Showing 96001 words to 99000 words out of 178785 words
yana sauke ƙafafunsa dake kan centre table ɗin suma ya zauna da ƙyau. Duk Anam najinsu, amma tai biris abinta. Yay ƴar gyaran murya da sake zama serious, hakan yasa itama Anam ɗagowa ta dubesa. Bai yarda ya kalla kowaccensu ba, cikin bada umarni ya fara karanto addu'ar da MANZON ALLAH ya horemu dayi a yayinda wani zama ya haɗamu makamancin hakan, kafin ya ɗora da faɗin, “Ina son ku bani dukkan hankalinku nan.”
Babu wasa a cikin umarninsa, dan haka duk suka sake nutsuwa kowacce ta ajiye wayar hannunta, sai dai Anam bata canja daga yanda take zaune ba, dan taji daɗin zaman. Itama Fadwa dai tana yanda take ɗin sai muskutawa datai yanda zatafi sakewa da ƙyau.
“Da farko zan fara da godema UBANGIJIN daya haɗamu a ƙarƙashin wannan inuwa, hikimarsace hakan kuma rubutaccene daga taskarsa tun kafin zuwanmu duniya. Gaba ɗayanku ina horanku da bani haɗin kai na wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin gidan nan, ina kuma tuna muku tsoron ALLAH a cikin zaman da zamuyi. Ku dukanku matsayi ɗaya gareku a gareni, fatana ku cicciɗani da bani goyon bayan tsaida adalci a gareku. Ban yarda wata ta haɗa da shirka ko zalinci ba a wannan zaman, duk wadda tai hakan bazan yafe mata ba. Fadwa dake zan fara dan kece babba, duk da a shekaru na tabbatar zakuyi sa'anni koda tsiran zai-zama kaɗanne. Ki riƙe girman da ALLAH ya baki waje zaunar da adalci a gidan nan garemu baki ɗaya, kin fita sanin ilimin zaman gidan nan, kin fita sanin abubuwa akaina a yanzu zaki iya nusar da ita idan kikaga bata fahimta ba cikin sauƙi. Duk wata fitina da zata taso zan iya fara hukuntakine matsayin babba dan haka sai ki kiyaye”.
Cikin danne komai dake a ranta ta jinjina masa kai da sakin murmushi. “Insha ALLAHU zaka sameni fiyema da yanda kake so a gidan nan Soulmate. ALLAH ya bamu zaman lafiya”.
“Amin ya rabbi” ya faɗa yana maida dubansa ga Anam da duk take saurarensu. “Juwairiyya!”. Ɗago idanunta tai ta ɗan kallesa batare data amsa ba. Shima bai damu da amsawar tata ba ya cigaba da faɗin, “Ina fatan zaki bani haɗin kai wajen wanzar da zaman lafiya a gidan nan kema, sannan ki ɗauka Fadwa matsayin babba a gidan nan ku zauna lafiya, saɓanin hakan ba yana nufin zan hukuntata bane ita kaɗai, har dake zan haɗa domin matsayinku duk ɗayane a gurina. Abinda baki fahimtaba daya shafi gidan nan ko ni zaki iya zuwa gareta ta sanar miki”.
Kanta ta ɗan jinjina da faɗin, “Insh ALLAH”. A ƙasan maƙoshi.
“Bana son jin wani abu saɓanin abinda nake fata a gareku, dan yanzu ba da bane, a cikin gidana kuke ƙarƙashin ikona ku duka, zan iya ɗaukar kowanne irin mataki akan duk wadda ta shirya bani matsala ko raina ƴar uwarta. Mu dukammu jini ɗaya ne ku dinga tunawa da hakan a duk sanda shaiɗan ya bijiro muku da wani abu a zuciya ko wasu a cikin dangi. Dan na tabbatar a yanzu kowanne zai iya zama ashana da fetur ɗin cinnama gidana wuta adalilinku, kuma bazan amince ba, zan ɗauka mataki akan duk wacce ta bada wannan fuskar a cikinku da su wanda zasu iya kasancewa zagaye daku wajen haddasa min fitina” Bai jira amsarsu ba ya cigaba da faɗin, “Akan kwana, idan aka cire kwanaki bakwai miye tsarinku?”.
