Showing 81001 words to 84000 words out of 178785 words

Chapter 28 - Babu So Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

32822

garesa saboda baya son su Daddy suga kamar bai ɗauka shawararsu ba......
        A ɓangaren Mamie da Abie ma duk da wannan rana ta tilon ƴarsu tazo musu a yanayin da basu gama shiryata yanda suke so ba hakan bai hanasu kasancewa cikin ɗunbin farin ciki ba, dan albarkar auren suke nema mata ba wai tsarabe-tsaraben cikinsa ba. Fatansu ALLAH ya bata zaman kafiya da zuri'a masu albarka ita da mijinta. Suna zaune a ɗakin Abie da take barci suna kallonta fuskikinsu murmushi ya kasa sauka, ga ɗunbin tausayinta da ƙaunarta na ratsasu. Abie ya kauda kai gefe yana murmushi ganin Mamie na sharar hawaye, cikin son danne nasa dake ƙoƙarin sakkowa ya miƙe yana kai waya kunnensa tamkar zaiyi kira ya gudu a ɗakin......
        Ƙananun maganar da suka fara fitowa a bakunan mutane saboda jin yanda ɗaurin aure ya kasance suka fara yawaita a gidan har wasu a dangin Mommy ya fara isa kunnuwansu. Da yawansu mamaki suke nunawa jin yanda al'amari ya kasance dan su dai basu san da wannan aure ba. A cikin ƙanen Mommy da abin ta jisa tamkar saukar aradu ta kasa haƙurin shanyewa kamar kowa ta shiga neman Mommy. Da ƙyar ta samota a sashen gwaggo wajen tsoffi na ƴan uwa da ƙawayen ta da suka taru acan.
        “Ke ko lafiyarki kuwa Samira kika shigo mana kamar wadda take a rikice”. Gwaggo ta faɗa ganin yanda aunty Samiran ta shigo har tana cin tuntuɓe. “Gwaggo dole kike ganina a haka, wani mummunan labari nake jiyowa yana tashi a gidan nan dana gaza gaskatawa, Aunty dama akwai auren wata bayan Fadwa akan Shareff?”.
      “Samira ban son takale-takalen masifa ina cikin farin cikina wane aure kuma?”.
  “Humm aunty kenan, aure nawane aka ɗaura a gidan nan yau, kidai bincika dan yanzu naji anata ƙus-ƙus wlhy wai dama matarsa ce sai dai yau aka sanar.” A rikice Mommy ta kalli gwaggo, itama gwaggon kallonta takeyi baki buɗe. Cikin ƙarfin hali gwaggo tace, “Nifa sam bamma gane wannan soki burutsun nakiba wlhy Samira”.
       “Nima da nake faɗa mukun na kasa ganewar, inaga bincikawar dai kamar ya kamata kuyi”.
Suɓucewa plates dake a hanun Mommy sukayi, ƙirjinta na matuƙar bugawa da sauri-sauri. Fitt ta fito ɗakin Gwaggo na ƙwala mata kira amma bata juyo ba. A yanda ta fito ɗin yaja hankalin mutane da yawa suka shiga binta da kallo. Kai tsaye sashen Daddy ta nufa, sai dai koda ta shigo bata samu kowa ba sai kwanikan abinci dake barbaje alamar anci. Har bedroom ta leƙa, nan ma babu kowa a ciki. Da sauri ta shiga laluben wayarta dake cikin handbag ɗin hanunta da take tara kuɗin yinin bikinta dan yau takeyi, hannunta ma rawa yake, tadai samu da ƙyar ta lalubo number Daddy tai dailing. Sai da ta kusan tsinkewa ya ɗauka, babu ko sallama tace, “Daddyn Shareff wani shirme nakeji yanzun, nazo sashenka kuma baka nan?”.
