Showing 162001 words to 165000 words out of 252835 words

Chapter 55 - HAJAR COMPLETE NOVEL DOCUMENT

tamau ya kalleta yace "ba kiji me nace ba..", ba musu ta janyo veil din ta saka a ka sai kuma ta kalli window ta ɗaure fuska, har suka isa gidan babu wnda yace da wani ƙala, ita kam Hajar daman tinda ta kalli window ba ta sake juyowa ba, tinda ya ganta da veil yake jin wani suya a zuciyarsa, saidai kuma yasan inda za su zo bbu maza and glass din motarsa tinted ne, yana gaba tana biye dashi suka shiga main building din gidan, sosai Mami taji dadin ganin Hajar, da ladabi Hajar ta zaune ƙasan carpet ta gaida Mami snn ta mata barka dawowa kanta a ƙasa, Mami ta amsa mata da fara'a tana kallonta da kyau, ba taga damuwa a tare da ita ba hakama jikinta, Hajar ta gaida Sakeena da itama take zaune a palour tare da Mami, Sakeena tace "lfy lou alhmdllh Hajar.. ya gida..?", Hajar tace "Alhmdllh", Sakeena tace "toh masha Allah", bayan minti uku Hajar tace "zan je wajen Hajiya..", Sakeena tace "Okay toh wajen iron lady zaki..?", Hajar ta gyaɗa kai tace "Eh" da haka ta tashi ta fita walking gently, Sakeena tace "Mami yarinyar nan na da nutsuwa wllh", Mami tayi murmushi tace "sosai ma kuwa ni na gani da ta zauna a gidan nan", Nurain ne ya fito daga bedroom din Mami don suna shigowa tare da Hajar ya shige ciki. tinda Hajar ta shiga wajen Hajiya ta gaisheta tayi zamanta a can, Noor ce ta shigo tana ganin Hajar tayi murmushi tace "ynxu Yaya take gyamin kinxo..", Hajar tayi murmushi tace "An dawo lfy..?", Noor tace "alhmdllh", Hajiya na kallon Noor tace "wai ni waye zai buɗe min wnn jakar da aka nannaɗe min ita da leda da gam, duk anbi an ƙadabaibaiye min kaya sai kace na sata, daman Sa'udiyyar nan basu da yarda sam, ka bar ganin fatarsu jajir zuciyar ɓaka ce, inba baƙin hali ba meye na rufe min jaka salon dai sai an baka wahala kafin ka buɗe", Noor tace "Iron lady ba sai kin koma can gidan zaki buɗe jakan ba", Hajiya tace "Wane can gidan kuma... ga mai rabin kaya nan tazo mai ake jira, marmaza ki kirawo min wanda zai farke jakar nan na fitar mata da abunta..", Noor tace "bari na kira miki Yaya ya buɗe miki", Hajiya tace "Wai Usuman, toh ai kar naje ya gwada ƙarfi ya tsinke hannun jakar na riga na yiwa Asabe alƙawarinta", Noor tace "Iron lady mene kuma na tsinka hannun jaka kawai fa ledan za'a ɓare, nima don aiki nake a kitchen da ni zan cire miki", Hajiya tace "Au toh..", door aka buɗe Nurain ya shigo da sallama, Hajiya tace "shknn ma ba sai kin kirasa ba gashi nan yaxo", Nurain ya ƙarasa shigowa ciki ya zauna kan Sofa, Hajar na ɗaga kanta sukay ido huɗu dashi, da sauri ta miƙe tabi bayan Noor wacca ta fita ynxu, Noor ta juyo ta kalli Hajar tace "au tasowa kikay..?", Hajar tace "muje na tayaki aikin", tare suka wuce kitchen, Noor ta buɗe oven ta ciro cookies din da ta zuba tace "saura ƙiris ya babbake Hajiya ta riƙeni da surutu", Hajar dai tayi tsaye a kitchen din tana ta kallon Noor dake aikin flour, ta kwaɓa wancan ta soya wancan ta gasa wancan, ita dai tinda ba tasan me za tayi ba saidai ta temaka mata da kneading dough, suna cikin aikin Sakeena ta shigo, tana kallon Noor tace "An ɗora lunch..?", Noor ta girgiza kai tace "Garban bai dawo