Showing 51001 words to 54000 words out of 299981 words
ya taru yai mata yawa a rai don a gurin Jamila matar Nura kawai take dan samun sassauci a gidan,
Ko shi ba wani can mai yawa ba saboda ta fahinci a kwai rashin mutunci a tare da Kubura din,
Gashi kimanin kwanaki takwas ke nan rabon da taga Nura a idon ta,
Kullun bata sani dawowan shi kuma bata sanin fitan shi gidan,
Sai da abinda take zato ko tsanmani shine, yana dawowa ne a cikin dare da,asuba yake kuma,barin gidan,
Jamila ce ta dan tako a inda take zaune tana cewa kauna ta wallahi yau naso naga mai gidan akan zancen kayan store din mu amma kuma lafins nane daban fada maki tun jiya ba ki fada mai, gashi yafita kuma ina ga mai ma na yau kawai ya rage,
Tace a cikin dan sakin fuska aiko da tun jiya naji da na fada mai ,gashi ya fita tun safe kamar yadda ya saba fita,
Jamila tace ai nace laifina ne amma kada ki damu zan dan yi dubara don baza rasa abin yi ba ai,
Ta mike dingis dingis ta yi hanyar fita waje ta kiran yar aikin su dake daga waje,
Kubura tabita da wani wawan kallo tana cewa gurguwar banza kawai sai na ture dan kafa gudan wata rana naga tsiyan botsewa ta bayan nan,
Har kwana goma,sha bata sake ganin Nuran ba sai a daren na sha biyar ne tana kwance a cikin dare taji motsin shigowar mutum dakin,
Dakyat ta bude nauyayan idanuwan ta dake cike da,barci a cikin su,
Ta gefen ta ya kwanta a hankali inda yaja bargo ya dan rufe su aciki a tare,
Batai tsanmanin cewa ya kai ga gamsawa da abinda yake so ba taji yaja tsaki,
Inda ya mike yakai wani lokaci a gurin window dakin a tsaye can taji yabar dakin a cikin bacin rai,
Gaban Kubura ya yanke ya fadi inda take cewa kar,dai ace shiga tsakanin su akayi da angon nata Nura,
Haka gari ya waye mata a cikin tunanen abinda ke faruwa a tsakanin su da mijin nata,
Sai dai tasha alwashin cewa zata ci gaba da boye sirinta bazata yarda har mazauna gidan su fahinci cewa akwai matsala a tsakani ta mijin nasu ba ,
Abinda bata sani ba shine Jamila ksllon ta kawai takeyi don ta,fahinci akwai matsala tun farko a tsakanin mijin nasu da amaryan shi Kubura,
Don ita fa Uwargida ce duk wani motsi na duk wanda ke acikin gidan yana a idanuwan ta,
Sai dai kawai ta nuna rashin ko in kula a fili tunda ba a tambaye ta komai ba a zance,
Idan mutum ya ga Kubura zai yi zaton cewa tana a tare da farin ciki saboda akwai ci da sha a gidan ga sutura na alfarma,
Abu guda yai mata nisa shine so da kauna mijin da take zaune a gidan shi a matsayin mijin aure,
Kubura karo na farko da tazo gida inda take matukar son hanin mahaifitar ta don duk fadin duniyan nan babu wanda zata iya fadawa matsalan ta,sai mahaifiyan nata,
Kubura wace ta,shigo gidan su da yar makalalan fara,a a fuskan ta,
Amma bai hana su Ummi da Atika su fahinci cewa akwai matsala a tare da ita,
Atika ce uwar shishigi take cewa da mai gidan naki kuke be ?