Kai tsaye ya gano abinda taji ɗin, dan haka a dake yace “Ina waje tare da mutane, idan na shigo sai muyi magana...” ƙitt ya yanke wayarsa tana ƙoƙarin dakatar da shi. Tsananin tsoro ne da firgici ya ƙara saukar mata. Tabi wayar da kallo kamar zata gano Daddy ɗin a ciki. Kai ina bazata iya haƙuri ba sam, akalar kiran nata ta maida ga wani yayansu data tabbatar Daddy baya ɓoye masa komai dan abokinsa ne shaƙiƙi tun ƙuruciya. Bugu biyu ya ɗauka, tai ƙoƙarin shanye tashin hankalinta dan tasan saita lalama Yaya Awwalu zai faɗa mata abinda take bukatar. Bayan ta gaishesa yake cemata tayi haƙuri bai shigo ya mata an ɗaura aure ba wani uzirine ya taso masa amma zuwa anjima zai dawo gidan.
“A'a babu komai Yaya ai kai mai yine, yanzuma na kiraka ne saboda inji ko kana tare da abokin naka dan zuwa anjima ina son ka ɗan ƙarama Maheer faɗa kasan yaran nan da taurin kai, Shareff ya fisa haƙuri da biyayya tunda kaga shi duk aurarrakin nan zaɓinmu ne amma ko yau bai tada hankalinsa ba akai”.
Yaya Awwal yay ƴar garan murya irin ta manya da ɗan murmushi, “A'a karki damu shima zai kwantar da hankalinsa ai, kuma hankalinsa aiba ɗaya dashi Mustapha ba. Amma zan shigo ɗin insha ALLAH, yaya jikin shi Mustapha ɗin ma? Dan ina tambayar bangansa ba akace yana asibiti babu lafiya”.
“Eh wlhy zazzaɓine ya kadashi amma da sauƙi, inagama yau za'a sallamosa tunda ba'a kai amarya babu ango ba”.
A karon farko yay ƴar dariya mai sauti da faɗin, “Wannan gaskiya ne, ALLAH dai ya basu zaman lafiya da haƙuri da juna tunda duk gidane, sai dai dan ALLAH kiyita ƙara nusar dashi da tausarsa tunda su duka ƴan uwansa ne kar zuminci ya samu matsala azo ana hai hai babu daɗi. Gaba ɗayansu ɗaya suke a wajensa babu wadda tafi wata.......”
Tunda ya fara jawabin nasa na ƙarshe jikin Mommy ya hau rawa, bazata iya jin ƙarshen zancem ba dan haka ta yanke wayar. Hajijiya taji tana neman ɗibarta, a dai-dai nan Gwaggo da taga shiru bata dawoba ta biyota ta shigo. Salati ta saka da riƙeta da sauri. “Ke ko kina lafiya zaki kashe kanki Nafisa?”.
Kuka Mommy ta fashe da shi, “Gwaggo sun kasheni, wlhy sunyi a banza, har abada jinina dana Usman bazasu zauna a inuwa gudaba. Gwaggo na rantse yau duk masifar da za'ai a gidan nan sai dai ayi sai Shareff ya saketa, ni Muhammad zai cima amana, ni Muhammad zai yaudara ya zalunta.....”
“K wai miya farune kin sani a duhu?!”.
“Gwaggo aure fa suka ɗaurama Shareff da ɗiyar maƙiyana, wai ƴar gidan Usman. Kuma tabbas batun yau ba ma.”
“Ƴar gidan Usman?!!”.
Gwaggo ta faɗa a razane, Mommy bata amsa mataba ta mike fuu ta fito hanunta dafe da kanta dake juya mata. Gwaggo na ƙoƙarin tsaidata yanzu ma bata saurareta ba. kai tsaye hanyar gate tayi, Samira ta biyita da sauri. “Yaya! Yaya miya faru ne? Da gaske ne ko?”.
Bata iya bama Samira amsaba ta fisgi gyalenta tai waje, kasancewar anata ɗaukar ƴan biki da kawosu ta samu a napep. Daddy daya hangota da yake suna zaune a ƙofar gidan cikin runfa ya miƙe, sai dai kafin yazo har napep ɗin tabar wajen.......

