Showing 93001 words to 96000 words out of 178785 words

Chapter 32 - Babu So Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

32819

ɗaukarta raini, sai dai a yanzu baya buƙatar wani tashin hankali dan haka baice komaiba yay ficewarsa. Sashensa ya nufa, ya ɗauka key ɗin mota da lap-top bag ɗinsa ya sake komawa sashen Anaam, har yanzu Mubarak na nan bai wuce ba, yana tsaye daga bakin ƙofa yace, “Ni na wuce office”.
     Ɗagowa tai ta ɗan dubesa, ganin fuskarsa babu alamar wasa ya sata shanye abinda ke bakinta, a taƙaice tace, “ALLAH ya bada sa'a”. A kan laɓɓa ya amsa mata ya juya ya fita. Miƙewa Mubarak yay shima, “Aunty Anam bara naje nima akwai aiken aunty a wajena kar taita jira”. Fuska ta ɓata cikin damuwa, sai dai batace masa komai ba ta gyaɗa kanta kawai. Tanaji tana gani ya fita ya barta ita ɗaya. Sai taji gaba ɗaya sashen ya mata girma da faɗi na rashin sabo, haka kawai kukan da taketa fatan kartayi ya kufce mata, sai da tayi mai isarta sannan tai zaman cin abincin da Mubarak ya kawo, tana kammalawa barci ya kwasheta a falon batare data shirya hakan ban.
        Cikin barci sautin mahaukacin kiɗa dake tashi a gidan ya karaɗe mata kunne, ta tashi a ɗan zabure tana dafe kanta daya sara mata, a dai-dai nan su Amrah suka shigo falon. Su duka kanta sukai suka rungumeta, cikin dauriya da jin daɗin ganinsu ta janye hanunta tana kallonsu fuskarta da murmushi. Aysha tace, “Uhhm su Blood matar Yaya Shareff, wlhy har kin canja dare ɗaya”.
      Kai kawai Anam ta girgiza tana hararta, Amrah ta kwashe da dariya ita da Husnah. Cikin salon ƙara tsokana Aysha tace, “ALLAH karkiji wasa blood, sai sheƙi kikeyi kamar hasken farin wata, ba kamar matar Yaya Maheer ba da muka tarar wujiga-wujiga da ita tana faman kuka”.
       Kafin Anam da zancen ya tsikara tace wani abu Husnah ta karɓe da faɗin, “ALLAH nima taban tausayi, kamar ma wadda bata cikin hayyacinta, daga ganinta zamuyi sa'anni da ita amma kamar bata da wayo sosai wlhy, ko ƴar 18years bazatai wannan sakaka ɗin nata ba ai balle ita”.
         Amrah da batace komaiba ta ɗan girgiza kanta, “Ni kam sai naga ba laifinta bane wlhy, kamar matsalar daga Yaya Maheer ne, kugafa yanda yaketa mazurai kamar ba shi ba. Anya kuwa auren soyayya sukayi sisters?”.
      Tsitt sukai lokaci guda kowa na nazarin maganar Amrahn, Anam ta fara furzar da numfashi tana faɗin, “Inaga kubar zancen nan haka dan ALLAH kamar zaifi. Wai shi wannan kiɗan daga ina yake fitowa?”. Aysha ce ta taɓe baki da jan tsoki, “Daga ina kuwa inba sashen aunty Fadwa ba, shaggun ƙawayen nan natane su Sima fa kamar a gidan. Halan Yaya baya nan ne ko?”.
      Kai kawai Anam ɗin ta jinjina batare da tace komai ba, ta kuma daƙile maganar duk da ta fahimci tana cin bakunansu. Basket ɗin da suka kawo ta jawo gabanta tana buɗe kulolin ciki, da haka ta ɗauke hankalinsu da zancen abincin babu wanda ya ƙara sakko maganar kidɗan dana gidan Maheer.