Kubura tai wani dan tabe fuska tana cewa yanzu ya ajeni ya tafi bazai samu shigowa ba sai yadawo,
Ummi ta dan karaso ida suke tana wa Kubura din yaya, gida da mutanen gidan ba,wai sun damu da sai ta,shigo ta gaida su ba,
Badon komai ba,sai don sani halinta da,sukayi na tsageranci tun a gida balle yanzu da take ganin cewa ita ma matar daki ce kamar kowa,
Daki mahaifiyan ta ta shiga inda mama Saude wace ke wanki a bakin kwatan gidan ta taso tabi yar nata daki wace ta shigo da,alamar a gajiye take,
Mama Saude na,shiga daki ta,samu Kubura kwance saman gado rigingine,
Tace a cikin yar fara,ar ta ashe kuna tafe shine bamu sani ba nadan maki tanadin wani abu,
Dagowa Kubura tayi daga kwancen da take tace cikin bata fuska mama barshi kawai ba wanan bane matsala,
Sai ga hawaye shar daga idanuwan Kubura tana fadin mama wallahi a kwai matsala sosai,
Kofa Mama ta,duba da,sauri idan babu mai shigowa dakin a lokacin,
Tace wa yar nata share hawayen ki kada wani yazo ya,ganki a haka kina kuna,
Juyawa mama tayi zuwa waje don ta dan saka mutana fita daga zargi inda tabar kubura din tana darzan kukan ta ita kadai a daki sai da tai mai isar ta tagaji don kan ta ta share hawayen ta,
Mama Saude wace duk abinda take hankalin ta a tashe yake,sai faman tunane take ko daga ina aka samu matsala da yarta,
Shin da abokiyar zaman ta ne ko da maigidan nasu ne take da,matsala,
Mama Saude ta koma dakin a lokaci yar nata ta dan samu natsuwa daga kukan da takeyi
Jin shigowar mahaifiyar ta yasa ta dan dago kai tana sauke sanyayar ajiyar zuciya,
Mama Saude ta samu guri ta zauna don ta ji may ke faruwa da yar nata alfaharin ta,
Ki natsu Kubura ki min bayanin may ke faruwa,ne wai daga ina kuma matsala ta,fito maki, tafa a cikin dan tausa murya,
Cikin dan sauta murya take cewa wallahi mama daga Nura din ne amma don kwata kwata tun ranan da na,shiga gidan ban da wani matsayi mai muhinmanci a gare shi,
Sai kiramin yake wai muncuce shi mun zalunce shi mun mai munafunci,
Da,sauri mama tace mata a kan may kuma Kubura ?
Mama nima ban sani ba wallahi abinda dai yake yawan fadamin ke nan a duk ranan da muka kasance a tare dashi,
Kubura ko kin taba sanin wani da namiji ne a,waje kafin kiyi aure, ?
Da sauri Kubura ta dago kai a cikin hawaye tace wa uwar nata ,a,a mama, wallahi ban taba kwaci da kowa a waje ba,
To idan ko har hakane shiga tsakanin ku akayi ke nan ?
Kubura tana kokarin tsayar da hawayen ta take fadin nima wallahi mama tunanen da nakeyi ke nan ,
Don wallahi matar nan tashi ba karamar munafuka bace don nuna min take wai ita ta Allah ce a fili gata abin tausayi amma,sherin ta yai yawa,
In kin ga yadda yake wani nan nan da ita da yaran ta a gidan sai abin ya baki mamaki kamar ba gurguwa bace,
Mama Saude tace ai nasan irin su ko bagani dasu ba,a gida badon ina tsaye ba agidan nan da ai yanzu sai tarihi na ko,
Don haka ya zama dole mu dauki mataki akan ta zata san da cewa dani take, ai,,,
Haka kubura tai yini daga baya tadan sake jiki tafito waje inda suka dan taba hira da matan gidan nasu sama sama,
Har take tambayan Ummi labarin Aisha Ummi bata bata amsa ba amma Atika ke fada mata cewa ai Hamza ya koma makaran ta sokoto karo ilimi,
Kubura tace wata sabuwa kuma,
****** ********** ******
Abinda ya daure min kai yanzu shine tun tafiyan Hamza makaranta na rage yawan aiyukan da,nake a gidan Umma Rabi,
Yanzu a tsakani na da ita sai wani haba haba take min, ba tsangwama ba,takura,,
Idan ina daki itace zata kwada min kira tace nazo ko nafito mu sha iska a,waje,
Akan shigo da,waya wani lokaci daga waje wurin abokan shi sai mu gaisa da shi, daya bayan dayan ,
Sai dai hiran da shi da Umma yafi daukan lokaci don bata bari na dauki lokaci muna hira, balle ma ni may zance mai,
A wani safiyane muka tashi da labarin cewa motar yan zuwa kasuwar kauye ta,yi accident,
Hakan yasa hankalin mu tashi don mun san cewa akwai mutanen uguwar mu masu zuwa don da farko har da Ibrahim za ai wanan tafiyan amma sai daga baya yace bazai samu zuwa ba don rana yayi a lokacin,
