Showing 135001 words to 138000 words out of 252835 words

Chapter 46 - HAJAR COMPLETE NOVEL DOCUMENT

you Uncle..", Ayman ma ya kwaikwayi sister din tasa yace "shenkiyu Anchul", Sakeena tace "oya go to your room kuyi game a tab", da gudu suka ruga zuwa room din nasu da ledar chocolate dinsu a hannu. Nurain na kallon sister din tasa yace "Amm Madam...", Sakeena ta ɗauki remote control na TV ta rage volume ta maida nutsuwarta kansa tace "please karka min wani wala wala brother, ranar nan muna mgana a gida ka ringa mayar da ita not serious", Shafa kansa yayi ya sauke ajiyar zuciya yace "ya subhanallah... in dai wnn mganar ne ai mun gama, nafa gaya miki komai..", ta haɗe gira tace "ka gayamin komai as in how...?", ya gyara zamansa yace "listen sister you need not to worry, your brother here bashi da wani matsala ke kinfi kowa sani aii..", tayi tsaki tace "in banda kafiya ba, idan ka kafe akan abu ai babu me iya juya maka ra'ayi..", yace "Nah..?", tace "yess you", yace "Okay fine, nasan duk mtsalan dai akan wnn yarinyar ne kuma na gaya miki ni favor kawai na mata nake zaune da ita cause she's not my type and choice..", Sakeena tace "but Abba's choice right...", ya ɗaga shoulder baice komai ba, Sakeena tace "sai dai ka saki jiki da ita snn zaka gane wace ce kuma kaima tasan wane kai.. i think I told you" ta ƙarashe faɗin hakan ne lokacin da ta miƙe tsaye, kitchen ta shiga ba ta daɗe ba ta fito, ta ajiye trayn da ta fito dashi kan Centre table ta koma ta zauna a position dinta tace "gashi nan na ajiye maka abincin da kace sai ka dawo zaka ci", ya shafa kansa yace "am full..", ta galla masa harara tace "open it first kafin kace wani am full..", ƙaramar warmer din ya buɗe yaga miyar spinach ce da taji lafiyayyen smoked fish da pure palm oil, medium warmer din kuma pounded yam da zafinta don da magrib ta ruɗata, kallonta yayi yace "Please serve me..", zuba masa tayi, kaɗan yaci ya ture ya zuba ruwa a glass cup yasha, few minutes ya miƙe yana jan rigarsa yace "Good night, a miƙan gaisuwa wajen Abban kids", tace "Ohk, baya gari ma next tomorrow zai dawo insha Allah", yace "Ohk", ganin ya nufi ƙofa kai tsaye ta bisa da kallon mamaki kuma da gaske fita zaiyi tace "Nurain your wife", ya juyo yace "Ai kince na bar miki ita ta kwana..", Sakeena ta buɗe baki kafin tace "we are not from same planet... ka jira matarka ku wuce gida" tana kaiwa nan ta shiga ɗakin da Hajar take, zaune ta sameta kan carpet ta jingina da jikin gado, tin ɗazu da ta idar da sallah ta tashi zata fita tana gaf da palour taji muryarsa da scent dinsa shiyasa ta dawo ɗakin tayi zamanta, har compound Sakeena ta raka Hajar da ledar da ta haɗa mata sha tara ta arziƙi, ganin fitowarsu Nurain dake tsaye bakin gate ya fita, Hajar ta yiwa Sakeena godiya tana riƙe da ledar da ta bata ta fita, ta ringa kallon motarsa da already ya bude ya shiga, sauke kanta tayi ta ƙarasa ta buɗe front seat ta shiga ta rufe, ya ringa kallonta kamar a lokacin ya fara ganinta, kaifin idonsa akanta yasa ta juya ta ɗan kallesa, ido huɗu sukay tayi sauri ta ɗauke kanta tana kallo window ta turo baki, murya ƙasan maƙoshi yace "nuna min inda aka gutsira a jikinki..", da sauri ta juya ta zuba masa lulu eyes dinta ba tace komai ba, yana kallon cikin idonta yace "uhmmm answer