Kanin Ajali
Chapter 8 of 34
da dai bamu da tausayi don mahaifin mu yana tsaye a kan mu.
Dama yan uwan shi kowa na nuna kulawan shi akan mu a matsayin su na yan uwan mahaifin mu din a gare mu.
Saidai mu bamu ganin hakan da suke muna dan abu kadan zamu dauka don mahaifiyar mu bata da raine ake muna wani abin da bai dace ba.
Yinin ranan haka nayi shi a dakin ba wani walwala a tare dani sai ma gyaran dakin da na tsiri yi tankar mahaifiyar mu tana nan a cikin sa ne kamar yadda naga tana yi idan munzo tare da ita garin.
Sai yama lis na watsa ruwa a jikina kofan umma na dawo na zauna muna hira da yan uwana a gurin ta fito daga daki tana fadin kin ga dama kin fito ke nan don maganan da nayi maki jiya kike fan fushi haka yau.
Nace ba haka na bane aikin dakin mu nayi don yayi kura da yawa sosai ta tace ke dai kika sani idan kin sa kanki a damuwa haka ma yan uwan ki ba zasu sake ba don basu ga kina walwala ba .
Shiru nayi ina fadin a raina walwala ai ya kare a gurin mu umma tunda mun rasa mahaufiyar mu ko a duniya.
Maganan ta ne ya dawo dani ga tunanen da nakeyi tana fadin idan ba zamu iyacin abincin da akayi ba a gidan mu dafa taliya muci da dare.
Don mahaifin mu bai barmu munzo hakana ba garin sai da ya sawo muna duk wani cimar daya san muna amfani dashi a can muka zo dashi gida.
Tambayan kanne na nayi idan zasu ci da sauri suka amsa min haka yasa na tashi don in dafa muna taliyan tunda suna son ci na sani dolene kawai yasa suke cin abincin gari.
Mungama muka taru a gurin umma din nan mukaci taliyan sai dai itako kallo bai ishe ta ba tuwon ta da aka kawo muna taci.
Bamu wani dade ba muka kwanta don dare yayi a lokacin sai dai ni ba barci ne nayi ba na dai kwanta ne ina tunanen duniya a lokacin.
Tunda muka zo ko hanya bai hadani da jamilu ba har yakai satin mu daya da zuwa garin duk ko shima yana cikin garin a lokacin.
Yau ya kama kasuwan kauyen mu ne kowa sai hada hadan sana,ar shi yakeyi don fita dashi gurin yan kasuwa in ka debe mu da bamu komai sai dai mu wanke mu saka don yanayin mu daya dan banbanta dana yan gari.
Sai dai duk da haka ba,a barmu a baya ba don muma munyi kwalliya mun saka kaya masu kyau don muna da muradin shiga kasuwan mu dan zagaya.
Saboda akwai kudi a hannun mu bayan wanda baba ya ba umma don lalurar mu na yau da kullun da wani matsala daka taso a gare mu a gidan.
Kamar yadda tsoho keda naci a kudi haka ma yaro yake da kunata akan kudi don su sauran basu san baba ya bamu kudin ba a hannu na.
Mun gama shiri muka sallami umma don abokai na da suka shigo don mu fita sai dai ni abinda ke ban mamaki shi su hafsa kawana ba karatun sukeyi ba kuma su ba aure sukayi ba har yanzu.
Mun fita mun dan zaga abin marmari na sayo muna da kannen na don mun dade bamu ci ba a can mun juyo zamu dawo gidane muka hade da su jamil da kungiyar su.
Ashe sun saka ido a kan mu suga fitowan mu take dan leken asirin su ya sheda masu mun fito garin muna zagawa a kasuwan sai gasu sun sha kwaliyan su zakace ba yan kauye bane su.
Kallon juna mukayi na sada kaina kasa don kunya su a dole ga samarin da suka ga yan mata suka zo da guntun turancin su don su burge mu saboda mun fito birni musan sun iya turanci.
Da sumaiya kawanta suke turancin sai kanne na maza da muke tare suke buga turanci dasu suna jin dadin yadda yaran ke amsa su.
Na dago yana fadin baby ya kike ne kwana biyu bamu hadu ba ya mukaji da hakkurin rashin mama kuma sai lokacin naji wani iri a raina.
Don haka nake da an min maganan mama hankalina sai ya tashi sosai mutuwan ya dawo min sabo a raina.
Mun dan dade a gurin tsaye dasu suka rokeni da dare in basu lokaci su samay ni a gida mu kara gaisawa don nan ido yayi muna yawa akan mu.
Na matsu in bar gurin haka yasa mukai sallama dasu muka wuce zuwa gida inda kannena maza suka bisu kamar yadda suka bukata suyi.
