Murucin Kan Dutse
Chapter 39 of 146
mutanen gidan nan ta wuce tare da yaran ta kowani part sai da ta shiga tai masu sallama.
Muna tsatsaye a haraban gidan tafito sai naji wasu hawaye sun zo min a lokaci daya naji wani tukukin bakin ciki da tashin hankali ya toshe min zuciyana idona ya rufe anty na fadin to Rama ubangiji Allah ya sada mu da alherin sa don Allah kiyi ta hakkuri da yaran nan na barki maki su amana a hannun ki.
Koda ta juyo don mu hada ido sai taga kuka nakeyi nan ta tako ta karaso gare ni ta rungumay ni take itama ta fara kukan a wurin.
Kuka mukeyi sosai sai da muka ba duk wanda ke gurin tausayi gajiye itama kukan takeyi tana dan share hawaye da bayan hannun ta.
Daddy yana zaune cikin mota ta ya kura muna ido tausayi mu ke bashi, sosai yana mamakin bai taba ganin so da shakuwa irin haka ba a rayuwan wasu kamar namu.
Ganin bamu da niyar sake juna ga yara har sun fara kuka yasa yafito daga mota hannun shi na saye a cikin aljihun wandon shi.
Yazo inda muke a hankali ya jawo hannun matar shi yana ce is ok please kuyi hakkuri hakana, kamar wacce zata tafi, baza ta dawo ba wanan kukan haka.
Ina tsaye muna kallon suka ja mota aka fita dasu daga haraban gidan ranan haka muka wuni suku suku damu.
Da kyat na samu yaran suka sake jikin su don ban sha wani wahala ba gurin ganin na samu sun sauko.
Da dare ina shirin kwanciya ne wayan anty ya shigo min ina ganin bakon nomba nasan cewa itace na dauka da murnana na yaran suka taru suka rufa min muka shiga gaisawa dasu.
Har daddy sai da ya gaisa da yaran yai hira dasu sosai kamar ba kudi ake kashewa ba.
Washegarin tafiyan su na shirya yaran don an koma schools dani dasu bamu dauki lokaci ba mukai sallama da Gajiye tare da kara jaddda mata takula ma anty da part din ta duk da na rufe duk inda ya kamata na rufo a part din muka fice zuwa makaran ta.
Can muka hade da Zarah take ta min korafi wai anyi sallah amma naki neman ta har aka kare wasan sallah.
Hakkuri na bata tare da fada mata cewa cewa anty na bata da lafiya yanzu haka ma an fita da ita zuwa ganin likita waje.
Ta tausayawa anty tare da fatan Allah ya bata lafiya takece aiko taga na ramay sosai a lokacin.
Murmushi nai mata don bani wani dogon magana da ita wanda ya shafi shirin gidan su anty na.
Haka mukaci gaba da gudanar da rayuwan mu dagani sai yaran babu rana daya da Hindatu ko Zulfa suka leko part din da sunan sunzo su duba mu suga wani hali muke ciki nida yaran .
Da farko ina shiga na gaidasu da kwana amma da naga bamu gaban su gaba daya sai muka daina ba ruwan su damu muma ba ruwan mu dasu a gidan.
Yau ban shiga school ba muna zaune a falo Gajiye ta mike tana cewa zata shiga ta hada miya don tayi abinci tunda rana.
Hankalina naga handout dina da nake karan tawa jikina saye da wani bakin, dongon riga ya dan matseni sosai ya fitar min da surar jikina da kyau kaina babu ko dan kwali akai.
Naji ana nocking din kofan part din mu kafin na nace yes naji an turo kofan an shigo .
Dago kai nayi naga waye mai shigowan a lokacin wani matashi shine ya shigo saurayi ne da ganin shi gashi da matukar kwarji a tare dashi.
Abu daya ne ya dan raba su da daddy shine shi gajere ne amma fari ne sol kamar daddy.
Kamar su da daddy yayi matukar yawa sosai da gani ba sai an fada ma ba akwai alaka ta jini a tsakanin su.
Karasowa yake tsakiyan falon haka yasa namike tsaye daga inda nake zaune tare da mashi sannu da zuwa.
Kallon mamaki nake mai a lokacin don yadda ya shigo muna kai tsaye ga shi da ganin sa ka san boko ya huda shi sosai.
Fuskan shi a sake yakarasa ya samu kujera ya zauna sai bayan ya zauna yake cewa dani barka dai yan mata nan na shiga gaidashi a cikin mutunci.
Bin part din yake da ido zuwa can yake cewa ya naji gidan kamar masu gidan basa nan ?
Na bashi amsa da cewa eh basa nan sunyi tafiya sai mu da yara ne kawai a gidan.