me young lady..", haɗe gira tayi ta zare idonta daga cikin nasa ta kalli window, ajiyar zuciya yayi ya kunna motar, a ɗan firgice Hajar ta juya jin saukar numfashinsa a saitin fuskarta, ta sake shigewa cikin kujera ganin fuskarsa gaf da ta ta, yasa hannu ya janyo seat belt ya mata fastening, ya ɗan kalli slim pointed nose dinta kafin ya sakko da idanunsa zuwa pink lips dinta, slowly ya kai dubansa kan wuyanta that is fair ya hango jelar gashi biyu da ta leƙo ta sauka akan fatar wuyan, Hajar ta sake shigewa cikin kujera da cracking voice tace "stop staring at me..?", gaba ɗaya hancinta ya cika da ƙamshinsa and she can even feel his breathing, ya ɗago idonsa yace "is there anything to stare at...", ya koma ya zauna a seat dinsa ya ɗora hannunsa kan steering, after few seconds ya sauke handbrake ya fara driving, ita dai tinda ta kalli window ba ta sake gigin juyo da kanta ba, kawai irin kallon da ya mata ne ya tsaya mata a rai, ta ringa nanata gani ba taɓawa ba asarar ido a zuciyarta, saida suka hau babban titi ta fahimci dalilinsa na ɗaura mata belt, ai kam ta runtse idonta gamm ta jingina da kujera ko kyakkyawan motsi ba tay ba. suna isa gida yayi parking motar, sai a lokacin Hajar ta buɗe idonta, ƙoƙarin cire belt din ta fara amma ta kasa, ganin tana kiciniyar cirewa ya matso ya cire mata yana lura da yadda ta runtse idonta, da sauri ta buɗe motar ta fita ta nufi entrance, shima fitowa yayi ya rufe motar da haka yabi bayanta, ya ciro key ya buɗe ƙofar entrance, ba ta ko kalli inda yake ba ta shige ciki direct kuma ta haura sama da ledarta a hannu, bayanta yabi da kallo yana sauke ajiyar zuciya, ya sakawa ƙofar lock ta ciki kafin ya haura sama zuwa ɓangarensa.

★Da safe Maimuna da Sa'adatu suna shirinsu na zuwa schl din gogi, Sa'adatu har ta saka uniform tana zaune ƙasan leda tana irga kuɗin da suke rage mata, kallon Maimuna dake shafa BSC cream a fuska tayi tace "wai ke Maimu me yasa kin fiya hauka da baragada ne, nace miki ki dena shafa irin wnn mayukan a fuskarki amma kinƙi ji, ba kya jin kunya a dubi hannunki da fuskarki aga uban banbanci...", Maimuna ta rufe robar man tace "ba kiga safa nake sakawa a ƙafa ba, hannun kuma na ƙunshesa a hijabi, wllh duk masifarka baka isa ka gane ainahin launi na ba", Sa'adatu ta taɓe baki bata ce komai ba, Maama ta shigo tana gyara ɗaurin ƙirji tace "Au baku gama shiryawa ba.. yakamata kuyi da jiki dan ga malam can tsakar gida yayi takkwaba nasan so yake yaga kun fita..", Sa'adatu ta tashi ta saka hijab dinta na uniform ta ɗauki jakarta, Maimuna na gama shiryawa suka fito tsakar gida tare, Sa'adatu ta ɗan haɗe rai ganin Baba kafin ta wurga masa wata shegiyar gaisuwa daga tsaye, kallonta kawai yake bai amsa ba, Maimuna ta gaishesa irin mai spring din nan wcca da ita gwara babu, itama bai amsa mata din ba, Baba yace "ina kuke zuwa idan kuka fita daga gidan nan da nufin makaranta..?", Sa'adatu tace "ina kwa zamu idan ba makaranta ba..." bata rufe baki ba Baba ya gaura mata mari, Maimuna ta kwalalo ido jikinta na rawa, Sa'adatu dake riƙe da kuncinta tace "daman ni nasan Baba ka tsaneni a gidan nan, kawai sai ka zabgan mari dan ka tambaye ni na baka amsa", Baba ya juya yana kallon ɗakinsu Naseer yace "Nasiru zo nan", daga cikin ɗakin Naseer ya amsa babu jimawa