Yalon da muka sayo kasuwa ne nake wankewa a bakin kwatan shiyan umma kanne na suka shigo da leda shake da abin motsa baki suna fadin cikin murna Jamil ne ya saya masu.
Ina kokarin fadin su rage murya kada umma ta jiyo su sai ko gata tafito but daga dakin tana fada cikin hasala wani jamilun din badai na gidan babbaku ba danayi mashi iyaka daku ?
Wanan yaron kamar jikan mayu da bakin naci haka na fada mai na mashi iyaka daku a garin nan Baffa kanina yace umma mu hadiza ne da za a hanamu fita gurin shi.
Dakuwa tayi mai da hannu tana zagin shi tace dama zubin arnan da gare ka dan nema mara kunya ya juya zuwa dakin mu yana bata rai da zagin da tayi mashi din.
Ko kafin in zo dakin na samu ya fitar da kayan yana ci fada na fara mai don may suka karbo mai kayan shi yanzu gashi sun sa umma fada damu haka.
Yace idan ke baki ci ki barmu muci ai ba rokon shi mukayi ba ko tun ina jin haushi har na dauki gwangwanin maltina daya na bude ina kurbawa.
Daidai lokacin umma ta dago labulen dakin tana fadin watau ma bakuji maganata ba ko in kuce kwadai ne ai wurin shi zaku mutu.
An fada maku kauye ana haka ne a banza idan yasa maki asiri a ciki fa garin bakin kwadai ki bishi kamar karya kuwa.
Dan maltinan dana fara sha ne nake kokarin amayarwa don abinda naji umma ta fadi don ina tsoron asiri kamar yadda umma din ta fada.
Kanina yace humm, abin da a gaban mu ya sai muna wani magani zai sa a ciki kuma ni dai tsoron maganan umma ya kamani don haka naki cin komai a cikin kayan suka cinye shi tas suna santi.
Kamar yadda mukai alkawari da su da dare sai gasu sun aiko inzo da yake mai wayau suka aiko sai umma bata san na fita ba har na dawo bata sani ba .
Daddan kalaman shi gare ni sunyi tasiri sosai a raina tun daga wanan ranan muke haduwa duk dare ba tare da kowa ya san da haka ba cikin iyayyena har umma din.
Sai ranan ne ta gane hakan aiko mun sha masifa dan gaba dayan mu ta hade tayi muna tas tare da alkawarin sai ta fada ma mahaifin mu wanan maganan.
Tsoron kada ta fadi yasa na kama kaina kwana biyu don ina matukar tsoron mahaifin mu din tunda ya muna warning akan hakan da dadewa.
Sai dai dadadan kalaman jamil suna min yawo har yanzu a zuciyana sun ki fita min a raina sai nake ganin duk duniya babu mai kaunata da yan uwana irin shi.
Haka yasa alamarin shi yaki fita a raina sam hakana nake samun in dan kebe dashi mu danyi hira sama sama dashi ba tare da an fahunci hakan ba a gida.
Don ita umma tana ganin na fita batun shi a yadda nake nunawa a gabanta gashi dogon hutu muka samu zamu share wurin wata biyu a gida kafin mu koma lokacin ana bada hutu yadda ya kamata ba irin yanzu ba don damana ne.
Jamil dai dan kauye ne amma ya banbanta da mutanen kauyen mu wuein iya tsara kwaliyan shi da shigashin daban yake shi sai dai gajere ne baida wani tsayi sosai irin na wasu maza.
Zan iya cewa ko mu dake abuja bamu fishi iya kwaliya ba don haka yake kamar mace wurin tsara ado da shiga kamar dan wasu manyan mutane can.
Niko irin matan nan ne daba wani kyau gare ni ba can ina dai tsaka tsakiya ne kawai don banda abinda za a zuzuta a gare ni sai dai ilimin kawai da Allah ya bani.
Baba kabiru ya kawo muna ziyara a dan zaman mu na kauyen da mukeyin hutun mu tare da wasu kayan da zamuyu amfani dashi irin sabulun wanka su omo da man shafi sai taliya da idomie daya zo muna dashi.
Kwanan shi daya a tare damu ya koma tare da fadin idan lokacin komawan mu ya matso umma ta sheda mashi da wuri.
Munji dadin kayan dama wanda mahaifin mu ya sai muna ya kusa karewa sai maneji mukeyi dasu kawai gashi bai kara bi ta kan mu ba tunda ya turo mu kauyen.
Kanne na na yawan maganan shi akoda yaushe sai ince dasu aiki ne yayi mashi yawa sun san yadda aikin su yake.