★Tun ɗazun ya farka saboda zuwan gayyar abokansa da sukaje ɗaurin aure. Shidai kallon mamaki yake musu, dan baiyi tsamanin ganinsu haka da yawa ba a waje ɗaurin auren ƙanin nasa. Suko sai faman washe baki suke da tsokanarsa a sigar daya kasa ganewa dan kowa ya kasa fitowa fili yace wani abu saboda ganin Fadwa tare da shi. Ga kuma dama Dr Jamal ya rokesu kar suce komai anan Please. Basu wani jima sosai ba suka fita acewarsu zasuje cin abinci zuwa anjima zasu dawo duk da Doctor yace maybe ma zuwa dare su sallamesa. Bayan fitarsu Fadwa ta dawo kusa da shi. Ganin yanda tai kicin-kicin da fuska sai yaji wani iri, hannu ya miƙa mata alamar tazo, tai kamar zata noƙe sai kuma ta nufesa ganin yay mata alamar roƙo. Jikinsa ya jawota ya rungume, ya sakar mata sumba a gefen wuyanta tare da ɗaura kansa a kafaɗarta yay shiru. A hankali ta lumshe idanunta da haɗiye kukan dake neman ƙwace mata.
“Shii!!”.
Ya faɗa a hankali cikin kunnenta yana kai hannu ya tallafo fuskarta ya juyo da ita...... Burumm ta faɗo ɗakin kamar an jehota. Su dukansu sukai saurin kallon ƙofar, ganin Mommy ya sashi janye jikinsa cikin jin tsananin kunya, Fadwa kam wani irin takaici ne ya tsargi ranta kamar ta dannama Mommy zagi. Mommy kam da sam hankalinta bama yakai kan yanda suke ɗin ba ta jefa masa takarda da biro saman jiki......
“Rubuta mata saki uku yanzu-yanzun nan da manyan baƙi yanda iyayenta zasu gani da ƙyau bama ƙanana ba...”
Cikin tsananin mamaki da rashin fahimta yake duban mahaifiyar tasa. Yayinda ƙirjin Fadwa yay wani irin mahaukacin dokawa tamkar gagarumar aradu ta bada sautin fashewa. Ita dai tasan ita kaɗaice matarsa ai........
Takarda da biron ya tattara ya ɗauka, a hankali cikin muryar mara lafiya ya dubi Mommy. “First luv ban gane ba. Wazan saka?”.
“Shegiyar yarinyar da aka ɗaura maka aure da ita a ɓoye mana, inba hakaba zan tsine maka Al-Mustapha, tsinuwa mai muni kuwa da a duniya ko kai bazaka ƙara morar kanka ba balle waninka!!”.
A kusan tare zuciyarsa data Fadwa ta nema wantsalowa waje. Cikin rawar lips shi yay ƙarfin halin faɗin, “A...Aure kuma? First luv n... Ni aka ɗaurama aure??”.
Sake fusata ta tambayar tayi, cikin tsananin kaushin murya ta sake bashi umarni batare data amsa masa tambayarsa ba. “Bani da lokacin maka wani bayani anan, dan wlhy zan iya tsine maka Al-Mustapha. Da manyan baƙi cikin sakanni ashirin kacal ka rubuta Kai Al-Mustapha Muhammad Shareff, ka saki ƴarsu Anam Saki uku har abada bakai babu ita. Inko ba hakaba shinuwa zata tabbata a kanka bayan cikar waɗan nan sakannin”.........✍