ya fito, tini marasa kunyar suka sha jinin jikinsu, Naseer ya ƙaraso kusa da Baba ya rage tsaho yace "gani Baba..", Baba yace "yaran nan kullum idan suka fita daga gidan nan da shirin zuwa makaranta toh ba ita suke zuwa ba, ranar Alhamis naje makarantar tasu wajen principal yake gayamin tin ranar da aka kaisu basu sake zuwa ba, wata bakwai knn basa zuwa makaranta", da wani irin takaici Naseer ya dubi ƙannen nasa, tsawa ya daka musu yace "ba zaku tsugunna ba kuka wani tsaya ƙerere", zubewa sukay a ƙasa ko wacce na zare idanu, Baba yace "su gaya maka inda suke zuwa, kuma daga yau na soke zuwa makarantar...", babu irin barazanar da Naseer bai musu ba amma ko wace shegiya taƙi faɗar inda take zuwa, Naseer na kallon Baba yace "Baba ka bari na naɗi halittar yaran nan tinda an bisu ta lallami da arziƙi sunƙi su bada haɗin kai..", Baba ya girgiza kai yace "A'a Nasiru idan icce ya bushe bazai tankwaru ba, duka na nawa kuma, da ace suna jin duka da babu wacca zata sake laifi a cikinsu, rabu dasu Allah ya shiryesu, kawai dai kar wacca ta sake fita a gidan nan...", sai kuma ya kallesu da wani irin takaici yace "ku tashi ku ban waje, Allah ya shiryeku..", bazar bazar suka miƙe suka shige ɗaki, Naseer ya bisu da kallo zuciyarsa na tafasa don ji yake kamar ya bisu ɗakin ya farfasa musu jiki. Maama dake tsaye jikin labule kaff ta ji abinda ya faru, hura hanci kawai take tana gyatsine, ta lura dai ƴaƴanta aka sakawa idanu a gidan nan, zanin data ɗaura a ƙirji ta kunce ta dawo dashi ƙugu, gaba ɗaya alherin nata sun zube sai kace slippers, wata Tshirt me warin dauɗa ta saka ta fita daga ɗakin tana hura hanci wnda ya kusan cika fuskar tsabar ydda yake kamar tukuba, ɗakin Baba ta afka babu ko sallama, Baba ya dakata da sargafe kayan da yake jikin raki ya juya yana kallonta, ta ƙarasa ciki still tana hura hanci tace "mal ka ringa jin tsoron Allah kuma ka ringa kwatanta adalci a tsakanin ƴaƴan da Allah ya baka..", Baba ya gyara tsayuwarsa yana kallonta da kyau, tace "kawai saika ringa bin diddiƙin yara kana musu bita da ƙulli duk dan ka gano laifinsu, meye na binsu kaga inda suke zuwa, tinda Hajara take zuwa makaranta ka taɓa bin bayanta ne sai su, sbd daman ka tsanesu kuma baka sonsu, toh rabbil izzati dai yana sama yana gani... haba dan Allah kuma hakan duk bai isheka ba saida kazo bainar nasi a tsakar gida ka titsiyesu kana musu terere, toh a gsky nagaji karka sake wulaƙanta min ƴaƴa..", Baba ya sauke ajiyar zuciya ya nuna ƙofa yace "fitar min daga ɗaki..", ta sake hura hanci tace "bazan fita ba saina gama amayar da abinda yake zuciyata, ita waccar shegiyar mai salalon tsiya ai harta gama karatun baka taɓa titsiyeta kace ina ta tafi ba sbd ita ƴar mowa ce, su kuma su Sa'adatu da suke borori har neman laifin da zaka liƙa musu kake, karfa ka manta kafin ayi ɗaran akay kwanɗi ehee saida ka samesu kafin ka samu ita Hajarar ƴar gaba da fatiha..", ba ƙaramin hasala Baba yayi ba, ƙirjinsa har zafi yake masa, da kakkausar murya yace "nace ki fitar min a ɗaki..", ta taɓe baki tace "nan nan kaje ka nannago uban kayan abinci munaji muna gani ka aikawa Hajara...", katseta yayi da faɗin "Rabi daga yau baki da dama ko hurumin shigo min ɗaki har abada kuwa, igiyar auren da ta rage a tsakaninmu itama na datseta kije na