ba..", Sakeena tace "Alright plxx yana kawo perishable stuff din sai a ɗora", Noor tace "Sure", Sakeena ta kalli Hajar tace "you are here dear..?", Hajar ta gyaɗa kai tana cigaba da kneading dough din da take, Sakeena ta bar kitchen din bayan ta ɗebi doughnut da cookies, few minutes aka kawo perishable stuff din, mai aiki ce ta shiga dasu ta ringa ajiyewa a inda ya dace, Hajar ta matsa gaban sink ta wanke hannunta tace "me za a dafa..?", Noor ta ware ido tace "ke za kiyi girkin..?", Hajar ta ɗauki clean towel tana goge hannunta ba tace komai ba, Noor tace "Anything since you are the cook", Haɗaɗɗen Abinci mai rai da lafiya Hajar ta girka, tana gamawa Noor ta fara serving, ta zubawa Abba da Mami a different warmers, ta zubawa Hajiya potatoes porridge da Hajar din ta mata. Da yamma Mami na zaune main palour tana attending Son din ƙawarta Haj Fati, Noor ta fito daga part din Hajiya ta gaida baƙon dake palour tare da Mami, Mami tace "Noor kawo masa abinci da drink..", yace "A'a alhmdllh zan wuce ne ma..", Mami tace "A'a ka jira", Noor ta tashi ta shiga kitchen, ruwa da lemo sai snack din da ta yiwa boyfriend dinta da zai zo kawai ta ɗebar masa, don ko ƙwayar abinci ba a rage ba, an cinye tass, Nurain kam tana ganin plate biyu yaci, Noor na ajiye trayn ruwa da lemon ta wuce room dinta zata shirya zuwan saurayinta, Nurain ya sauko daga stairs yana ɗabi'arsa na jan riga, ganin Mami zaune palour tare da guest ya dakata, hannu ya miƙawa baƙon sukay musabaha, Mami tace "ka ganesa...?", Nurain yace "Sure" sai kuma ya dubi baƙon yace "Ahmad right..?", yace "yeah", Nurain har zai koma sama sai kuma ya shiga ɓangaren Hajiya, kan rug ya tarar da Hajiya ga Hajar gefenta tana yanka mata papaya, Nurain ya shafa kansa yace "ke da kika ce kin daina shan ta", Hajiya tace "Ai kaɗan zan sha yadda ba zata gundureni ba", yace "Ohk" sai kuma ya fakaici kallon Hajar da kanta ke ƙasa tana yanka papaya, key din mota ya ciro daga pocket ya jefar kan carpet daga kusa da ita, da wutsiyar ido Hajar ta kalli key din, Nurain ya duƙa kamar zai ɗauki key din ya rage murya sosai yadda Hajiya baza taji ba yace "karki fito palour" da haka ya miƙe ya fita, ko yanka uku na papayan Hajiya ba tasha ba tace "fita da ita ƴar nan ta gundureni wllh", Hajar tace "tom", har zata fita sai kuma ta dawo ta ajiye plate din papayan ta rufe, Hajiya tace "du Allah fita da ita", ba yacca Hajar ta iya haka ta ɗauki plate din ta fita, saida tazo tsakiyar main palour snn ta lura da baƙon dake zaune kan Sofa, shi kaɗai ne a palourn Mami ta shiga ciki zata ɗauko masa saƙon da zai kaiwa Mother dinsa, yana ɗago kansa daga latsa wayar da yake sukay ido huɗu da Hajar, sosai zuciyarta ta buga ganinsa a nan ɗin, ya ringa kallonta babu ko ƙiftawa, Nurain dake tsaye can ƙarshen stairs yana kallon palourn ya wani irin murtuke fuska, saida eyebrows dinsa suka haɗe, da sauri ya fara sakkowa daga stairs din, kafin ya kawo ƙasa Mami ta fito daga part dinta da paper bag a hannunta, Hajar ta saukar da kanta ta wuce kitchen da sauri, Ahmad ya bita da kallo wnda ya sake fusata Nurain dake tsaye daga bakin stairs, har wani yaji yaji zuciyarsa ke masa, innalillah babu fa veil a jikinta ya subhanallah, Ahmad ya