Hakan kan sa su manta da zancen don ko kadan ban bari su shiga damuwa a garin koda yaushe ina tare dasu sai mazab dakan dan fita yawo duk da muma ba wani shamaki akai muna da fita ba kowani lokaci.
Ban san yadda akayi umma tasan da wanan zancen ba na ina kebewa da Jamil ranan ta haukace muna sosai tace ko mutuwa zanyi ba zan auri jamil ba wahal da kaina kawai nakeyi a banza.
Kuma ko bayan ranta mukai aure dashi sai ta taso muna fatalwa ta hana mu zaman lafiya wanan zancen nata ne ya kara tsoratani.
Sai ma na matsu mu koma abuja mu bar garin don samun salama a raina da saukin komai don fitinan ta ya isheni har muka kusa komawa schoool muka fara shirye shiryen komawa abuja.
Duk da muna sa rai zamu koma da umma ne tunda ita ke zaune damu a can dama tun bayan rasuwan mama.
Ashe abin ba haka yake ba don umma ta tace bazata koma wanan gari ba sai dai mahaifin mu ya barmu a nan mu zauna tare da ita din.
Ranan sai ganin baba kabiru mukayi yazo garin sun dade daki da umma dasu baba yushau da baba musa suna tattaunawa akan zancen mu ne ashe.
Bamu dai san yadda akayi ba baba kabiru ya fice da bacin rai yakai dare a garin mun dauka a nan zai kwana sai da yazo sallaman mune yake fada muna tare da wata gwagon mu zamu tafi don haka mu shirya nan da kwana uku zamu wuce.
Bamu san matar ba da akace zamu tafi da ita mudai burin mu kawai muga mun koma Abujan gurin mahaifin mu ko ta halin kaka.
Ranan tafiyan mu yazo motar da baba kabiru yayo muna shata zata kaimu har abuja ta iso muka shirya sai lokacin ne muka san matar da zamu koma Abuja da ita ta zauna damu a can.
Muka dauki hanyan abuja cike da bacin ran rabuwa da yan uwa da abokan arziki da zamuyi a nan gida Allah ya sauke mu lafiya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:49 PM - 🤔🤔🤔: 🙆🏼♂️ KANIN AJALI 🙆🏼♂️
9️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI DA CIKAWA DA IMANIN UBANGIJI A KARSHEN MU UBANGIJI YASA MUFI KARFIN ZUCIYAR MU AMIN 👏
TO ANCE KADA INJA ALLAH YA ISA BAI DACE BA, KUMA SAI KU MUNA ADALCI, KU DAINA FITAR MUNA DA NOVEL DON GIRMAN ALLAH, DON HAKA WACE TA FITAR KUMA KA GANI KA KARANTA SAI MU BARKU GA ALLAH SHIKE NAN SHI YASAN TSAKANIN MU DAKU, , ,
Bamu dade da dawowa daga gida ba sati daya na kara na koma school don na samu baba ya gama min shirin komawa makaranta.
Nan na bar kanne na da gwagon mu da muka zo da ita na barsu ban gama fahintar yadda rayuwan ta yake da yadda zata zauna tare da yan uwana.
Don hankalina sam bai kwanta da yanayi wanan matar ba don ina ganin zatayi fada don haka zata kwasa da kanne na a gida dana barsu tare.
Ban yi wani nisan zango ba mahaifina yakawo min ziyar sai dai na kula ya danyi rama kadan da baki wanda na dauka duk yana cikin damuwa rashin mahaifiyar mu da yanayin da yake ganin mu a ciki na ban tausayi.
Ga maganan auren shi tun bayan rasuwan mahaifiyar mu bamu kara jin magana ba a gidan itama kanta ta rage kiran shi kamar baya can.
Ashe rikici suka yi da ita wai ba zata zauna ta dubu yaran shi ba shikuma ya yace ba zai iya rabuwa da yaran shi ba gaskiya.
Shine rikicin da sukeyi a tsakanin su har ya kawo tsaikon auren mukaji shiru zuwa wanan lokacin don mun ki jinin matar tundai kauna ta summaiya bata kaunan ai maganan karin auren baba a gaban ta ko kadan.
Yanzu zata kama zagi tana aibanta matar har wace ta hada auren zata zage ko a gaban waye duk da ba wani shekuru ke gare ta ba amma akwaita da tsananin kishin tsiya.
Ita a dole tana taya mahaifiyar mu kishi tana fadin ai da baba baiyi zancen auren ta ba lafiya kalau maman mu ke haihuwanta.
Wanan ke nan wanan time din mun dawo gida na samu kanne na sun rama sunyi baki raina ya baci da ganin hakan ko ban tambaya ba nasan zaman su da gwagon namu ne babu dadi.