sakeki..", Maama ta kwalalo mici micin idanunta waje ta dafe ƙirji bakinta na rawa tace "Adamu ni ka saka...? Ni..?", ta fashe da matsanancin kuka, Baba yace "zan rufa miki asiri babu wanda zai san babu aure a tsakaninmu, idan kinga dama sai kije ki yiwa kanki terere a bainar nasin da kika faɗa, amma daga yau babu ni babu ke kuma na shata miki layi da shigowa ɗakina", kuka Maama take wiwi harda fyace majina tace "da girmana da gemu na saida tsufa ya fara kamani zakamin irin wnn sakin na wulaƙancin", a fusace Baba ya fita ya bar mata daƙin don ko ganinta baya son yi, bayan wani lokaci Maama ta fito daga ɗakin idonta sun suntuma sun sake ƙanƙancewa, Umma dake gaban rariya tana rege wake ta ɗaga kai ta kalleta, Maama tace "shegiya mayya uwarki kike kallo", Umma ta ɗauke kai tana taɓe baki, Maama ta shige ɗakinta tana cigaba da rusa kuka, ƴaƴanta sukay cirko cirko akanta suna tambayarta lfy, babu wnda ta tankawa, gaba ɗaya ta wani gigice ta susuce, abu ɗaya take ta maimaitawa wato "da girmana da gemu na".

★Da wuri Hajar ta farka da safe sbd jiya da wuri ta kwanta, ta shiga toilet ta tsala wankanta ta fito ɗaure da towel, gaban mirror ta tsaya tana kallon kitson kanta, ta warware jelolin da ta naɗe da zata shiga wanka, taja stool ta zaune tayi shafe shafenta, tana gamawa ta dakko kaya ta saka, kasa ɗaura ɗan kwalin kayan tayi sbd har wani zugi fatar kanta ke mata, wata hula mara nauyi mai santsi ta saka, daga haka ta feshe jikinta da turare mai sanyin ƙamshi wnda ke cikin kayan da Sakeena ta bata jiya, a hankali ta buɗe ƙofa ta fita, shima a lokacin ya buɗe ƙofar ɓangarensa, da sauri ta ɗauke kai ta wuce ta tsaya gaban stairs ba tare da ta fara sauka ba, juyowa tayi taga yana tunkaro stairs din, ba tare da ta kalli gabanta ba kawai ta saka ƙafarta zata fara sauka, ai kam ƙafar tayi gaba suu, kawai ji tayi an fixgota baya, yasa hannu ya tallafo ƙugunta ta baya yayinda ita kuma ta damƙe gaban rigarsa ta yiwa kanta support, wani juyin masa yayi da ita ya jinginar da ita da bango, har lokacin hannunsa ɗaya na riƙe da ƙugunta ɗayan kuma shoulder dinta, Hajar ta ajiye numfashi kafin ta buɗe idonta ta ringa kallon hannunta da har lokacin yake damƙe da rigarsa, da sauri ta sakesa ta haɗe rai, ɗago kanta tayi ta kallesa wnda hakan yasa ya dena ganin baƙin gashinta da hular kanta ta zame sbd santsinsa, kawai kallon eye balls dinta yake, ta sauke idonta tana jin ƙamshinsa har ƙwaƙwalwar kanta, a bazata ta sake ɗaga kai tana kallonsa jin yayi motsi da hannunsa dake ƙugunta, ta juya lulu eyes dinta tana kallonsa tace "please let go off me"......✍️
💛 HAJAR 💛

{60..}
Kallonsa take tana jira ya saketa, ta ɗan turo baki tana turesa da iya ƙarfinta amma ko gezau, zaro ido tayi jin ya janyota jikinsa sosai, zuciyarta ta buga da ƙarfi ta fasa masa ƙara da iya volume dinta, da sauri ya saketa ya toshe kunnensa, da gudu ta shige room dinta tayi banging door, ƙofar da ta rufe ya kalla yace "Silly girl..", ya zura both hands dinsa a pocket kafin ya sauka downstairs, kitchen ya shiga yayi making coffee ma kansa, riƙe da cup din coffee da saucer dinsa ya fito ya haura sama, a tsakiyar makeken bed dinsa ya zauna, ya janyo Laptop ya kunna, yana operating system din at same time yana sipping Coffee, he was just starting at the