Showing 102001 words to 105000 words out of 178785 words

Chapter 35 - Babu So Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

32812

zuri'armu ba.....”
     Cikin tarar numfashin aunty Malikan tace, “Aunty wlhy nayi dukkanin ƙoƙarina, ban aikata wani abu saɓanin wanda kukace nayi ba”.
         Ajiyar zuciya aunty Malika ta sauke. “Haka nake sonki ƴa tagari, ki zama jaruma kuma jajirtacciya a gidanta bawai lusara ba. Kamar yanda na faɗa miki yanzu ba'a bin boka ba'a bin malam akan kishi, kissa da kisisina da magungunan mata sune takubban ƴaƙar kishiya musamman irin taki da babu abinda ta sani sai kauɗi da buɗewar ido a cikin masu jajayen kunne. Kafin duniya ta goge mata idanu ta hango abinda kikema sakaci ki jajirce ki ƙwaci mijinki da wannan damar inba hakaba dare zaiyi miki, dare mai duhun tsiya da tafin hanunki ma sai kin gagara gani balle hanyar ceton ranki. Dan haka yanzu ki tashi ki haɗa breakfast mai rai da lafiya irin wanda baki taɓa masaba, kije ki shirya musu a sashen nasa kamar yanda ya buƙata”.
      Hawayenta ta share, duk da sam wannan shawarar batai mata daɗi ba amma zata jure, dan ita shaidace taga alfanun danne zuciya a jiya, badan ta shanye komai ta maidashi ba komai ba Shareff bazai ko dubeta ba akan abunda ta dinga masa tun daga fara rikicin auren nan. Amma gaskiyar su aunty Malika namiji tamkar yaro yake, duk kunnasan da kai da zarar ka lulluɓesa da kwalba sai kaifinsa ya zama mara tasiri ya koma haska maka zuciya da hasken wutar daka kunna masan. Da layin barci da dauriya ta shirya breakfast mai sauƙi kuma mai daɗi tamkar ba Fadwa mai babbake abinciba. Maimakon ɗauka takai sai ta fara shiga wanka, tsaf ta shirya cikin doguwar rigar lass ta caɓa ado tamkar ita ɗince amaryar, ta baje jikinta da kalolin turarren da tasan yafi so da ƙauna sannan ta fice ɗauke da basket ɗin data haɗa komai cikin yauƙinta da iya taku...
         Fitowarsa da ga bedroom yayi dai-dai da shigowarta. Sanye yake shima cikin ƙananun kaya masu taushi da rashin nauyi yanata bulbula ƙamshi. Ta sakar masa murmushi da faɗin, “Good morning Soulmate”.
      Idanunsa ya lumshe da jinjina mata kansa, laɓɓansa shima da ɗan murmushin. “Morning dear! how are you?”.
      “Alhmdullh” ta faɗa tana kauda kumburarrun idanunta da yakema kallon tuhuma, tasan shi mutum ne mai saurin fahimta, amma zatai duk yanda zatai domin hanasa hakan a wannan karon. Hanunsa ɗaya dake cikin aljihun wandonsa ya zare dai-dai yana ƙarasowa gareta, ya amsa basket ɗin. Batai musun bashi ba. Cikin zolaya da cigaba da kafeta da idanunsa dake tsumata ya kashe mata ido ɗaya.
      “Ai da nasan haka zan dinga samun gatan nan a wajenki dana jima da ƙara aure gaskiya”.
   Har cikin ƙwaƙwalwar kai maganar nan ta soketa. Harta kasa ɓoyewa fuskarta ta canja, amma sai tai ƙoƙarin saita kanta ta hanyar maida abun wasa ta hararesa da juya baya kamar tayi fushin wasa. Basket ɗin ya ajiye ya rungumota ta baya yana ɗaura habarsa akan kafaɗarta da murmushi bisa fuskarsa. “Juyawa Shareff ɗinki baya yana nufin lalacewarsa matata. Amma da gaske wannan aure yamun ranar zama ɗan gatan Fadwa”.
         Ita shaidace bai iya ƙaryaba, ko tace baya ɓoye-ɓoye. Duk abinda ya fito a bakinsa koda mai ɗaci ne shine iya gaskiyar dake zuciyarsa. Ta sani tayi kuskure a baya na gazawar bashi kulawa, duk da taci matuƙar burin hakan a garesa kafin aure......
   Jan hanunta da yay ya katse mata tunani, ya zaunar da ita a kujera yana faɗin, “Kinga jirani anan ina zuwa”. Kafin ta samu damar tuhumarsa harya fice. Ta bisa da kallo zuciyarta na ƙuna har hawaye na ciko idanun nata. Duk da gargaɗinta da zuciya keyi haka ta miƙe ta nufi bedroom ɗinsa wai ko zata samu sauƙin ranta idan bataga alamar abinda take tsoro ba.....

