Murucin Kan Dutse

Chapter 142 of 146

hankalina yafi kwanciya dasu a ciki.
Nacd zan fadawa Aisha din don yanzu ta fita ta tafi aurin matar da zasu dauka don gyaran Amira din.
Yace gyara wani irin gyara kuma ni dai murmushi nayi sai Zulfa ne tace dashi kai dama ka dauka haka ake dunkula mace akaita gidan mijin ta kai tsaye ba wani dan kwaskwarima tare da ita.
Balle wanan Amaryan yar gata duk kawayen uwar ta madu ido a bude sun san komai ko su da kan su zasu iya mata komai ai.
Nace kai haba dai abin ya zama sheri kuma ai anty gyara kan Amira ta sha shi sai dai muce Allah ya bada zaman lafiya kawai.
Nace a kasalance shike nan ni zan tafi don aiki muke a can aka kirani yanzu din.
Yace tunda kika ji na kiraki aikin san magana zanyi da ke ko nace na dauka wanan maganan ne kawai ai.
Yace to bashi bane zauna kijirani ina zuwa sai yaci gaba da aikin shi kawai.
Dan lokaci kadan Zulfa ta mike tana fadin bari naje na duba yaran nan don yanzu nasan suna can sun min kaca kaca da shiya na.
Ta mike ta fice ta barni dashi zaune a wurin tana fita yake cewa dani komai dai ya kammala ke nan ko don banji kince dani komai ba again ?
Nace dashi ina ganin ba komai ai da nayi magana cikin daure fuska ya dan dago yana ksllona don jin yanayin da nai maganan.
Wai ke may kuma ke faruwane haka kike wani shan kamshi dake haka tun dazu nake lura dake a hakan.
Nace may fa kawai dai daurowa ne yace ba gaskiya bane wanan maganan ko dan maganan da akayi dazun ne kikewa wanan cikan kina batsewa haka ?
Nace dan magana fa kace daddy fisabillilahi yanzu ni may ye laifina a cikin wanan zancen haka da har ka rufe idon ka kai min haka don kawai na tura Amira wurin dangin uwar ta.
Kuma na ga dai wanan maganan ai munyi shi dakai ranan ko yace amma kuma ai daga baya da sukai min rashin mutunci na fada kada a kaita.
Nace yanzu sunzo sun bada hakkuri ai na dauka komai ya wuce ne ko idan kuma na hanata zuwa yadda suka bukata sai kuma nai wani sabin laifi ga hakan.
Yace ba dai kin tura ta ta tafi din ba ina shike nan nace kasan da hakan kuma ka rufe ido ka nunawa mutane ni ba kowa bane ga yaran da maganan.
Yai murmushi tare da ture takardun dake gaban shi yace dani yanzu dai in waban ne laifina ayi hakkuri ina shike nan ko ?
Nace ai hakkuri ya zama dole gare ni tunda haka Allah ya doro min wanan nauyin a kaina dole duk yadda yazo min na rungumay shi da hannu biyu.
Yace haka ake son musulmi dama da hakkuri amma kin daure haka aiko jama an dake tare dake bazasuji dadin ki ba don haka a washe don Allah.

Don Allah wanda na bata wa rai yayi hakkuri dani yanayi ne idan anyi la akari da yadda ake samun novel din a baya da kuma yadda yanzu yake delaiy gurin samun shi.
Ayi hakkuri dani please ba haka naso ba nima da fatan an sha ruwa lafiya yan uwa Allah ya sada mu da rahamarsa da gafaran sa albarkacin wanan watan mai albarka da muke ciki

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE ONLINE NOVEL NE NA KUDI, , , , ,
107

