Showing 105001 words to 108000 words out of 178785 words

Chapter 36 - Babu So Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

32834

zubawa ba.
     Ba bori da tujarar Mommy bace kawai ke wanzuwa a gidan, harda Gwaggo Halima dake ganin ƴan uwan nata sunma ɗiyarta gudan jininta rashin adalcin raɓata kishi da ɗiyar ɗan uba. Itama dai bata da burin daya wuce ta ɗakko Fadwa ta dawo gida har sai Shareff ya saki Anaam sannan ta koma, sai dai baban Fadwa ɗin yay mata katanga da hakan. Hasalima ya bata sharaɗin ko gate ɗin gidansa ta taɓa da nufin fita a bakin aurenta da babu dawowa har abada. Dan shi mutum ne da dama baida wasa sam, badan haka ba da ya jima da zama mijin hajiya a gidansa saboda azabar Gwaggo Halima. Hatta da yaransa suna matuƙar shakkarsa, kuskuren da aka samu kawai shine siyasa ta kwashe kaso mafi yawa na hankalinsa har takai a yanzu bai iya saka idanu a kansu. Gwaggo Halima ta nutsu a gidanta cikin matuƙar tashin hankali da baƙin ciki, tasan ko giyar wake tasha bazata taɓa gangancin rabuwa da uban ƴaƴanta ba, domin yin hakan a gareta ba ƙaramin nakasu bane, shiyyasa ta nutsu a gida zuciyarta na mata zafi da raɗaɗi musamman naƙin jin Fadwa har a waya dan Abbansu yayi seizing wayar tata duk dan kar suyi waya, ya kuma hana har ƙanenta zuwa gidan Fadwan wannan shine dalilin da yasa a ƴan gidan su babu kowa a kusa da ita sai su aunty Malika dake matsayin ƙanne ga Abban nata.

        Yau ma dai kamar kullum tun bayan kai Anaam gidan Shareff da tujarar Mommy aka tashi gidan. Sai dai babu wanda ya kulata sai Gwaggo ce da tazo wuya ta fito tai mata tatas a tsakar gidan saboda ita kam dai haukar Mommy ɗin ya fara kaita maƙura. Tun Mommy na ƙoƙarin son nunama Gwaggo irin ɗaci da zafin da takeji a zuciyarta har tayi shiru ta koma kuka...
      “Gwaggo baki san irin zafin da nake ji bane a zuciyata wlhy, ji nake kamar na tsinema Shareff na huta. Ni yaron nan zai wulaƙanta a idon duniya ya nuna ubansa ne ya isa da shi bani ba!!”.
      “Ai taimakonki yay, saboda yin biyayya ga mahaifin nasa ne ya janyowa igiyoyin aurenki cigaba da wanzu har yanzu a gidan nan shi da Usman. Ban san mike damun kankiba Nafisa, ina wayonki ina hankalinki ne? Kinbi kin ruɗa kanki akan ɗan abu ƙanƙani da maganinsa ke'a hanunki cikin sauƙi.....”
          “Gwaggo taya zakice cikin sauƙi? Da'a sauƙine Shareff zai kai iyanzu bai saki yarinyar nan ba har zuciyata ta cigaba da ƙuna?”.
   “Kinbi hanyar da bazai saketa ɗinneba ai. Idan kin shirya cin nasara akan ɗanki sai ki nutsu ki dawo hayyacinki” ta ƙare maganar da miƙewa ta fice tabar Mommy da binta da kallo cikin rashin fahimtar kalamanta........