     Zuwansu ya matuƙar ɗauke mata hankali, da taimakonsu ta gyara ko'ina duk da babu wani datti, zuwa la'asar wasu daga cikin ƴan uwa danginsu Abie ɓangaren mahaifiya sukazo. kayan gara na fulawane da ƴan abubuwan daba'a rasaba suka kawo mata saboda baƙi da zasu ɗan ringa shigowa ganin ɗakin amarya, harda drinks mai ɗan yawa da ruwan roba. Sai lokacin sukaji sautin kiɗan dake tashi a sashen Fadwa ya tsaya, babu wanda yay magana suka cigaba da harkokin gabansu.......✍




_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/23, 10:16 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_42_*


.........Tsitt gidan ya koma bayan wucewarsu, sai ta sake komawa sukuku da ita. Cikin dauriya ta ƙarasa saka turaren wutar dasu Amrah suka fiffido mata da fresheners masu ƙamshi ko'ina ya ɗauki ƙamshi dama sannan ta wuce bedroom yin wanka. Koda ta fito shiri tai cikin doguwar riga mara nauyi ta ɗan gyara fuskarta da sakama jikinta ƙamshi ta tada sallar magrib. Bayan ta idar ne wani tsoro ya dinga tsikarar zuciyarta, dan shirun gidan yayi yawa matuƙa, sauƙin ma akwai wutar nepa dan anguwar suna samun wuta sosai. Bata damu da rashin ganin Shareff balle tunanin ya dawo gidan ko bai dawo ba. Tana nan zaune saman sallayar taji tsoronta na ƙara girma, sai ta ɗauka wayarta ta fara karatun alkur'ani a ciki.....

A daidai nan motar Shareff ta shigo gidan, a gajiye yake matuƙa saboda yau yayi yawo ne sosai cikin wani katafaren aikin babban estate da companyn su ke aikin ginawa. Yana China aka fara aikin, tunda ya dawo kuma ciwo ya kwantar da shi bai samu zuwa ya duba ba sai yau. Kai tsaye sashensa ya nufa, mamaki ya kamashi ganin ko'ina tsaf an gyara, ga wani ƙamshin turaren wuta na musamman na tashi ba irin wanda ya sani ba. Hatta da toilet ɗinsa tsaf yake sai ƙamshi ke tashi, ya ɗan saki huci wani kaso na gajiyarsa na raguwa dan shi mutumne mai tsaftar tsiya da kuma son tsafta. A gurguje ya zura jallabiya ya fesa turare ya fice massallacin anguwar tasu da ake ƙoƙari tada salla....

