Showing 48001 words to 51000 words out of 178785 words
ta fito, duk da ranta a ɓace yake saboda kiran da take jera masa yaƙi dagawa sai ta danne saboda shawarar su Sima da take hange mafita a gareta basai ta cigaba da tada jijiyar wuya a wajensa ba. Ta ɗanesa tare da maƙalƙalesa, ko kulada yanayinsa batai ba ta haɗe bakinsu. Ƙoƙarin janyeta yay yana kauda kansa kodan maigadi da yake da tabbacin zai iya hangosu amma ta hanashi damar hakan. Dole yay ta maza ya tura murfin motar da kafarsa ya ɗauketa gaba ɗayanta yay sasheta bayan ya raba bakinsu da ƙyar. A kujera ya zube da ita jikinsa, babu wani ɗaga kafa ta sake maida bakinta kan nasa. Baya buƙatar komai a halin yanzun, sai dai bazai iya ƙin bata hakkintaba koda ace faɗan doke-doke sukai indai ta nema zai biya mata, balle ma baya buƙatar haɗa wata matsala tasa ta waje da cisgunawa iyalinsa wannan alƙawarine ya daukama kansa insha ALLAH, laifinta kuma zai mata hukunci a lokacin daya shirya. Duk da babu wani karsashi tare da shi ita ke kiɗanta tana rawarta bata damuba, sai da ta tabbatar ta isar da saƙon da take bukata sannan ta barsa tana mai kallonsa cikin ido cike da so da kaunarsa.
“I love you my Soulmate”.
Idanunsa ya ɗan lumshe ya buɗe akanta. Batare da yace komai ba ya lakaci hancinta da yatsansa. Sai kuma ya ɗanbi falon da kallo. Ganin komai tsaf yaji haushinta ya ragu a ransa. Ya ɗan rungumota jikinsa da sumbatar hancinta. “Haka nake so na dinga ganinki k da gidan nan a koda yaushe”.
Kai ta jinjina masa tana murmushi da faɗin, “Zaka sameni mai aikatawa”.
“ALLAH yay miki albarka bari naje na ɗan watsa ruwa”.
“Kodai ka fara cin abinci”.
Ɗan kallonta yayi na wasu ƴan mintuna, “Sure baiyi ƙauri ba na yau?”.
“ALLAH bai yiba”.
“Okay muje”.
Duk da ba son cin abinci yake ba haka ya dinga turawa, dan babu makusa a girkin sai abinda ba'a rasa ba. Dan kawai ya bata ƙwarin gwiwar cigaba dayi kamar hakan ya yaba tare da saka mata albarka..
★★★★★
Kwanaki sun cigaba da shurawa Anam na samun lafiyar ƙafarta. Tun daga ranar dai bata sake ganin Shareff a ƴan dubiya ba. Sai dai takanji maganarsa yazo gidan ko su Amrah suce mata yazo. Dan kamar da gayya sai ya daidaici lokacin da bata falon yake zuwa. Bata damu ba, dan a wannan gaɓar bama ta buƙatar ganin nasa sam. Tana son ƙara zama nesa da shi dan tunanin da aunty Mimi keyi a kanta ya gushe har abada. Kwanakinta biyar ta take ƙafarta sarai ta koma zuwa aiki. Kullum takan shiga gaida matan gidan cikin gida kamar yanda Mamie ke jaddada mata. Sai dai kuma iyakar Mom da Aunty Amarya kawai take zuwa ta gaida bata shiga sashen Mommy dana Gwaggo. Wajen aiki kam tare suke fita da Khaleel, wataran ya dawo da ita wataran Yaseer ya maidota dan yanzu ta ɗan fara sakin jiki da shi ganin bai nuna mata wata alama data danganci soyayya sai abota kawai. Muzzaffar ma yasha gwada zuwa ɗaukarta a office ɗin amma taƙi bashi fuska sam, hakan yasa ya fara zuwa gida kai tsaye dan shikam dai yaga matar aure. Tun tana noƙewa harta ɗan fara sakewa saboda huɗubar Aysha. Sai dai duk da hakan taƙi yarda ta amsa tayin son sa. Tana dai saurarensa darajar Abbansa abokin Abie ne kuma abota mai ƙarfi tun ƙuruciya dan tare sukai secondary school, a yanzu haka kuma suna ɗan huɗɗar kasuwanci tare.