_________________________________

         Gaba ɗaya yau bashi da ra'ayin fita ko'ina, sai dai hakan bai hanashi yin wasu ƴan ayyuka ba ta cikin system ɗinsa. Zuwa yanzu babu kowa a sashen nasa, itama Fadwa tunda ta fita bata dawo ba. Shi kuma bai nema kowaccensu ba yanata harkokin gabansa har akai kiran sallar zuhur. Shigarsa bedroom ɗinsa domin ɗauro alwala ya sashi jan tsaki, dan yana nan a yanda suka tashi barci suka barshi. Har cikin rai abin ya sosa masa zuciya, yana da mace har biyu a cikin gida amma sashensa ya gagara samun shara. Ba yau ya saba ganin hakan ba, sai dai bazai yarda itama Anaam ta zama haka ɗin ba tunda yaga Fadwa ta fara gyara nata halayen itakuma. Jiya itace tai masa gyara, bazai yuwu kuma yau tayi ba bayan ba itace ta kwana a ɗakin ba.
      Koda ya fito sai da ya leƙa sashin Fadwa dan tabbatar data tashi yin salla kamar yanda musulinci ya koyar da duk magidanci na ƙwarai. Da mai-aikinta data dawo ya fara cin karo a falo, ta zube har ƙasa tana gaidashi. Hannu kawai ya ɗaga mata ya nufi bedroom ɗin Fadwa ɗin. Kwance ya sameta tana ramuwar barcin data hana kanta yi daren jiya, ya ɗan kafeta da ido na wasu sakanni kafin ya tasheta. Ɗagowa tai da ƙyar tana kallonsa cikin rufewar idon barci..
     “Tashi kiyi salla sai ki koma ki kwanta”.
   Da ƙyar ta iya amsa masa da to, yasan kaɗan daga aikinta yana fita ta koma, dan haka ya cigaba da tsaiwa a kanta har sai da ta tashi ta shiga toilet sannan ya fito. Sashen Anaam ya nufa, itama dai bai sameta a falo ba sai bedroom, saɓanin Fadwa ita kwancen kawai take amma ba barci take ba. Taji shigowar tasa amma taƙi ɗagowa ko sau ɗaya balle ta nuna tasan da wanzuwarsa. Tun a kallo ɗaya ya fahimci ba barci take ba, sai dai idanunta sun nuna taci kuka duk da suna a rufe dan ta cire glass ɗin.
      “Ki tashi kiyi salla”.
  Bata tanka masa ba, kuma bata motsaba ya juya yay ficewarsa. Idanunta ta buɗe ta raka bayansa da harara tana laɓe baki. Sai da yaja kusan mintuna uku da fita sannan ta tashi domin gabatar da sallar, a ranta tana addu'ar zuwan jininta a nan kusa.
        Bayan ta idar da sallar saman sallayar ta cigaba da zama tana sharar hawaye, buƙatar kasancewarta da iyayenta ce ke damunta. Abinda Shareff ɗin yay mata ɗazun a dalilin makircin Fadwa har yanzu yana cizon mata rai. Ta san tun farko dama ya tsaneta, taya bazai goya bayan matar son sa ba koda ace itace mai gaskiya. Itako ta ɗauka alwashin baza'ai nisa ba balle har su sami galabar ƙuntata shi da matarsa, a yau ɗin nan za'ayi mai yuwuwa ita ba shashasha bace...
      Yawaitar ƙamshin turarensa a ɗakin ya tabbatar mata shigowarsa, amma sai tai kamar bata jiba duk da taji sallamar da yayi ciki-ciki. Ta gabanta yazo ya gitta ya zauna a bakin gado ta kusa da ita kaɗan, dan ƙafarsa ɗaya ma akan sallayar take. Ido ya ɗan tsura mata na wasu sakanni, tayi kicin-kicin da fuska tamkar bata san da shigowarsa ba...
     “K kina ganin ba'a isa ace miki kinyi ba daidaiba kenan? To bari na faɗa miki matata ba abin rainawarki bace, a baya kunyi abinda kuke so k da ita, amma a yanzu bazan ɗauka raina juna daga kowaccenku ba. Dole ne duk mai buƙatar son zama lafiya da ni ta zauna da ƴar uwarta lafiya a gidan nan kuma cikin girmamawa da daraja juna!”.
     Yanda yay maganar a kausashe ya sata jin zuciyarta a wuya, hawaye ne suka shiga rige-rige sakko mata saman fuska, “Ni bance ina buƙatar zaman gidan ba ai, balle naima wata ƴar iska biyayy.....”
    Bummm ya buge mata baki da bayan hannu. Ba ƙaramin zafi ne ya ratsata ba, ta dafe bakin tana kallonsa da idanunta da sukai jazur ta cikin glass, sai dai babu hawaye yanzu a cikinsu sai tsantsar baƙin ciki da ƙunar zuciya. Ya miƙe tsaye yana nunata da yatsa. “Idan kin isa mara kunya a gidan nan ki sake yima matata ko kallon banza kiga yanda zanyi dake mara kunyar banza”
       Hawayen da take riƙewa suka ɓalle mata, ganin zai fice bata amayar dana cikintaba ta miƙe zumbur, “Idan na zauna kenan har za'ayi yadda za'ayin dani, inda kun kwantar da hankalinku ni dama banzo wannan gidan naku da niyyar zama ba, matar taka kuma wlhy tasa a ranta bashi taci, dan ni naci uwarta iya wasan data ɗau layin muyi, dan bata kai matsayin mace ba a wajena. Itace jaka da har take tunanin mijin nata wani abin a SO ne, ni baka cikin irin mazan dazan iya SO Yaya balle muradin zama a shi gidan, ƙaddara ce ta kawoni nan badan rasa masoya ba. Zan kuma barsa a yanzun nan bari na har abada, dan ALLAH kuyi kwaɗon juna ku cinye......”
         A wani irin mugun fusace ya juyo gareta, dan har ya saka kafarsa ɗaya zai fice a ɗakin batare daya kulata ba, sai dai kalamanta na ƙarshe-ƙarshe sun masa saukar mashi ne a tsakkiyar ƙirji. Ko ɗar bataji da yanayin nasa ba dan itama zuciyar tata irin tasance kuma a wuya take fiye da tasan. Kallonta yake da jajayen idanunsa da suke neman wargaza duk wani ƙwarin gwiwar ta amma ta dake.........✍     