For how long zasu kai a can na bi bayan kujera ina cewa ina ga zasu dauki lokaci a can don sunje ganin likita ne a can.
Matsalan Saade ke nan na gyada kai a hankali tare da fadi a raunane da eyyh.
Yace Allah ya bata lafiya ?
Nace amin yamike yana cewa ni zan koma dama na sauka garin ne nake cewa bari nazo na gaidasu.
Nace to barin kawo ma ruwa ka dan sha ko kada ka tafi baka sha komai ba agidan.
Yace na dauka ai rowa zakiyi min don naga kamar kina tsorona baki sanni ba ko ?
Nace gaskiya ban san ka ba.
Yace nima ban san ki ba ai ke sister din Saade ne ko ?
Na ce dashi eh anty nace ita.
Yace ni brother din Yusuf ne maigidan nan mamana da dadd din shi thesame mother thesame dadd suke.
Nace Allah sarki bari na dauko ma ruwan na wuce zuwa kitchen can na samu gajiye nake fada mata anyi bako ne yanzu.
Na dauko goran ruwa da kwalin juice hade da cup a wani dan ture na kawo mai falin.
Bayan na aje mai na koma inda nake zaune da farko na zauna a kujera muna fuskantar juna dashi.
Yace amma ban san Saade na da sister ba haka da farko ?
Nai dan yake ina cewa bazakan sani ba don ba a nan nake zaune da farko.
Daga ina kike daga kai nayi ina kallon shi don tambayan yai min tsauri da yawa nagaji ma da hiran don ban saba tsayawa magana da maza ba mai tsayi.
Na bashi amsa a takaice tare da daukan takardana ina cewa daga kauye nake.
Anya kuwa sam bakiyi kama da yar kauye ba nagani a nan ?.
Nace shi dan kauye har wani kama ne dashi dama can ?
Yace well koma dai daga ina kike ni dai nidai nasan bada kauye kike ba don banga alama ba anan.
Ya na tsiyayya ruwa a cup yake cewa koma may ye dai ni dama nazo ne na duba su don na dade bani kasan nan shekara na bakwai bana nan sai shekaran jiya na dawo shine nace bari nazo na duba su dama.
Nace Allah sarki tare da bude takarduna danake karan tawa ya dauki cup din da ruwan yana tsiyayawa a cup din a hankali yakai cup din bakin shi, yafara shan ruwan yana min kallon kurullla na dago kaina don jikina ya bani yana kallona ne dama.
Yai saurin kawar da idon shi a gareni yayi murmushi yana cewa kina karatu ke nan naga kin mayar da hankalinki ka alama handout ne kike karan tawa ko ?
Cikin basarwa nake cewa dashi eh ina karatu ne anan b u k nake ya mike daga inda yake ya nufo gurin da nake zaune tare da mika hannu alaman na miko mai takardan ya gani.
Ya dan duba yana kada kai yace ok da alama dai zamuyi babban likita ke nan a gidan nan nan gaba.
Nace eh to kusan haka din ne in Allah yardan muna da hakan, na bashi amsa.
Yayi murmushi tare da cewa wonderful .
Shekara nawa kenan kike yanzu da farawa nace ?
Nace karshen shekara ta biyu nake zan shiga na uku ke nan insha Allahu nan bada jimawa ba.
Masha Allahu hakan yana da kyau Allah yasa mu ci amfanin aikin da ake karantawa a family baki daya.
Nace amin a sanyayye tare da gyara zama na saboda yadda yazo gap dani ya tsaya a gaba na haka.
Nan yake cewa karatu sai an daure balle irin wanan naku mai tsawon shekaru haka don haka sai ki dage ki mayar da hankalinki sosai don amfanin ki nan gaba.
Nace insha Allahu zan dage da karatun duk na matsu ya fice sai dai baida alaman fita yadda ya tsare ni da tambayoyi haka.
Don ni ban taba tsayawa hira da wani da namiji ba koda kuwa course mates dina nane bana sakin jiki dasu sam.
Amma sai gashi yau shi wanan din da ban ko san sunan sa ba ya kafe ni da surutun tsiya a gida.
Daga cikin aljihun shi ya ciro kwalin sigari yana kokarin kunnawa a lokacin.
Wani kallo da ban san na watsa mashi ba na harara na watso mai a lokaci daya sai naga yai murmushi yana cewa sorry fa na manta ne ku matan hausawa bakwason cigiratte a kusa daku.
Nace ba matan hausawa ba kawai ai duk wanda yasan ciwon kan shi da daranjan kan shi bai wanan dabian mara kyau ko a gaban waye.