A haka kwanakin hutun Shareff suka cika, Maheer ma ya koma katsina wajen nasa aikin tun satin daya shige. Da farko Shareff baya zuwa gidan da safe sai ya taso aiki yake shigowa ya gaidasu. Sai randa yazo sallama da su aunty Mimi da zasu koma Malaysia saboda yara makaranta ya samu Yaseer ya kawo Anam gida. Kuma har cikin gida Yaseer ɗin ya shigo gaishe da su Mamie, a yanda suka amshesa da alama ba wannan ne ma farko ba kamarma ya zama ɗan gida. Komai baice ba, sai dai koda Yaseer ya gaida shi hannu kawai ya ɗaga masa, daga karshe ma ya miƙe ya fice batare da an kammala sallamar ba. Da kallo kawai aunty Mimi ta bisa tana ƴar dariya, Anam kam ta taɓe baki da sake maida hankalinta ga Yaseer tana dariyar maganar Amrah kamar ma bata san da Shareff ɗin ba. Dan koda ta shigo ta gansa a taƙaice tace “Yaya good evening” tai wucewarta. Shi kuma bai amsa mata ba sai hararar da yabi ƙafafunta da su dan kansa a duƙe yake yana daƙilar waya.
Washe gari da shi akaima su aunty Mimi rakkiya airport, daga can kuma yay wucewarsa office. Anam kuma suka wuce tare da Khaleel daya buga mata warning ɗin kar ta sake tabi wata mota zai zo ya maidata gida da kansa koda bai tashi aiki ba. Badai tace masa komai ba, amma ta bisa da kallon mamaki. Hakan kuwa akai, tun kan ma a tashi aiki yazo yana zaman jiranta, washe gari ma haka sukai haka har kusan sati biyu da su Mamie suka fara shirin komawa suma. Nan fa hankalin Anam ya tashi, ta dinga kuka da magiyar zata bisu Mamie tace bata isa ba. Daga ƙarshe tai mata kaca-kaca sannan ta dawo lallashi da nasiha. Haka tanaji tana gani suka tafi suka sake barinta a Nigeria ita kaɗai. Cikin gida ta sake komawar dai sashen Mom dan nasu gidan an rufe kuma, ranar haka ta yini sukuku kamar mara lafiya, da ga ƙarshe ma har zazzaɓin sai da tayi. Sai da Khaleel ya samo mata magani.
Su Mamie juma'a suka wuce, dan haka bata fita ko'ina ba sai monday tai shirin zuwa wajen aiki. A cikin ɗaya a dogayen abaya da Mamie tazo mata da su tai shirin, bayan ta saka kayan hidimar ƙasa a ciki dan sanyi takeji yau. A hankali ƙamshinta ke fita, ga black skin nata na shining exactly cikakkiyar ƴar Africa. Bisa matsawar Mom ta zaman yin breakfast da abinda take iya ci da Mom ta jura girka mata batare da gajiyawa ba. Kaɗan ma taci ta miƙe tana faɗin, “Alhmdllhi”.
“Badai ƙoshi ba?”.
Mom ta faɗa tana kallonta. Murmushi tayi mai sanyi tana jinjina kanta, dan gaba ɗaya ta zama wata sukuku. “ALLAH Mom na ƙoshi, yau kwata-kwata banajin cin komai ne”.
“Anjima fa zaki iya jin yunwa”.
“To Mom bara naje da shi office ɗin”.
Babu musu Mom ta juye mata a kula mai ƙyau. Sai da ta jira Khaleel yasha shayi shima sannan, fita yay akan ta samesa waje zai shiga ya gaida jama'ar gidan. Saboda kar yasata binsa zuwa gaida su Mommy da tun kan su Mamie su wuce bata zuwa gaida su, shiyyasa ta noke akan zata samesa a mota. Sai da ya fita da kusan mintuna huɗu sannan ta fito. Waige-waige ta shigayi a harabar gidan babu alamar motarsa, tasan yakan kaita waje wani lokacin, dan haka ta nufi gate idan ya fito kawai sai su wuce.