Anan dai Fadwa ce kawai ta amsa, Anam kam dai shiru tayi. Fadwa tayi matuƙar danne raɗaɗin da takeji ta maye gurbinsa da murmushi, “Ni dai a nawa shawaran Soulmate kwana bibbiyun is ok ai ko?”.
“Okayyy!”
Ya faɗa cikin ɗan jan y ɗin da maida dubansa da Anam, taƙi cewa komai, taƙi kuma yarda ta kalla kowa. Sai dai tana jin idanunsa masu kaifi a kanta, kanta ta sake duƙarwa da tura baki gaba dan ita kam kunya ma maganar ke bata, fahimtar hakan da yayi ya sashi ɗauke idonsa da faɗin, “Hakan yayi kawai. Duk mai girki itace zata ciyar da kowa na gidan nan abincin dare, zakuma muci tare anan. Na cire safiya da rana ne saboda mafi yawan lokaci ina fita da wuri, na rana kuma bana gida kowa zata iya ra'ayin kanta amma zata bama maigadina tilas. Sai dai a weekend zakuyi har na safe kamar dai gobe”. Ya ƙare maganar yana kallon Fadwa..
Sam hakan baima Anam daɗi ba itama, amma batai magana ba. Fadwa dai ta amsa masa da “ALLAH yasa haka shi yafi alkairi”. Ya amsa da amin batare daya damu da rashin cewar Anam ɗin ba dan yasan a komai yanzu baƙuwace dole suyi mata uziri na kunyar zaƙewa akan wasu abubuwan har zuwa sanda zata zama ƴar gida. Daga haka ya rufe taron da addu'a. Anam ta fara miƙewa da nufin tafiyarta dan barcine cike da idonta har goma saura...
“Bani yogurt ɗin”.
Ya faɗa cikin katseta da bada umarni yana ƙoƙarin canja chennal a tv. Bata da zaɓin daya wuce dakatawar duk da idonta har lumshewa sukeyi. Amma hakan bai hanata ɗan tura baki ba dajin kamar ta saki kuka. Miƙewa Fadwa tai tana faɗin, “To ni bari naje na kwanta, sai da safenku”. Ta ƙare maganar da matsowa ta ɗan sumbaci gefen fuskarsa kamar ɗazun sannan ta fice tanama Anam ɗin saida safe itama.
Sosai hakan ya soki zuciyar Anam, harta kasa amsa mata, ɗagowa yay ya ɗan kalleta yaga fuskarta kicin-kicin. Glass cup ɗin data cika da yogurt ɗin ta miƙa masa. Tsaii ya ɗanyi yana kallonta batare daya amsa ba, sai hakan ya ƙara tunzurata, ta ɗago idanunta dake cikin gilashi ta kallesa. Saurin janyewa tai tana ɗan yamutsa fuska. “Yaya dan ALLAH ka amsa zanje na kwanta barci nakeji”.
Bai amsa ɗin ba, bai kuma daina kallonta ba, saita sake dubansa a marairaice kamar zatai kuka. Ɗan murmushin daya tsaya iya laɓɓa ya saki batare data gani ba, amsa yay da sake maida hankalinsa ga television ɗin. Ƙara miƙewar tai yunƙurinyi.
“Ki jira na gama ki tafi da kayan”.
Ya faɗa batare daya kalleta ba. Ai kamar ta ƙwala kuka taji, amma sai ta koma ta zauna batare da tace dashi komai ba, jin sosai barcin na rinjayar idonta ta naɗe har ƙafafunta a kujerar kamar ɗazun. Kallonsa ya cigaba dayi yana shan yogurt ɗin da cin dubulan ɗin kaɗan-kaɗan har aka kammala hirar da yake kallo a tashar ta NTA da wani babban ɗan siyasa na jihar ta kano. Ya juyo da tunanin itama kallon take sai ya samu harma tayi barci. Kafe fuskar tata yay da kallo na wasu sakkanni kamar mai nazari, sai kuma ya kai hannu ya zare gilashin nata a hankali. Tashi yay ya fita, bai jima sosai ba ya dawo da keys ɗin sashenta a hanunsa ya ajiye...