       ★Da sallama ya shigo akan laɓɓansa idanunsa nabin ko'ina na falon da kallo, yayinda ƙamshin dake tashi ke masa maraba da amsa sallamar tasa. Samun falon shiru bai hanashi cigaba da kutsa kai ciki ba har zuwa bedroom ɗinta. Anan ɗin ma dai tsaf, sai dai babu alamar tana a ciki. Ya ɗanyi jimm na tunani sannan ya fito, falon ya dawo ya nufi hanyar kitchen...
     Tsaye take ta juyama ƙofa baya tanata kici-kicin saita sabon oven da take son ɗumama meat pie da take son yin breakfast da shi. Bluetooth ne a kunenta tana sauraren sabuwar waƙar mawaƙin nata da wata ƙawarta ta tura mata daga can malaysia, hargitsin bikin nan ya hanata zaman ji sai yau ta tuna da ita. Atamfa ce jikinta, wadda akaima ɗinkin fitted gown da yabi jikinta ya kwanta luff da fidda surarta matuƙa tamkar an zanata da pen, daga cinya zuwa ƙasa rigar ta buɗe matuƙa har tana zan ƙasa daga can baya. Bata cika son irin kayan nan ba, amma gargaɗin Mamie da nasiharta ana gobe za'a kawota ya sata daurewa ta tsara zata dinga sakawar insha ALLAH koda ba kullum ba. Bata iya ɗaura ɗan kwali ba, dan haka a maimakonsa saita kawo hula ta saka irin ta zamanin nan mai kama da ɗan kwalin. A jikinta taji tamkar ana kallonta, gabanta ya faɗi ta juyo da sauri dan dama dauriya kawai take na kasancewa ita kaɗai..........✍



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/23, 10:16 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_48_*


