Showing 108001 words to 111000 words out of 178785 words
babu mai takura mata yau take saka kayan barci. Da sauri ta haɗe ƴar saman kayan barcin nata da bata kai ga ɗaure igiyarba tana waro idanu na mamakin ganinsa, shima janye idanunsa da suka riga suka gama kalle abinda take rufewar yay cike da basarwa. Maƙoshinsa da yay bushewar wucin gadi ya kai hannu ya shafa yana kaiwa zaune a bakin gadon..
“Bani ruwa mara sanyi”.
Ya faɗa murya a shaƙe.
A hankali ta saki numfashin data riƙe, tamkar jiran umarnin take dama tai wuf ta fice. Jikin ƙofar ta jingina tana sauke nannuyan numfashi idonta a rufe, sai kuma ta buɗe tana ƙarema kanta kallo, a cikin zuciyarta kam kanta take bama ƙwarin gwiwa na baiga komaiba. Ta ɗan buɗe Jacket ɗin tana kallon ƙirjinta da kusan rabi ke bayyane ta sama, dan ƴar rigar cikin ƙarama ce sosai, babu bra kuma a jikinta, hakama wandon iyakarsa rabin cinyarta, sai ya zam saka iya su tamkar mutum baida maraba da zigidir. Ta samance har kusan ƙasa mai santsi da kauri. fuska ta ɗan marairaice da haɗa yatsun hanunta biyu tana jujjuyawa a saitin fuskarta dake a ƙwaɓe kamar zata saki kuka. “Wayyo ni Mamie idan ya gani ya gama dani”. Sai kuma ciki girgiza kan cikin bama kanta ƙwarin gwiwa tace, “Insha ALLAH bai gani ba. Yes bai gani ba”. Ta kara maimaitawa cikin tabbatarma kanta. Sai dai kuma zuciyarta taƙi gamsuwa.........✍
🤭Idan ma ya gani ba sadakinsa bane, kujimin ƴar iya😝🚶🏻.
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/23, 10:16 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*
*_❤🔥BABU SO....!!❤🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*
https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718
*_50_*
..........Tasirin maganganun Gwaggo ya hanata sukuni, ta kasa zaune ta kasa tsaye ta kuma gagara basu fassarar data dace. Gwaggo dai uwa ce a gareta, domin mahaifiyarta haihuwarta kawai tai da shayar da ita. Dan tun daga yaye da Gwaggo ta ɗakkota bata sake waiwayen gidan mahaifinta ba sai da yawo. Ita ɗin tarbiyyar Gwaggo ce kuma rainonta. Ta samu gata irin wanda alƙalami bazai iya zanawa ba a takkada da ga gareta, domin kuwa a zamanin ƙuruciyarta kosu Muhammad (Daddy) dake ƴaƴan MB Shareff na cikinsa basu kaita jin daɗi ba a hanunsa. Gwaggo wata irin mutum ce da gane zuciyarta sai ALLAH, hakan yasa har Umma Hajarah tabar duniya bata taɓa hankaltuwa da wacece Gwaggo ba. Ba Umma Hajarah ba hatta su Daddy a yanzu basu fahimci kaso talatin cikin ɗari ɗin halayen Gwaggo ba sam, duk wannan faɗi tashin nasu akan zumincin da suke tada jijiyar wuyan ganin bai salwance ba. Tai gajeren murmushi da sauke ajiyar numfashi mai nauyi, dan tabbas mafitar data kasa nutsuwa ta samo akan wannan auren da bazata taɓa yarda da tabbatuwarsa ba tana wajen Gwaggo. A ganinta miya rage? Kawai ta kwantar da hankalin nata bisa shawarar tsohuwar ta kuma bita daki-daki domin cimma nasara. Sai dai a sanin datai mata kota tunkareta a yanzu bazata samu abinda take buƙataba dan haka zata barta har zuwa safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu......