Motsawa tai, taɗan buɗe ido kaɗan saita gansa dishi-dishi, da farko ta zata yanar barcin data fara ɗaukarta ce, sai ta rumtse idon ta sake buɗewa amma still taji raunin ganinta a bayyane. Cikin sauri ta kai hannu ta shafa fuskarta, jin babu glass ɗinta ya sata kai hannu ta fara laluben cinyarta zuwa kujerar, dan falon babu fitila mai haske ya kashe. Hanun ta janye da sauri saboda sauka da yay a gurbin da bashi tai hasashen kaiwa ba. Shiko tamkar bai jitaba yay biris. Cike da borin kunya ta sauka a kujerar tana ƙara duddubawa, saida ta tabbatar dai ba gani zatai ba sannan ta dubesa fuska a tsume, sai dai shakkarsa bai hana bayyana cikin tsumewar tata ba.
“Yaya MM gilashi na fa?”.
“Kin bani ajiya ne?”.
“Toni inma ban bakaba dai ai a falonka ya ɓata”..........✍
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/23, 10:16 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*
*_❤🔥BABU SO....!!❤🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*
https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718
*_44_*
...........Banza yay mata kamar baiji ba, sai ma ƙoƙarin mikewa yake bayan ya latse remote tv ya mutu. Ganin zai bar wajen tai saurin riƙo hanunsa dan in har ta bari ya wuce bazata iya kai kanta ko nan da ƙofar fita ba saboda da gaske bata gani da ƙyau a cikin duhu sai da taimakon glass ɗin.
“Yaya Please ka bani”.
Hanun nata ya kalla tare da ƙoƙarin juyowa, da sauri ta janye nata a yanayin jin kunyar aikatawa. Kafeta yay da idanu yana ƙarema fuskarta kallo kai tsaye, yayinda ita kuma ta kasa ɗagowa ta kallesan. A cikin ransa yake faɗin, (Fitsararriya ashe kinada kunya?). A zahiri kam babu alamar wasa tare da shi yace, “Muje ki kwanta”.
“Ina ɗin?”.
Ta faɗa cikin waro makantattun idanunta da mai kallo a haka bazai taɓa tunanin rauninsu ba saboda girma da hasken dake cikinsu tamkar wadda ke iya hango abinda ke faruwa a kilomita huɗu na gabanta. Gab da ita ya matso har tana iya jin saukar numfashinsa a fuskarta. Cikin magana tamkar mai raɗa “A inda kike?”.
Baya taso jan jikinta bugun ƙirjinta na daɗuwa amma sai ya hana hakan ta hanyar tokare hanun kujerar da take jiki da hanunsa. Duk sai ta daburce. Ture hanunsa tai da ƙarfi, tai gaba da nufin guduwa ƙafarsa ta nema taɗeta tai gaba zata faɗi ya riƙota, ɗan fisgota yay ta faɗo jikinsa, baima jira tako maida numfashi ba ya ɗauketa cakk ɗinta yay hanyar bedroom ɗinsa dan ya gaji shima kwanciya yake buƙata. Inko ya biye mata sai dai su raba hali. Watsal-watsal take da son ƙwace jikinta tana faɗin, “Ni wlhy ka saukeni bana so, bana son haka Yaya MM, ALLAH zan cijekaaa!!”. Ta ƙare faɗa da ɗan ƙarfin sautin daya sakashi direta a saman gadonsa da sauri.
“Kina da hankali kuwa? Fasan kunne zakiyi?”.
Mikewa tai cikin sauri da nufin barin masa ɗakin dan ita kam dai bazata taɓa yarda ta kwana a ɗakinsa ba, gidan nasa ma domin yin biyayya da iyayenta ne da son cimma burinta cikin sauƙi zaisa ta zauna har zuwa lokacin data ƙayyadewa shirinta. Bai hanata ba dan tuni ya zare keys ɗin ɗakin, sai ma toilet daya nufa cikin halin ko'in kula. Jin ƙofar a kulle ya sata juyowa da sauri duk da ba fes take iya ganin komai ba amma kasancewar da fitila tana gani fiye da acikin duhu. Sosai hankalinta fa ya tashi, dan abu ɗaya zuciyarta ta iya bijiro mata zaisa yay mata hakan, a gareta kuma shine abu na ƙarshe da bazata iya mallaka masa ba koda a yau zaice zai mata dukan da shine kawai abinda take shakka da tsoro tattare da shi. Haɗiye duk wani fargabanta tai tai tsayuwar sojan badakkare a jikin ƙofar tana dakon fitowarsa. Tsahon mintuna 6 sannan ya fito duk tana lissafa ta hanyar kallon agogon dake bangon ɗakin. Yi yay tamkar bai ganta ba ya hau zame jallabiyar jikinsa. Bayyanarsa a zahirinsa da ga shi sai boxer ya sata juya masa baya da sauri tana ambaton sunan ALLAH. Kayan barci ya ɗakko a wadrobe ya saka harda fesa turare kamarma bai ganta ba. Ya haye gadonsa yana faɗin, “Baƙya buƙatar kwanciyar ne?”.