Murmushi mai kama da yake yayi tare da kakaro murmushi a fuskan shi a lokaci guda.
Ya kalli a gogon dake daure a hannun shi yace ok beauty ni zan tafi koda baki fada min sunan ki ba amma ni zanci gaba da kiranki da beauty kamar yadda ya dace dake din.
Yace zan tafi gida kada hajiyata taga na dade tai min fada ina na tsaya haka ni kuma ban iya fada mata nayi gamone da wata zukekiyar budurwa a gida brother na.
Sai lokacin na danyi dariya har fararen hakora na suka baiyana a fili nace fada kuma kamar wani dan karamin yaro can ?
Au baki san ana ma babba ma fada bane idan yana fita yawo akai akai ko yayi wani abinda ba daidai ba a rayuwan shi ?
Nace Allah sarki hakane fa amma kuma gashi naga ba aima fadan shan taba ba kuma ?
Yace cikin murmushi tare da hade yawun bakin shi tare da dan rankwafowa gare ni kamar mai rada yana cewa.
Kin san yaro ya iya yiwa manya wayo yanzu kaf gidan mu ba wanda yasan da ina shan cigari yanzun ma daurowa tayi hakan.
Nace cikin mayde bakina kadai bari zaifi ma alheri a rayuwan ka don badadewa ba za, a gane hakan tunda kadawo gaban iyayye.
Yace hakane fa kin kawo shawara mai kyau kuma anan zan kula da hakan insha Allahu.
Har ya juya ya fara tako yake cewa sai dai kuma beauty bata ban wayan taba mu dan dinga gaisawa ko jefi jefi.
Nace ban da waya ai don ni karamace anty da daddy suna hanani rike waya a gidan nan.
Kallona yayi cikin mamaki kamar zaiyi magana sai kuma ya ci gaba da tafiya har ya kai kofa sai kuma ya tsaya yana saka hannun shi ga aljiihun shi ya ciro waya guda biyu yana cewa dani.
Ungo wanan kafin su dawo sai muna gaisawa dake ta nan ko yaya kika gani beauty ?
Nayi murmushi nace kabar wayan ka don ni bani ketare maganan magabata na gaskiya.
Yace ba kidai son gaisawa danine kawai amma ai bazakice min baki da saurayin dakike gaisawa dashi ba ta waya yadda kike babba yarinya dake haka ?
Nace saurayi ni na kada kaina cikin dakewan fuska nace kun kun kun badai Rahama ba kan sai dai idan wata can.
Yace nice name kamarki kamar sunan ki suna mai dadi haka ai yanzu ma koba komai kinga aina karu da sanin sunan ki ai.
Yatako zuwa inda nake cikin wani murya mai kama da umurni yace karbi wayan nan Rahama please.
Kabar wayan ka ni ina da waya sai dai na baka nombata kawai ka saka a naka ka kirani dashi.
Ya sauke wani asirttacen ajiyan zuciya yace dama nasan cewa yarinya haka kamarki bazata rasa waya ba ai.
Na fara karanto mai yana sakawa a wayan shi yace ya gode sai kin jini ke nan.
Ban amsa mai ba yasa kai yafice daga part din na sauke ajiyan zuciya tare da bin shi da kallon takaici.
Nai nadama da bashi nomban wayan da nayi ranan don yana fita ya fara kiran layina wai yana sheda min ya isa gida lafiya.
Nace a gaida mutanen gida yace zasuji insha Allahu ya gode.
********* ********* *********
Tun muna damuwa da kadaicin dake damun mu a gida har muka sake jikin mu muka koma normal life din mu yaran sun fimu sake jikin su sosai don ba wani damuwan komai a tare dasu tunda suna samun kulawa tankar uwar su na gida.
Idan ka gansu neat dasu ba kazanta ba yunwa ba damuwa akan komai koda yaushe suna lake a jikina yadda suke so.
Abinda kuma sule so ban kiuyan yi masu shi ko yaushe haka yasa suka kara sake jikin su sosai damu.
Ga gajiye tana nata kokarin sosai don ina bata girma yadda ya dace a matsayin ta na wacce ke gaba dani a gidan.
Matsala ta daya yanzu shine bakon da yakira kan shi da suna Ibrahim yada yake kokarin kutso kan shi a cikin rayuwana.
Don yawan wayan shi na matukar damuna a yanzu zai kirani a yini kusan sau goma albarka.
Sai dai ban yarda na sake jikina dashi ba na fahinci yana son kulla alakar soyayya ne dani wanda ban tashi yin soyayya da ko wani da namiji ba alokacin nan da nake tsakiya ga karatuna.
