Showing 201001 words to 204000 words out of 252835 words

Chapter 68 - HAJAR COMPLETE NOVEL DOCUMENT

yace "where is your phone...?", ta nuna masa kan bedside, sakinta yayi yaje ya ɗauki wayar ya zura a pocket, ita dai ta bisa da idanu ba tace komai ba, yace "Muje ki kwanta Dear..", gado ta nufa tace "Anan zan kwanta ni..", bai saurareta ba ya riƙo hannunta yace "Toh ni kuma fa pillow zanyi hugging tonight...", yana riƙe da hannunta har suka isa ɓangarensa, kwantar da ita yayi kan gado ya gyara mata pillow, yaja duvet ya rufa mata zuwa shoulder, pecking forehead dinta yayi yace "Sleep tight.." da haka ya nufi door ya fita, yana fita palour ya ciro wayarta daga pocket, ya tarar bbu message ko missed call, ajiyar zuciya yayi don yasan ba'a kai ga kiranta daga gida ba, but yasan dole za'a kirata kuwa, da shike sim din Hajar sabo ne kuma bbu wnda yasanta dashi sai Umma da Mu'azzam, kuma a cikinsu bbu wnda ya kira. gaba ɗaya daren nan Nurain bai rintsa ba yana gadin Hajar, ko motsi tayi sai ya sani don sosai yayi cuddling abarsa, sau uku yana jin tana firgita, sai jikinta yayi wani karrr kamar mai jin sanyi, yawan firgitar da ta ringa yi ne yasa ya fara mata karatun Alkur'ani a kunne, ai kam bata sake firgitar ba, wajen ƙarfe uku Hajar ta farka sakamakon Cramps din da yake kartarta har cikin bacci, mutsu mutsu ta ringa yi don sosai cikin ke mata ciwo, Nurain ya buɗe lumsassun idanunsa yace "Mene ne..?", a hankali tace "Cikina", tashi yayi da ita a jikinsa ya kunna hasken ɗakin, yace "ina ne yake ciwon..?", ta masa pointing lower abdomen dinta hawaye ya ciko idanunta, wani magani ƙwalli ɗaya tak ya bata ta haɗiya, ai kam ɗipp taji ciwon ya ɗauke ta koma ta kwanta, bata sake farkawa ba kuma sai asuba, Tinda ta tashi da asuba gabanta yake yankewa yana faduwa haka nan saddan, har wni jiri jiri ta ringa ji tsabar ycca gabanta ke faɗuwa, a haka dai tayi sallar asuba bayan ta idar ta haɗe kanta da gado tana Azkar, Nurain na dawowa masallaci ya duba ɗakinsa yaga bata nan don haka ya biyota room dinta, ya ƙaraso inda take jigine da gado ya duƙa gabanta, da sanyin murya tace "barka da Asuba...", Calmly yace "Good morning how was your night...?", tace "lfy alhmdllh..", yace "Masha Allah... ya ciwon cikin..?", tace "ya dena", ya ringa kallonta ganin kamar tayi weak, ya sauke numfashi a takaice sai kuma ya ɗagota ya zaunar da ita gefen bed, a gefenta ya zauna ya kamo hannunta with care yace "Hajar..", tace "Na'am..", slowly yake murza hannunta yace "kin san dai duk wni mai rai mamaci ne, kuma Allah baya barin wni don wani muddun sa'insa yaxo ko..?", wni irin bugu zuciyarta tayi ta ringa kallonsa bbu ko ƙiftawa, ta gyaɗa kai a hankali, yace "ki shirya zamu fita tare before 7 kinji..", shida da rabi Nurain ya sake dawowa ɗakinta ya tarar har tayi wnka ta shirya, amma kana ganin yanayin kasan a tsorace take snn ga gabanta da yake ta faɗuwa, mug din da ya shigo dashi mai ɗauke da thick tea ya miƙa mata yace ta shanye yana dawowa, Hajar ta zauna da nufin shan tea din amma ƙiri ƙiri ta kasa haɗiya, da ƙyar ta iya shan rabi, next dawowar da Nurain yayi da car key a hannunsa, hijab din data fitar ta ɗauka tasa akan doguwar rigar jikinta ta atamfa, A motar ma lallaɓarta ya ringa yi yana gaya mata maganganu