Mun samu kebewa da sune suke fada min ciwo sukai tayi har da kwanciya asibiti nayi masu sannu baba ma yai min bayanin irun ciwon da sukayi a bayana din sosai.
Abin farko dana fara kula dashi wanan gwagon tamu sam jinin mu baizo daya da ita ba idan ina falo tana daki idan kuma daki nake ita tana falo don a dakin mu ta sauka.
Ranan cikin dare ina barci na falka na ganta tsirara tsaye da wani kwarya a kaina wani irin ihu na yanka gashi mahaifin mu baya gida yana aikin dare ne ranan.
Ihu na ne ya tayar da yan uwana a tsorace duk da basu san may ya faru ba suma suka shiga tsoron a lokacin.
Ban iya fada ma kowa abinda ya faru ba ranan sai dai muna yar tsama da wanan matar da aka kira da gwagon mu mai zama damu.
Sai ta so ta dora min tsangwama tana fadawa mahaifi mu wai ina mata rashin kunya nan zai kamani ya zage ni fes a kanta.
Abinda bamu sani ba ashe matar manyace aka dauko aka kawota zama damu abuja cikin rashin sani wanan yawan ciwon da yan uwana ke fama dashi duk itace ummul,abasin ciwon su.
Kwatsam sai ga umma ta dira abuja kamar daga sama tana zuwa matar tasha jinin jikin ta nan umma ta shiga yadda magana kamar haka.
Mugu sai dai ya harari kayana ya barshi, idan yace zai taba kayana sai dai su tafi tare da maishi banci dan kowa ba babu mai zuwa ya taba min nawa.
Idan mutum yace shi takaman shi sheri ne ya zo karshen sheri a rayuwan shi don asirin shi ya kusa tonowa a garin nan ire iren maganganun da umma kan zauna a falo tana sakewa ke nan.
Idan baba yana gida zai tambayi umma wai da ita da waye take wanan magana haka sai tace mai ya barta ta fadi ai mashi yasan kanshi.
Ranan dai gwagon ta tayar da hankali wai zata koma gida tunda umma tazo dama don babu kowa tare da mune baba kabiru ya roketa tazo.
Batai wani kwanaki ba ta tafi ta barmu bayan baba yayi mata goma sha tara na arziki tana ta godiya aka sakata a mota da zai kaita jahan mu.
Ranan ne umma ta zauna da baba tana fada mashi mugun halin gwagon namu da taji daga baya wanda hakan ne ya tayar mata hankali ta biyo mu.
Mahaifin mu dariya yayi yana fadin may yasa kuke yarda da irin maganganun nan don Allah wanan duk camfine wallahi.
Nan nake fada masu yadda na ganta ranan da bamu kara shiri da ita ba har ta tafi ke nan umma tace kaji ba aniyar kura ta bita ba a cikin kayana ba kan.
Na koma school na bar gwagon mu a nan inda wanan zuwa da yar gurin baba musa tazo sai da mahaifina ya nuna rashin yardan shi akan zuwan da tayi da yarinyar da farko.
Don shi bai ra,ayin rike dan wani a rayuwan shi yasa nashi ma bai yarda yan uwa suka dauka ba ina makaranta ne ciwo ya kama mahaifin mu lokacin mahaifitar mu tana da shekara biyu da rasuwa ke nan.
Sai dai bai kwanta ba tsatsaye yake jiya muna samun hutun makaranta umma tace tunda yaji sauki gida zatazo damu mu kwana biyu.
Mun dawo gidane muka barshi can sai kuma ya samu sauyin wurin aiki ya koma Niger state da aikin shi satin mu uku da zuwa gida ke nan ya samu wanan sauyin.
Lokacin ne abubuwa suka taru sukai mai yawa dole yazo yayi reporting don kada ya samu matsala satin shi biyu a minna har ya samu gida inda zai zauna da iyalin shi sai kuma ciwo ya dawo mashi sabo.
Da yan wuein aikin sukaga ba zasu iya ba aka tada mota a kawo shi gida wurin iyalin shi da yamma lis suka iso wurin baba kabiru dashi.
Hankalin baba kabiru ya tashi sosai yadda yaga dan uwan shi ya koma a lokaci guda ciwon dai baiyi kama dana asibiti ba sam.
Haka dai suka dauke shi zuwa asibiti suna hadawa dana gargajiya da farkon zuwan shi yana magana don har yana ma baba kabiru bayanin yadda yake jin jikin nasa a lokacin.