........Hannunsa daya ɗaga kamar zai mareta ya dunƙule, yanda ilahirin fuskarsa ta canja kammani ya matuƙar girgiza zuciyar Anaam amma ta sake aro jarumatar dole ta baibaye tata fuskar da zuciya da shi.
    “Ita ƙaddarar data kawoki, ita zata dawwamar dake a cikin gidan sai dai ki haɗiyi zuciya ki mutu! idan kuma k kin isa mara kunya ce ƙafarki ta taka ko gate mugani stupid girl”.
    Kafin ta samu damar cewa wani abu ya fice a ɗakin, hawaye ne suka cigaba da rige-rigen sakkowa a kumatunta, zubewa tai a saman gadon ta rufe fuskarta da tafukan hanunta. Taja tsahon mintuna tana kukan kafin kiran daya shigo wayarta ya katse mata shi. Amrah ce, kamar bazata ɗauka ba sai kuma ta ɗaga takai kunne batare da tayi magana ba. Daga can Amrah tamkar mai tsoron ajita ta fara faɗin, “Kina jina Anaam?”. A taƙaice tace mata eh kawai.
      “Ke kaɗai ce?”.
Cike da ƙosawa tace, “K dalla faɗi abinda zaki faɗa”.
   “Mtsoww! K daɗina dake masifa. Ina yarinyar na ƙawar Fadwa da muka gansu ranar da aka kai lefen Yaya Maheer?”.
         “Amrah dan ALLAH ki barni wane shirmene wannan?”.
“K Please karki kashemin waya maganace mai muhimmanci wlhy. Ina dai kin ganeta”.
    “Muje na gane, kamar Bibah suke kiranta”.
        “Yes! Exactly ita fa. Kin san yanzu ana tsaka da rigima a gidan nan kin san Mommyn su Yaya Shareff tana nan har yanzu tanata rikicin sai an raba aurenku, na fito daga gida zanje zan shiga cikin gidan kawai naga Bibah ɗin tare da Gwaggo da Maman Bibah a lungun mai shop ɗin nan, shine fa na lallaɓa naje kamar zan sayi abu a shagon, ki duba WhatsApp ɗinki na turo miki voice recording ɗin dana musu dan naga yanzu ma kin fini gane wani hausan”.
      Kamar Anaam zata gwaleta sai kuma tace mata “Okay” a taƙaice ta yanke wayar. Daga can Amrah bata damuba dan ta saba da halin Anaam tun suna yara, sai dai a yanzu ma ta fahimci kamar a cikin damuwa take dan muryarta da alamar tayi kuka.
      Taso share zancen Amrah ɗin amma sai yayta tsunkulin zuciyarta. Data ɗinta ta buɗe tare da shiga in box ɗin Amrah ɗin. Maganar ya ɗanyi ƙasa sosai, da alama ba gab take da su ba. Earpiece ta saka yanda zataji da ƙyau. Maman Bibah ce ta fara magana cikin alamun ɓacin rai.
    _“Amma ba haka kikai min alƙawari ba, kin tabbatar min idan shirinki na zubar da cikin nan na Fadwa ya tabbata da Shareff ya dawo zakiyi duk yanda zaki ya aure Bibah, sai kawai naji wai ga wadda ya aura, kin kuma ƙi saurareni tun ranar ɗaurin auren nan, na kira ta waya Gwaggo da kinji muryata sai ki kashe”.
      Da ɗan zafin rai Gwaggo ta amshe da faɗin, “Haba Luba, wace magana kikeyi haka. Kina zaton zan faɗi abinda bazan cika bane, ai ni na fara miki tayin haɗa Bibah da Mustapha saboda ganin dacewarsu, na kuma tabbatar miki kasancewar Fadwa a gidan bazai hanata shiga ba duk da ƴar uwa take a gurinta itama. To amma su Muhammadu sukai wannan sarƙa-sarƙar da kema kin san gwagwarmayar da aketayi na hana faruwarta. Ba yin kammu bane, kuma bamu san sun ɗaura auren nan ba. Amma ki kwantar da hankalinki, ni bana rama alkairi da sharri, Bibah kamar ta shiga gidan Mustapha ne ta gama. Yanzu dai kuje gida zanyi duk yanda zan a satin nan na leƙi gidan naku kinga wani zai iya ganinmu anan, kuma za'a iya zargin wani abu shiyyasa ma nace kada ku ƙaraso gida mu haɗu anan”.
      Mamaki, al'ajabi, ruɗani duk suka dirga a zuciyar Anaam lokaci guda, ba komai ta fahinta a zancen ba, sai dai maganar zubar da cikin Fadwa da su Bibah suka bata shawarar yi ta fahimci cewar Gwaggo ce ta sakasu su bama Fadwa shawaran kenan, sannan Bibah ma son Shareff take kuma Gwaggo ta mata alƙawarin samunsa matsayin miji duk da da wadda ta haifi mahaifin Fadwa, da maman Mommyn Shareff, da Kakar Bibah wadda ta haifi Mamanta da Gwaggo uwarsu ɗaya ubansu ɗaya. Kai kai kai wannan makirar tsohuwa da abin mamaki take, ta ƙyalƙyale da dariya dake tabbatar da ƙunar zuciyarta a bayyane. Cikin bushewar zuciya da cin alwashi ta jinjina kanta.   
        “Yes bazan tafi ba, amma Yaya badan kurarinka ba, sai dan koyama matarka da Mommy da aunty Halima hankali har da kai kanka a dalilin tsohuwar banza Gwaggo, yanzu na ƙara fahimtar matar nan itace take ƙulla komai dake a family ɗin nan tabbas. Zan tabbatar mata *Karen bana! Shike maganin zomon bana* kuwa..