monitor while his mind was totally not there, wani thinking din yake daban, ya ajiye cup din kan bedside, ajiyar zuciya yayi yace "Silly girl..", ya kalli agogon da yayi tickling 8 dot, ya ɗauki wayarsa yayi dialing numbern mai masa wankin mota yace masa yazo ya ɗauki motar, yana gama wayar ya tashi ya shiga bathroom, tsaf ya gama shirinsa ya ɗauki briefcase dinsa ya sauka downstairs, compound ya fita ya wuce parking space, babu jimawa kira ya shigo wayarsa, mai wankin motar ne ke kira ya sanar masa cewa yazo, direct Nurain yace ya shigo, bayan me wankin motar ya tafi da black car dinsa ya shiga other car din tasa ya bar gidan, hospital ya wuce wajen tara saura, tini ya fara attending patient da suke Queue suna jiransa, ƙarfe sha biyu saura ya gama da patient din, zaune yake kan office chair dinsa yana kallon glass nameplate mai ɗauke da sunansa, yayi stretching kansa feeling a bit better don ya gaji da zaman, knocking door akay yace "yess", Dr Marwan ne ya shigo da file da big sealed envelope a hannunsa, ɗaya daga cikin kujeru biyu da suke gaban table ya samu ya zauna, exchanging greetings sukay, Dr Marwan ya ajiye file da envelope din kan table yace "here nayi recording komai, ga hoton thorac din nan shima..", Nurain ya gyaɗa kai yace "what about the heart..?", Dr Marwan yace "itama akwai hoton ta", Nurain yace "alright i will check it later..", Dr Marwan yace "Ohk.. this week ne zaku tafi symposium din ko..?", Nurain yace "yeah it's going to start next week monday toh i think before then zamu tafi...", Dr Marwan yace "Ohk Lagos ne ko Abuja..?", Nurain yace "Abuja ne", Dr Marwan yace "okay.. sai anjima" da haka ya fita daga office din. Da yamma Nurain na zaune palourn Mami, Noor ma na zaune itama da Apple Laptop dinta tana kallon wani Chinese movie tana cin croissant, Nurain yace "kun gama exams din ne Noory..?", Noor tayi pausing movie din tace "yeah..", yace "saura jiran result", tace "Eh", wayarta ce ta fara ringing, ɗaukar wayar tayi tana satar kallon Mami sai kuma ta miƙe a hankali ta bar palourn, Nurain na kallon Mami yace "Mami yaushe ne tafiyar naku..?", tace "ohh i think ranar Saturday haka naji Abba yace", Nurain ya gyaɗa kai bai ce komai ba, sai ƙarfe takwas ya yiwa Mamin tasa sallama kafin ya bar part din nata, ya fita babban compound din gidansu, Noor ce ta fito compound din itama da small carton box a hannunta tace "Yaya", ya dakata da tafiyar ya juya yana kallonta har ta ƙaraso tace "Ya ga wnn please ka kai ma Hajar" ta fada tana miƙa masa box din, amsar box din yayi yace "sure", tace "thank you... good night" da haka ta wuce cikin gida, Nurain na isa gida direct ɓangarensa ya wuce, bayan yayi wanka ya saka white pajamas masu sweat pant, yayi combing hair dinsa kafin ya zura room slippers ya fita paloun sa, ajiyar zuciya yayi ya ɗauki box din daya ajiye kan kujera ya fita ɗakin, murɗa ƙofar room dinta yayi ya shiga bayan yayi sallama ƙasan maƙoshi, Hajar dake zaune kan carpet ta rufe jikinta da duvet bayanta jingine da bed ta ɗago ta kalli ƙofa, da sauri ta ɗauke kanta, ya ajiye box din kan makekiyar chest of drawers dake room din, ganin ya fara tafiya towards her tayi sauri ta kwanta ta rufe har ka tana turo baki, ya duƙa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login