Nan dai baba kabiru ya gane abin kamar sammune akai mashi hankali ta kara tashi sosai umma ta samu labarin ciwon nasa inda hankalin ta yayi matukar tashi
Dama yan uwan shi kowa na nuna kulawan shi akan mu a matsayin su na yan uwan mahaifin mu din a gare mu.
Saidai mu bamu ganin hakan da suke muna dan abu kadan zamu dauka don mahaifiyar mu bata da raine ake muna wani abin da bai dace ba.
Yinin ranan haka nayi shi a dakin ba wani walwala a tare dani sai ma gyaran dakin da na tsiri yi tankar mahaifiyar mu tana nan a cikin sa ne kamar yadda naga tana yi idan munzo tare da ita garin.
Sai yama lis na watsa ruwa a jikina kofan umma na dawo na zauna muna hira da yan uwana a gurin ta fito daga daki tana fadin kin ga dama kin fito ke nan don maganan da nayi maki jiya kike fan fushi haka yau.
Nace ba haka na bane aikin dakin mu nayi don yayi kura da yawa sosai ta tace ke dai kika sani idan kin sa kanki a damuwa haka ma yan uwan ki ba zasu sake ba don basu ga kina walwala ba .
Shiru nayi ina fadin a raina walwala ai ya kare a gurin mu umma tunda mun rasa mahaufiyar mu ko a duniya.
Maganan ta ne ya dawo dani ga tunanen da nakeyi tana fadin idan ba zamu iyacin abincin da akayi ba a gidan mu dafa taliya muci da dare.
Don mahaifin mu bai barmu munzo hakana ba garin sai da ya sawo muna duk wani cimar daya san muna amfani dashi a can muka zo dashi gida.
Tambayan kanne na nayi idan zasu ci da sauri suka amsa min haka yasa na tashi don in dafa muna taliyan tunda suna son ci na sani dolene kawai yasa suke cin abincin gari.
Mungama muka taru a gurin umma din nan mukaci taliyan sai dai itako kallo bai ishe ta ba tuwon ta da aka kawo muna taci.
Bamu wani dade ba muka kwanta don dare yayi a lokacin sai dai ni ba barci ne nayi ba na dai kwanta ne ina tunanen duniya a lokacin.
Tunda muka zo ko hanya bai hadani da jamilu ba har yakai satin mu daya da zuwa garin duk ko shima yana cikin garin a lokacin.
Yau ya kama kasuwan kauyen mu ne kowa sai hada hadan sana,ar shi yakeyi don fita dashi gurin yan kasuwa in ka debe mu da bamu komai sai dai mu wanke mu saka don yanayin mu daya dan banbanta dana yan gari.
Sai dai duk da haka ba,a barmu a baya ba don muma munyi kwalliya mun saka kaya masu kyau don muna da muradin shiga kasuwan mu dan zagaya.
Saboda akwai kudi a hannun mu bayan wanda baba ya ba umma don lalurar mu na yau da kullun da wani matsala daka taso a gare mu a gidan.
Kamar yadda tsoho keda naci a kudi haka ma yaro yake da kunata akan kudi don su sauran basu san baba ya bamu kudin ba a hannu na.
Mun gama shiri muka sallami umma don abokai na da suka shigo don mu fita sai dai ni abinda ke ban mamaki shi su hafsa kawana ba karatun sukeyi ba kuma su ba aure sukayi ba har yanzu.
Mun fita mun dan zaga abin marmari na sayo muna da kannen na don mun dade bamu ci ba a can mun juyo zamu dawo gidane muka hade da su jamil da kungiyar su.
Ashe sun saka ido a kan mu suga fitowan mu take dan leken asirin su ya sheda masu mun fito garin muna zagawa a kasuwan sai gasu sun sha kwaliyan su zakace ba yan kauye bane su.
Kallon juna mukayi na sada kaina kasa don kunya su a dole ga samarin da suka ga yan mata suka zo da guntun turancin su don su burge mu saboda mun fito birni musan sun iya turanci.
Da sumaiya kawanta suke turancin sai kanne na maza da muke tare suke buga turanci dasu suna jin dadin yadda yaran ke amsa su.
Na dago yana fadin baby ya kike ne kwana biyu bamu hadu ba ya mukaji da hakkurin rashin mama kuma sai lokacin naji wani iri a raina.
Don haka nake da an min maganan mama hankalina sai ya tashi sosai mutuwan ya dawo min sabo a raina.
Mun dan dade a gurin tsaye dasu suka rokeni da dare in basu lokaci su samay ni a gida mu kara gaisawa don nan ido yayi muna yawa akan mu.
Na matsu in bar gurin haka yasa mukai sallama dasu muka wuce zuwa gida inda kannena maza suka bisu kamar yadda suka bukata suyi.