Washegari tunda safe masu zuwa bauchi suka shirya tafiyan don su samu su dawo a lokaci.
Bayan tafiyan su anyi wasu event da ya shafi yan matan bukin na Amira wanda akasarin su sunzo ne daga Abuja don taya ta murnan bukin nata.
Sai yamma lis su Zarah suka dawo garin a gajiye suna ta faman yabawa irin taron da akai masu a can da kuma irin namijin kokarin da mukaiwa Amira din a dakin ta.
Don duk wani kayan kitchen da uwa zataiwa yar ta nice na sayawa Amira su da komai da ya dace na nauyin uwa a gare ni.
Haka uban nata ba a cewa komai don ya gwadawa yarsa gata sosai yadda ya dace duk wani uban da ya dace yaiwa yarsa don nuna hali.
Sun yaba sosai ga abinda idanuwan su ya gano masu a gidan na Amira da aka gyara mata shi.
Mutane nan suka shiga magana kan irin wannan gatan da aka gwadawa Amira din wanda itace ya ta farko da ya aurar ta jikin shi.
Haka yasa kowa ke son zuwa ya ganewa idanuwan shi abubuwan da ake fadi da akwai a gidan na Amira a can bauchi.
Mun tashi da aiki washegari don tun karfe hudu muka falka aka shiga yin abubuwan abinda ya dace na sha,anin bukin.
Koda gari zai waye an gudanar da komai a yadda ya dace, ayi shi don haka muka samu sararin da muka samu hutu da kimtsa kan mu sai taron jamma, a da muke muna kuma ciyar dasu da abinda ya sauwaka na bukin da muka tanada.
Daga hakan ne aka daura aure aka shiga shirin wucewa da amarya sai daga bayane nake jin ai shi daddy da kansa ne zasu kaita shi da Bashir aminin shi.
Kamar yadda yayi da za akai Aisha wannan ma haka akayi akan amira din don sai da muka gurji kukan mu a wurin kafin mama laraba da anty Asmau suka ja hannun ta suka fice da ita a falon tana kuka ina kuka har suka bacewa gani na.
Haka na wuni cikin rashin walwala a tare dani haka nai ta gudanar da harkan buki har mutane suka watse aka barni da bakin da suka zo min daga wasu garuruwan wurin bukin.
Bayan bukin kwana biyu kawai na yi a kano na kwasa sai Abuja don akwai aiki a gabana banda wani lokaci na hutu a gare ni.
Nan na bar Hindatu a kano wai bata gama abinda takeyi ba a garin ni dai na kwasa da yarana muka bar garin.
A na samo wata yar aiki sai dai ba yarinya bace ita ta dan manyanta hajiyan harka ce ta sama min ita don haka da ita muka dawo garin.
Nazo da yar wurin Suwaibana daga can da zata zauna dani sai kanina Audi daya biyo ni don zai fara karatu shima yanzu saboda sun kiyi a can sun tsaya shiririta wai neman kudi.
Saukina ma shine daga Aisha har Amira duk a Abuja muke zaune dasu ko ba kullun ba dai zan dan dinga ganin su a gidan wani lokaci.
Sannu a hankali na ke koyar da Tani mai aiki dana dauko babu wani tsangwama ko takurawa a gare ta don nima tai muna tsakani da Allah yadda muke mata din.
Ban samu matsala da ita ba don tana da hakkuri sosai matan saboda zama da yara dole sai da hakkuri tare dasu.
Tafiyan Nasir ya taso sai faman shiri muke yi na tafiyan nashi tare zamu tafi dashi mukai shi mu dawo ni da daddy sai ga wani tafiya zuwa India ya taso min daga wurin aiki inda zanyi wata uku a can don wani nazari da aka tura mu mu uku .
Wanan dalilin ne ya hana tafiyan dani a lokacin don haka na shirya ma yaron komai daya dace tare da mashi alkawarin zamuzo muyi mai hutu acan U,S din insha Allahu in na samu lokaci.
Na riga su barin kasan inda nai tafiya da kananan yarana sai Maryam dana dauko don su Aisha na karatu a lokacin.
Inna ta da mama Altine ne zasu zauna da yarana a gidan sai dai kafin ta yarda da hakan sai da akakai rana da ita daddy da kansa yaje ya dauko min ita acan kauyen mu.
Su na bari da yaran a gida su zauna min dasu don kula yadda ya dace na tafi wanan tafiyan idan nayi shi akwai alheri sosai gare ni cikin sa ba don hakan ba ba zan bar Nasir ya tafi badani ba irin yadda yaron ya nuna damuwan shi ga rashin zuwa dani a lokacin.
Gida ne aka kama muna kowan mu mai dakuna biyu da falo sai kitchen don haka na samu wani makaranta a kusa na saka yaran a nan.
Haka yasa banda matsalan komai na ci gaba da abinda ya kawo ni kasan nakan kira yara muyi waya dasu dasu inna mu gaisa dasu sai ranan muna waya ne Aisha take fada min cewa anty daddy fa yayi aure bayan ki.
Duk da maganan ya barna min rai amma sai nake cewa cikin dakewa ashe har yayi auren ko ?
Tace anty dama kin san da zancen auren ke nan ashe, nace da ita na sani mana tunda ba fasawa zaiyi ba ai.
Tace sukan maman Ihisan fada sukayi da daddy sosai sai da mamanta tazo garin baki ga matar ba wata lukekiya da ita wai yar kasuwa ce irin shi Dubai take zuwa nace kuma dai.
Tazo satin ta daya ta wuce bata dawo ba yun lokacin nan dai taita bani labarin yadda zuwan matan aka kwashe da daddy har yake cewa inda Rahama ce ba zata taba nuna tashin hankali haka ba ga duk auren da nakeyi amma ke sai ankai ruwa rana dake ko yaushe baki girma.