Dama ya damay ranan wani yamma ya matsa yana son yazo gida ya ganni nake cewa dashi yanzu ko lokacin kaina banda shi..
Don karatun jerabawan da nakeyi wanda ya matso min a lokacin don haka yayi hakkuri kada yazo.
Yake cewa ba matsala Allah ya bada saan jerabawa zai jira har nagama exam sai ya fara zuwa nace dadai yafi kan.
Yace amma zaici gaba da kirana muna gaisawa a waya kamar yadda mukeyi.
Nace hakan ma gaskiya ba karamin takura bane a gareni gaskiya don hakan yana yawan dauke min hankali ga karatuna.
Ikon Allah Rahama yaya kike son nayi to?
Nace ban gane yaya nike son kayi ba da da babu ni yaya kakeyi a baya ?
Yace hakkuri nace to ko yanzu shi zakayi din idan kaga kana iyawa.
Naji yayi murmushi yace amma idan nazo gaida yaran brother dina zakiyi min alfarma ina ganin ki ko bamu gaisa ba ko ?
Nagane wani salon wayau yake son yi min kuma anan.
Nace ai gidan ku ne nan kana da ikon zuwa duk lokacin da kaga dama amma ba wurin Rahama dai kan don ban da time ni yanzu.
Mukai sallama bayan yai min godiya yakashe wayan nima na kashe tare da bin wayan da harara kamar shine a tsaye gabana.
Dama muna waya ina jin call na shigo min na duba naga anty ce a layin da sauri nai salati nace kaji sheri ko har anty ta kirani sau biyu wanan dan surutun ya hanani ji.
Da sauri na kirata bata daga ba har kiran ya tsunke dama nasan idan ta gani zata kirani again.
Sai ko ba akai ko second ba kiranta ya shigo min a wayana da rawan jiki na dauka ina sallama.
Muryan ta radau ta karba min sallama na na fara gaida ita bayan mun gaisa ne take cewa dani.
Dawa kike waya haka mai tsawo Rama nai maki kira har biyu baki daga waya ba ina jin ana samin line busy.
Nace lah Anty ba wani bane fa wani can yake damun rayuwa na kwanan wai shi dan uwan daddy ne yace wai ko sunan shi Ibrahim ?
Tace da karfi Ibrahim Ibrahim kamar tana mamaren sunan can tace badai Ibrahim din gwago Safiya ba nace haka yace.
Tace yaushe Ibrahim ya dawo kasan kuma har ya gan ki nace ranan ne yazo neman ku shine ya ganni ya tsireni da surutu har ya matsa min sai da ya karbi lanbar wayana.
To ki dai yi a hankali don in dai Ibrahim ne nasan yana da matar dake jiran shi tun bayan tafiyan shi acikin family din su.
Nace anty ni ina ruwana dashi shine kawai ke haukan shi shi kadai amma ni inani ina tsayawa wani shirmay yanzu.
Tace dadai yafi maki alheri wallahi ki natsu ki kama kanki irin su ba abin yarda bane don sun san yadda zasu sace zuciyar mace.
Ta tambayi yaran nace da ita gasu nan sunyi barci yau sunce sunyi game ne a school shine suka gaji sukai barci da wuri.
Ta tambayi gajiye nace tana kitchen tana wanke wanke tace na gaida ita nace zataji take cewa dama na kira nane naji lafiyan ku don tun safe yau bamu gaisa ba daku.
Nace lafiya kalau muke anty yaushe zaku dawo ne anty duk gidan ba dadi wallahi baki.
Tace cikin dariya Rama dawowan mu ba yanzu ba gaskiya don akwai maganin da nake sha ga kuma daddy ku akwai ayukan da yakeyi a nan.
Mukai sallama tana cewa na shafa mata kan yaran idan sun tashi ince mummy tana gaishesu nace zasuji anty.
Daddy dake tsaye fitowan shi ke nan daga wanka ya kashe ta da ido yana cewa dawa kike waya naji kina kiran Ibrahim.
Tace Rama ce mana nakirata har sau biyu bata daga kira ba tana waya shine yanzu ta kira nake tambayan ta dawa take waya take ce min wai Ibrahim din gidan gwago safiya ne.
Yace da wani irin murya mai kaushi Ibrahim Ibrahim kuma ?
Yaushe ya dawo garin har ya gan ta kuma ?
Tace wai ya kwana da dawowa bayan tafiyan mu ya dawo garin yazo gida shine ya ganta ya takura mata kuma sai da ta bashi layinta.
Tabashi layinta kuma ita Rahama bata da hankaline da zata dauki layinta taba mutum irin ibrahim mayaudari dashi.
Wanan dan iskan yaro tayi haukane halan da zata ba Ibrahim layin wayan ta kuma ?