Yalon da muka sayo kasuwa ne nake wankewa a bakin kwatan shiyan umma kanne na suka shigo da leda shake da abin motsa baki suna fadin cikin murna Jamil ne ya saya masu.
Ina kokarin fadin su rage murya kada umma ta jiyo su sai ko gata tafito but daga dakin tana fada cikin hasala wani jamilun din badai na gidan babbaku ba danayi mashi iyaka daku ?
Wanan yaron kamar jikan mayu da bakin naci haka na fada mai na mashi iyaka daku a garin nan Baffa kanina yace umma mu hadiza ne da za a hanamu fita gurin shi.
Dakuwa tayi mai da hannu tana zagin shi tace dama zubin arnan da gare ka dan nema mara kunya ya juya zuwa dakin mu yana bata rai da zagin da tayi mashi din.
Ko kafin in zo dakin na samu ya fitar da kayan yana ci fada na fara mai don may suka karbo mai kayan shi yanzu gashi sun sa umma fada damu haka.
Yace idan ke baki ci ki barmu muci ai ba rokon shi mukayi ba ko tun ina jin haushi har na dauki gwangwanin maltina daya na bude ina kurbawa.
Daidai lokacin umma ta dago labulen dakin tana fadin watau ma bakuji maganata ba ko in kuce kwadai ne ai wurin shi zaku mutu.
An fada maku kauye ana haka ne a banza idan yasa maki asiri a ciki fa garin bakin kwadai ki bishi kamar karya kuwa.
Dan maltinan dana fara sha ne nake kokarin amayarwa don abinda naji umma ta fadi don ina tsoron asiri kamar yadda umma din ta fada.
Kanina yace humm, abin da a gaban mu ya sai muna wani magani zai sa a ciki kuma ni dai tsoron maganan umma ya kamani don haka naki cin komai a cikin kayan suka cinye shi tas suna santi.
Kamar yadda mukai alkawari da su da dare sai gasu sun aiko inzo da yake mai wayau suka aiko sai umma bata san na fita ba har na dawo bata sani ba .
Daddan kalaman shi gare ni sunyi tasiri sosai a raina tun daga wanan ranan muke haduwa duk dare ba tare da kowa ya san da haka ba cikin iyayyena har umma din.
Sai ranan ne ta gane hakan aiko mun sha masifa dan gaba dayan mu ta hade tayi muna tas tare da alkawarin sai ta fada ma mahaifin mu wanan maganan.
Tsoron kada ta fadi yasa na kama kaina kwana biyu don ina matukar tsoron mahaifin mu din tunda ya muna warning akan hakan da dadewa.
Sai dai dadadan kalaman jamil suna min yawo har yanzu a zuciyana sun ki fita min a raina sai nake ganin duk duniya babu mai kaunata da yan uwana irin shi.
Haka yasa alamarin shi yaki fita a raina sam hakana nake samun in dan kebe dashi mu danyi hira sama sama dashi ba tare da an fahunci hakan ba a gida.
Don ita umma tana ganin na fita batun shi a yadda nake nunawa a gabanta gashi dogon hutu muka samu zamu share wurin wata biyu a gida kafin mu koma lokacin ana bada hutu yadda ya kamata ba irin yanzu ba don damana ne.
Jamil dai dan kauye ne amma ya banbanta da mutanen kauyen mu wuein iya tsara kwaliyan shi da shigashin daban yake shi sai dai gajere ne baida wani tsayi sosai irin na wasu maza.
Zan iya cewa ko mu dake abuja bamu fishi iya kwaliya ba don haka yake kamar mace wurin tsara ado da shiga kamar dan wasu manyan mutane can.
Niko irin matan nan ne daba wani kyau gare ni ba can ina dai tsaka tsakiya ne kawai don banda abinda za a zuzuta a gare ni sai dai ilimin kawai da Allah ya bani.
Baba kabiru ya kawo muna ziyara a dan zaman mu na kauyen da mukeyin hutun mu tare da wasu kayan da zamuyu amfani dashi irin sabulun wanka su omo da man shafi sai taliya da idomie daya zo muna dashi.
Kwanan shi daya a tare damu ya koma tare da fadin idan lokacin komawan mu ya matso umma ta sheda mashi da wuri.
Munji dadin kayan dama wanda mahaifin mu ya sai muna ya kusa karewa sai maneji mukeyi dasu kawai gashi bai kara bi ta kan mu ba tunda ya turo mu kauyen.
Kanne na na yawan maganan shi akoda yaushe sai ince dasu aiki ne yayi mashi yawa sun san yadda aikin su yake.