★Jin kamar motsinsa yasa ta bar wajen da sauri, ruwan ta ɗakko ranta duk a dagule na rashin ƙwaƙwaran hujjar ya ganta ko bai ganta ba. Sai dai wani gefe na zuciyarta na ƙarfafata akan ta dake ta fuske kawai, (haba sai kace ba Anaam ba! karki bada mata mana). Da wannan kurarin ta dake ta koma bedroom ɗin, inda ta barsa nan ta samesa, sai dai yanzu ya warware lap-top ɗinsa a saman stool ɗin mirror daya jawo gabansa alamar aiki zaiyi. Ganin yana ɗan kusa da side drawer na gado saita ɗaura anan, sai faman riƙe rigar take da hannu ɗaya duk da a yanzu ba'a ganin komai jacket ɗin ta rufe ruf. Duk yanda taso zuciyarta nutsuwa ta gagara, ta ɗan saci kallonsa, hankalinsa gaba ɗaya yana ga aikin da yakeyi, hasken screen ɗin laptop ɗin ta haske fuskarsa. Gani tai ya ƙara mata wani ƙyau da kwarjini, ta haɗiyi yawu da ƙyaƙyƙyafta idanu domin abinda take son faɗa mai nauyi ne, sai dai gaskiya bazata iya jurewa ba gara dai ta tabbatar.
Murya a noƙe tace, “Yaya MM!”.
“Uhhyim”
Ya amsa mata batare da ya bar abinda yake ba. Sai da ta sake juya maganar a ranta kafin ta furta kamar zatai kuka.
“Dan ALLAH in tambayeka zaka gayamin gaskiya?”.
Karon farko ya ɗago ido ya ɗan kalleta, tai saurin sauke nata idanun ƙasa. Idanun nasa ya sake maidawa ga aikinsa. Harta fidda rai da amsawar tasa ma.
“Malama kiyi maganarki kai tsaye”.
Baki ta tura gaba da ɗan murguɗawa kaɗan harda masa ƙaramar harara, zuciyarta sai ƙwaɓarta take amma wata na ingizata kuma. Cikin in ina da tsantseni ta cigaba da magana. “Dan ALLAH ɗa..zun da ka shi...go k...a...ga..n..ni k..o?”. Ta ƙare maganar kamar zatai kuka.
Cak ya tsaya da ga danna keyboard ɗin laptop da yake yi, ya ɗago idanunsa da suka canja launinsu tun ɗazun ya kalleta. ɗan ƙara tsuke fuska yay tamkar abinda take maganar a kai bashi ke neman hanasa sukuni ba, murya a dake ya bata amsa kai tsaye...
“Kina min talla na ƙara gani ne?”.
Babu shiri ta ɗago da sauri, sai ko idanunta cikin nasa. Ta zabura baya tana zagaya hanunta ta saman kanta “God forbid! Sai kace wata ƴar iska?. Kuma nidai ALLAH ya gani ai tambayarka nayi, dan zuciyata ta kasa nutsuwa nasan ka iya fuskewa da mazuranka bayan kuma k..k..k.....” ta kasa ƙarasawa saboda kallon da yake jifanta da shi mai matuƙar yawan aji-aji na fassara.
“Ni dai naji, shike nan sai da safe. Dan ALLAH a dinga knocking idan za'a shigo”. Ta ƙare maganar da zagayawa bayansa da hayewa gado tana murguɗa baki. Zaune ta tashi da sauri, muryarta na rawa kamar zatai kuka, “Ni Juwairiyya, nifa kamarma cakai ina maka talla ka ƙara gani!, kenan ka gani ɗin fa? Wayyo Mamie na, ki roƙamin gafarar ALLAH Yaya ya fara komaw......”
Muƙut ta haɗiye zancen ganin ya hawo gadon, ta zabura zata wulƙita ƙasa ya damƙota. Gaba ɗaya idanunta sukai wiƙi-wiƙi tamkar an kama tsohon kwarto a ɗakin surukarsa. Duka hannayenta ya maida baya ya riƙe da hannu ɗaya, ta shiga girgiza masa kai cikin magiya da roƙo muryarta na rawa tabbacin kuka na gab da zuwa. Ƙafafunta da take turzawa ya sa ƙafarsa ya danne, ya kai ɗayan hanunsa kan igiyar rigar tata, ja ɗaya yay mata ta warware dama ɗaurin zarge tai mata. Rigar ta buɗe, ƙara ta fasa masa, babu shiri ya kai hannu ya rufe bakin. Muƙutt ta haɗiye abinda ya rage bai fito a bakin nata ba, idanunsa da suka ƙara canja launi ya watsa mata, “Ba haka kike so ba na buɗe na gani”.