Maimakon amsa sai ta fashe masa da kukan ƙarya. “Yaya dan ALLAH ka bani key da glass ɗina na wuce barci nake ji, ALLAH haka babu ƙyau, kuma kaina zai iya yin ciwo”.
“Idan kin so hakan kenan”.
Ya amsata yana jan bargo cikin halin ko'in kula. Kukan ƙaryar tata ta dakatar zuciyarta na mata zafi, sai dai hango keys ɗin a bedside drawer ɗin inda yake ya saka mata jin sauƙi, cigaba tai da tsaiwa a wajen har kusan minti ɗaya kafin ta nufi wajen cikin sanɗa da tunanin yayi shammatarsa ta warto. Tana gab da isa ya fiddo hanunsa dake cikin duvet ya ɗauke, rigarsa ya ɗaga ya ɗaura saman cikinsa ya maida bargon ya rufe. Ganin ta dakata daga yunƙurin tahowar ya ɗan buɗe ido yana kallonta a sigar da ita bata fahimci haka ba musamman saboda matsalar nata ido.
“Gashi anan ki ɗauka”
Kanta ta ɗauke idonta na ciko da ƙwalla na gaske a yanzun. Dan tsaf ta fahimci tarko ne ya kafa mata. Hannu tasa ta share hawayenta, sai kuma ta taka da baya-baya ta koma saman kujerar dake a bedroom ɗin ta zauna..........
★Tun barowarta sashen nasa ta kasa zaune ta kasa tsaye, sai faman kaikawo take hawaye masu zafi na kishin mijinta na ragargazar zuciyarta tamka irin kowacce macen da aka kawowa abokiyar zama, ba ita kaɗai ba, irinta da yawa sukan azaftu matuƙa da rashin barci da ƙunci a irin waɗan nan kwanakin bakwai da amarya takan samu matsayin na amarcinta. Kai wasu ma borinsu har yakan zarta natan, ga masu ƙarancin imani ma kwana suke shiryama zukatansu munanan abubuwa harma da masu aikatawa. To ita dai Fadwa saita kasance a jerin masu azaftuwar ƙuntatama kai da ƙiyasta abubuwa da dama da bai dace zuciya ta ƙiyasta ɗin ba ta kasance duk da su Aunty Wasila sun bata tabbacin hakan bamai faruwa bane ta kasa nutsuwa, sai dai babu tunanin mugunta ko shirka a ciki, ita dai kawai mijinta take hangowa da wata a yanayin da ita kaɗai ta sanshi.
Tsahon lokaci ta ɓata tsaye jikin window tana kuka da dakon kallon hanyar tsumayen fitowar Anam da mijinta, amma sai saɓanin hakan ne ya biyo baya, domin kuwa shi kaɗai taga ya fito zuwa sashen Anam ɗin, bai kuma ɗauki tsahon lokaci ba ya fito ya sake komawa nasa sashen. Neman zubewa tai ƙasa kuka mai cin rai na kufce mata dajin tsananin tsanar su Daddy da take ganin sun ƙulla wannan aurenne saboda basa ƙaunarta ita da mahaifiyarta dalilin asiri da Abie da Mamie da aunty Mimi sukai na raba kansu tamkar yanda a koda yaushe Gwaggo ke faɗa. (karku ga laifin Fadwa, a haka aka raini zuciyarta, a haka ta girma da ƙiyayyar waɗanda bata da wani tabbataccen laifinsu a zahirin rayuwarta, da yawa iyaye na kuskuren wajen ƙoƙarin fidda matsalarsu da ƴan uwansu ga ƴaƴansu, sun kasa gane hakan yanada matuƙar tasiri ga zukatan ƴaƴan, dan in har akai wasa su ƴaƴan zasu tashine da ƙiyayya mafi muni da tsauri ta waɗan nan ƴan uwan nasu koda ace su daga baya sun haƙura sun yafema juna ne. Shiyyasa mafi yawan zuminci ke ƙara lalacewa da taɓarɓarewa a zukatan kowacce zuria fiye da ƙyamatar kafurci. Tasirinsa ne a tsakanin *_Anam da Fadwa_* duk da suna amsa sunan jini ɗaya, amma tunda ba uwa ɗaya ta haifi iyayensu ba, sun ɗauki hakan babbar tazara da bazata iya basu wata ƙyaƙyƙyawar jituwaba sai ƙyara da hantarar juna kawai. Sai kuma ga *KISHI* ya ratsa, wanda yake zamtowa linzami na rasa imanin *MATA* da yawa a dalilin zafafawa, ko da sunada tabbacin bazasu iya canja ƙaddara ba).