yiwa Mami sallama bayan ya amshi bag din da ta basa, ya yiwa Nurain ma sallamar wnda ya amsa sama sama da haka ya wuce, Mami ta kalli Nurain ganin yadda ya ɗaure fuska tace "Ah ah Son this is not you, why are you frowning...?", ajiyar zuciya ya sauke ya shafa kansa, Mami tace "Come" da haka ta tashi ta shiga part dinta, bayanta Nurain yabi yana kallon ƙofar kitchen. After 20mins Hajar na zaune palourn Hajiya duk jikinta yayi sanyi sbd ganin Ahmad da tayi, toh ko dai ɗan uwansu ne, ƙofa aka buɗe, Nurain ne ya shigo har lokacin fuskarsa ba ta saki ba, yace "we are going home now", ta gyaɗa kai ba tace komai ba, ya ɗaga murya da ɗan tsawa yace "ba kiji bane..?", ba Hajar ba har Hajiya dake gyangyaɗi saida ta farka a firgice, Hajiya ta micincina ido tace "waye wnn ya ɗauki haƙƙina..?", Nurain ya ajiye numfashin da yafi kama da huci yace "Am waiting outside saura ki daɗe" da haka ya fita yayi banging door, Hajiya ta saki baki tace "bari ubanka ya dawo wllh saina gaya masa abinda kamin, ji fa fuskarsa sai kace tsohon hadari, wai yaushe Usuman ya zama haka ya mayar da fuskarsa ta Sa ƙarfi da yaji". Hajar dai tini ta yafa veil dinta ta ɗauki hand bag dinta, Hajiya ta dubeta tace "ke kuma lfy kike saɓa jaka..?", Hajar ta duƙa tace "tafiya za muyi Hajiya..", Hajiya ta buɗe baki sai kuma ta rausayar da kai tace "toh ai shknn, shiga ƙurya za kiga wasu ledoji gaban madubi ki ɗakko babbar ki kawomin..", Hajar tace "tom" da haka ta tashi ta shiga bedroom din Hajiya, babu jimawa ta fito tana jan ƙatuwar ledar da Hajiya tace ta ɗakko, Hajar tace "gashi Hajiya", Hajiya tace "Ai naki ne ƴar nan tsarabarki ne..", Hajar was shocked ta ma rasa me za tace, wnn uban kayan duka nata ne, ko da ta fara yiwa Hajiya godiya katseta tayi tace "A'a ƴar nan bafa maula kikay ba, lokacin da kike shaƙe yajin man zafi da loko babu wnda yaji babu wnda ya gani", Nurain ya sake shigowa ya tsaya daga bakin ƙofa yace "ke!!..", Hajiya tace "ka fita idona Usuman ya zaka ringa firgita ƴar mutane", yace "Hajiya cewa nayi fa ta fito..", da haka Hajar ta yiwa Hajiya sallama ta fita, ɓangaren Mami ta shiga don yi mata sallama, nan ma dai Hajar da leda ta fito wcca Mami ta bata, saida Hajar ta gayawa Mami cewa Hajiya ta bata kaya, tana fitowa Nurain dake tsaye main palour ya sunkuci ledar da ta ajiye a palourn wcca Hajiya ta bata yayi waje with speed, ita dai tabi bayansa walking gently, ikon Allah da kariyarsa ce ta kaisu gida, don gudun da Nurain ya ringa falfalawa ba a cewa komai, Hajar taga izaya iya izaya kuma taga ƙarshen walagigi a mota, a palour ya dangwarar da ledar da ya temaka mata da ita ya haura sama, Hajar ta taɓe baki ta bisa da kallo, mutum sai kace mai Junnu ko me akay masa oho, ita dai taja ledarta ta haura sama abinta. bata sake fitowa ba har dare yayi, bayan tayi sallar isha'i ta shiga wanka, tana fitowa ta tarar da missed calls from Anty Jamilah, ta zauna gefen gado ta shiga calling back, da sauri ta kalli door jin an buɗe, ta ajiye wayar ba tare da tayi ending call din ba, hijab dinta ta fara wawake zata saka, ya shigo ɗakin girarsa a haɗe yace "A can gidan me nace miki akan fitowa palour...?", turo baki tayi tace "ni ka dena shigo min ɗaki kuma ka dena