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/23, 10:16 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_49_*


.........Da sauri ya saketa yana yarfar da hanun, tako kwashe da dariya ga hawaye sharɓan a fuskar. “Kaɗan ma ka gani indai nice Yaya”. Ta faɗa cikin riƙe ƙugu da murguɗa baki.
    Idanunsa da har sun kaɗa alamar cizon ya shigesa matuƙa ya ɗago yana kallonta da kaiwa zaune cikin kujerar dake kusa da shi. Ƙoƙarin barin falon tai tana masa gwalo, zamewa ƙafarta tai a dalilin turza carpet tai baya zata faɗi. Da ƙyar ta samu nasarar dafe kujerar da yake zaune, samun rinjayen jikinta a nasa ya tilasta mata zubewa kansa inba hakaba dole sai ta faɗin. Jikinta har rawa yake wajen son yunkurawa ta tashi ya sake saka ƙafa ya taɗota ta koma. Ya saƙalo hanunsa ta saman ƙugunta ta yanda bata isa sake ko yunƙurin tashin ba, fuskokin su gab suna shaƙar numfashin juna. Idanunta dake cikin gilashi ta shiga ƙyafta masa zuciyarta na wani irin bugu da sauri-sauri saboda bata taɓa tsintar kanta a cikin irin wannan halin tare da namiji ba bayan shi, ta sake yunƙurin tashi gaba ɗaya dan kunya ta gama dabaibaye rayuwarta bakinta cike da tsiwa tana motsashi sai dai bayajin abinda take faɗa. Ƙafarsa yasa ya sake harɗeta da manneta da jikin nasa dai-dai lokacin da Fadwa ke ƙoƙarin shigowa falon ɗauke da ƙaramin basket a hannu, cak numfashinta ya tsaya, sallamar datai niyyar rangaɗawa ta maƙale a maƙoshi.
      Idon Anaam yaga Fadwa sarai, dan haka ta dakata daga yunƙurin tashi da takeyi duk da tsumar da jikinta ke mata, shiko da bai lura da Fadwan ba saboda baya ya bata kaɗan sai ya kamo haɓar Anaam ɗin tare da sake matso da fuskar tasa gab da tata. Ya ɗan ɗage girarsa ɗaya a sama yana kallonta cikin tsakkiyar ido.
     “K bakin ki bazai taɓa mutuwa ba ko?”.
      A salon da yay maganar ba ƙaramin tsargawar zuciya ya saka Anaam ba, sai dai tai matuƙar daurewa wajen tura masa bakin nata sabida tunawa da Fadwa a wajen. Lips ɗin ya ɗalla da ɗan yatsa, babu shiri taja kanta baya da ƙoƙarin dafe bakin ya hana hakan ta hanyar buge hanun ya ɗaura nasa lips ɗin akan nata. A matuƙar bazata abin ya zomata. Cikin tsumar jiki ta ƙanƙamesa zuciyarta na luguden daka a ƙirjinta tamkar zata wantsalo dan wannan shine second kiss nata a tsayin rayuwarta duk da kuwa ta kasance girman cikin jajayen fata. Ko saurayi irin na school ɗin nan Anaam bata yarda tayi koda ance ana sonta, sai takai ma tsiwarta da rashin ragowa yasa matasan samarin makarantar tasu na shakkar tararta da abinda ya shafi soyayya, kaɗan daga aikinta ta maka tatas a gaban kowa ita ba ruwanta, hatta da ƙawa ɗaya gareta itama dan hali yazo ɗayane shiyyasa suke shiri, dan itama fitinanniya ce ta bugawa a bangon class. Hakama data shiga jami'a bata shiga sabgar kowanne namiji duk nacinsa kuwa inba akan abinda ya shafi karatu bane ba.