masu taushi, ita dai kawai jinsa take don har ynxu bai gaya mata ainahin me ya faru ba, tini zuciyarta ta karye a karo na farko da tayi mgana tace "dan Allah me ya faru...?", tayi saurin goge hawayen da suka hau zarya kan cheeks dinta without her consent, Calmly ya kamo hannunta yace "Ba komai, just say Allahumma ajirni fi musibati wa aklufuli khairan minha..", wnn ne time na farko da Nurain yaji yana shakkar faɗar abu, bai san how she will react bne idan ya gaya mata kai tsaye, baya so ya karya zuciyar Baby wife dinsa, Hajar taji zuciyarta ta dawo maƙogoro har tana jin bugunta a kunnenta bayan taga inda motarsu ta tsaya, wni irin kyarma jikinta ya fara wnda ya ratsa har zuwa lips dinta, tini ta zare hannunta daga nasa ta juya ta ɓalle murfin motar ta fita, tini shima ya buɗe motar ya fita don da zafin nama ta amshe hannunta snn ta buɗe motar wnda bai san tana dashi ba, har wani gurɗewa ƙafafuwanta suke ta nufi lungun gidansu, habawa ai tini Hajar ta kwasa a guje don gani take tafiyar bazata kaita ba, bata ma lura da mutanen da suke soro ba kawai ta afka cikin gida, shima tsakar gidan a kusan cike yake da mutane, da ƙarfi ta ƙwala kiran "Umma..!!" sai kuma ta afka ɗakin Umman, Anty dake riƙe da Umma wcca ba ta san inda kanta yake ba ta ɗaga kai ta kalli Hajar, shima ɗakin Umman a cike yake da ƴan uwanta, Anty da idanunta sukay jajir ta dubi Wasilah da Hafsah tace "ku riƙeta..", Hajar kam tinda taga Ummanta a wnn halin zuciyarta ta fahimci me ya faru, ji tayi mararta ta wani mugun ɗaure tamkar zata tsinke ta fita daga jikinta, ta fasa wata ƙara har saida kunnenta ya dauɗe, lokaci guda ta sulale ƙasa idanunta suka wulƙile.....✍️
💛 HAJAR 💛

{82..}
Ana idar da sallar juma'a aka sallaci gawar Baba, abinda yasa aka jinkirta jana'izar sbd ƴan uwansa na Yola da suka roƙa a ɗaga musu ƙafa suma su samu jana'izar dan uwansu, jana'iza kamila aka yiwa Baba kuma ya samu ɗumbin mutane, daga nan aka wuce dashi gidansa na gsky, Sosai mutuwar Baba ta wujijjiga mutune musamman ma dai iyalansa, Hajar na kwance ɗakin Umma bata ma san inda kanta yake ba tin bayan da aka fitar da gawar mahaifinta, suman da tayi na farko bata farfaɗo ba saida aka yi ta yayyafa mata ruwa ana mata fifita, tini fashin watanta yaxo bayan ɗaurewar da mararta tayi don it was behind the corner, ta samu dai taga fuskar mahaifinta kafin a fita dashi, kawai Allahumma ajirni fi musibati wa aklufuli khairan minha take furtawa, don bakinta ya kama addu'ar tin a mota da yace ta ringa faɗa, addu'ar ce tasa ta ɗan ji sassauci amma hakan baisa ta dena rusa kuka ba har saida ta fita daga hayyacinta, Umma kam har aka fita da gawar Baba ba ta san inda kanta yake ba, Nabilah kam wni lungu ta shige ta ringa kukan rashin mahaifinta kamar ranta zai fita, gaba ɗaya ta tsani ganin Maama da Maimuna da ita kanta Sa'adatu don gani take su suka kashe Baba, shiyasa ma taƙi zama a ɗakin Maama don bata son ganinsu, wajen ƙarfe biyu ana cikin jimamin mutuwa sai ga Balaraba ta shigo da wasu mata police biye da ita, fuskar nan ta Balaraba ta suntuma suntum kamar an buga mata iska da ƙatuwar bandage a goshi, idonta ɗaya saida ya nutse tsabar yacca fuskarta ta kumbura, tini Balaraba ta ringa kallon mutanen dake tsakar gida tana neman Maama, da bata ganta ba ta