Tana jin hakan yadda yake magana a hasale dariya
Muna tsatsaye a haraban gidan tafito sai naji wasu hawaye sun zo min a lokaci daya naji wani tukukin bakin ciki da tashin hankali ya toshe min zuciyana idona ya rufe anty na fadin to Rama ubangiji Allah ya sada mu da alherin sa don Allah kiyi ta hakkuri da yaran nan na barki maki su amana a hannun ki.
Koda ta juyo don mu hada ido sai taga kuka nakeyi nan ta tako ta karaso gare ni ta rungumay ni take itama ta fara kukan a wurin.
Kuka mukeyi sosai sai da muka ba duk wanda ke gurin tausayi gajiye itama kukan takeyi tana dan share hawaye da bayan hannun ta.
Daddy yana zaune cikin mota ta ya kura muna ido tausayi mu ke bashi, sosai yana mamakin bai taba ganin so da shakuwa irin haka ba a rayuwan wasu kamar namu.
Ganin bamu da niyar sake juna ga yara har sun fara kuka yasa yafito daga mota hannun shi na saye a cikin aljihun wandon shi.
Yazo inda muke a hankali ya jawo hannun matar shi yana ce is ok please kuyi hakkuri hakana, kamar wacce zata tafi, baza ta dawo ba wanan kukan haka.
Ina tsaye muna kallon suka ja mota aka fita dasu daga haraban gidan ranan haka muka wuni suku suku damu.
Da kyat na samu yaran suka sake jikin su don ban sha wani wahala ba gurin ganin na samu sun sauko.
Da dare ina shirin kwanciya ne wayan anty ya shigo min ina ganin bakon nomba nasan cewa itace na dauka da murnana na yaran suka taru suka rufa min muka shiga gaisawa dasu.
Har daddy sai da ya gaisa da yaran yai hira dasu sosai kamar ba kudi ake kashewa ba.
Washegarin tafiyan su na shirya yaran don an koma schools dani dasu bamu dauki lokaci ba mukai sallama da Gajiye tare da kara jaddda mata takula ma anty da part din ta duk da na rufe duk inda ya kamata na rufo a part din muka fice zuwa makaran ta.
Can muka hade da Zarah take ta min korafi wai anyi sallah amma naki neman ta har aka kare wasan sallah.
Hakkuri na bata tare da fada mata cewa cewa anty na bata da lafiya yanzu haka ma an fita da ita zuwa ganin likita waje.
Ta tausayawa anty tare da fatan Allah ya bata lafiya takece aiko taga na ramay sosai a lokacin.
Murmushi nai mata don bani wani dogon magana da ita wanda ya shafi shirin gidan su anty na.
Haka mukaci gaba da gudanar da rayuwan mu dagani sai yaran babu rana daya da Hindatu ko Zulfa suka leko part din da sunan sunzo su duba mu suga wani hali muke ciki nida yaran .
Da farko ina shiga na gaidasu da kwana amma da naga bamu gaban su gaba daya sai muka daina ba ruwan su damu muma ba ruwan mu dasu a gidan.
Yau ban shiga school ba muna zaune a falo Gajiye ta mike tana cewa zata shiga ta hada miya don tayi abinci tunda rana.
Hankalina naga handout dina da nake karan tawa jikina saye da wani bakin, dongon riga ya dan matseni sosai ya fitar min da surar jikina da kyau kaina babu ko dan kwali akai.
Naji ana nocking din kofan part din mu kafin na nace yes naji an turo kofan an shigo .
Dago kai nayi naga waye mai shigowan a lokacin wani matashi shine ya shigo saurayi ne da ganin shi gashi da matukar kwarji a tare dashi.
Abu daya ne ya dan raba su da daddy shine shi gajere ne amma fari ne sol kamar daddy.
Kamar su da daddy yayi matukar yawa sosai da gani ba sai an fada ma ba akwai alaka ta jini a tsakanin su.
Karasowa yake tsakiyan falon haka yasa namike tsaye daga inda nake zaune tare da mashi sannu da zuwa.
Kallon mamaki nake mai a lokacin don yadda ya shigo muna kai tsaye ga shi da ganin sa ka san boko ya huda shi sosai.
Fuskan shi a sake yakarasa ya samu kujera ya zauna sai bayan ya zauna yake cewa dani barka dai yan mata nan na shiga gaidashi a cikin mutunci.
Bin part din yake da ido zuwa can yake cewa ya naji gidan kamar masu gidan basa nan ?
Na bashi amsa da cewa eh basa nan sunyi tafiya sai mu da yara ne kawai a gidan.