Amma Baba Mudi yana a cikin motor cewa Ibrahim wanda yazo yana fada muna,wanan labarin na tashin hankali,
Hakalin mutane duk a tashe yake a lokacin kafin aji labarin halin da suke ciki,
Sai zuwa dan rana akasamun labarin cewa al,amari da sauki sai dai sunji ciwo daga cikin su akwai masu kariya wasu kuma basu ji ciwo ba ma sosai,
Shi Baba Mudi yadan samu gwaucewa a kafadar shi hakane yasa bayan an ja mai akadawo dashi gida daga asibiti,
Yan uwa da abokan arziki sai shiga suke don zuwa duba lafiyan Baba mudi wanda a zahiri yake jin jiki,
Duk yaran shi masu aure a lokacin suna gida gurin ganin jikin mahaifin ns su,,
Ganin hakane yasa Ibrahim wanda ke zaune waje yana ganin mutane na ta shiga yashigo gidan ,
Yana kwada min kira a kwance nake lokacin dakina kadaici yana damuna,
Sai nake jin kiran daga sama na taso zuwa waje don naji may yake kirana dashi haka ,
Ina daga labulen dakin nawa na hango shi a tsaye zai shiga dakin Umma yana fadin ki shirya ki shiga gidan ku ki gaida Baba don naga duk yan uwan ki sun shigo gidan, don duban jikin malam din,
Kinga ke gaki a kusa ke ce yadace ace kin fara shiga, amma baki shiga ba har yanzu ,
Yadda ya fahinci fuskana yasa shi gane cewa umurni nake jira daga gurin Umma,
Ibrahim yace kai tsaye jeki shirya ki shiga ki duba lafiyan shi, ki dan zauna har zuwa lokacin da zaku watse,
Umma ce tafito daga bandaki hannun ta dauke da tsohuwar butar ta duk ta mokade take cewa,
Tau rasa kunya kaine ma mai bata umurnin fita ke nan ko,?
To dakata kaji ko mijin da ya ajeta bai isa yace tafitaba kai tsaye ina cikin gidan nan,
Ibrahim yace Umma yanzu may ye rashin kunya aciki mahaifin su ne fa ya auna arziki duk yan uwanta dake nesa sun shigo sai ita dake nan manne dasu ne za,a ce har zuwa yanzu bata shiga ba,
Umma wanan ai sai ki sa mutane su zarge mu akan yarinyar nan, wallahi dama gashi an fara fadin cewa kece ke takurawa yarinyar nan,
Kin ga za,a ce ai fon bashi ya haife ta ba yasa bata shiga gaida,shi ba,
Umma ta aje butan dake a hannun ta tana cewa cikin salati tare da tafa hannun ta,
Ibrahim bai bari ta furta komai ba yake cewa, yanzu dai Umma,don Allah ki bari ta tafi kawai koma maye daga baya zamuyi maganan,
Ya shige dakin ta don ya dauki abincin shi a ciki yayin da yabar Umma a waje tana ta faman sababi dashi,
Daki na koma na gyara jikina na canza tufafin jikina tare da sake hijjab dina,
Na samu Umma a bakin randar ruwan ta tana zuba ruwa a wani kwano mai fadi,
Nake ce mata a,sanyayye Umma zan tafi sai na dawo, ki gayar min dashi don dazun da,aka dawo dashi na,shiga don ina waje suka dawo,
****** ********** ******
Baba yana kwance a saman katuwar tabarman roba a barandar kofan turakan shi Atika tana daga gefe tana mai fitara a hankali,
Nashigo gidan da,sallama na idanuwa na akan baba wanda ke cije labben shi ya na gyara kwanciyar shi a hankali,
Direct inda yake na nufa ina mai gashe shi tare da mashi sannu da jiki da auna arziki,
Daga nan nagaisa da,su mama Saude da Ummi na, dake daga cikin kitchen tana aiki,
A hankali na mike inda na kwabe hijjab dina na rataye a saman kofan dakin Ummina na shiga kitchen din muka karasa aikin a tare,
Su Kubura suna dakin mama Saude suna tahira a cikin kyalkyala darita kamar ba mahaifin su suka shigo dubiya,ba,
A tare Ummi ta,saka muna abinci dasu acikin wani katon ture duk da naci abinci a gida amma Ummi tace naje mu hada hannu dasu,
Anty Sa,a ce kece min bayan nadan samu guri a can gefe na zauna,
Yar Agwai ke dai ba,ruwan ki da zuwa gurin kowa kin yanke zumunci da kowa ko ?
Nai murmushi ina cewa anty ai zan zo sai yadawo gari zan shigo in gaida ku,
Kubura ta tabe baki tana cewa idan ma baki shigo ba ba sai ki ta zama cikin wanan rubaben gidan naku ba,
Anty Sa,a tace haba Kubura wanan wani irin zance ne kuma haka sai kace ba yar uwar ki ba,
Yar Agwai din ?