Tun daga shigowarsa ta farko har fitarsa a idon Fadwa ne dake leƙe ta window, taji matuƙar farin cikin ganin sashensa ya nufa ba sashen Anam ba. A ranta tace, (anya wannan amaryar kuwa ta cika amarya?) sai kuma ta bushe da dariya ranta fes, musamman data tuna sanda take cin nata amarcin yanda ya dinga nanan da ita kamar ƙwai. Amma sai gashi yau harda fita aiki bai kuma tashi dawowa ba sai yanzu. Gaskiyarfa su aunty Malika hayaƙi ba nata baneba, dole ta kwantar da kai taga da mi shegiyar ta shigo, shima kuma ina ya dosa... Falonta ta sake kalla taga komai tsaf ga ƙamshi na musamman irin wanda ta saka a sashensa na tashi, hakama jikinta babu wata makusa wando da rigar sun matuƙar amsarta. Ta sake sakin murmushi da ɗaukar sweet ɗinta mai ƙamshi ta jefa baki ta koma cikin kujera ta ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya tana daukar ɗan guntun bidiyo da zata poster a tiktok kodan maƙiya da suka tasota gaba da izgilin an mata kishiya a watanni biyar kacal.. Tana tsaka da editin ɗin bidiyon ya shigo falon da sallama. Da sauri ta fito daga tiktok ɗin tana ajiye wayar fuskarta da ɗan murmushi tace, “Sannu da dawowa”.
Sosai mamaki ya ƙara neman kashesa, dan kuwa ya jima baiga Fadwa cikin irin wannan tsaf ɗin ba ita da sashenta. Cikin ɗan salo ta tashi tsaye tana faɗin, “Soulmate wai mi kake kallo ne haka kamar baƙo a sashen?”.
A karan farko ya ɗan ware idanunsa a kanta da sakin guntun murmushi, kansa tsaye dan bai iya ɓoye-ɓoye ba yace, “Dama da gaske ne mata idan aka musu kishiya sunfi yin hankali da tattalin miji?”.
Duk da maganar ta mata zafi sai ta dake, cikin murmushi ta matso kusa da shi ta rungumesa. “Haba Soulmate kamarya? Da bana tattalinka?”. Hannayensa duka biyu yasa ya ɗago fuskarta ya riƙe a tafin hanunsa, yayinda itama nata hannayen ke zagaye da shi sun manne da juna. Kallonta yake cikin ido, kaifinsu na sake narkar da ita a soyayyarsa da ƙaunarsa harma da kishinsa mai tsanani, dan tasan mijinta irin mazan da mafi yawan mata basa kalla su kauda ido ne saboda abubuwa da yawa daya tara musamman miskilanci dake saka mafi yawan mutane shakkarsa har ita a karan kanta... A hankali ya hure idanunta, tai saurin rimtsewa ta sake buɗewa cikin nasa da har yanzu suke a kanta. “Da gaske kin canja, haka nake so ki kasance mai yawan kula akan komai my love. Indai kika riƙe zaki mallaki Al-Mustapha a tafin hanunki cikin sauƙi”.
Wani irin shauƙin daɗi ne ya ratsata, ta sake rungumesa da jin kamar su dawwama a haka. Lallai kwallin idonka idona ɗin nan yayi, cikin ƙanƙanin lokaci ga aikinsa kai babu abinda zatace da su aunty Safarah sai ALLAH ya biyasu. A hankali ya janyeta a jikinsa, da sumbatar goshinta. “Bara naje naga ƙanwarki itama, dan ina son na zauna daku yanzun nan”.
Kanta ta gyaɗa masa tana murmushin yaƙe, bai sake cewa komaiba ya fice ransa na ƙara sanyi da canjawar tata......