wuce ɗakinta da police women din biye da ita, ɗakin Maaman bbu wasu mutane sosai don ba tada wasu shaƙiƙan ƴan uwa duk karume karume ne, Balaraba ta kyallaro idonta da ya nutse ciki ta kalli Maama wcca tayi wni wujiga wujiga don sosai mutuwar Baba ta taɓata, shekaru talatin da wni abu sune tare da bawan Allahn nan, Balaraba tayi nuni da Maama tace "gata can..", ɗaya daga cikin ƴan sandan tace "Baiwar Allah zamu tafi dake can police station sbd muna tuhumarki da ƙoƙarin kisan kai", wata daga cikin karumen ƴan uwan Maama mai suna Jummai tace "ku kam ba ku san gidan mutuwa ba, baiwar Allahn nan fa mijinta ne ya rasu ko dawowa daga kaisa...", ƴar sandar ta ɗaga mata hannu tace "mu hukuma kawai aikinmu muke, an bamu umarnin kamota daga sama dole mu wanzar da aikinmu", haka nan ƴan sandar nan suka kaɗo Maama daga ɗaki tana rusu kuka kamar ba gobe tace "Dan girman Allah karku gwadamin wnn rashin imamin, ku barni da jimamin rashin mijina mna..", Balaraba tace "Ni imamin kika gwada min da kika tsiyayarmin da ruwan ido..", kuka wiwi Maama take tana turjewa don tini ƴan sandan suka fara janta, gashi jama'a bbu wnda yace uffan kawai kallon Maama suke suna taɓe baki, toh daman wa zai ce wni abun halinta ne yaja mata, gashi bata zauna lfy da maƙota ba bare su dubeta, da kyar Maimuna ta rarrafo daga ɗaki ta maƙale jikin ƙofa, ilahirin jikinta shatin belt ne da Huzaifa ya lakaɗa mata duka, ga kuma cikinta dake azabar ciwo kamar zai tsinke, lokaci zuwa lokaci kuma tana yin bleeding kuma shima tin jiya, Sa'adatu ma maƙalewa tayi daga jikin window tana kallon yadda ake jan Maama sai kace Akuya, Balaraba na cewa "Ni kaɗai nasan irin nakasta ni da kika yi, saida na zubar da jini yafi gwangwani huɗu ga uban ɗinkin da akay min ruɓi shida a goshi..", haka nan ƴan sandar suka tisa ƙeyar Maama daga gidan tana kuka Wiwi, hijabinta ya wani waskace ya koma gefen kunne sai haɗa gumi take tamkar tsohuwar kuturwa, Maama ta haɗa hannayenta tana kallon Balaraba tace "ki duba irin halin da nake ciki Balaraba kar kisa a kaini chaji Ofis da ɗanyen mutuwar mijina..", Balaraba ta taɓe baki ta kalli yan sandan tace "Ofisa ku kaɗata du Allah" don so take a kai Maama police station a sakata a cell, kuɗi sosai Balaraba ta biya domin a zane Maama idan an kaita cell. Sai yamma liƙis snn Naseer yayo bailing Maama, ko da yaje police station din sai ya tarar sun jibgi Maama sai kace jaka, da yayi mgana akan dukan sai suka ce ai gardama ta musu, saida Naseer ya biya dubu ashirin don Balaraba cewa tayi sai an bata kuɗin da ta kashe na magani, Balaraba dadi har cikin ranta don ta sami kuɗin da zata biya bashin da ta ciyo ta bawa ƴan sanda don su nakaɗawa Maama duka, ranta washar tinda an jibgi Maama. Sai a washe gari snn Umma ta fara watsakewa, ynxu kam har tana iya amsa gaisuwar wnda suka zo mata ta'aziyya ba kamar jiya ba, Hajar ta ɗan samu kuzari amma ba wni sosai ba, bata iya jimawa a zaune saita kwanta, manyan idanunta duk sun ƙanƙance kuma still bata dena kuka ba, gsky ta amshi tsumangiyar mutuwar mahaifinta, da yammacin ranar saiga Mami tare da Sakeena, a ɗakin Umma Anty ta saukesu, bayan sun gaisa da Umma suka mata ta'aziyya, Hajar dake zaune ɗakin ta gaida Mami, Mami ta amsa with care snn ta mata ta'aziyyar mahaifinta, Hajar