      Bayan sallar la'asar sai gasu Amrah, tayi farin ciki da zuwansu matuƙa, musamman Ikram mai shegen surutu da bakinta baya shiru. Suka shiga buɗe kulolin abinci dake a falon wanda ita bama tasan da su ba, sai dai kai tsaye ta gane Fadwa ce ta kawosu tana ciki. Koda suka tambayeta ita ta dafa? Kai tsaye tace musu matar gidan. Amrah dai kasa ɓoye mamakinta tai sai da tace, “Wai kina nufin Fadwa?”.
      “Bayan ita akwai wata matar ne a gidan?”. Ta faɗa batare data kalli Amrah ɗin ba. Harararta Amrah tai da faɗin, “Banza kefa idan kina kan dokin zuciya ba'a maganar arziƙi dake”. Shiru Anaam ɗin tamata hankalinta na kan hotunan su Gwaggo da Amrah ta dauka. Dukansu ta tura cikin wayarta, daga haka suka cigaba da hira.
      An fara kiran sallar magrib Shareff ya shigo, fuskarsa murtik da alama har yanzu ransa a ɓace yake. Ikram ta sheƙa da gudu garesa dama tun ɗazun take tambayar yana ina Anaam ta mata shiru. Ɗaurewar fuskar ya ɗan sassauta yana shafa kan Amrah.
    “Autah yaushe kuka zo?”.
Hanunsa cikin nata tana murmushi tace, “Yaya tun around Four. Inata tambayar aunty Anaam kana ina? Taƙi amsani”.
       Kallonsa ya kai ga Anaam ɗin, anyi sa'a itama ta ɗago nata idanun a lokacin. Janyewa tai cikin salo tana ɗan taɓe baki, shima sai ya janye nasan yana ayyana (Zanyi maganinki ne) a ransa. Gaishe sa su Amrah sukai, ya amsa musu yana ficewa da basu umarnin tashi suyi salla. Bai dawo gidan ba sai da aka idar da sallar isha'i. Kai tsaye nan ya zarto domin maida su Ikram gida. Anaam jitai kamar karsu tafi, tai musu rakkiya har wajen motarsa, sai da taga ficewarsu sannan ta nufi komawa suka kusa cin karo da Fadwa.
      Kallon kallo sukema juna, Fadwa ta saki siririyar dariya tanama Anaam kallon sama da ƙasa. “Amarya! Amarya! Ta ango baƙya laifi ko kin kashe ɗan masu gidaaa hhhhh. Uhhm kamar haka ake kirarin ko?”. Tai maganar cikin sigar tambayar rainin wayo ga Anaam dake kallonta ita dai. Dariya Fadwa ta sake kwashewa da shi “Oh sorry amarya, ALLAH kina bani tausayi, dan ban taɓa gamo da amarya irinki ba ko'a hikayoyin marubuta. Dama tsiyar auren cushe kenan fa”. Ta ƙarayin ƴar dariya da matsowa gaban Anaam dake kallonta uwa ta samu tv ko bata fahimtar yaren da take magana da shi. Cikin yin ƙasa- ƙasa da murya murmushi shimfiɗe a fiskarta ta cigaba da faɗin, “Zan baki shawara ƙyauta dana tabbatar zatai miki amfani ƴar turawa, karki bari ki zubar da ƙuruciyarki da lokutanki masu muhimmanci a inda ko kallonki ba'a da bukatar yi, gara ki taimaki kanki, ki tattara komatsanki kibi tsoffinki ku koma inda kuka fito koda baki gama serves ɗin ba, koda yake dama mun san bashi akazo yiba neman miji akazo. Bokanku ya iya aiki tunda gashi kin samu ta hanyar cushe, sai dai kuma akwai matsala mai yawa dan basu jehoki gurbin daya dace ba, gara ki sani tun yanzu, wannan gidan sai ya zame miki tamkar kurkuku mafi muni da ƙuntata a rayuwarki, kina da zaɓin taimakon kanki ko cigaba da zaman cin kwakwa, AL-Mustapha Muhammad Shareff anyisa ne domin Fadwa Sadiq Dakata kawai”. Ta kare maganar da ƙyafta mata ido.
       A karon farko Anaam ta saki murmushi tana girgiza kai. “Hauka maganinka ALLAH, ke kuma sanyin da wannan yanayin yazo miki. ALLAH ya ƙara afuwa”. Tai gaba abinta.
    “Ubanki ne mahaukaci ƴar iska”.
Anaam ta cigaba da tafiyarta tana dariya batare data waiwayita ba. A falo ta zube maganganun Fadwa na dawo mata ɗai-ɗai cikin amsa kuwwa. Tabbas bata da burin yin dogon zango a zaman gidan nan, sai dai ya zame mata dole zaman a yanzu kodan kawo ƙarshen makircin Gwaggo, na biyu zata cika burin iyayenta akan zumincinsu da suketa ƙoƙarin ganin sun toshe duk wata hanya da zata wargazashi. Na uku Fadwa, dolene ta koyama Fadwa hankali ta kuma tabbatar mata sufa *Mata suna suka tara* lokaci shi zai nuna *Zarah*. Na huɗu Mommy, na karshe Shareff, zata tabbatar masa da cewar ita ɗin ba kanwar lasa bace, daga shi har matarsa sai ta goge musu hadda a cikin gidan nan...
      Ta saki murmushi a karon farko bayan ta kammala rubuta dukkan abinda ta gama lissafawa a cikin wayarta sannan ta mike. A dai-dai nan ya shigo falon da sallama ciki-ciki. Itama ciki-cikin ta amsa masa tana ƙara tsume fuska. Shima dai tasa fuskar a tsuke take, ya ajiye ledar hanunsa yana kallonta tamkar mai harara. “Shi wancan ɗakin da kika bari babu gyara waye zai gyara miki?”.
       Shiru kamar bata jisa ba, ya sake dubanta a harzuƙe.
      “Baki jini bane?!”.
    Baki ta tura gaba, cikin magana ƙasa-ƙasa da tunanin bazaiji ba tace, “Matar taka ta gyara maka mana”.
    “Tunda ita ta kwanar miki a ɗakin ko”.
Kallonsa tai, dan batai zaton yaji ba, ta kauda idanunta da sauri ganin kallon da yake mata. Ƙafa ta ɗaga da nufin barin masa falon cafka ɗaya ya fisgota ta dawo gabansa. Marmar ta farayi da idanu da ƙyaƙyƙyaftasu, ta fara mutsu-mutsun ƙwacewa ya murɗe hannun. Ƙaramar ƙara ta saki da ƙanƙame masa hannu ta fashe da kuka. “ALLAH zai sakamin, kuma wlhy komi kamin sai na sanar da su Daddy...”
      “Bakin ki bazai mutu ba kenan?”. Ya faɗa da ƙara matse hanun. Wata muguwar wawura ta kaima hanunsa ta ƙallara masa cizo a ƙaramin yatsansa..........✍