*_🙆🏻Ni balki wannan jidali har ina. Wannan fa shine TA LEƘO TA KOMA!. Shareffuddeen zaɓin Mommy ko zaɓin Daddy?🤐🚶🏻._*
      



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

[11/3, 7:19 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_35_*


_ASSALAM ALAIKUM DEARIES ... BARKAN KU DA KOKARI .. KAMAR KODA YAUSHE. WANNAN KARON MA MUNA BARAR ROKON KU WAJEN TEMAKAWA CHANNEL DIN SUDEIS DAKE MANHAJAR YOUTUBE_

_YARO NE DAYA TASHI DA SON KARATUN ALQURANI ME GIRMA. YA KE KUMA KWADAYIN GADON ME SUNAN SA SHEIKH SUDEIS. DAN ALLAH A TEMAKA A DANNA MASA SUBSCRIBE. A KUMA YI VIEWING DA LIKING. A TEMAKA DA SHARING MA... JAZAKUM ALLAH KHAIRAN AS YOU DO...💕_

Assalamualaikum dear sisters and brothers.

Welcome to ummu sudais YouTube channel🥰
A channel where the Holy Quran is been recited from different Angles.
Click on this link and listen to the Beautiful recitation that will melt your heart
https://youtu.be/Lafgc749sK8

Your subscription to our channel is of Great important. Please help us grow our channel by subscribing and liking our videos fisabilillah.
Thank you so much

--------------------

..........Cak numfashin Fadwa ya ɗauke daga ƙirjinta, idanunta suka fara ganin duhu-duhu, tai baya luuu zata faɗi dan wani irin mugun hajijiyace ta lulluɓe ganinta da jinta saboda maganar tazo mata ne tamkar saukar nokiliya.... Laɓɓanta matuƙar rawa suke na alamar sonyin magana, amma bushewar yawun dake taimakawa maƙoshinta ya hanata damar hakan. Sai faman raba idanu take a tsakanin Mommy dake tsaye tamkar bajimar zakanya taga abin farautarta da Shareff da alamu suka nuna shima yayi ƙamewar wucin gadi ne saboda wani dalili na mamakin furicin Mommy ɗin ko wani abu daban da bata hasaso ba.....
     Shigowar Daddy ɗakin tamkar an jehosa ta maido Shareff a tashi sumar tsaywar jinin data riskesa tabbacin hasashen Fadwa, dan shima dai jinsa da ganinsa a take suka rabu da gangar jikinsa baki ɗaya, sai idanunsa ne kawai tsaye ƙyam akan Mommy na tabbacin bashi da maraba da sumamme.
        “Bazan hanashi bin umarninki ba, sai dai nima a nawa umarnin, wlhy! Wlhy! Wlhy!! Idan har Al-Mustapha ka saki Mamana! Nima zan saki uwarka dai dai da adadin sakin da ta sakaka ka rubuta!!.......”
    “Dana haɗa jini da Usman da Ai'sha gara na barka har abadan abidina Muhammad!!”. Mommy ta tari numfashin Daddy a tsawace.
“Okay fine! Haka kikace ko?. Kai Al-Musta..........” Shigowar Abba da Dr Jamal ta hana Daddy ƙarasa faɗar abinda ke bakinsa, sai dai wani irin mugun kallo da yake bin Mommy da shi, har cikin ranta yake ratsata, sai dai zuciyarta tayi bushewar da take jin zata iya ɗaukar koma minene daga garesa akan wannan auren da rabashi shine kawai samun nutsuwar ruhi a gareta. Gwaggo ta riƙo hanunta tana faɗin, “Altine kina lafiya kuwa? Kai Muhammadu karka sake cewa komai kumuje gida”.
       Mommy ta fusge hanunta daga riƙon da Gwaggo taimata. “Wlhy Gwaggo babu inda zanje sai Al-Mustapha ya saki yarinyar nan, dan bana buƙatar auren nan ya sake minti guda a kansa!!”.
        Dr Jamal da gaba ɗaya ya rikice cikin roƙo yace, “Dan ALLAH Mommy kiyi haƙuri, bara na basa sallamar sai aje gida wannan maganar bata nan bace ba”. Kafin tace wani abu Gwaggo taja hanunta suka fice, ganin shima Daddy ya fita ya sata yarda ta bita. Abbah ya kama Shareff shi da Doctor Jamal. Wata Nurse kuma ta kama Fadwa da har yanzu babu alamar ta dawo hayyacinta.......