       Ta kowanne ƙofar jininta saƙonsa shiga yakeyi jikinta, ya kashe dukkan wani sauran kuzarinta da yunƙurinta, sai da ya barta dan kansa ta samu damar kife kanta a ƙirjinsa tsigar jikinta na tashi, shekara ashirin da uku ba shekara sha uku bace, itama mutum ce tamkar kowa kuma lafiyayya dake samun ingantaccen abinci mai gina jiki, ga kwanciyar hankali, giɓin rashin mahaɗinne kawai tattare da ita dama. Samuwarsa gareta a halin yanzu kuwa tamkar motso mata dukkan abinda ke ɓoye a cikin jininta ne ko tana so ko bata so.. Hannayensa duka biyu ya ɗaura a saman bayanta, tare da kai bakinsa saitin kunenta murmushin dake ta ƙoƙarin son bayyana kansa a fuskarsa na ƙoƙarin kufce masa.
       “Daga yau da wannan zan dinga punishment ɗin bakin rashin kunyar tunda shi idan aka faɗa sai ya maida”.
     Janye kanta ta rinkayi dan yanda yake maganar a cikin kunenta da busa mata numfashi sai yake neman sake hargitsa mata lissafinta. Nasarar janye jikinta ta samu ta silale ƙasan kafafunta, shiko ko'a jikinsa, sai ma umarni daya bata cikin kame murya.
          “Malama tashi ki bani abinci, muje kuma ki gyara bedroom ɗin can yau komin dare”.
     A yanda take kai a kife cikin cinyoyinta ta gallaro masa harara da murguɗa baki, sai da taja wasu sakanni sannan ta miƙe bisa shawarar zuciyarta, dakewar kuwa tai itama, tai kicin-kicin da fuska ta kuma ƙi yarda tako kalla sashin da yake. Bataga Fadwa ba yanzu, da alama tuni taba kafarta abinci. Haka kawai taji murmushi ya suɓuce mata ta ɗan harari ƙofar tamkar har yanzu tana a wajen ne. 
      Fuskarta a gefe tace, “Nifa banda abinci anan”.
   Ɗan dagowa yay daga latsa wayar da yake ya dubeta, sai kuma ya dubi ledar daya shigo da shi ɗin wadda yasan sarai itama ta gani ɗin. Sake maida kansa yay ga wayar batare da yace komai ba. Jitai kamar ta makesa dan duk tana kallonsa ta gefen ido, batare da ta sake magana ba ta ɗauka ledar ta nufi kitchen tana kwaikwayon yanda yay magana cikin bada umarni shi a dole mai kame girma bayan ya gama tsotse mata baki.
       Bayan wasu mintuna ta dawo da abinda ke cikin ledar cikin plate data juyo sai ruwa da lemo da cup duk ta haɗo a saman tray. Ta ajiye a saman centre table batare data yarda ko sau ɗaya ta kalla sashen da yake ba. ALLAH ya sota ma waya yakeyi, takoyi wuff tabar wajen. Da kallo ya bita harta shige, ya ɗauke kansa da ɗan furzar da numfashi yana cigaba da sauraren Fharhan....

