Showing 51001 words to 54000 words out of 178785 words

Chapter 18 - Babu So Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

32873

shawarar kiran biyu daga cikin ƙawayenta da tafi aminta da su. Cikin sa'a kuwa dukta samesu, umarnin suzo gareta ta bada kai tsaye kai kace itaɗin haihuwarsu tai. Babu ko wanda ya musa mata saima tabbatarwa kafin mintuna shafiyar data basu zasu iso.
     Hakan kuwa akai, dan mintuna goma sha biyu bai gama cika cif ba Sima da Amal suka iso. Amal da Sima ƴaƴan talakawane fitik, sun haɗune da Fadwa a media. Komai tayi a shafinta na istagram cikin yabonta da mata Comments suke, idan wani ya zageta zasu haƙiƙice wajen kareta koda kuwa akan gaskiya aka zagetan. Waɗan nan garkuwa da suka dinga bata yasa ta fara kulasu har takai da sun haɗu a zahirin rayuwa. Da farko ganin su ba ƴaƴan kowa bane yaso sakata ja baya da su, sai kuma hakan ya gagara dan suna taka rawar gani a duniyarta ta yanar gizo sosai. Dole ta buɗe bakin aljihu wajen gyara su Sima ɗin ta hanyar siya musu kayayyakin sawa da kaisu wajejen gyaran jiki na manyan yara. Maimakon ƙananun man bleaching da suke shafawa saita ɗaurasu akan manyan harka masu tsada, dan ita Amal ma allura akai mata. Cikin ƙanƙanin lokaci ta canja musu rayuwa suka fara karo da manyan yara. Fadwa nada wasu ƙawayen bayan su Sima dan ita macece mai yawan kwashe-kwashen ƙawaye, ita da mafi yawan ƙawayenta sunyi matuƙar suna a media musamman tiktok a yanzu dake taka rawar gani a rayuwar yaranmu. Komai na rayuwar Fadwa da ƙawayenta a bayyane yake, duk inda zasu samo location ko baground ayi vedio bai musu wahalar zuwa koda a wajen kano ne. A ɓangaren lalacewa bazamuce dukansu a lalace suke ba, dan kuwa akwai wanda a cikinsu da yawa babu ruwansu da mazan inba a ɗan ɗauka vedio ba ko abota shikenan. Fadwa na ɗaya daga cikinsu, dan tunda ta tashi Shareff kawai take gani a idanunta da soyayya. Hakan yasa duk haɗuwar namiji ko kuɗinsa bai cika zama a gabantaba inba wani abun hanunsa take buƙata ba, tana samu kuma zata watsar da shi a wuce wajen. Duk kuma tanayi cikin taka tsantsan da Shareff baisan hakan ba. Hatta harkar media ɗinta Shareff bai sani ba kasancewarsa mutum da yafi damuwa da aikinsa fiye da komai, idan ka gansa a yanar gizo akan abinda ya shafi cigaban rayuwarsane ba kalle-kallen banza ba, sai ko ganin labarai masu muhimmanci da yafi ziyartar irinsu bbc koya zauna ya kalla a talabijin ma yafi masa sauƙi. Amma a wani lokaci Fharhan ya taɓa masa shaguɓe da tsiyar da Fadwa ke tsulawa a yanar gizon harya nuna masa wani vedio. Ransa ya ɓaci matuƙa duk da iyayensune suka matsa ya auri Fadwa tun baya kulawa haryaji ya fara sonta saboda son da take masa bana wasa bane. Sosai ya mata faɗa da gargaɗi harda barazanar barin rayuwarta inhar ya sake ganin wannan shirmen banzar daga gareta. Tayi kuka da alƙawarin dainawa a lokacin har sai ta baka tausayi. Daga haka bai sake bin diddiginta ba dan baida wannan halin sam ga waninsa, ya daiyi imanin yanda yay mata insha ALLAH bazata sakeyi ɗin ba. Sai dai kuma ba hakan bane, dan kuwa ko sati biyu kasa cikawa Fadwa tai saboda ta riga ta saba, amma tabi shawarar ƙawayenta ta samu Fharhan har gida tai masa cin mutunci da gargaɗi bayan ta gano shine ya nunama Shareff vedion. Daga haka ta cigaba da harkokinta sai dai cikin taka tsantsan. A ɓangaren shaye-shaye kam basa shan komai sai shisha da yaranmu suka maida fashion a yanzun, wanda ta koyane shima wajen wata ƙawar tata har su Sima suma suka koya a wajenta...