         Sun sami gida ya gama hargitsewa shima. Dan Gwaggo Halima da komai yaje kunnenta gaba ɗaya ta haukace, sai zagin Abie take da tone-tone, dan waje ta fito tana faɗar maganganu marasa daɗi, Abie ya miƙe ya shige cikin gidansa, amma sai ta bisa har can. Jin zagi da tonan asirin yayi yawa Aunty Mimi ta kasa haƙuri duk da kowa ya santa mutumce mara faɗa da son hayaniya. Amma zagin mahaifiyarsu da Gwaggo Halima keyi bazata iya jurewa ba ta fara tayata. Cikin ƙanƙanin lokaci hayaniya mai tsanani ta tashi dan dangin Mommy irinsu Samira tuni sun shigo gidan suna taya Gwaggo Halima.
     Ran Daddy ya ƙara ɓaci, yayinda hankalin Abbah dana Shareff sukai matuƙar tashi su kuma. Da ƙyar Gwaggo ta hana Mommy shiga gidan, yayinda Dr Jamal ya taimakawa Shareff zuwa ciki, wasu mata kuma suka kama Fadwa da zuwa yanzun ta fara kuka sai dai babu uhhm babu uhhm-uhhm.
      Daddy kam daya faɗa gidan Abie lafiyayyun maruka guda biyu ya sauke akan fuskar Gwaggo Halima. Tamkar ƙiftawar idanu gidan yay tsittt, ya kuma sauke mata wasu biyun da suka saka zukatan mafi yawan mutane girgiza. Gwaggo Halima maiji da kanta, Gwaggo Halima babbar mace hamshaƙiya mai taƙama da tunƙaho da sunan mijinta da muƙaminsa koda a tsakkiyar cikin dangine, yau itace ake saukema waɗan nan marukan, dole ne gida yay tsit. Daddy ya ɗaga hannu zai sauke mata na huɗu Abie ya riƙe masa hannu. Cikin tsananin damuwa yake girgiza masa kai alamar roƙo. Ɗagowa Gwaggo Halima tai tare da ware hannu zata mari Abie taji an riƙe mata hannu tare da murɗesa. Abbah ne da wannan aikin, ransa a matuƙar ɓace tamkar bashi ba.....
“Ko'a mafarki kikai tunanin wannan kuskuren sai mun tabbatar da nadama a rayuwarki Halima!!”. Kalaman Abbah dake amsa sunan ƙani a gareta sukai matuƙar ratsa kunnuwanta dama duk wanda ke a wajen.
      Sosai fa gida ya ƙara harmutsewa da ruɗewa. Har hayaniyar ta saka Anaam dake barcin wahala farkawa. Tun farko ma Mamie ce da hankalinta ya tashi ta rurrufe windows yanda bazai kawo kunnen Anam ɗin ba, sai dai ƙurar data sake tashi a yanzu tafi ƙarfin ta farko. Da ƙyar aka fidda Gwaggo Halima dake cigaba da ɗurama Abie da Mamie da Aunty Mimi harma da su Daddy zagi daga gidan. Sai dai can cikin gidan ma Mommy ce ke borin sai Shareff ya saki Anam. Shiko ya shige bedroom ɗin Daddy ya kulle kansa sai faman dukan ƙofa take da tabbatar masa zata tsine masa.
       Yana jinta, sai dai baya gane mi take faɗa saboda hajijiyar dake juyawa da kansa. Yana zaune bakin gado hanunsa dafe da kansa hawaye na zirara akan fuskarsa. Tunda yake a rayuwarsa bai taɓa ganin makamancin irin wannan tashin hankaliba. Daddy da gaba ɗaya idanunsa sun rine da ɓacin rai ya fisgo Mommy dake faman jijjiga ƙofarsa tana jaddama Shareff ya buɗe kota tsine masa. Babu zato ko tsammani ya sakar mata nata lafiyayyun marin itama da iyakar ƙarfinsa. Dan tsabar azaba da firgita sai da ta faɗa kan kujerar dake daura da ita hannunta duk biyu dafe da wajen da ya maretan.
      “Muhammad ni ka mara?!!”.
“Idan kika ƙara cewa tak ma, zan iya miki dukan mutuwa ba mari kawai ba!!”.
Kalamansa sunyi matuƙar razana duk wanda ke'a falon. Sai dai shi a garesa babu ko gezau ya sake tabbatar mata ta hanyar faɗin “Idan kuma kinji ƙarya bismillah gwada na tabbatar miki!!”.
     Bakin kuwa tai shirin buɗewa zatai maganar dan zuciyarta ta rigada ta bushe Gwaggo tai saurin toshe mata shi, dan ita kam taga tsantsar wutar bala'in dake ci a cikin idanun Daddy irin wadda bata taɓa ganiba a rayuwarta. Duk yanda Mommy taso Gwaggo ta sakar mata baki taƙi, nanfa suka hau kokawa, sai dai ALLAH ya taƙaita abun a dalilin shigowar yayun Mommy maza da Abbah yay kiransu a waya harda wanda ta kira ɗazun taji komai a bakinsa da ƙanin mahaifin Fadwa.
      A tsakar gida dai ƴan biki masu gudun tashin hankali tuni sun fara zare jikinsu suna guduwa dama Magrib tayi, wanda kuwa zasu kwana anan da ƴan son ganin yaya za'a ƙare na zaune jugum-jugum, ƴan bani na iya kuma nata ƙus-ƙus. Fitowar su Daddy zasu wuce massallaci ya saka gidan ɗaukar tsit dan ko'ina akwai hasken wutar nefa, sai dai wasu basu daina magana ƙasa-ƙasa ba sosai musamman waɗanda ke'a ɗan nesa da su.....

Bayan sallar isha'i duk wani mai faɗa aji a gidan ya hallara a sashen Daddy ne. Dan hatta Anam da bayan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login