For how long zasu kai a can na bi bayan kujera ina cewa ina ga zasu dauki lokaci a can don sunje ganin likita ne a can.
Matsalan Saade ke nan na gyada kai a hankali tare da fadi a raunane da eyyh.
Yace Allah ya bata lafiya ?
Nace amin yamike yana cewa ni zan koma dama na sauka garin ne nake cewa bari nazo na gaidasu.
Nace to barin kawo ma ruwa ka dan sha ko kada ka tafi baka sha komai ba agidan.
Yace na dauka ai rowa zakiyi min don naga kamar kina tsorona baki sanni ba ko ?
Nace gaskiya ban san ka ba.
Yace nima ban san ki ba ai ke sister din Saade ne ko ?
Na ce dashi eh anty nace ita.
Yace ni brother din Yusuf ne maigidan nan mamana da dadd din shi thesame mother thesame dadd suke.
Nace Allah sarki bari na dauko ma ruwan na wuce zuwa kitchen can na samu gajiye nake fada mata anyi bako ne yanzu.
Na dauko goran ruwa da kwalin juice hade da cup a wani dan ture na kawo mai falin.
Bayan na aje mai na koma inda nake zaune da farko na zauna a kujera muna fuskantar juna dashi.
Yace amma ban san Saade na da sister ba haka da farko ?
Nai dan yake ina cewa bazakan sani ba don ba a nan nake zaune da farko.
Daga ina kike daga kai nayi ina kallon shi don tambayan yai min tsauri da yawa nagaji ma da hiran don ban saba tsayawa magana da maza ba mai tsayi.
Na bashi amsa a takaice tare da daukan takardana ina cewa daga kauye nake.
Anya kuwa sam bakiyi kama da yar kauye ba nagani a nan ?.
Nace shi dan kauye har wani kama ne dashi dama can ?
Yace well koma dai daga ina kike ni dai nidai nasan bada kauye kike ba don banga alama ba anan.
Ya na tsiyayya ruwa a cup yake cewa koma may ye dai ni dama nazo ne na duba su don na dade bani kasan nan shekara na bakwai bana nan sai shekaran jiya na dawo shine nace bari nazo na duba su dama.
Nace Allah sarki tare da bude takarduna danake karan tawa ya dauki cup din da ruwan yana tsiyayawa a cup din a hankali yakai cup din bakin shi, yafara shan ruwan yana min kallon kurullla na dago kaina don jikina ya bani yana kallona ne dama.
Yai saurin kawar da idon shi a gareni yayi murmushi yana cewa kina karatu ke nan naga kin mayar da hankalinki ka alama handout ne kike karan tawa ko ?
Cikin basarwa nake cewa dashi eh ina karatu ne anan b u k nake ya mike daga inda yake ya nufo gurin da nake zaune tare da mika hannu alaman na miko mai takardan ya gani.
Ya dan duba yana kada kai yace ok da alama dai zamuyi babban likita ke nan a gidan nan nan gaba.
Nace eh to kusan haka din ne in Allah yardan muna da hakan, na bashi amsa.
Yayi murmushi tare da cewa wonderful .
Shekara nawa kenan kike yanzu da farawa nace ?
Nace karshen shekara ta biyu nake zan shiga na uku ke nan insha Allahu nan bada jimawa ba.
Masha Allahu hakan yana da kyau Allah yasa mu ci amfanin aikin da ake karantawa a family baki daya.
Nace amin a sanyayye tare da gyara zama na saboda yadda yazo gap dani ya tsaya a gaba na haka.
Nan yake cewa karatu sai an daure balle irin wanan naku mai tsawon shekaru haka don haka sai ki dage ki mayar da hankalinki sosai don amfanin ki nan gaba.
Nace insha Allahu zan dage da karatun duk na matsu ya fice sai dai baida alaman fita yadda ya tsare ni da tambayoyi haka.
Don ni ban taba tsayawa hira da wani da namiji ba koda kuwa course mates dina nane bana sakin jiki dasu sam.
Amma sai gashi yau shi wanan din da ban ko san sunan sa ba ya kafe ni da surutun tsiya a gida.
Daga cikin aljihun shi ya ciro kwalin sigari yana kokarin kunnawa a lokacin.
Wani kallo da ban san na watsa mashi ba na harara na watso mai a lokaci daya sai naga yai murmushi yana cewa sorry fa na manta ne ku matan hausawa bakwason cigiratte a kusa daku.
Nace ba matan hausawa ba kawai ai duk wanda yasan ciwon kan shi da daranjan kan shi bai wanan dabian mara kyau ko a gaban waye.
Murmushi mai kama da yake yayi tare da kakaro murmushi a fuskan shi a lokaci guda.