Hakan kan sa su manta da zancen don ko kadan ban bari su shiga damuwa a garin koda yaushe ina tare dasu sai mazab dakan dan fita yawo duk da muma ba wani shamaki akai muna da fita ba kowani lokaci.
Ban san yadda akayi umma tasan da wanan zancen ba na ina kebewa da Jamil ranan ta haukace muna sosai tace ko mutuwa zanyi ba zan auri jamil ba wahal da kaina kawai nakeyi a banza.
Kuma ko bayan ranta mukai aure dashi sai ta taso muna fatalwa ta hana mu zaman lafiya wanan zancen nata ne ya kara tsoratani.
Sai ma na matsu mu koma abuja mu bar garin don samun salama a raina da saukin komai don fitinan ta ya isheni har muka kusa komawa schoool muka fara shirye shiryen komawa abuja.
Duk da muna sa rai zamu koma da umma ne tunda ita ke zaune damu a can dama tun bayan rasuwan mama.
Ashe abin ba haka yake ba don umma ta tace bazata koma wanan gari ba sai dai mahaifin mu ya barmu a nan mu zauna tare da ita din.
Ranan sai ganin baba kabiru mukayi yazo garin sun dade daki da umma dasu baba yushau da baba musa suna tattaunawa akan zancen mu ne ashe.
Bamu dai san yadda akayi ba baba kabiru ya fice da bacin rai yakai dare a garin mun dauka a nan zai kwana sai da yazo sallaman mune yake fada muna tare da wata gwagon mu zamu tafi don haka mu shirya nan da kwana uku zamu wuce.
Bamu san matar ba da akace zamu tafi da ita mudai burin mu kawai muga mun koma Abujan gurin mahaifin mu ko ta halin kaka.
Ranan tafiyan mu yazo motar da baba kabiru yayo muna shata zata kaimu har abuja ta iso muka shirya sai lokacin ne muka san matar da zamu koma Abuja da ita ta zauna damu a can.
Muka dauki hanyan abuja cike da bacin ran rabuwa da yan uwa da abokan arziki da zamuyi a nan gida Allah ya sauke mu lafiya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:49 PM - 🤔🤔🤔: 🙆🏼♂️ KANIN AJALI 🙆🏼♂️
9️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI DA CIKAWA DA IMANIN UBANGIJI A KARSHEN MU UBANGIJI YASA MUFI KARFIN ZUCIYAR MU AMIN 👏
TO ANCE KADA INJA ALLAH YA ISA BAI DACE BA, KUMA SAI KU MUNA ADALCI, KU DAINA FITAR MUNA DA NOVEL DON GIRMAN ALLAH, DON HAKA WACE TA FITAR KUMA KA GANI KA KARANTA SAI MU BARKU GA ALLAH SHIKE NAN SHI YASAN TSAKANIN MU DAKU, , ,
Bamu dade da dawowa daga gida ba sati daya na kara na koma school don na samu baba ya gama min shirin komawa makaranta.
Nan na bar kanne na da gwagon mu da muka zo da ita na barsu ban gama fahintar yadda rayuwan ta yake da yadda zata zauna tare da yan uwana.
Don hankalina sam bai kwanta da yanayi wanan matar ba don ina ganin zatayi fada don haka zata kwasa da kanne na a gida dana barsu tare.
Ban yi wani nisan zango ba mahaifina yakawo min ziyar sai dai na kula ya danyi rama kadan da baki wanda na dauka duk yana cikin damuwa rashin mahaifiyar mu da yanayin da yake ganin mu a ciki na ban tausayi.
Ga maganan auren shi tun bayan rasuwan mahaifiyar mu bamu kara jin magana ba a gidan itama kanta ta rage kiran shi kamar baya can.
Ashe rikici suka yi da ita wai ba zata zauna ta dubu yaran shi ba shikuma ya yace ba zai iya rabuwa da yaran shi ba gaskiya.
Shine rikicin da sukeyi a tsakanin su har ya kawo tsaikon auren mukaji shiru zuwa wanan lokacin don mun ki jinin matar tundai kauna ta summaiya bata kaunan ai maganan karin auren baba a gaban ta ko kadan.
Yanzu zata kama zagi tana aibanta matar har wace ta hada auren zata zage ko a gaban waye duk da ba wani shekuru ke gare ta ba amma akwaita da tsananin kishin tsiya.
Ita a dole tana taya mahaifiyar mu kishi tana fadin ai da baba baiyi zancen auren ta ba lafiya kalau maman mu ke haihuwanta.
Wanan ke nan wanan time din mun dawo gida na samu kanne na sun rama sunyi baki raina ya baci da ganin hakan ko ban tambaya ba nasan zaman su da gwagon namu ne babu dadi.