“ALLAH ya kiyaye wlhy”. Ta faɗa da sauri tana son motsa jikinta ko yaya amma yayi mata riƙo na gaske.
“Idan wannan bakin naki ya sake cewa (tak!) saina yage ɗayar ma silly girl”. Ya ƙare maganar hannunsa na sauka saman wuyan rigar da gaba ɗaya ya bayyana ƙirjinta saboda girmansa, rabin jikin nata ma duk a waje suke gashi ta kamata tsam kasancewar roba ce sannan copy lass mara nauyi.
Fashewa tai da kuka na tsananin borin kunyar daya jefa rayuwarta a ciki, dan ita harga ALLAH bada tunanin komai tai tambayar ba. Sai da ya tabbatar ya firgita ta sannan ya saketa, wani irin kwakusa ta kaima duvet ta ƙudundune har kanta...
Ƙara danne abinda ke hargitso masa brain yay da ƙyar ya koma ya zauna. Robar ruwan data kawo masa ya ɗauka, batare da yabi takan kofin ba ya ɓalle murfin ya dasa a baki. Tass ya shanye ruwan yay wurgi da robar yana rumtse idonsa da jijjiga kai tamkar mai girgije ruwan cikin suma. Ture stool ɗin da laptol ɗinsa ke kai yayi yana jan wani bahagon tsaki, toilet ya nufa cikin sassarfa kai kace ingizashi ake da remote.
Anaam da bata san yanai ba na maƙure cikin bargo tayi luff takaicin kanta da kanta ya gama dabaibayeta. Ji take tamkar ta ciji kanta dan haushi. A gaba ɗaya abinda ya faru sai yanzu take iya lissafa rashin wayonta, mima ya kaita masa tambayar? Ta cije lip da ƙarfi tana kaiwa gado mugun mintsini tamkar shine ya mata laifin.. Jin shirun ɗakin yayi yawa ta ɗan leƙo kanta kaɗan, wayam babu shi a ɗakin, jitai wani farin ciki ya ratsata, ta miƙe da sauri ta dire a gadon, ƙofa taje ta sakama key duk a tunaninta fita yay a ɗakin. Ranta fess ta juyo tana karkaɗa keys ɗin da faɗin, “ALLAH na gode maka daya fita azababbe, sai iya fassara mutum akan abinda ba haka yake ba, kuma ban yafe ba ganinmun jiki da akai da way......”
Numfashinta ya tafi zuuu ta haɗiyeshi tare da yawu, da ƙyar ta iya ɗago ido kaɗan ta kalla abinda taci karo da shi. Shine ɗin dai ba wani ba, zirr! Zirrr! Zirrr!! Haka jininta ke gudu a cikin jijiyoyinta yana kaima zuciyarta da ƙwaƙwalwa rikitattun saƙwanni masu tabbatar da firgicin mutum a cikin idanu. Miya rage? Kawai ta kwasa da gudu tabar ɗakin nan. Zuciyarta ta ayyana mata cikin ƙarfafawa domin ta tabbatar babu makawa yaji abinda take faɗa ɗin.
Hannu ya miƙa masa alamar ta bashi keys ɗin. Cikin langaɓe kai da girgiza shi, hannunta ɗaya na tattare da rigarta da taketa faman kare ƙirji. “ALLAH bafa da kai nake ba, kayi haƙuri zan maka bayani yanda zaka fahimta...”
“Nazo na amsa da kaina kenan?”.
“A'a wlhy, ni dai ba sai kazo ba, daga nan ma zan maka bayani”.
Yunƙurin matsota yay, da sauri ta jefa masa keys ɗin ya cafe. Cikin aljihun wandonsa ya zurasu da nuna mata gado. “Wuce ki kwanta”.
Hankali tashe ta buɗe baki zatai magana....
“Idan kika furta (A) sai na miki fata-fata a ɗakin nan. Idan kuma kinji ƙarya bismillah”.
Summ summ ta wuce hankalinta a matuƙar tashe. Ya raka bayanta da wani shegen kallo tamkar idanun nasa zasu wantsalo waje........✍
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/23, 10:16 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*
*_❤🔥BABU SO....!!❤🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*
https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718
*_52_*
..........Sake maido da ita yayi da riƙo fuskarta cikin hanunsa da ɗage gira sama. “Faɗi abinda ke ranki mana yarinya. Koba angon bane?”.