A jiya kasancewar su Aunty Malika tattare da ita ya sama zuciyarta salama da ɗauke kaso mafi yawa na hankalinta, musamman da zuciyarta ta dinga ayyana mata Shareff a sashensa ya kwana. Amma yau ganin zahiri ya hanata nutsuwa balle fahimtar kanta da kanta a matsayin abinda bazai iya canjawa ba ko samuwar ikon hanawa tamkar kowacce mace irinta. Kuka taci bana wasa ba, wanda ya jata lokaci mai tsayi har kusan ƙarshen dare sannan barci ɓarawo ya fara rinjayarta. A hankali ta sulale akan gadon ƙirjinta cike da nauyi tamkar yanda idanunta ke tattare da nauyin barci. (Koma dai miye ta bani tausayi, mu ƙiyasta kammu a matsayinta bisa adalci na rayuwa. ALLAH ka bamu kishi mai sauƙi da bazai sakamu a nadama ba🙏🏻😣).
★A lokacin da Fadwa ke can tana kuka da tunanin kasancewarsu a tsakkiyar lambun fure mafi girman daraja a garesu ba hakan baneba. Anam ta jima zaune akan sofa barci na rinjayarta tsoro na fisgota, sai dai bata da wata mafita ko ƙwarin gwiwa saboda babu ɓarawo mafi iya sata kamarsa. Kujerar 1sitter ce guda biyu, hakan yasa bata samu gamsuwar kwanciyarba duk da ta naɗe dukan jikinta a kanta. Daga inda yake kwance yaka hango yanda take mutsu-mutsu tamkar magen data sha matsa a hanun mafarauta. Guntun murmushi kawai ya saki, akan laɓɓansa ya furta “Azababbiyar yarinya”. Yana lumshe idanunsa dake cike da barci. Kusan mintuna goma ya bata domin barcinta ya ƙara nauyi sannan ya miƙe a hankali ya taka gareta. Cikin dabara ya ɗagata gaba ɗayanta yakai saman gadon ya kwantar yana danne dariya. Shi baima taɓa tunanin tanada nauyin barci hakaba, hijjab ɗin ya zare mata sannan yaja mata bargo shima ya koma ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya. Tsakanin Anam da Fadwa bai san wanene yafi wani daru ba. Itama yaso zuwa sashenta yay mata sai da safe amma tsoron abinda zai tarar ya sakashi haƙura. Bai taɓa tunanin da gaske *MAZA* najin shakkar matansu a irin wannan lokacin ba, dan duk yanda yake jin kansa da mazantakarsa da ƙin ɗaukar shirme sai nauyi da kunyar Fadwa ke zagaye da jininsa duk da auren nasa yazo a cikin wani kashine da yasha banban dana sauran maza mafi yawa irinsa.
Numfashi ya furzar a hankali da juyowa gaba ɗayansa yana facing ɗinta, kallon fuskarta yake a cikin wani irin yanayi mai sanyi da zungurar zuciya, ya matsar da fuskarsa gab da tata tare da saƙala hanunsa saman jikinta ya rungumota a nasa jikin sosai, kamar wadda aka isarwa da saƙo ta buɗe ido, sai dai rashin ganinsa da ƙyau ya sata jan numfashi ta haɗiye tare da nasa da yake busa mata saman fuska. Jan jikinta tasoyi baya ya ƙara matseta.
“Yay......”
Kalmar ta kasa ƙarasuwa a zahiri tamkar yanda taso furtawa sai a cikin