Tawani dan tabe baki can gefe sai uwale ce ta canza topic din hiran a,daidai lokacin da za,a fara cin abincin dana kawo,
Wai ya zancen wanan abin da kikace zaki aiko min dashi ne ranan?
Nan suka fara hiran irin kayan matan da suke amfani dashi,
Da kuma irin yadda abubuwa ke gudana a tsakanin su da mazajen su,
Wani irin mamaki ne ya rufe a urin bayanan da,suke tun dai Kubura da yarta,
Nan suke musulta abinda ya dace mace ta soma yiwa namiji wanda zai sa macen shiga cikin rayuwan namiji har abada,
Tsit nayi zakace ai bani gurin sai sauraren zancen su nake yayin da idan sun fadi wani magana nakan ji shi a matsayin rashin kunya ne,
Don tayaya za,a ce mace ta zage tanawa namijin irin bayananan da,suke ta fadi a fili,
Ganin hiran nasu bazai kare ba na mike zuwa gurin kara gaida Baba sai a lokacin na shiga daki gurin mahaifiyata,
Tana zaune da yaranta suna cin abinci wanda nake gani tashin su ke nan daga barci take basu abinci
Bayan na zauna ne Ummi ke ce min to yaya labarin mijin naki ?
A kunyace na amsa mata da fadar lafiya kalau ,
Tau ki daiyi ta hakkuri don duk matar da mijinta yake karatu sai tayi hakkuri,
Hakama zama da sararkuwa sai ki yi hakkuri k8n kai zuciya nesa,
Don koda yake naga ai zaman naku ba,wani tsangwama sosai,
Aiki dai ne kuma kin riga da kin iya su ko tun a nan gida don haka ki ta hakkuri, kin dai san irin halin da nake ciki a gidan nan ni duk abinda muti
Um zai yi na kan barshi da,Allah don Allah bai barci ,
Na amsa a hankali da fadan To Ummi nagode insha Allahu zan kula kamar yadda kike fada min kullun,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
👑 SARAUTAR MATA 👑
1⃣5⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Na kamla duk wani aikin da zanyi a,wanan safiyan don yanzu ba,wani aiki mai yawa nakeyi ba,
Don sau daya,muke dada abinci tinda Yaya Hamza baya gari,
Abinci dare kawai nake dafawa inda da rana zamu gyara sauran tuwo ko yan cima muci sai dare kuma za,a ci mai zafi
Hakan yasani yau yanke shawaran na tafi vidan zarah nakai mata,ziyara kamar yadda,nai mata alkawari kwanakin baya,
Zama babu wani abinyi a gidan zaman haka kawai ya fara isata, banda yadda zanyi don tun tafiyan Hamza sai komai na gidan ya tsaya muna cif, ba wani motsi a gidan kamar baya,
Yau dai na yanke shawara a raina zan cewa zan tambayi Umma zance zuwa gurin Anty Zahar kamar yadda nai alkawari zuwa a gaban ta,
Da,daddare kuwa suna zaune gaba daya diyan Umma suna a tsakar gida zaune a,saman tabarma suna cin abinci,,
A can daga karshen tabarman kadan nazsune sai dai zaman tankar a takure nake a gurin ,
A hankali na kira sunsn Umma tare da dan sunkuyar da kaina a kasa a hankali,
Abinda duk yadawo da hankalin su a gare ni ke nan lokaci guda,
A cikin ladabi na fara mata magana da cewa Umma dama ina son na tambaya ne ina son zuwa gidan anty Zahar ne kamar yadda nai mata alkawari ranan ,
Nakarashe zancen a cikin dan kara dukar da kaina kasa a hankali,
Yar nan wai wanan futar da kike yawan yi haka na may nene ?
Don kinga mijinki baya gari shike nan wani son fita yawo yazo maki a,rayuwa,
To bazaki ba shin gidan Zarah yin ma ma wai kawai don son zuwa ganin may ?
Wani iri naji a raina tare da kokarin hade yawun da suka taru min a bakina masu daci,
Kafin na karasa hade su sai naji muryan Ibrahim yana cewa Umma yaushe Aisha tafita gidan nan banda labari,
Shiru Umma tayi tai banza dashi tankar bata jishi ba yace ko fitan da tayi zuwa gaida baban su shine fita Umma,?
Asmau tace ni wallahi Umma, Aisha dai ce amma ina zan iya ta zama gida haka ko da yaushe cabdi gaskiya nikan zanta zuwa gida kuna ganina koda yaushe,
Amma gaskiya Umma k8 barta dan Allah dai ta tafi gidan Anty don bata taba fitaba fa,
Jibrin yace wanan ai ta zama kifin rijiya bakauya