      “Baby Fady mike faruwa duk kin tada mana hankali?”.
    Amal ta faɗa cikin nuna tsananin damuwa da tashin hankali.
   “Miyema bai faruba Amal. Na tsaneta, na tsani yarinyarnan fiye da mutuwata amma Soulmate ya kasa fahimtar hakan. A yanda nakeji ALLAH zanfa iya kasheta ma....”
         Idanu duk suka zaro na tsorata da kalamanta. Cikin girgiza kai da tarar numfashinta Sima tace, “Kinga nutsu kimana bayani yanda zamu gane Please. Wacece? Miye haɗinta da mijinki kuma da har ya kasa fahimtarki?”.
   Maimakon amsa saita fashe musu da kuka. Hankalinsu sake tashi yayi, suka zagayeta suna lallashi. Sai da tayi mai isarta sannan ta fara basu labari. Da farko sun yabama salonta na kissing mijinta gaban Anam. Daga ƙarshe suka nuna tsantsar takaicinsu da biyema yarinyar da su Shareff sukai na yarda da wai taji ciwo.
    Sima tai murmushi tana kaɗa kai da taune lips. “Karku damu inada shawara, wadda nasan inhar kika bita Fady har abada yarinyarnan sai ta fita rayuwarki, nifa tun randa muka haɗu da itan nan a Saloon tare da shi nasan yarinyarnan ba ƙaramar ƴar bariki bace, sai da kika sake sanarmin haihuwar turai ce tashin can na ƙara tabbatar da e lallai hasashena nakan hanya ashe. To a wannan karon aurensa kike, dolene kiyi komai domin ki rabata da mijinki dama hanyar gidanki gaba ɗaya......”
      “Nifa wannan dogon bayanin naki ya isheni Sima. Dan ALLAH ki faɗa kawai ina saurarenki”.
   “Hhhh daɗina dake wutar ciki Baby Fady. Kwantar da hankalinki, indai dan wannan yarinyar ce mai kama da ƴar tsanar roba kisa a ranki zamaninta ya shafe a duniyarki zo muje daga ciki”.
     Bedroom ɗinta suka shige, suka shiga famfata tako ina. Sun ɗauka kusan mintuna arba'in kafin su fito fuskarta washar da murmushi kamar ba'itace a birkice ɗazun ba. Ganin har lokacin Shareff bai dawoba ta sakasu su gyara mata gidan. Duk da yanda ta sakasu aikin cikin bada umarni ya sosa musu rai haka suka zage suka hau mata gyaran lungu da saƙo, itako tana zaune a falo tana duba Comments na sabon posting da tai ɗazun a tiktok kafin su Anam suzo. Dan danan ko ina ya ɗau ƙamshi. Ta nuna musu jin daɗinta, amma duk da haka sai ta sakasu su mata girkin dare kuma tare da gyaro sashen Shareff. Kowacce da hanzari ta amsa ita zata gyara sashen Shareff ɗin. Hararsu ta shiga yi, sai dai kuma batare komaiba.
     Da sauri Amal ta waske da faɗin, “Na fahimci kowa girkinne bayaso, to muyi girkin tare aje a gyara can ɗin tare”.  Sima tace, “To hakan yafi kam”. Sai a lokacin Fadwa tai dariya da faɗin, “Duk zame-zamenkun dai sai kunyi, inba hakaba na fasa sayen ashoben Meerah ɗin”.
    Suma dariyar suka shigayi da faɗin ai ba'ayi hakaba duk zasuyi. Hakan kuwace ta kasance. Sukai mata girki tare da gyaro sashen mijinta batare da hakan ya dameta ba. Dan hatta bedroom da toilet saida suka gyaro masa. Tsakar gida kuwa dama maigadi ke sharesa fes shiyyasa da wahala kaga datti. Ganin magrib ta kusa ta basu kuɗin ankon datai alƙawari da cewa su tafi mijinta ya kusa dawowa bata bukatar ya dawo ya gansu. Basuce mata komai ba akan hakan sai dariya da sukayi kawai, tai musu rakkiya har gate suka wuce.

