsaye sai ta kuta tafita tana yan maganganu,
Har akaci aka,sude bata saka kanta cikin duk harkan sunan da akayi ba abinci ma da aka kai dakinta cewa tayi afita dashi bata so,
Hamza yai muna kokari sosai sai dai gurin kayan tufafin da ya,samin daidai ne da wanda yasa wa Biba din, don adalci
Kayan yara ne dai gaskiya sunsha kaya sosai gurin shi da gurin yan uwa, nan ma saida tai mashi korafi akai,
Bai kulata ba don yasan fitina halintane bata raina abin magana ita ita dai ko yaushe ai jidali shine zaman lafiyan ta,
Saidai bata da riko da zaran tayi masifan sai kuma ta sake tadawo tana neman shiri kamar ba ita ba hakan yasa sam bai sake mata yadda take so
Bayan suna da kamar kwana biyu sukai waya da mahifina yake fada mashi kaya suna hanya ya turo kafin ya shigo amma kuma ance custom sun kama,
Bai gama magana da abokin shi dan custom wanda sukai NYSC tare ba, sai ga kiran Umma yana shigowa,
Ya dauki wayan bayan yagama magana da mutumin,yakira Umma da daukan shi Umma tafara mashi korafi akan zancen auren Ibrahim
Yake cewa Umma na fada maki a nan gida zan mashi gina yanzu kuma ga zancen auren Sa,a ga zancen kayan mu da aka rike muna, duk sune a gabana , ko may tace mashi oho, yadai yi murmushi kawai,
Yagama wayan yana cewa komai yazo ana son kwantar da hankali a cikin sa amma Umma bata ganen haka ko dukiyan nawa take son na kwashe lokaci guda nayi lalurar dasu,
Ba wanda yai magana a cikin mu don duk muna gurin a lokacin,
Hakan baima Umma ba washegari tunda safe sai gata sai dai tai rashin sa a har yafita zuwa Kamba, gurin kayan su,
Ni ina dakina kwance
don na dan samu barci a lokacin Biba ce a falo tana gyaran gurin ta,
Sun gaisa da ita take cewa ina yake ne tace wa , Umma tace maigidan mana don naga yana son raina min wayyo kamar yana bakin ciki da dan uwan shi,
Sai Biba tace, kai amma dai Umma wai wanan abin da kukeyi zaku barmu da,arzikin mu kuwa, ?
Cikin mamaki Umma ta kalle ta tace, ban gane arzikin ku ba tace ko na kine to kullun ace kawo a kawo kamar an samu saniyar tatsa,
Ran Umma yai matukar baci kamar habiba har zata tsaya don rashin ta ido tana fada mata wanan magana haka,
Hannu Umma ta daga zata mareta sai Biba ta rike hannun Umma din tace akan may daga fadar gaskiya,
Sai ta tura Umma baya iya karfin ta da baya tafadi tafada saman glass din flower dake tsaye gefe,
Wani kara Umma tayi tamike tana cewa cikin mamaki ni kika yar a kasa Habiba,
Kadan kika gani wallahi, in tsoho baiji kunyan hawa jaki ba jaki bazaiji kunyar kadashi ba,ai,
Cikin fushi Umma takara kai mata duka itama rai bace tajuyo takai ma Umma wawan mari kayauuu,
Daidai lokacin hayaniyar su da ya tayar dani har yara muka fito da saurin mu,
Biba tana huci tace wallahi dadin aure ba zai sa ina tsaya har uwar miji ta doke ni ba, sai faman huci suke yi, gaba dayan su,
Madina tace Umma jini yana zuba a jikin ki dubawa mukayi gaba dayan mu,
Jini a kafan ta da hannuwan ta duk kwalba ya soke ta ga idon ta da yai kwancin marin da akai mata,
Innalillahi nace habiba yaya akai haka dan Allah haba in rai ya baci ai hankali ke nemoshi amma hakan baiyi ba,wallahi,
Umma ko take hawayen bakin ciki suka rufe ta sai tafara kuka tana sharan hawaye,
Tana cewa yau na,shiga uku Habiba nikika mara tace ni ban mareki ba ki kadai mareni,
Da kyat na lalashi Umma nace ta tashi a kaita gida, don kada ta zauna bakin ciki ya kasheta don sai faman ajiyan zuciya takeyi,
Tun yana can yan uwanshi suka buga mai waya yadawo ranshi a bace gidan su yafara zuwa yaga Umma wace har ta bayan duwawunta duk kwalba ya soketa,
Ya shigo gida rai a bace tun daga kofa yake kiran Biba da karfi idanuwan shi sun kada sunyi jawur, dasu,