A wajen gate ɗin kuwa ta samu motar Khaleel tare da makanike, ta ɗanyi tsai tana kallon motar da tai fakin a kusa da motar Khaleel ɗin. Kamar tasan motar, sai dai ta manta mai ita dama yaushe ta taɓa ganinta.... Horn ɗin da akai ya sata haɗiye sauran tunaninta. Makaniken dake duba motar Khaleel ya ɗago yana kallonta “Hajiya kamar dake ake fa”.
Ba laifi yanzu kanta ya ƙara buɗewa da jin hausa fiye da yanda tazo, ta jinjina masa kanta kawai batare da tace komai ba. Da farko bataji zataje ba, sai kuma ta canja shawara da tunanin ko Yaseer ne ya ɓadda kama. Murmushi ta saki akan wannan tunanin tana nufar motar.
Yanayin sanyinta a tafiyar ya sashi kafeta da ido cike da nazari, gashi bayan murmushin dake fuskarta babu wani alamun nishaɗi ko farin ciki a tattare da ita.
Zuciyarta ta gama yanke mata shawarar Yaseer ne, hakan yasata nufar ɗayan gefen batare da neman sanin waye ba ta buɗe ta shiga cikin ƴar dariya tana faɗin “Lallai ma Yaseer, kana tunanin ɓadda kama zata sa na gaza gane k.....” Sauran kalmomin suka kasa ƙarasa fita a bakinta saboda ƙamshin turaren da sai a yanzu ta samu nutsuwar banbancewa. Da sauri ta juyo batare data ƙarasa rufe motar datai yunƙurin yi ba. Har cikin rai ta tsorata da katoɓararta, amma sai ta dake cikin son kame kanta tace, “Oh Yaya yi haƙuri, ALLAH nama zata Yaseer ne ina kwana!”.
Shiru kamar bazai amsaba, dan tunda ta shigo bai kalleta ba ko sau ɗaya. Idanunsa da suka surku da ɗan ja ya ɗago ya zuba mata. Ƙoƙarin dannewa da ɓoye tsoranta take a fili, ta kai hannu kan ƙofar da nufin buɗewa ta fice ko zata samu damar shaƙar iska yasa lock.
(Ya ALLAH, wannan mutumin zai iya cinyeni fa a motar nan wlhy gara na lallaɓa) ta ayyana a zuciyarta. Idanu ta marairaice kamar gaske ta ɗago tana kallonsa, “Yaya kayi haƙuri ALLAH ban san kai bane”. Motar yayma key batare da yace mata komai ba ya fisgeta har yana bulama bakaniken dake duba motar Khaleel ƙasa.
Sunayen ALLAH kawai take ambata a ranta dan tasan itakan yau sai romanta za'a samu a hanun mugun nan......
“Mina faɗa miki akan yaron nan kwanaki?!”. Ya faɗa a kausashe dai-dai yana hawa kan babban titi. Kallonsa tai fuska a dake, ta kuma ɗauke da sauri saboda tasa fuskar ma tafi tata dakewar. Cikin ɓata fuska da tura baki tace, “Toni Yaya bamfa san wa kake nufi ba ai”.
Komai baice mata ba, ya cigaba da driving nasa, sai da suka iso dai-dai wajen nata aikin yay fakin daga ɗan nesa. Da mamaki ta kallesa, “Yaya yanaga ka tsaya na.....?”
Rinannun idanunsa daya dasa a kanta ya sata haɗiye sauran maganar muƙut, tai ƙoƙarin ɗauke idonta ya hana hakan cikin tsareta da nasa da duk suka firgitata. “Ni kike faɗama bakisan wa nake magana akai ba.”
Da ƙyar ta fisgi idanunta tai ƙasa da su zuciyarta na bugawa da sauri saboda yanayinsa ya masifar tsoratata. Da sauri ta rumtse idanunta saboda jin yatsun hanunsa a kan haɓarta, ya ɗago fuskarta sosai tare da matsota garesa har suna iya shaƙar numfashin juna. “Buɗesu kona mareki!!”.