      Shawarar da suka bata ce ta sata goge duk wani ɓacin ranta har na rashin dawowar Shareff gidan har yanzu. Wanka tayi tare da tsara kwalliya mai ma'ana. Ta tsuke cikin wandon jeans da top da sukai matuƙar fidda ainahin ƙyawunta da ƙyawun sura. Kamar yanda gidan ke kamshi itama kamshin take bulalawa. Ganin yanda tai ƙyau saida tai ɗan shot video tare da bin waƙar da akafi yawan challenge akanta a yanzu ta ɗaura a shafinta na tiktok da istagram. Ita ɗin mai followers ce, cikin ƙanƙanin lokaci likes ɗinta suka fara hauhawa, video ɗin ya fara trending ko'ina kamar ita kaɗaice ke lokaci. Sosai farin ciki ya mamayeta damuwarta ta ƙara gogewa baki daya musamman da ƴan koranta na kusa suna koɗata da zafafan Comments. Yayinda masu kishi da ita da ganin ta fisu suka fara jefa Comments na baƙar magana harda masu zagi, a gefe masu gaya mata gaskiya na jeho nasu akan ya kamata ta rage yin video da ƙananun kaya da gashi a buɗe kodan igiyoyin aure dake a kanta a halin yanzun. Su Sima ne suka taƙarƙare wajen maida murtani ga masu irin wannan Comments da masu zaginta, itako sai ma ta kashe datar acewarta sai Comments ɗin sun taru zatazo ta duba....

      ★★★

   Ɓacin ran jin asalin abinda ya faru daga bakin Anam duk da bashi take faɗawa ba da tabbacin Fadwa ce ta kira Mommy ta sanar mata wannan Accident ɗin ya hanashi komawa gida. Dan ya tabbatar in har ya koma a yanayin da yake zai iya yanke mata kowanne irin hukunci da yazo masa a rai. A yanzu kuma baya buƙatar haka a garesu, dan bazai so ace daga yin aure sati ɗaya kwana biyar da tarewa hakan ya fara faruwa ba. Office ya wuce kai tsaye, inda Fharhan da Khaleel sukai mamakin ganinsa tunda sun san duk wani abinda zai iya kawosa office ɗin sun kai masa shi har gida ya duba.
       Ko gaisuwar da sakatariyarsa ke masa bai amsa ba, hannu kawai ya ɗan ɗaga mata duk da washe baki da take faman yi da tayasa murnar aurensa. Har ya kama handle ɗin ƙofar office ɗinsa zai shige ya juyo. “Bana bukatar kowa yasan ina nan ok”.
      “Yes sir”.
Ta faɗa cike da girmamawa a garesa. Shigewarsa yay harda murzama ƙofar key, bai zauna a cikin office ɗin ba ya shige ainahin ɗakin da yake gudanar da zane-zanensa. Har mafi yawan ma'aikata suka tashi babu ɗuriyarsa, Khaleel yaso shiga ya dubasa sai kuma ya fasa saboda tun bayan shigiwarsa ya biyo bayansa amma sakatariya ta sanar masa yace baya bukatar kowa. 
     Kiran sallar magrib ya sashi fitowa, shiru companyn alamar kowa ya tafi gida, sai masu gadi su biyu kawai dake gate. Nan ya tsaya yay salla tare da su a massallacin dake cikin company ɗin sannan ya fito. Harya ɗauka hanyar gidansa ya canja, gidansu ya nufa, sai dai kai tsaye a gate ɗin gidan su Anam yay horn, mai gadi ya buɗe masa ya shige.
 