Ya kalli a gogon dake daure a hannun shi yace ok beauty ni zan tafi koda baki fada min sunan ki ba amma ni zanci gaba da kiranki da beauty kamar yadda ya dace dake din.
Yace zan tafi gida kada hajiyata taga na dade tai min fada ina na tsaya haka ni kuma ban iya fada mata nayi gamone da wata zukekiyar budurwa a gida brother na.
Sai lokacin na danyi dariya har fararen hakora na suka baiyana a fili nace fada kuma kamar wani dan karamin yaro can ?
Au baki san ana ma babba ma fada bane idan yana fita yawo akai akai ko yayi wani abinda ba daidai ba a rayuwan shi ?
Nace Allah sarki hakane fa amma kuma gashi naga ba aima fadan shan taba ba kuma ?
Yace cikin murmushi tare da hade yawun bakin shi tare da dan rankwafowa gare ni kamar mai rada yana cewa.
Kin san yaro ya iya yiwa manya wayo yanzu kaf gidan mu ba wanda yasan da ina shan cigari yanzun ma daurowa tayi hakan.
Nace cikin mayde bakina kadai bari zaifi ma alheri a rayuwan ka don badadewa ba za, a gane hakan tunda kadawo gaban iyayye.
Yace hakane fa kin kawo shawara mai kyau kuma anan zan kula da hakan insha Allahu.
Har ya juya ya fara tako yake cewa sai dai kuma beauty bata ban wayan taba mu dan dinga gaisawa ko jefi jefi.
Nace ban da waya ai don ni karamace anty da daddy suna hanani rike waya a gidan nan.
Kallona yayi cikin mamaki kamar zaiyi magana sai kuma ya ci gaba da tafiya har ya kai kofa sai kuma ya tsaya yana saka hannun shi ga aljiihun shi ya ciro waya guda biyu yana cewa dani.
Ungo wanan kafin su dawo sai muna gaisawa dake ta nan ko yaya kika gani beauty ?
Nayi murmushi nace kabar wayan ka don ni bani ketare maganan magabata na gaskiya.
Yace ba kidai son gaisawa danine kawai amma ai bazakice min baki da saurayin dakike gaisawa dashi ba ta waya yadda kike babba yarinya dake haka ?
Nace saurayi ni na kada kaina cikin dakewan fuska nace kun kun kun badai Rahama ba kan sai dai idan wata can.
Yace nice name kamarki kamar sunan ki suna mai dadi haka ai yanzu ma koba komai kinga aina karu da sanin sunan ki ai.
Yatako zuwa inda nake cikin wani murya mai kama da umurni yace karbi wayan nan Rahama please.
Kabar wayan ka ni ina da waya sai dai na baka nombata kawai ka saka a naka ka kirani dashi.
Ya sauke wani asirttacen ajiyan zuciya yace dama nasan cewa yarinya haka kamarki bazata rasa waya ba ai.
Na fara karanto mai yana sakawa a wayan shi yace ya gode sai kin jini ke nan.
Ban amsa mai ba yasa kai yafice daga part din na sauke ajiyan zuciya tare da bin shi da kallon takaici.
Nai nadama da bashi nomban wayan da nayi ranan don yana fita ya fara kiran layina wai yana sheda min ya isa gida lafiya.
Nace a gaida mutanen gida yace zasuji insha Allahu ya gode.
********* ********* *********
Tun muna damuwa da kadaicin dake damun mu a gida har muka sake jikin mu muka koma normal life din mu yaran sun fimu sake jikin su sosai don ba wani damuwan komai a tare dasu tunda suna samun kulawa tankar uwar su na gida.
Idan ka gansu neat dasu ba kazanta ba yunwa ba damuwa akan komai koda yaushe suna lake a jikina yadda suke so.
Abinda kuma sule so ban kiuyan yi masu shi ko yaushe haka yasa suka kara sake jikin su sosai damu.
Ga gajiye tana nata kokarin sosai don ina bata girma yadda ya dace a matsayin ta na wacce ke gaba dani a gidan.
Matsala ta daya yanzu shine bakon da yakira kan shi da suna Ibrahim yada yake kokarin kutso kan shi a cikin rayuwana.
Don yawan wayan shi na matukar damuna a yanzu zai kirani a yini kusan sau goma albarka.
Sai dai ban yarda na sake jikina dashi ba na fahinci yana son kulla alakar soyayya ne dani wanda ban tashi yin soyayya da ko wani da namiji ba alokacin nan da nake tsakiya ga karatuna.
Dama ya damay ranan wani yamma ya matsa yana son yazo gida ya ganni nake cewa dashi yanzu ko lokacin kaina banda shi..