Bayan ta idar da sallar isha'i har shafa'i da wutirinta tayi, batajin wata yunwa dan haka ta yanke shawarar shan yogurt kawai da Mamie ta sakko a cikin drinks ɗin da aka kawo mata, fita tai da nufin ɗakkowa ta dawo bedroom ɗin, da tasha zatai kwanciyarta dan ita dama akwai saurin barci. Koda ta ɗakko yogurt ɗin sai ta haɗo da dubulan guda ɗaya dan tana matukar sonsa balle wannan da yasha riɗi da zuma mai ƙyau. Daga wutar falon har ta kitchen duk kashwa tai, sai dai kuma rashin sabo yasa ta manta da rufe ƙofar falon ta wuce bedroom, tamkar jira tana shiga ana ɗauke wuta, dai-dai nan shima ya ɗaura hanunsa a handle ɗin ƙofar falon nata ya shigo. Ƙarar data saki ce ta ratsa masa dodon kunne, karo sukaci a tsakkiyar corridor ɗin bedrooms ɗin nata, sai kawai ta zabura ta sake fasa wata ƙarar.
Da ɗan lalube ya samu ya riƙota a cikin duhun ya manneta da jikinsa da lalubo kunenta yana faɗin, “K! Calm down ni ne fa”. Yanda yay maganar cikin raɗa ya saka tsigar jikinta tashi baki ɗaya, ta sake ƙanƙamesa da sakar masa wani shagwaɓaɓɓen kuka.... Baice mata komai ba, sai dai yana shafa bayanta a hankali hawayen na sauka a ƙirjinsa duk da bata kai har can sama ba saboda rashin tsahonta, dan shi sai da ya ɗan ranƙwafo sosai ya samu rungumeta da ƙyau. Maido wuta da akai ne ya sakata haɗiye sauran kukan ta shiga sakin ajiyar zuciya, sai kuma kamar wadda aka cikara ta zabura ta janye jikinta... Bai hanata ba ya saketa, suna haɗa ido tai saurin juya masa baya tana tura baki gaba. Bayanta ya ɗan tsurama ido, sai kuma ya zagayeta ya wuce bedroom ɗin nata. Da mamaki ta wara idanunta da basu gani da ƙyau tana binsa da kallo dan batama san inda glass ɗin nata ya faɗa ba, “Wannfa ai shine ƙarfin rai mai sata da sallama” ta faɗa ƙasa-ƙasa tana harar ƙofar. (Ƙarfin hali ɓarawo da sallama bahaushiyar malaysia😹😜).
Bin bayansa tai dan taga mi zaiyi mata a ɗakin. A bakin gado ta samesa zaune da wayarta a hanunsa. (Ƙarfin hali....) ta raya a ranta da nufar glass ɗinta dake yashe a ƙasa ta ɗauka ta saka. Dai-dainan ya ɗago ya dubeta ya kauda kai. “Babu abinci a gidan ne?”.
Bata fahimci tambayar tasa ba, dan haka ta gagara cewa komai, sake ɗagowa yay ya dubeta yana ajiye wayar tata. “Baki jini bane?”.
“Ni ban san zakaci ba shiyyasa naba maigadi, naga da safe da aka kawo baka ci ba, na rana daya rage ne na bashi na kumace kar Mom ta aiko na dare”.
“Kin bani na safen ne da kikaga ban ciba” ya faɗa cikin kafeta da ido, kallo ɗaya tai masa ta maida nata ta rissinar dan wani irin girma da kwarjini ya ƙara mata. Sai taji gaba ɗaya tsiwar tata bazata yuwu ba. Shima ɗauke nasa idanun yay a kanta batare da ya damu da rashin amsawar tata ba ya ƙara jeho mata wata tambayar. “K mi kika ci?”.
Ƙasa-ƙasa tamkar mai tsoron a jita tace, “Zansha yogurt”.
Maida kallonsa yay ga yogurt ɗin da dubulan data ajiye a bedside drawer, dama ruwa ta tuna bata ɗakkoba ta shirya komawa ɗakkowa aka ɗauke wuta. Jin baice komaiba ta saci kallonsa, “Kaima na kawo maka?”. Ta faɗa ganin har yanzu idonsa akan dubulan ɗin.
Miƙewa yay batare da yace komai ba, sai da ya ɗanzo gab da ita sannan. Idanunsa a kanta kansa tsaye yace, “Ki kawo, ki kuma haɗo da ruwa”.
Raka bayan nasa tai da hararar gefen ido, cikin kwaikwayon maganarsa da umarnin nasa ta maimaita abinda yace tana ciccijewa kamar dai yanda yayi. Sai kuma ta taɓe baki ta matsa wajen hijjabin sallarta ta ɗauka ta saka sannan ta fito duk tunaninta yana a falonta yana jira. Sai dai koda ta fito wayam, babu shi babu alamarsa. Cikin mamaki tace, “Wai miye nufinsa? Nakai masa can sashensa ko mi? Hu'umm”. Mi kuma ta tuna oho mata sai ta murgiɗa baki ta nufi kitchen ɗin nata.....

Tun shugarsa sashen Anam tana laɓe tana leƙe ta wimdonta da kallon agogo, ganin ya wuce mintunan datai tsammani zuciyarta ta sosu, ƙwafa tayi cikin takaici da son danne abinda ke ranta tana cusama kanta huɗubar su Aunty Malika, koda ya fito jitai kamar taje ta kamasa da duka amma babu damar hakan, barin wajen window ɗin tai ta shiga bedroom, ƙara gyagygyara jikinta tai da ƙara turare ta ƙara kwallinta da jambaki sannan ta fito hanunta riƙe da wayarta ta yano siririn mayafi batare da tunanin basu kaɗai bane ita da shi. Cikin yauƙi da yanga ta nufi sashen nasa tana murmushin data aro ta yafa ma kanta.....
A dai-dai lokacin Anam da batasan akwai zama ba ta shiga falon nasa bayan tayi sallama da knocking ya bata izinin shiga. Zaune yake a saman 1sitter ya miƙe ƙafafunsa duka biyu saman centre table da lap-top akan cinyarsa yana aiki. Ɗan ɗagowa yay ya dubeta da amsa sallamarta ya maida kansa ya cigaba da aikinsa. Ta ɗanyi mamakin jin falon na kamshi yanzu kuma a gyare tsaf ba kamar ɗazun da safe data shigo ba, sai dai ba huruminta bane hakan sai kawai ta ajiye a saman centre table ɗin gefen ƙafarsa kaɗan. A niyyarta data ajiye ta juya ta fita, sai dai tana ajiyewar kafin ta ɗago Fadwa ta shigo da sallama...........✍