kallona babu kyau haram ne" da kyar ta ƙarashe tana kallon hijab dinta dake can nesa kuma so take ta ɗakko, kawai ganinsa tayi a gabanta, ba ƙaramin bugu zuciyarta tayi ba ta tashi zumbur ta ja da baya, ganin yadda ya haɗe fuska ta buga ƙafarta a ƙasa tace "wai ni na maka laifi da zaka zo ka huce a kaina, ai Hajiya ce ta aikeni...", ya katseta da faɗin "da Hajiya ta aikeki sai akace ki fito palour without veil or hijab, ko baki san kinada aure ba...", wani kallo ta wurga masa tace "Aure kuma.. wace take da auren..?, toh saidai wata ba ni ba don ni ban taɓa aure a rayuwata ba", tsuke idanunsa yayi yace "really..", tace "yess kar kaga don kace na saka mayafi a ka na saka hakan baya nufin komai..", ba ta ankara ba sai gani tayi hasken ɗakin ya ragu, tana ganin ya taho inda take ta wani zaro ido, da gudu ta kyalla da nufin shiga bathroom amma ina don tini ya fixgota gami da haɗata da jikin wardrobe, ta tsala ihu ta fara turesa da duka hannayenta har da ƙoƙarin cixo, kawai saukar warm lips dinsa taji a nata, tsabar shock da firgita sai ta dena tura san, after few seconds ta dawo daga duniyar daskarewar da tayi, ta daddage da iya ƙarfin da Allah ya bata ta hankaɗasa, idan yayi gezau toh tabbas ya raba lips dinsa da nata, da hannu ɗaya ya riƙe duka hannayen da take kokawar dasu, ɗayan hannun kuma ya zare ribbon din da ta ɗaure gashinta kafin ya nutsar da yatsunsa cikin lallausan gashin nata still kissing her passionately, rawar da jikinta yake ce tasa towel dinta da daman ya fara sakwarkwacewa yabi jikinta ya faɗi ƙasa, da kyar Nurain yayi controlling kansa ya raba lips dinsu, sai a lokacin Hajar ta samu wani chance din kurma ihu, ƙoƙarin zubewa tayi a ƙasa yayi saurin ɗaukarta calak ya ajiyeta bisa gado, tsoron kar ya kalleta a haka yasa tayi saurin rumgumesa ta fashe da kuka tace "wayyoh Allahna na shiga uku na lalace, Ummana", Hajar ba tasan cewa wani ruwan ta janyo ba, Ehen a yau dai an fitar da part one na raini, bai kyaleta ba saida ya tabbatar ya firgita ƴar farka, a hakan ma saida ya kai zuciyarsa nesa don bai mata komai ba, tamkar zata shiɗe haka take jan shessheƙa, ganin zata sauka daga gadon ya janyota jikinsa a kasale, ta sakar masa kuka da dasasshiyar muryanta, bai saketa ba ya kuma rungumeta, da sauri ta ɓoye fuskarta a ƙirjinsa tana shessheƙa, ya ɗora kansa a kan nata hugging her tightly, lumshe idonsa yayi yana shaƙar ƙamshin da gashinta ke fitarwa, ya sauke ajiyar zuciya kafin ya rage murya a saitin kunnenta yace "har ynxun ma baki da auren Silly girl?"......✍️
💛 HAJAR 💛

{69..}
Sam Hajar taƙi ta buɗe idonta bare ta fahimci me ya faɗa, jikinta har rawa yake cause ba tayi tsammanin hakan da yayi mata ba, why did he touches her body that way, sosai yake jin ydda jikinta ke kyarma, tsoron da yake so taji din taji knn, a daidai saitin kunnen nata ya sake mgana yace "ki bani amsana Silly girl... are you still single...?", nan ma dai ta masa banza ta cigaba da shessheƙa a hankali, yace "Alright since you don't have an answer now shima na bar miki bashi, next time dole sai kin bani amsana", yana gama faɗin haka ya saketa ya tashi daga kan gadon, ya nufi door yana buttoning rigar Pajamas dake jikinsa, Hajar na jin fitarsa