Yabon banza nace da ita shi dai ya sani yaje yai tayi ai watarana yana gani zai bar matan wanan wani irin rayuwane ma daddy kamar wanda keda bakin uwa akan sa.
Mun yi sallama da ita ta barni da wanan damuwar a raina ni kadai a kasan mutane daga karshe na tattara na watsar da zancen don ba zan yarda na saka wanan zancen ya ja min matsala ba.
Sai dai ina jiran shi ya fada min da kan shi kancewa yayi auren wanan karon nayi alkawarin zai jini sosai ba dadi don abin ya ishe ni hakana wallahi.
Har ina batun dawowa bai fada min ba nima ban mai magana ba akai sai gashi ranan na kira su Inna muna waya dasu nake fada masu karshen wata zamu dawo insha Allahu.
Sai bayan mun gama hiran mu nace tabawa yaran sai naji tace dani Yarinya dama ina son muyi wani magana dake kafin ki dawo nace to Inna ta.
Tace ba wani abu bane nasan a gurin ki don kin saba da hakan daga mijin ku don ya kara aure a bayan ki don haka kada ki yarda naji wani abinda bai dace ba ya fito daga gare ki kan wanan maganan kamar yadda ya uwan zaman ki sukai mashi.
Shiru nayi sai naji tace kina ko jina yarinya nace ina jinki inna ta ba ruwana da zancen auren shi ni matsala na daya shine idan ya tabbatar da lafiyan matan da yake aure ai shike nan .
Duk da dai nasan ba zai yarda yana aure haka ido a rufe ba don yana da wayen wan shi akai amma ni mace ba a kaina zata zauna ba ai shi da ya dauko shiyasan abin shi can.
Tace haka nake so ji dama a gare ki don Allah ki taushi zuciyar ki irin yadda kika saba don shima ya fadi hakan da bakin shi a gurin sulhun da akai masu da ita wanan hindatun kishiyar ki.
Nace kai maman Ihisan ma dai da wani abu take wallahi mata nawa yake daukowa agidan a yaya ake karewa dasu irin su daddy ai sai ido kawai don abin nashi kamar mai bakin uwa akai.
Inna tace min ai ba kama bane don ance uwar ce tace dashi a lokacin marigayiya na da rai da zai auri su Zulfa take cewa da ita indai kishi ne sai dai taitayi mata hudu sai ya zauna dasu a gidan tana gani ba fashi.
Nai dariya tare da fadin Allah sarki ita Allah bai nufa tagani ba amma su gashi ai suna gani da ran su shiyasa ba a son uwaye nawa diya furci ko yayane cikin bacin rai .
Inna tace hakane sai dai ai bamu ganewa ne kawai odan ran mu ya baci a lokacin komai mutum zai iya furtawa yanzu dai kinga bako a kan shi bane ta furta amma da yake abin ya shafe shi kinga shi da yake nata a gunshi furcin ya sauka ai.
Inna Allah dai ya kuauta amma abin na daddy ai sai addua kawai don ni na rasa may yake ganewa ga wanan yawan auren da yake yi har nakan yi tunanen nace ko dai mune din baya jin dadin zama damu yasa yake hasashen wasu a waje.
Tace ummm, umm yarinya ba haka bane fa abune da ubangiji ya halasta masuyin shi shi kuma kinga yana da halin shi da zai yi wanda ma baida hali yayi wanan kokarin haka rabu da namijin baushe idan yasa rai ga yin abu bawai gazawan ku bane ko wani abu haka dai Allah ya doro mai wanan rayuwan kuma.
In bashi ba ai masu hali ma basu faye yawan aure hakan ba nagani ku dai sai kuyi ta hakkuri dashi kawai tunda haka Allah ya nufe ku da gani.
Nace nagode inna tace may ye na godiya ki dai godewa Allah da bai aza maki zafin kishi irin na hauka ba akai duk da kinayi amma ai ba irin na wasu ba har a wuce wuri akai.
Munyi sallama inna ta barni da tunanen irin matakin da naso daukawar wa daddy kan wanan aure sai naga ai duk maganan inna gaskiyane ba karyaba.
Babu abinda na rasa a rayuwana yanzu duk da ina da hanyan samu ai shi bai rage min komai ba na hakkin na daya rataya a wuyan shi don haka may zai sa na tsaya batawa kaina lokaci kan wanan shirmayn nabaya ma da yayi iba suka kai balle wai wata matafiya kuma can.
Matsala dai daya ne sai na saurara na sa ido naga ita kuma damay ta shigo gidan idan har bata shiga da sunana ba irin na Raliya da Niima may zai damay ni kuma da ita.
Bata zama bana zama banga abin damuwa ba akai kowa tashi ta fishe shi don miji mai aure aure ai ba dan goyo bane na ma godewa Allah da baiyo ni mai rawan kai ba akan miji da zan tsaya nuna ni watace a wurin shi ko wani abu.
Don wanan matsalar ne ke damun hindatu take wanan zafin kishin haka akan shi ya kamata ace tasan waye mijin mu wa muke aure muke zama dashi.
Shi fa mutum ne irin mazajen da basu da gwana a wurin su amma har yanzu basu gane hakan ba sam.
Mutimin da dan matsala kadan zai iya rufe ido a gaban kowa yai maka tas bai dauke shi komai ba ina wata wai mowa a wurin shi ko bora.
Gashi iya gwargwado yana kokarin shi wurin baiwa kowa hakkin ta a tsakanin zamantakewar mu , sai dai da yake mu matane bamu ganin wanan kokarin da yake a kan mu.
Don a kullun gani muke ai ya karkata a wani bangaren yabar sauran mata ke nan ba a iyamu duk kokarin namiji a kan mu sai mukai zuciyar mu akan abokiyar zaman mu maga may take dashi may suke da miji wanda shine wahalan mu a yau.