_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/23, 10:16 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_43_*


........Shine ya amsa sallamar tata, da ɗan ɗagowa yana kallonta. Ta ƙaraso zuciyarta na mata zogi irin wanda aka san kowacce mace da kishi ke saka mata. Amma sai ta dake ta sakarmasa murmushi kamar yanda shima yake mata. Ɗan sumbatar gefen fuskarsa tai da bashi side hug. Nanma murmushin ya ɗanyi da lumshe mata ido irin na godiya...
     Anam taji wani irin tsammm a jikinta, dan tunda aka kawota gidan sai yanzu ne suka haɗu da Fadwa, wani irin ƙululu yazo ya tokare maƙoshinta akan abinda Fadwa tai masa duk da bawai kallonsu take ba. Amma sai ta dake ta fasa ɗagowar datai niyyar yi, goran ruwan ta ɗauka ta ɓalle bakinta, ta tsiyaya rabin glass cup data haɗo da shi ta ɗago ta miƙa masa fuskarta a tsuke...
    “Gashi”.
  Idanunsa ya ɗago ya kalleta, tai saurin janye nata saboda haɗuwa da sukai cikin na juna, sai ta ɗan tura baki gaba jin ya haɗa hanunta da kofin duka ya riƙo, kafin ya zare kofin yana faɗin, “Thanks” a samman lips ɗinsa...
     Ta gefen ido Anam ta dubi Fadwa datai wani zaman ƙasaita tamkar bata ganta ba, lips ɗinta ta ɗan cija na kasa a ranta tana ayyana (Tabbas bana son mijinki bakuma zan zauna da shi ba. Amma kafin nabar gidan nan saina tabbatar miki zama birin wasana a tsakkiyar kasuwa kamar yanda nai alƙawari tunda naga haka kike buƙata) A zahiri kam sai ta saki lallausan murmushi, dai-dai ya gama shan ruwan ya miƙa mata kofin sai akan idonsa. Idanunsa ya ware da ƙyau yana mata kallon mamaki, amma saita kauda kamar bata gansa ba. “A saka yogurt ɗin?”. Ta faɗa a hankali kamar mai raɗa.
     Kallon Fadwa ya ɗanyi, ganin idonta a kansu itama fuskarta kamar da ɓacin rai amma ta dannesa da murmushi ta ƙarfin tsiya ya sakashi dubar Anam da itama tata ke bayyanar da murmushi har yanzun. “Bari na kammala aikin nan zan sha”. Ya faɗa yana maida kansa ga lap-top ɗin...
      “Okay” ta faɗa a taƙaice da komawa kujerar gefansa ta zauna, har ƙafarta ta naɗe zuwa saman kujerar, hakan ya bama zaman nata damar facing ɗinsa, amma saita maida hankali wajen buga game a waya kamar yanda itama Fadwa dake zaune ta ɗayan gefensa ƙafa ɗaya kan ɗaya itama kujera daban, hankalinta ke kan waya tana duba Comments na mutanenta.
     Aikin yake sai dai lokaci-lokaci yakan ɗan kalla kowaccensu ta gefen ido, dariya suke bashi, dan kowacce ta tsume ita a dole hankalinta nakan wayane bata damu da ƴar uwarta ba, amma a zahiri babu ɗigon walwala akan fuskarsa. Kusan mintuna 17 ya kammala abinda yakeyi, system ɗin ya ajiye da furzar da numfashi yana ɗan lanƙwasa yatsun hannayensa daya haɗe waje ɗaya. Kallonsa Fadwa tai, ta saki ɗan murmushi da faɗin, “Waldon sir!”.
      “Thanks you dear”.
   Ya amsa mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login