        Duk suna falo gaba ɗaya zagaye da Anam dake faman rakin za'a gasa mata ƙafa da ruwan zafi. Taƙi yarda Mamie tai mata hakama aunty Mimi da suka dawo ɗazun. Amrah ce ta kira Abie, isowar Abie ɗin kusan dai-dai da shigowarsa, kusan su duka suka juya suna kallonsa da amsa masa sallamar da yayi. Cikin girmamawa ya rissina ya gaida Abie da Mamie, aunty Mimi ma suka gaisa.
     Tun shigowarsa ta ƙara ƙarfin kukanta, takuma ƙi yarda tako kalli sashin da yake. Haushinsa takeji sosai batare da tasan dalili ba. Takaici ya saka Mamie daka mata tsawa..
     “Wai wane kalar iskanci ne hakan Anam? Shin ke ɗin ƙaramar yarinyace da kowa zaita fama dake akan abinda zai amfaneki.....”
    Da ido Abie yay mata alamar tayi haƙuri, ta ɗauke kai da ƙoƙarin barin wajen cikin takaicin ƴar tata. Abie yay murmushi da maida kallonsa ga Shareff da ke faman daƙilar waya kamar bai san abinda ake a falon ba, sake kallon Anam ɗin yayi cikin sigar lallashi “Mamana to Yayanki yay miki ko?”.
       Da sauri ta ɗago tana girgiza kanta, “Garama kowa yamin akan shi yamin Abie”. Ta faɗa cikin zafi-zafi da share hawayenta. Amrah ta taɓe baki da barin wajen, yayinda aunty Mimi da Abie ke dariya.
     “To saboda mi baki son nashi? Bayan tun ɗazu muke nan ana fama dake ga ruwan har sun huce”.
        “Aunty Mimi nidai bana so ke kimun”.
    Aunty Mimi zata kai zaune Shareff da har yanzu bai nuna yasan mi suke ba ya dakatar da ita. “Aunty barta, a canja ruwan dai”. Babu musu Aunty Mimi ta bashi waje ya zauna, ruwan zafin ta ɗauka ta nufi kitchen. Anam kuwa ƙafarta ta shiga ja baya, sai dai ta kasa jan jikinta saboda table daya tokare ta. Shi dai bai kulata ba har aunty Mimi ta dawo da ruwan, Abie kuma dama yayi ficewarsa saboda wayarsa da aka kira. Ganin yanda ruwan ke turirin zafin ya ƙara ɗaga hankalin Anam, cikin marairaicewa take duban Aunty Mimi amma tai kamar bata gantaba itama.
      “Ni wlhy bana son naka!!”.
Ta faɗa da ɗan ƙarfi da son sake jan jikinta baya ganin ya amshi towel babba da ƙarami a hanun aunty Mimi. Babban ya ɗaura akan cinyarsa batare da ko kallonta yayi ba, ƙafin kuma ya saka ƙaramin a ruwan zafin, ƙafar tata ya kamo takai hannu zata rike, wani mugun kallon daya sata janye hanunta babu shiri ya watsa mata,
      “Idan hanunki ya sake kawowa nan saina ɓallashi shima kiyi jiyyarbaki ɗaya”.
   Kamar ta rushe da kuka takeji, sai dai tayi alwashin bazata bar hakan ta faruba insha ALLAH. Yana ɗaura towel ɗin daya naɗoma ruwan akan kafarta dake kan cinyarsa alwashin nata ya zama tarihi, dan da gaske kukan ta sanya musu mai ƙarfi tana ƙanƙame ƙafar aunty mimi dake kusa da ita tana matso masa towel ɗin daga ruwan zafi.
     Sosai yanda takeyi ɗin ke neman sakashi dariya, amma ya danne da ƙyar ya cigaba da daddana mata ƙafar a nutse. Ta haɗa uwar zufa kafin a gama, hatta da aunty mimi da tasha riƙo ta haɗa tata zufar dan ba riƙon wasa Anam tai mata ba. Su Amrah da kukan Anam ɗin ya sasu sake fitowa dole sun kasa daurewa sai dariya suke kwasa, aiko ta wawushi throw pillows ta shiga jifansu da shi. Duk yanda yaso daurewa kasawa yay sai da ya shiga layin ƴan dariya da Abie ma ya dawo yana yin tasa a gefe, Mamie ma dake a kitchen dariyar take kwasa  dan borin Anam dabanne dana kowa.
      Ba ƙaramin ƙuleta dariyarsa tayiba fiye data kowa, shi dai da baisan laifinsa ba bai bartaba sai da ruwan ya huce ya shafa mata man da aka bata a asibiti sannan ya saki ƙafar da kumburin har ya fara saɓewa, sai ga mutuniyar gyangyaɗi na ɗibar idonta. Da ɗan sauran murmushin da bai bar fuskarsa ba yake tambayar aunty Mimi ko taci abinci dan yana son tasha maganinta.
      “Inafa taci, tunda Aysha ta kawota fa takema mutane bore a gidan nan har sai da Mamie ta mata tas. Anam ɗin ya kalla cikin ido, babu zato hararar data wullo masa ta iso garesa. Da sauri ta kauda fuskarta dan batai tunanin zai juyo ba. Abie dake kallosu a gefe yace, “Bara na maidata ɗaki sai taci abincin acan kawai ta kwanta”.
      Dakatar da Abie ɗin yayi cike da girmamawa, dan bai kamata shi yana wajen ba yabarsa yay jigilar ɗaukar Anam ɗin. Cikin matuƙar zaro idanu da suɓutar baki Anam tace, “Wai Yayan ne zai ɗauke ni?”.
       Harara ya wurga mata, ta kauda kai gefe cikin ƙunƙuni take faɗin, “Ni dai ALLAH bana so, garama a nemomin wheelchair........”
    Ranƙwafowarsa kanta na shirin ɗaukar nata ya sata haɗiye abinda take faɗar da sauri tana ƙoƙarin zabura gefe...........✍