Buɗewar tai da sauri saboda kusancinsu ba ƙaramar rikitata yay ba, hatta shi kansa yana iya jin sautin bugun zuciyarta ta hanyar ɗagawa da ƙirjinta ke ɗanyi da sauri-sauri..........✍
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
0913484810_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107 ko
[10/28, 11:42 AM] My Zafafa: *_Typing📲_*
*_❤🔥BABU SO....!!❤🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_16_*
.........“Ita kuma f...”
Bai karasaba Abie ya bashi amsa da faɗin, “Mamana Juwairiyya (Anam)”.
“Woow masha ALLAH! Masha ALLAH. kace ɗiyar tawa ma ta girma ashe. Damma ƙaramin jiki ya ɓoye shekarun”.
Gaidashi Anam tayi batare data sake yarda ta kallesu ba, ya sanya mata albarka itama da mata sannu akan ciwonta tare da addu'ar samun sauki. Su Maheer suka amsa da amin, banda Shareff dake ƙoƙarin ciro wayarsa a aljihun wandon jeans ɗin jikinsa da kira ke shigowa. Saurayin ya karaso gabanta idonsa ƙyam a kanta ko ƙyafatawa bayayi. Ɗagowa tai itama ta kallesa. Ya kashe mata ido ɗaya yana sake faɗaɗa murmushinsa. Cikin ɗan rankwafowa da murya can ƙasa yace “Kona ɗaukeki da kaina”.
Kanta ta girgiza masa tana satar kallon su Abie da Shareff dake waya duk da idonsa baya kansu, amma abinda bata sani ba kunnensa sarai yaji masa abinda saurayin ya faɗa. Shima ɗan janyewa yay daga kusa da ita ya mikama Shareff daya gama wayar hannu. Fuska ɗauke da murmushi yace, “I'm Muzzaffar Abu Kalla”.
Cikin ido ya kallesa da ƙyau. Ganin su Abie a wajen ya sashi yarda ya mika masa nasa hanun kamar mai ciwon baki yace, “Al-Mustapha Muhammad Shareff”.
“Nice name and nice to meet you”.
“Same”.
Shareff ya faɗa a takaice yana janye hanunsa. Muzzaffar ya mikama Maheer shima suka gaisa. Hakan yayi daidai da fitowar Aysha. Itama gaidasu tai su duka cikin girmamawa. Shareff yace ta kama Anam su shiga ciki. Sai da yaga shigewarsu sannan shima yayma abokin Abie sallama ya shige batare daya sake kallon sashen da Muzzaffar yake ba. Ganin haka shima Maheer yay musu sallam yabi bayansa.
Kai tsaye sashen Mommy suka nufa saboda kiranta dake ta faman shigo masa a waya, duk da kuwa ya ɗaga na farko ya tabbatar mata suna ƙofar gida zasu shigo yanzun. Amma ta kasa haƙuri da tunanin suna raina mata wayone kawai. Da sallama suka shigo falon, har yanzu tana tsaye sai faman kai kawo take kamar an bata gadin kayan falon. Babu zato babu tsammani ƙarar lafiyayyen mari ya shiga bada ƙarar amsa kuwwa a illahirin falon. Maheer ya dafe kuncinsa wata azaba na ratsashi, wani ta sake kifa masa a ɗayan kuncin nasa. Cikin huci mai nuna tsananin ɓacin rai take nunasa da yatsa. “Wannan kaɗanne namaka daga cikin abubuwan dana tanada maka inhar rayuwarka bata nisanta da jinin Usman da Maryam ba anan gidan wlhy wlhy Maheer.....”
“A wane dalili rayuwarsa zata nisanta da jininsa data kasance dolensa kenan Nafisa?”.
Muryar Daddy da basuyi zato ko sanin yana biye da su ba ta karaɗe kunnunwansu, ya dakatar da Mommy dake ƙoƙarin juyawa ga Shareff da mutuwar tsaye ta samesa sakamakon marin da Mahaifiyarsu ta sakarma ɗan uwansa na bazata
“Nafisa! Wai miyasa akoda yaushe kike son nuna ƙarfin iko akan ƴaƴanki wajen wargazamin zuri'ata? To bara kiji, na rantse da ALLAH, daga ranar da tunanin ƴaƴanki ya fara sauyawa zuwa shiga hurumin zumincina da ɗan uwana ko iyalinsa kamar yanda kike ƙoƙarin yi, zan tabbatar da shigarki nadama irin wadda bakiyi tsammani ba daga gareni. Idan kuma kinaga bazan iyaba saboda ɗaga miki kafa danai na tsahon shekaru ku ku gwada aikatawa ku gani”. Ya ƙare maganar da nuna su Shareff cikin tsananin ɓacin rai tare da juyawa ya fice batare da ya jira cewar waninsu ba.