Don karatun jerabawan da nakeyi wanda ya matso min a lokacin don haka yayi hakkuri kada yazo.
Yake cewa ba matsala Allah ya bada saan jerabawa zai jira har nagama exam sai ya fara zuwa nace dadai yafi kan.
Yace amma zaici gaba da kirana muna gaisawa a waya kamar yadda mukeyi.
Nace hakan ma gaskiya ba karamin takura bane a gareni gaskiya don hakan yana yawan dauke min hankali ga karatuna.
Ikon Allah Rahama yaya kike son nayi to?
Nace ban gane yaya nike son kayi ba da da babu ni yaya kakeyi a baya ?
Yace hakkuri nace to ko yanzu shi zakayi din idan kaga kana iyawa.
Naji yayi murmushi yace amma idan nazo gaida yaran brother dina zakiyi min alfarma ina ganin ki ko bamu gaisa ba ko ?
Nagane wani salon wayau yake son yi min kuma anan.
Nace ai gidan ku ne nan kana da ikon zuwa duk lokacin da kaga dama amma ba wurin Rahama dai kan don ban da time ni yanzu.
Mukai sallama bayan yai min godiya yakashe wayan nima na kashe tare da bin wayan da harara kamar shine a tsaye gabana.
Dama muna waya ina jin call na shigo min na duba naga anty ce a layin da sauri nai salati nace kaji sheri ko har anty ta kirani sau biyu wanan dan surutun ya hanani ji.
Da sauri na kirata bata daga ba har kiran ya tsunke dama nasan idan ta gani zata kirani again.
Sai ko ba akai ko second ba kiranta ya shigo min a wayana da rawan jiki na dauka ina sallama.
Muryan ta radau ta karba min sallama na na fara gaida ita bayan mun gaisa ne take cewa dani.
Dawa kike waya haka mai tsawo Rama nai maki kira har biyu baki daga waya ba ina jin ana samin line busy.
Nace lah Anty ba wani bane fa wani can yake damun rayuwa na kwanan wai shi dan uwan daddy ne yace wai ko sunan shi Ibrahim ?
Tace da karfi Ibrahim Ibrahim kamar tana mamaren sunan can tace badai Ibrahim din gwago Safiya ba nace haka yace.
Tace yaushe Ibrahim ya dawo kasan kuma har ya gan ki nace ranan ne yazo neman ku shine ya ganni ya tsireni da surutu har ya matsa min sai da ya karbi lanbar wayana.
To ki dai yi a hankali don in dai Ibrahim ne nasan yana da matar dake jiran shi tun bayan tafiyan shi acikin family din su.
Nace anty ni ina ruwana dashi shine kawai ke haukan shi shi kadai amma ni inani ina tsayawa wani shirmay yanzu.
Tace dadai yafi maki alheri wallahi ki natsu ki kama kanki irin su ba abin yarda bane don sun san yadda zasu sace zuciyar mace.
Ta tambayi yaran nace da ita gasu nan sunyi barci yau sunce sunyi game ne a school shine suka gaji sukai barci da wuri.
Ta tambayi gajiye nace tana kitchen tana wanke wanke tace na gaida ita nace zataji take cewa dama na kira nane naji lafiyan ku don tun safe yau bamu gaisa ba daku.
Nace lafiya kalau muke anty yaushe zaku dawo ne anty duk gidan ba dadi wallahi baki.
Tace cikin dariya Rama dawowan mu ba yanzu ba gaskiya don akwai maganin da nake sha ga kuma daddy ku akwai ayukan da yakeyi a nan.
Mukai sallama tana cewa na shafa mata kan yaran idan sun tashi ince mummy tana gaishesu nace zasuji anty.
Daddy dake tsaye fitowan shi ke nan daga wanka ya kashe ta da ido yana cewa dawa kike waya naji kina kiran Ibrahim.
Tace Rama ce mana nakirata har sau biyu bata daga kira ba tana waya shine yanzu ta kira nake tambayan ta dawa take waya take ce min wai Ibrahim din gidan gwago safiya ne.
Yace da wani irin murya mai kaushi Ibrahim Ibrahim kuma ?
Yaushe ya dawo garin har ya gan ta kuma ?
Tace wai ya kwana da dawowa bayan tafiyan mu ya dawo garin yazo gida shine ya ganta ya takura mata kuma sai da ta bashi layinta.
Tabashi layinta kuma ita Rahama bata da hankaline da zata dauki layinta taba mutum irin ibrahim mayaudari dashi.
Wanan dan iskan yaro tayi haukane halan da zata ba Ibrahim layin wayan ta kuma ?
Tana jin hakan yadda yake magana a hasale dariya