suka gaisa da Sakeena snn ta mata ya dadin haƙuri, sosai Sakeeena taji wni mugun tausayin Umma da Hajar don saura ƙiris kukan da take dannewa ya taho mata, bayan wni lokaci Sakeena ta dubi Mami tace "Mami su shigo ynxu..?", Mami na kallon Anty da ta kawo musu ruwa ta zauna gefen Umma bayan sun gaisa tace "Za'a shigo a muku gaisuwa", After few minutes Nurain ya shigo shi da Farooq, suna gaisawa dasu Umma snn suka musu ta'aziyya, Farooq ya dubi Hajar ya mata gaisuwa, ta amsa kanta a ƙasa don ita ko gaisuwar ma aka mta sai ta fara kuka, ynxun ma dai kukan ne ya taho, Nurain ya sauke numfashi yana kallonta da wutsiyar ido, gaba ɗaya jiya bai samu ya ganta ba don tinda akai jana'iza suka wuce gida tare da Abba, da yamma ma dai da ya dawo bai samu ya ganta ba har ya tafi after magrib, gashi wayarta na wajensa though yasan ma ko tana wajenta bazata ɗauka ba, Farooq ne ya fara tashi snn Nurain ya bisa suka fita, su Mami basu wni jima ba suka tashi zasu wuce, Umma tace "Toh mun gode sosai..", Mami tace "Allah ya kara muku hƙuri shi kuma ya masa rahasa yasa can tafi nan..", Umma tace "Ameen..", Sakeena ta matsa kusa da Hajar tana mata mgana a hankali, kawai gyaɗa kai Hajar take tana share hawayen dake zuba cheeks dinta, Umma ta ringa kallonsu hakama Anty, Sakeena ta saki hannun Hajar da ta riƙe tace "sai munxo gobe dear... Allah ya ƙara haƙuri..", Hajar ta gyaɗa kai sai kuma ta miƙe, Mami tace "yi zamanki daughter kinji..", Hajar ta saukar da kanta ta koma ta zauna, zaune kan tabarma su Mami suka tarar da Nurain da Farooq a soro, Farooq yabi bayan Mami da har ta fita, Nurain ya rage murya yana biye da Sakeena yace "Sister please how is she...?", Sakeena ta juyo ta kallesa tace "Toh partially..", ya sauke numfashi ya ciro wayarta da yake ta yawo da ita a pocket ya miƙawa Sakeena yace "please ki bata kafin mu wuce..", Sakeena ta amshi wayar ta juya ta koma cikin gida, bbu jimawa ta fito bayan ta kaiwa Hajar wayar. Da daddare wajen ƙarfe takwas Anty ta shigo ɗakin Umma, direct gado ta nufa inda Hajar ta duƙunƙune waje ɗaya, tapping dinta Anty tayi don tasan ba bacci take ba, Hajar ta miƙe zaune sai kuma ta kai hannu ta goge hawayen cheeks dinta, Anty ta girgiza kai tace "kinci Abincin kuwa Hajar...?", Hajar ta gyaɗa kai tace "Na ci", Anty ta duƙa ta bude plate din abincin sai kuma ta ɗago ta dubi Hajar, Hajar ta saukar da kanta ba tace komai ba, Anty ta sauke ajiyar zuciya tace "tinda kin ƙi cin wnn toh me zaki ci..?", Hajar tace "na ƙoshi ne..", Anty ta ɗan haɗe gira tace "A'a wne irin kin ƙoshi Hajar, na kawo miki kunun gyaɗa da Umma ta rage...?", Hajar ta saukar da kanta sai kuma tace "Toh..", Anty tace "yauwa bari na kawo miki tare da maganinki..", Anty na fita Hajar ta juya tana kallon wayarta da ta fara ringing, da fitilar wayar ta haska ɗakin don bbu Nepa, gashi kuma ana zafi shiyasa duk su Umma suka fita tsakar gida sai ita kaɗaice a ɗakin, tana ɗaukar wayar kiran ya katse, bbu jimawa wni kiran ya sake shigowa, a hankali tayi picking ta kara a kunne, da dasasshiyar muryanta tayi sallama, Nurain ya lumshe idonsa don he can feel the bitterness in her voice da sanyin murya yace "Baby wife...", ta saukar da kanta ta amsa a hankali, yace "please can you come out..?", ta gyaɗa kai a hankali