Mun samu kebewa da sune suke fada min ciwo sukai tayi har da kwanciya asibiti nayi masu sannu baba ma yai min bayanin irun ciwon da sukayi a bayana din sosai.
Abin farko dana fara kula dashi wanan gwagon tamu sam jinin mu baizo daya da ita ba idan ina falo tana daki idan kuma daki nake ita tana falo don a dakin mu ta sauka.
Ranan cikin dare ina barci na falka na ganta tsirara tsaye da wani kwarya a kaina wani irin ihu na yanka gashi mahaifin mu baya gida yana aikin dare ne ranan.
Ihu na ne ya tayar da yan uwana a tsorace duk da basu san may ya faru ba suma suka shiga tsoron a lokacin.
Ban iya fada ma kowa abinda ya faru ba ranan sai dai muna yar tsama da wanan matar da aka kira da gwagon mu mai zama damu.
Sai ta so ta dora min tsangwama tana fadawa mahaifi mu wai ina mata rashin kunya nan zai kamani ya zage ni fes a kanta.
Abinda bamu sani ba ashe matar manyace aka dauko aka kawota zama damu abuja cikin rashin sani wanan yawan ciwon da yan uwana ke fama dashi duk itace ummul,abasin ciwon su.
Kwatsam sai ga umma ta dira abuja kamar daga sama tana zuwa matar tasha jinin jikin ta nan umma ta shiga yadda magana kamar haka.
Mugu sai dai ya harari kayana ya barshi, idan yace zai taba kayana sai dai su tafi tare da maishi banci dan kowa ba babu mai zuwa ya taba min nawa.
Idan mutum yace shi takaman shi sheri ne ya zo karshen sheri a rayuwan shi don asirin shi ya kusa tonowa a garin nan ire iren maganganun da umma kan zauna a falo tana sakewa ke nan.
Idan baba yana gida zai tambayi umma wai da ita da waye take wanan magana haka sai tace mai ya barta ta fadi ai mashi yasan kanshi.
Ranan dai gwagon ta tayar da hankali wai zata koma gida tunda umma tazo dama don babu kowa tare da mune baba kabiru ya roketa tazo.
Batai wani kwanaki ba ta tafi ta barmu bayan baba yayi mata goma sha tara na arziki tana ta godiya aka sakata a mota da zai kaita jahan mu.
Ranan ne umma ta zauna da baba tana fada mashi mugun halin gwagon namu da taji daga baya wanda hakan ne ya tayar mata hankali ta biyo mu.
Mahaifin mu dariya yayi yana fadin may yasa kuke yarda da irin maganganun nan don Allah wanan duk camfine wallahi.
Nan nake fada masu yadda na ganta ranan da bamu kara shiri da ita ba har ta tafi ke nan umma tace kaji ba aniyar kura ta bita ba a cikin kayana ba kan.
Na koma school na bar gwagon mu a nan inda wanan zuwa da yar gurin baba musa tazo sai da mahaifina ya nuna rashin yardan shi akan zuwan da tayi da yarinyar da farko.
Don shi bai ra,ayin rike dan wani a rayuwan shi yasa nashi ma bai yarda yan uwa suka dauka ba ina makaranta ne ciwo ya kama mahaifin mu lokacin mahaifitar mu tana da shekara biyu da rasuwa ke nan.
Sai dai bai kwanta ba tsatsaye yake jiya muna samun hutun makaranta umma tace tunda yaji sauki gida zatazo damu mu kwana biyu.
Mun dawo gidane muka barshi can sai kuma ya samu sauyin wurin aiki ya koma Niger state da aikin shi satin mu uku da zuwa gida ke nan ya samu wanan sauyin.
Lokacin ne abubuwa suka taru sukai mai yawa dole yazo yayi reporting don kada ya samu matsala satin shi biyu a minna har ya samu gida inda zai zauna da iyalin shi sai kuma ciwo ya dawo mashi sabo.
Da yan wuein aikin sukaga ba zasu iya ba aka tada mota a kawo shi gida wurin iyalin shi da yamma lis suka iso wurin baba kabiru dashi.
Hankalin baba kabiru ya tashi sosai yadda yaga dan uwan shi ya koma a lokaci guda ciwon dai baiyi kama dana asibiti ba sam.
Haka dai suka dauke shi zuwa asibiti suna hadawa dana gargajiya da farkon zuwan shi yana magana don har yana ma baba kabiru bayanin yadda yake jin jikin nasa a lokacin.
Nan dai baba kabiru ya gane abin kamar sammune akai mashi hankali ta kara tashi sosai umma ta samu labarin ciwon nasa inda hankalin ta yayi matukar tashi