Biba tafito daga dakinta sabale da yarta a kafa wani wawan mari mai ji da lafiya ya kwashe ta dashi saida ta,wurgada yar ta kasa yarinyar ta tsala wani irin ihu na fito daki da sauri na dauki yarinyar yakara kai mata wani marin,
Tace yanzu don naki yarda da shawaran da Umma ta kawo min akan a hada kai dani a cuce ka kake min wanan dukan haka,
Tsayawa yayi yana kallon ta yace cikin fushi shawaran may takawo maki da har kika mareta,
Tace zuwa tayi fa,wai na bata hadin kai mu kori Aisha takawo min magani wai nasa maka ga abinci kaci sai kaji ranka ya fita ga Aisha da yaran ta baki daya ni sai na zauna ni kadai a gidan,
A take naga jikin Hamza yai sanyi ya juyo inda nake tsaye ina lalashi yarinyar dake kuka a hannu na,
Yace ita Umma tazo maki da wanan zancen tace harma maganin da ta bani yana a dakina don nan tabar shi ta tafi,
Don naki karba shine takai min mari nakuma naje na tare na juyo shine tafa saman glass din flower tafadi kasa,ta buge fuskan ta takara mikewa zata dakeni na rike mata hannu,
Kan shi yadafe yana fadin Innalillahi, Umma may nai maki haka kikeson ki kashe ni da raina,
Biba tace ta dade tana bani shawara kan nasan yadda nayi na mallake ka ka fita zancen Aisha saini kuma tace ko da ban fita ita zata dinga fita tana samo min magani tana kawo min,
Duk wani fitina da kaga inayi a gidan itace ke cewa wai kada na yarda ka maishe ni boran gidan ka,
Yace ya ishe ni haka Biba ya isa nace maki tace har yaran nan da aka haifa tace zata bani magani na shafa masu su lalace tun suna yara tunda bani na haife su ba,
Ido na ware waje nace su wa yan nan yaran da basu san komai ba za,a hada dasu,
Biba tace wallahi ta dade tana bani wai na shafawa Jidda da mimi su lalace, sai hafsat kawai zaka gani,
Yace Umma kin kashe ni wallahi Umma mai nai maki zaki min wanan sakaiyan haka Why Umma why me please,
Daki yamike yashige gwiwa ba karfi na mika mata yarta na ja yarana zuwa daki ina duban jikin su kamar ina son inga wani abu,
Nace Allah ga boyar ka Allah ka kare min yaran nan daga duk wani sheri kamar yadda kullun nake rokon ka,
Nidai nasan ban ma dan kowa sheri a duniya nan ba may naiwa Umma take bina da,wanan mugun alkaba,in haka,?
Kishi sai hausa kishi harda uwar miji tasaka a gaba kamar kishiyar saure, (fachala),,,
Bai fito ba kwantawa yayi abin duniya duk yafamay shi sai tunane yake barkatai kiran Ibrahim ne yashigo ga wayan shi ya kashe wayan gaba daya don yana son samun natsuwa a lokacin,
Tunane yake ashe abinda yasa ke nan in Umma tashigo sai ta,shiga dakin Biba tasan abinda take kullawa jinin shi kuma jinin ta,
Da akecewa tana fifita diyan Zarah da Asmau akan diyan shi yana take zancen ashe duk hakan gaskiyane bata son diyan shi da gaske,
Wata zuciya tace aiba diyan kane bataso ba kaine bata kauna kawai,
Yadade a kwance ya kulla wanan ya sance wancan har akai kiran sallah magriba ranan a gida yai sallah bai fitaba,
Nima ina dakina kunci da bakin ciki sun isheni a rayuwata sai kawai na yanke shawara nafita nabar mata gidan kawai shi yafi,
Tunda har kiyayya na ya shafi yara na za a salwanta min rayuwan su ga banza,
Wata zuciya tace min wawiya idan kin fita ma ai kin kara bada kafan ai masu yadda ake so dasu ke nan tunda bada,su zaki fitaba,,
Ita ko Biba tana dakin ta sai dariyan mugunta takeyi tana cewa in ke tsohuwar zamani ne nima ai yar zamani ne mu zuba nida ku wallahi,
Nagama da wanan saura wanan shegiyar mai zubin bozaye kuma kema ki shirya naki na tafe,
Sai bayan sallah ishai Ibrahim ya shigo gidan don yaga wani mataki Hamza ya dauka kan Biba din,
Ganin dakin a bude ga wuta yasa shi yin mamakin rashin daukan matakin da Hamza baiyi ba akan ta,
Sallama yake da karfi abinda yasa yaran fitowa suna mashi oyoyo Baban mu,
Tambayan su yayi ina babanku sukace yana dakin shu tunda ya doki mummy amarya,
Dakin ya nufa da,sallama yashiga dakin dan uwan nashi rai