“Kaima kasan bashi ɗin bane ba, dan auren wata uku ne, kamar yau ne zai ƙare”.
“Oh really?”.
Cike da confidence ta bashi amsa. “Ka rubuta ka ajiye”.
Wani ƙayataccen murmushi daya nema sumar da ita ya saki, yaja hancinta da kashe mata ido ɗaya har sannan murmushin bai bar fuskarsa ba. “Kin tabbatar zaki iya?”.
Da ƙyar ta iya jawo yawu mai kauri ta jiƙa bushashshen maƙoshinta tana ƙyaƙyƙyafta ido. “Babu tantama a alwashina Yaya MM”.
Juyata yay suka koma tsakkiyar gadon, ta koma ƙasa shi kuma ya dawo samanta. ƙara ta saki da ƙoƙarin son turesa sai dai ko gezau, ta fara jan numfashi da fesarwa da ƙyar dan gaba ɗaya ya sakar mata nauyinsa dan mugunta. Ɗan ɗagata yay sai dai ba duka ba, ya kalla cikin tsakkiyar idanunta da har sun canja launin farinsu zuwa ja harda tara ƴan ƙwalla. Murmushi ya kuma saki da shafa lips ɗinta kaɗan da yatsun hanunsa. Ya ɗan kashe mata ido ɗaya da kai bakinsa saitin kunenta ya fara magana kamar mai raɗan. “Wannan bakin naki ne zai kaiki ya baroki yarinya. Idan kikace zaki buga game ɗin nan dani zubar hawaye bata shirya barin idaniyarkiba kenan....”
Janye fuskarta tayi saboda wani zirrr da takeji a cikin jikinta. Cike da tsiwa da son hana ganin lagonta ta sake maido fuskar “Never for ever, ka rubuta ka ajiye Yaya nanda wata uku zamu koma gaban Baba Ibrahim da kai ka bani sakina, dan ni da kai bazamu taɓa son juna ba, kaima kasan da haka ai”. Itama ta ƙare maganar da salon kashe masa idanu daya nema ɗauke masa numfashi.
Jin zata zille yay azamar tareta da hannunsa, gaba ɗaya annurin fuskarsa ya gushe, cikin ɗan kausasa harshe da zuba mata idanunsa da launinsu ya canja tsakkiyar nata ya fara magana. “Kuma dole ki zauna da ni yarinya, zan kuma tabbatar miki da hakan ki rubuta ki ajiye”.
Alwashin nasa ya matuƙar tsaya mata a rai, amma sai ta basar cike da rainin wayo ta saki siririyar dariyar data saka tsigar jikinsa tashi. “Yaya MM kana wasa da wannan Anaam ɗin, amma dai muje zuwa, hausawa kance ba'a san maci tuwo ba sai miya ta ƙare, nanda cikar wata uku zan tuna maka wannan”.
“Ni kuma kafin cikar wata ukun zan maimaita miki”. Ya faɗa yana janye jikinsa a nata ya sauka a gadon baki ɗaya. Harara ta dallama bayansa zuciyarta na bugawa da sauri-sauri, harda sakin ɓoyayyar ajiyar zuciya. Ita kanta ta yabama kanta da kanta, dan tasan ba ƙaramin dauriya taiba na riƙe tsoronta. Sai da taga ya fice a ɗakin gaba ɗaya ta dafe ƙirji da rumtse ido. Sai kuma ta buɗe da ɗan mangarin kanta. “Stupid girl! Anaam kina da hankali kuwa?. Wayyo ni ALLAH miya kaini yin waɗan nan cika bakin yanzu idan yaƙi sakin fa?” (Sai ki kaisa kotu) zuciyarya ta bata amsa kai tsaye. (Ya zakiyi da su Abie kuma?) wani gefen ya tambayeta. “Shike nan na mutu” ta faɗa a fili tana sake dafe kanta. Ganin zata zarar da kanta sai ta miƙe cikin murguɗa baki da faɗin, “Koma miye bazan yarda yaci galaba a kaina ba. Kafinma wata uku nayi gaba abina”.
🤣To bara muga yaya wasan zai kaya ƴar mitsila😝.