        ★Gaba ɗaya brain ɗinta kusan daina neman yin aiki tayi, kukan da take sonyi dan taji daɗi ma yaƙi fitowa ko ɗigo ɗaya. Tasa ƙafa ta hankaɗe basket ɗin abincin data tafi da niyyar kaiwa Anaam ɗin saboda ganin Shareff ya shiga can, dan koda ya dawo sashenta ya fara shiga ya kai mata ledarta, da tace masa ga abinci cewa yay ya ƙoshi tunda bai daɗe da cin na rana ba. Taji haushi amma ta dake harya barota fuskarta da murmushi, yana fita ta zabgama ƙofar harara da faɗin, “Munafuki” (Ƴan uwana mata a kiyayi zagin miji koda a zuciya😕). Harta zauna zata buɗe ledar daya kawo matan sai kuma ta mike, abincin data shirya domin shi ɗin ta tattara cikin ƙaramin basket ta ɗauka da nufin zuwa ta kaima Anaam a gabansa, Cikin ranta har tana saƙa abinda zai faru dan tayi shirin kunna Anaam ɗin ta yanda yau ko kwana a ɗaki ɗayan ma sai ya gagaresu duk da tasan iya shi ɗinne zai faru a tsakaninsu saboda ta yarda da su aunty Malika ɗari bisa ɗari. Amma maimakon hakan sai tai gamo da abinda ya nema saka zuciyarta faɗowa ta baki, wai yau mijinta, abin sonta Al-Mustapha ne rungume da yarinyar data tsana fiye da komai a rayuwarta yana kissing. Ta rumtse ido da sauri komai na dawo mata tamkar a film, ƙara ta saki dayin cilli da throw pillows ɗin dake a kujerar da take ƙasa, hawayen da take ta faman son zubo mata na rige-rigen sakkowa a bala'in guje.....

     ★Rashin fitowarta har ya kammala wayar ya sashi kiran wayarta, tana zaune a bakin gado abubuwa da yawa na mata kaikawo cikin zuciya da ƙwaƙwalwa. Batare da sanin shi bane ta ɗaga kiran dan bata da wannan number tasa. Shiru batace komai ba, jin anyi shiru daga can ma tai sallama muryarta a sanyaye dan da gaske ya rusa mata dukkan ƙarfin jikinta da kuzari. Numfashi ya sauke a hankali, batare da amsa sallamar tata ba.
“Idan kika bari na sameki a ɗakin nan komi ya faru kiyi kuka da kanki”.
Sarai ta gane shine, kafin ta samu damar cewa wani abu har ya yanke wayar, ta dafe kanta dake sara mata kaɗan-kaɗan. Da gaske kunyarsa takeji, kunya irin wadda bata taɓaji akan waninsa ba, abinda yake mata yakan zo a bazata gareta. Sanin halinsa na cika magana idan ya faɗa ya sakata miƙewa ta fito. Kallo ɗaya tai masa bata sake ba, shiko baima nuna yasan da fitowarta ba abincin sa yake ci hankali kwance. Itama sai ta fice.
Da gaske bedroom ɗin yana a yanda suka tashi suka barsa, cikin taɓe baki da hura hanci tace, “Uhhm kaima dai ƙazaminne ashe”. Haka ta fara gyarawa ranta fal mita, bathroom dai koda ta shiga ta fahimci an wanke sa, amma hakan bai hanata sake wankewa ba. Tana saka freshener ya shigo, ido suka haɗa tai saurin ɗauke kanta. Shima baice komai ba ya nufi wadrob ɗinsa, ficewa tai dan Alhmdllhi ta gama. Hankalinta kwance ta koma sashinta, da tunanin sun rabu kenan tunda ta masa aikin sai yabi wani sarkin kuma. Ta tattare kayan da yaci abinci ta kai kitchen, ta fito ta kashe komai na wuta ta nufi bedroom ɗinta. Duk da tanajin tsoron kwana ita ɗaya hakan yafi mata sauƙi, insha ALLAH zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zataima Mamie magana a kawo mata mai tayata aiki ko motsinta takeji taji sauƙi. Ranta fal farin cikin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login