_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/23, 10:16 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_47_*



..........“Wayyo kaga kasa tayi fushi da abincin fa Soulmate”.
    “Ita ta sani”.
Ya faɗa cikin halin ko'in kula da cigaba da cin nasa. Fadwa zata cigaba da masa magiyar ya bita itama ya balla mata hararar. “Malama idan zaki ci naki kici bana son damuwa”. Shiru tai cikin kama baki kar kuma ƙaiƙayi ya koma kan masheƙiya. Har suka kammala breakfast ɗin babu wanda ya sake magana a cikinsu, sai dai cikin nishaɗi ta cigaba da cin nata a yanzu, amma a zahiri tayi kalar damuwa dan karya ramfota.

        ★★★

   Acan rijiyar zaki kam zaman lafiya yaƙi tabbata tsakanin Daddy da Mommy. Duk yanda kowa ke tausarta cikin ƴan uwanta akan ta nutsu abi komai a hankali amma fir ta nuna taƙi fahimta. Ita dai burinta kawai Shareff ya saki Anam. Babu kalar tujarar da su Mamie basa gani daga gareta, sai dai babu mai nuna yama san tanayi su dai fatansu zaman lafiya ga yarinyarsu. Babban abinda ke sake wutar tashin hankali a zuciyar Mommy shine rashin zuwan Shareff gidan, dan kuwa Daddy ya haramta masa sake zuwa gidan a yanzu har sai komai ya daidaita, kowa yasan yayi ne saboda Mommy ɗin. Gwaggo kuwa tunda ta nunama Mommy cewar ta kwantar da hankalinta zata nemo mafita, amma Mommyn ta murje idonta taima Gwaggo tas akan ita bata buƙatar wata mafitarta sai Gwaggo ta koma gefe ta naɗe hannu tai shiru, tayi tamkar ma bata gidan bata san borin da Mommy ɗin ke

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login