sai kuma ta ajiye wayar bayan ta katse, saukowa tayi dga gadon ta gyara hijab dinta, Anty ta shigo da cup din kunu ganinta a tsaye tace "Ina zaki...?", Hajar tace "shine yaxo..", Anty tace "Ohk.. idan kin dawo sai kisha kunun kinji...", gyaɗa kai Hajar tayi walking slowly ta fita tsakar gida, ta duƙa gaban Umma da ke zaune kan tabarma, ga Sabrah kusa da ita tayi bacci, ta gayawa Umma zata fita ƙofar gida, Umma ta jinjina kai a takaice, Hajar ta tashi ta nufi soro tana tafiya a hankali, bbu kowa a soron don tin bayan sallar magrib masu zama a nan din suke watsewa, su Naseer kuma ta gansu a cikin gida, ta saukar da kanta ta shiga soron da ya gama cika da pure scent dinsa, Nurain dake riƙe da wayarsa ya haska soron ya ringa kallonta without blinking, ta ɗan tsaya nesa dashi, with cracking voice tace "Ina yini...", ya juya ya kalli waje sai kuma ya ƙarewa soron kallo, lokaci guda ya janyo hannunta ta tafi gaba ɗayanta ta faɗa jikinsa, a hankali ya shiga patting bayanta yace "Ya haƙuri Baby wife..", ta kwantar da kanta hawaye na zarya cheeks dinta, ai kam tini ta jiƙa masa gaban riga da ruwan hawaye, haka ya cigaba da consoling wife dinsa har saida ya tabbatar nauyin zuciyarta ya ragu, tana jin bbu wanda ya mata rarrashin da ya shigeta kamar na mijinta, surely ta rarrasu don more than 60 percent na raɗaɗin da take ji ya ragu, ya kai soft palm dinsa ya goge mata ragowar tears din yace "please stop crying Allah ya jiƙan Abba..", sai wajen takwas da rabi Hajar ta shiga gida da bag din kayanta da ya taho mata dasu, other hand din nata kuma ledar kayan ciye ciye ce. Washe gari akay sadakar uku tinda kwanan keso Baba yayi, wajen sha daya na safe sai ga su Mami harda Hajjaju Hajiya da Noor da kuma Umminsu Farooq da Aysha, suka zo da uban abinci kala kala na sadaka, Anty da Umma ba ƙaramin mamaki suka sha ba ganin yacca surkan Hajar suke sonta, ga Iron Lady da suka ga tana mata wni tarairaya na musamman, Umma har cikin ranta take jin daɗi da Allah ya kai ƴarta gidan da ake sonta, yoh toh so mna idan dangin miji basa yi da kai ta ina zasu ringa maka irin wnn mutuncin, bayan 20mins da zuwansu Mami Anty Zulaihah ma tazo don tasan gidan tinda tare da ita aka zo ɗaukan Hajar, Khausar dake biye da mahaifiyarta ta ringa bin gidan da kallo tana yamutse fuska, tinda taji cewa gidansu Hajar Anty Zulaihah zata zo shine tace itama zata zo, Hajar ta duƙa ta gaida Anty Zulaihah wcca ta amsa mata da sakakkiyar fuska snn ta mata ta'aziyya, Khausar dai bata ko kalli Hajar ba bare ta mata gaisuwa, Hajar na lura da yacca ta ɗauke kai da ta ganta, ita kam bata damu ba don duk wnda ya wanko ƙafa yaxo gidansu sbd mutuwar Babanta ya gama mata komai, Hajar na kallon Khausar tace "Sannu Khausar", Khausar ta ɗan kalleta tace "Ya ƙarin haƙuri, Allah ya jiƙansa..", Hajar tace "Ameen..", ko 10mins su Anty Zulaihah basu ƙara ba suka tashi zasu tafi, zuwa lokacin har Khausar ta fara fifita da handbag dinta tana yamutsa fuska, kafin sallar Azahar su Mami ma suka tafi. Da yamma lokacin jama'a sun rage tururuwar zuwa Mu'azzam ya shigo gidan, kwaraɓaɓɓen kitchen din gidan da basa amfani dashi duk ya mutu sai uban shirgi ya buɗe, girgiza kai yayi ya bar bakin kitchen din,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login