ta wani irin mirgina ta shige cikin duvet ta rushe da kuka, sabo fil abinda ya mata yake yawo a brain dinta, gashi skin dinta ma ƙamshinsa take bare ta yage ta cillar da ita ko ta samu ta manta, da kyar ta iya miƙewa ta nannaɗe jikinta da duvet ta ɗauki kayan baccinta ta saka, komawa tayi ta kwanta ta dunƙule waje ɗaya sai kace mage. Da asuba ta tashi tayi sallah ta sake komawa ta kwanta, har ƙarfe bakwai idonta biyu bata koma bacci ba, ji tayi an buɗe ƙofa ai kam ta runtse idonta da sauri, walking gently ya ƙarasa shigowa ya isa bakin gadon, kallon fuskarta ya ringa yi sai kuma ya duƙa ya kalli eye lashes dinta da suke rawa, bai san lokacin da wani murmushi ya kufce masa ba ya juya ya bar ɗakin ya rufe mata ƙofa, downstairs ya sauka don daman fita zaiyi yanada appointment da safe daga nan kuma zai wuce hospital. Ƙarfe sha biyu da few minutes Hajar na tsaye gaban sink a kitchen tana wanke utensils da tayi amfani dasu, tana gama wanke wanken ta ciro vegetables daga fridge za tayi blending, stew mai ɗan yawa za tayi saita ajiye a fridge ta ringa amfani da ita na 2days, tana wanke pot da za tayi amfani da ita taji ƙarar bell, fitowa tayi daga kitchen din taje ta buɗe ƙofar, ta waro ido ganin Anty sai kuma ta rungumeta tace "Anty sannu da zuwa", a takaice Anty tace "yawwa", kan Sofa Anty ta zauna tana bin palourn da kallo, Hajar ta duƙa gabanta tace "Anty ina yini", Anty ta amsa a fixge, Hajar ta ɗago kanta sai kuma ta zauna kan kujera tace "yasu Humairah...?", nan ma dai a fixge Anty ta amsa mata, tini Hajar ta fara shan jinin jikinta a hankali ta tashi ta nufi kitchen, Anty ta bita da kallo ganin yadda ta canza, ba iya fatarta ne ya canza ba har jikinta, tayi wani luwai luwai abinta alamar dai hankalinta a kwance yake, babu jimawa Hajar ta fito ta ajiyewa Anty ruwa da lemon da ta ɗakko, Anty tace "sannu Hakima", Hajar dai ta saukar da kanta ba tace komai ba, Anty ta zuge handbag dinta ta ciro wayarta, tana kallon Hajar ta ajiye mata wayar daga gefenta, da sauri Hajar ta ɗago kanta jin muryanta na fitowa daga cikin wayar, conversation dinta ne dashi na daren jiya, muryarta raɗau tana cewa kar ya sake kallonta haram ne, sau ɗaya muryarsa ya fito inda yake cewa ba tasan tanada aure ba ta fito without veil or hijab shima ɗin ƙasa ƙasa, sai na muryarta da ya kusa fasa speaker din wayar tana cewa ita sam ba tada wani aure, daga nan voice din ya ƙare kuma daman anan Anty ta katse kiran, Anty ta ringa kallon Hajar da ta sunkuyar da kai kamar munafuka tace "Daman baki da hankali Hajar, a gidan aure akwai wani abu da yake haram ne, ko ba a kan idona wnn abun ya faru ba inaji nasan cewa da mijinki kike, Islamiyyar da kika je ta tashi a banza a wofi knn, wancan allon naki da ke sargafe ɗakin Umma ba shi da wani amfani, ko a Islamiyyar naku hka aka koya miki...?", Hajar tayi shiru ba tace komai ba zuciyarta na bugu, Anty ta daka mata tsawa tace "Amsa min tambayana shashasha kike wani sunkuyar da kai sai kace ta Allah bayan ga rashin hankalin da kike giggillawa", ba shiri Hajar ta girgiza kai tace "A'a", da faɗa Anty tace "ba haka aka koya miki a Islamiyyar ba knn naki salon iskancin ne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login