Daga ita har su da kallo suka bishi. Wani irin ɓacin rai na nuna kansa a fuskar Mommy. Ta watsama su Maheer wani mugun kallo batare data sake cewa komaiba itama tabar falon. Da kallon dai itama suka bita harta shige, Yaya Shareff ya sauke nannauyan numfashi da maida kallonsa ga Maheer, kafaɗarsa ya ɗan bubbuga alamar lallashi, dan fuskarsa duk tayi sayin yatsun Mummy.
Cikin ɗacin murya Maheer dake kallon yayan nasa ya ce, “Amma Yaya Mommy......”
Kai ya jinjina masa alamar baya son jin komai, ya ɗan ƙara bubbuga kafaɗarsa tare da ɗan hugging nashi ta gefe sannan ya fice. Maheer ya bisa da kallo....
Mommy da duk ke tsaye a bakin ƙofarta tana kallonsu tai ƙwafa. A ranta kuwa babu abinda take ƙullawa sai tabbatarma Daddy bataji maganarsa ba. Dan kuwa ko ana ha maza ha mata sai ta tabbatar da ƙiyayyar maƙiyanta a zuciyar ƴaƴanta ya jima baiyi abibda ya ɗauka alwashin ba. Iyaka dai yace ya saketa ko! To sai me, ko rabuwa tai da shi ta san yanzu Shareff da Maheer sun taka matsayin da zasu iya riƙe rayuwarta fiye da shi. Hussaina dake daga ɗakinsu tana sauraren komai itama ta ƙwalama kira, da sauri ta iso tana faɗin, “Gani Mommy”.
“Ki bimun Yayanku kiga ya tafine ko ya koma can gidan”.
“Okay Mommy”.
Ta faɗa tana ƙoƙarin ficewa. Maheer ma yabar falon, dan haka ta fita da saurinta sai dai kuma dole tayo baya ta ɓuya dan hango yayun nata a tare. Yaya Shareff na waya ne, sai Maheer tsaye a gefensa alamar jira yake ya kammala.
Wayar ya sauke bayan yayi sallama da Dr Jamal. “Miya faru kuma?”. Ya faɗa cikin kafe Maheer da idanunsa da launinsu ya canja gaba ɗaya. Shima Maheer ɗin kallonsa yake rai ɓace. “Ni zanje na ƙara duba Anam yanzu, dan bazan iya ƙinyin hakanba gaskiya”.
Wani irin murmushi da Maheer ya kasa bama fassara Shareff ya saki, sai kuma ya ɗago yana dubansa cikin ido “Brother be careful!”. Ya faɗa murmushin fuskar tasa na ɓacewa.
Da kallo mai ƙara harzuƙa zuciya Maheer ya bi Yayan nasa, dan tuni harya bar wajen ya nufi gate. Cikin dakewa itama Hussaina tazo ta wuce sa kamar aikenta akai, a mota ta samu Shareff, yana kwance cikin kujera idanunsa a lumshe, a can gefe ta ɓuya tana kallonsa, ya kai kusan mintuna goma a wajen kafin yayma motar key yabar anguwar. Juyawa tai ta koma gida, bata samu Maheer a inda ta barsa ba, dan haka takaima Mommy bayanan data aiketa. Jin Shareff bai shiga gidan su Anam ba yasa Mommy sauke nannauyar ajiyar zuciya, sai dai acan ƙasan ranta ta gama shirya makaman yaƙar su Mamie ta yanda inhar suka tashi tafiya sai sun wuce da ƴarsu wucewar da har abada bazata sake leƙo Nigeria ba balle ta raɓu mata ƴaƴa.
★★★
Duk da ta faɗama Mommy damuwarta hankalinta bai kwanta ba. Sai faman kaikawo take na neman mafita. Zuciyarta ce ta bata