★★★
Duk yanda taso danne zuciyarta yau ta musu breakfast kasawa tai, koda maman Abu kuma tace zatayi saita hanata. Kallo ɗaya zakai mata ka fahimci taci kuka sosai dan idanunta har sun nuna. Tun tana kallon agogo da tsumayen shigowar Shareff harta daina zuciyarta na cigaba da mata zafi da raɗaɗi. Da alama ya fita ko sallama bai mataba kenan dan yanzu dai lokacin zuwa office ya gota matuƙa, ta kuma tabbatar bazai zauna har zuwa yanzun bai fitaba dan bai haɗa aikinsa da komai ba. Zuwa yanzu ta yarda kuka rahama ne, dan jiya tayi kuma taji sauƙi da sassaucin zuciyarta. Amma yanzu ya gagara fita ko kaɗanne balle taji sauƙi. Wani irin tsanarsa da haushinsa takeji mara misaltuwa, zuciyarta kuma ta kasa tsayawa waje guda da tunanin abu biyu. Shin maganin su Aunty Malika ne baiyi aiki a kansa ba? Kokuwa dai asirin dasu Gwaggo suka jima suna faɗa iyayen yarinyar nan nayine yafi nasu ƙarfi. Kanta ya kulle, ta rasa ina zata kama. Zafafan hawayen da taketa son fitarsu suka sami damar silalowa saman kumatunta masu matuƙar zafi, daga haka kuka mai cin rai ya kufce mata har ya shigo bata sani ba.. Ƙamshin turarensa dake ƙara yawaita a ɗakin da hancintane ya sakata ɗagowa kaɗan ta dubi ƙofar. Tsaye yake cikin ƙananun kaya masu taushi da sukai matuƙar fidda ƙuruciyarsa ta matashin namiji alamar yau bai fita ko'ina ba kamar yanda tai hasashe. Wani irin damm zuciyarta ta bada sauti a cikin ƙirjinta, abinda zai hana Shareff fita office kam lallai ba ƙarami bane, hawaye ne suka sake ziraro mata, ta sake ɗago ido ta kallesa har yanzu yana a ƙofar tsaye hannayensa duka a cikin aljihun wandonsa idanunsa a kanta tamkar ya samu television. Sakkowa tai a gadon da gudu taje ta rungumesa. Murmushi ya saki mai faɗi, tare da zare hannayensa daga cikin aljihu shima ya rungumeta. Ta saki ajiyar zuciya da sake kanƙamesa. Kusan mintuna uku suna a haka tsaye kafin ya ɗagota, fuskarta ya rike a tafukan hannayensa yana raba idanu akan hawayenta, ya girgiza mata kansa yana binta da wani kallon ƙasa-ƙasa.
“Kukan bai isaba?”.
Ya faɗa idanunsa cikin nata.
Kasa jure kallon nasa tai dan tamkar yana zuba mata wasu maganaɗisune masu wahalar ja'inja. Tai ƙoƙarin maida idanun nata ƙasa amma ya hana hakan ta hanyar ɗora lips nashi kan nata. A tare suka lumshe ido. light kiss ya sakar mata. Taja numfashi da ƙyar da ajiyar zuciya mai ƙarfi.
Murmushi ya saki da kai goshinsa saman nata ya haɗe, “Kin huce ko?”.
Baki ta tura masa zata kautar da kan nata ya hana hakan. Dole ta haƙura ta tsaya tanata sauke ajiyar zuciya a jere. Sai da ya tabbatar ta nutsu sannan ya saketa suka koma bakin gado. tissue ya miƙa mata, babu musu ta amsa ta share hawayenta.
“Kin tashi lafiya?”.
“Alhmdllh”.
Ta faɗa a taƙaice. Shiru ɗakin ya ɗauka kamar wasu baƙin juna. Taso ta danne komai kamar yanda taga ya basar, sai dai bazata iyaba. Ta ɗan dubesa muryarta na rawa. “Yau bazakaje office ba ne?”.
Bai iya ɓoye magana ba ko kwana-kwana, dan haka kai tsaye ya bata amsa da “Haba dai Madam, ango a office ai a koro ni. Ko ke ɗin nan ai baƙya so ganina a can ba ko. Ina hutu ne sai monday insha ALLAH”.
Ido ta tsura masa ko ƙyaftawa babu, “Sati ɗaya fa kenan?”.
“Kinga sun ragemin mudu ba kamar lokacin naki amarcinba ko? Nima