_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
0913484810_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107 ko



*_ALLAH ka gafartama iyayrnmu_*😭🙏🏽
[10/28, 11:42 AM] My Zafafa: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_18_*

..........Sosai idanunta ke faman marmari ga ƙwalla na ƙoƙarin taruwa a cikinsu.
      “Juwairiyya!! Wlhy! wlhy! daga yau na sake ganin yaron nan ko wani ya ɗaukeki a motarsa koya kaiki gida sai na miki mugun dukan da zaki kasa tashi, kuma ki koma gidana da zama stupid kawai”. Ya ƙare maganar da ture fuskar tata gefe.
     So take ta fashe da kuka amma tana ƙoƙarin son dannewa, sai dai hakan bai hana rawar jikinta bayyana ba. A tsawace ya sake faɗin, “Get out of my car! Kafin na marmashe ƙashinki anan stupid”.
     Da sauri ta ɓalle murfin ta fice tamkar mai jiran umarnin nasa dama. Yaja dogon tsaki da figar motar yay gaba, badan titi bane da sai ya bula mata ƙura, murfin ma sai da yay gaba kaɗan yaja abinsa ya rufe.
     Duk yanda taso ƙoƙarin danne komai hakan ya gagara. Dole ta samu wani dutse a gefen titin ta zauna ta fashe da kuka. Duk abinda kaga Anam ta zauna yima kuka lallai ya taɓata sosai, dan tsiwarta da giringiɗishi bai cika barinta maida abu serious ba, ga kuma yanayin rayuwar data tashi a ciki, ita kaɗai a gidansu sannan a ƙasar da kowa kansa ya sani kawai.
     Ring da wayarta ta farane ya sata share hawayenta ta daga dan tasan su Mamie ne, a kullum tana waya dasu a irin wannan lokaci da kuma in zata kwanta. Video call ne, dan haka ta shiga son ɓoye damuwarta da murmushin farin cikin ganinsu. “Good morning my sweetheart”.
        Dukansu babu wanda ya amsa mata, dan duk da ƙoƙarin da take na ɓoyewa idanunta sun tabbatar musu tayi kuka. Abie yaja numfashi a hankali yana sake kafeta da ido. “Mamana mi yake faruwa da ke? Waya saki kuka? Ko baki da lafiyar ne har yanzu? A ina kike nan?”.
      A karan farko ta saki murmushi dan jin tambayoyin mahaifin nata a jajjere. Samun kanta tai da kasa faɗar gaskiya duk da ƙarya ko ɓoye-ɓoye ba halinta bane, ta sake share hawayen da suka ciko mata ido tana murmushi, “Abie ba komai fa, kawai kewarkuce har yanzu ALLAH. Kuma a wajen aiki nake ban dai shigaba ka gani”. Ta juya masa wayar yanda zai iya hango gate ɗin wajen.
     A jiyar zuciya suka saki shida Mamie, kafin su shiga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login