Mun gama abinda ya kaimu india na dawo da sakamako mai kyau akan course din da muka je inda da mun dawo zan zama consalta da zan iya shiga ko wani asibiti na kasan mu nai aiki mai amfani a cikin sa.
Ranan jumma, a da dare muka sauka lagos Nigeria ni da yarana da sauran abokan aikina wanda zamu dan tsaya lagos din muyi dan kwanaki don yin wasu cleares din wasu takardun mu a can.

Duk wanan abin maigidan bai masan mun dawo Naija ba yana can tare da amaryan shi sun tafi kaduna wai wani aiki ya kai shi can daga can zasu shiga kano da ita
Zaune yake a bakin gadon dakin hotel din da suka sauka shi da ita ya dauki waya yana hira da bashir nan dai yake wa daddy da sherin kadai san kaunata ta kusa dawowa daga course din ta gashi ina ga baka fada mata zancen auren ka ba ko ?
Ya dan shafo fuskan shi kadan yana sauke ajiyan zuciya yace hakane Bashir sai dai kuma ina ga ai ba zata rasa jin wanan nan labarin ba ko hindatu da zulfa zasu iya fada mata duk da nayi warning din su ga hakan.
Bayan gama wayan su da Bashir din a lokacin itama amaryan na gefe ta na kishingide tana waya da wata kawar ta na shakiyanci sai kwasan dariya suke yi ta wayan.
Gyara kwanciyar shi yake shirin yi yayin da yaji muryan amaryan nasa hajiya Samira tana fadin waini wanan matar taka da kowa ke magana a kanta tana ina ne wai ?
Da sauri ya dan juyo gare ta yake cewa mata wacce matar daga cikin matan nawa kike magana ne ?
Ta dan tabe baki tare da jawo room fresh tana dan fesawa a ko ina na dakin daga kwance tana fadin ita dai wacce ake cewa wai likita ko may ?
Murmushi yayi kawai yace a zuciyar shi anzo wurin indai Rahama ne ai zaki san ta ko sai dai a fili nuna mata yayi da cewa matatace mana ko wani abin ne sai tai shiru don ta fahinci irin yadda yai mata magana din.
Sunyi haka washe gari da safe ya shiga wanka na bugo nombar wayan shi baya kusa yana ban daki sai tai caraf ta daga wayan.
Muryana ne ya daki kunnuwan ta ina fadin hello daddy an tashi lafiya ya aiki ya iyali da sauran jama, an gidan ?
Ke ko wacece ta daina kiran wayan mijina da safe haka don bazan dauki wanan halin ba ga kowace mace.
Murmushi nayi nace ke kuma wacece karuwansa ne ko dadiron sa ko kuma wata yar aikin hotel ce.
Ki kama kan ki ga daukan wayan mijin wasu kina

Download complete TXT · Novel page