Showing 54001 words to 57000 words out of 299981 words
kawai koda yaushe tana gida gurin umma kamar wata tsohuwa can,
Umma tace tooo wooo ke nan kuna zugata ta fara kirkiro fita zuwa uguwa nan da can,
Umma, kofa kitso da kumshi Aisha bata fita zuwa sai dai kullun itace mai jagwalgwalawa kanta haba don Allah dai Umma a sasauta mata wanan abin haka man,
Umma ta juya inda nake zaune a marairaice tana cewa, kinji ai sun yardan maki saiki shirya idan kun tashi zuwa ku tafi,
Ni dama bawani abu bane ban son wanan irin yawan fitan na matan zamani yarinya da kurciyar ta kin ganta nan yau gobe ki gan ta can kamar ba aure take ba,
Aisha kan ba zatai haka ba Umma wace tun tana gidan su fita bai damay ta ba, ma,
Hira,sosai ake a gurin na rayuwan duniya wanda akasarin firan ya koma a can gurin yan uwan su wa yanda zance tun shigowa ni banga suna wani mu,amula dasu yadda ya dace ba,
Washe gari tunda safe na shirya don zuwa gidan anty Zahar yini,
Na fito a,cikin shirina na nufi kofan dakin Umma don in mata sallama da kuma kiran yar rakiyata Asmau don mu tafi,
Nace a sanyaye Umma na, shirya zamu wuce ta miko min wani leda tana cewa gashi ku kaiwa zarah kunce ina gaida ita,
Asmau tafito a cikin shirin ta inda na dauki ledan da Umma taba sako mukai mata sai mun dawo muka bar gidan,
****** ********* ******
Karatu sosai yake ba kama hannun yaro don shi dama mutum ne mai kwazo a,rayuwan shi,
Dan lokaci kalilan sunan shi yai fice a gurin dalibai da malamai a makaranta inda suka bashi classrep, na su,
Mutane suna mashi kallon sauri ne matashin wanda baida ko budurwa balle matar aure a gida,
Hakan yasa yan ajin nasu yan mata suke kawo mai hari don son kutsa rayuwan su gare shi,
Amma da yake shi mutum ne mai bahagon rayuwa sai ya,nuna masu tankat bai fahince su ba bai gane nufin su ba a kan shi,
Wani lokaci zai zauna yana tunanen gida Umma Aisha yan uwan shi, sai kuma shagon shi ,
Ga damana ta sauko yanzu hankalin shi ya koma ga noma tuburan hakan ne yasa shi yanke shawara cewa karshen wata zai dan je ya ziyarci gida kafin su fara texts da exam yadawo,
Sabon Abokin harkokin shi na makarata mai suna Nazifi, shine ya hango shi a zaune daga gurin da yake yana ta faman tunanen gida,
Nazifi ya karaso gaban shi inda ya dafa kafadar shi ya zama yake fadin mutumina yaya akayine na hango ka tun can zaune ka,shiga vabration, haka,
Hamza ya dan sauke ajiyan zuciya tare da gyara zaman shi yana cewa bari kai dai mutumin
Wallahi hankalina ya koma gida ne ina tunanen iyali na ne?
Dariya sosai nazifi yayi tare da dan tafa hannayen shi yana fadin wallahi har ka bani dariya sosai,
Wai iyalina sai kace wani magidanci wanda yabar mata a gida ,
Murmushi kawai hamza yaiwa Nazifi tare da mikewa tsaye yana fadin to da kai may kake nufi ne wai, ?
Yaro kai ke nan muje hostel mu samu abinda zamuci Nazifi yace da dai yafi maka wanan fargab dajin da kakeyi,
Maganar abokiin shi na,gida,ne ya fado mai a,rai inda dazai zo yake ce mai yasamu yar waya yasaya yabar daya koda yar nokia ce a,gida dayan kuma ya rike a hannun shi,
Sai yanzu yagane hikimar yin hakan da abokin nashi ya,bashi shawaran yayi kafin ya bar gida,
Don gashi yana,son sanin halin da yar mutane take a gida da ya barta tare da,Umma da yan uwan shi,
Yana gidan ma yaya,suka kwashe da,Umma, balle yanzu da bai kusa dasu
Duk da ga mata,nan wayayyu yan birni yana gani bila,adadi, amna sam hankalin shi bai taba,raya mai ya,shiga cikin so ko kaunar wata har sha,awa,yashiga ba shi kawai idan ma,wani abu yadan bijiro mai yakan dan tuna,da,yar matar shi da yabaro a gida duk da karama,ce amma,tafi mashi wa yanda ba halal din shi bane,
****** ********* ******
Mun shiga gidan sukuburan da,sallama sai yan kalle kalle nake tun a kofar shiga gidan, don wanan ne karo na farko da zan shiga gidan, nasu,
Gidane mai tarin iyali mata da yara a cikin sa don tun a kwanan shiga cikin gida zaka fara jin hayaniyar mata da yara yana tashi,
Parts, parts na mata biyu biyu suna,fuskantar junan su,
Anty Zarah tana tsakar gida tana shanya wankin da tayi mukai sallama inda ta tare mu da murna tana fadin, a,a yau matar yaya ne a gidan namu lalai yau ana ruwa a garin nan,
Ina yar dariya yayin da nakewa sauran matan da suka sako muna idanuwa don su kalleni da kyau,
Cikin yar siririyar muryata nake masu ina kwana tare da dan karasawa gurin su,
Matar da na ke zaton itace uwargidan su na,shedata don kwanaki da ta zo ta biyo bayan Zarah din yasa na gane ta,
Mun shiga dakin zarah duk da bawai takai sauran yan uwanta kayan daki bane amma dakin nata fes fes gwanin ban sha,awa,
Mun zauna tafita zuwa can sai gata da goran kunun zaki mai sanyi da ruwan leda a cikin wani dan madaidaicin ture,
Muna zaune muka fara,gaisawa da ita tana min wasan kaunar miji saidai ban iya mayar mata da,amsa don nauyin ta nake ji sosai,
Mun bata sakon Umma inda tabude ledan sai naga tadan tabe baki tana cewa ita mama kullun tana kashe kudin ta,a gurin wanan abin,
Ga wanda ta aiko min dashi last banyi komai dashi ba,
Aisha ki dauka,mana idan kina so kiyi amfani dashi,
Anty na maye fa ?
Da sauri ta juyo inda nake tana cewa ke kayan matane fa kuma masu kyau na rasa a ina Umma ke samo su haka masu kyau wallahi,
Tace bari wanan tabar nan nai maki bayani a kan su cewar wai Asamau dake dakin tare da,mu,
Asmau tace ni yanzu ma gidan su shemau, zan tafi na,dubota nabar ku kuyi ta hiran ku na matan aure,
Ta kalli kafata take cewa Aisha, don yayana baigari ki ka bar kafan ki hakan fari ba kumshi,
Baki san cewa zai iya fadowa a kowani lokaci ba garin nan
Asmau tace wanan aiko yaya yana gari bata gyara don ba ta fita zuwa gurin masuyi su gyara,mata,
Zarah tace Aisha kina karamar yarinya ga mijinki yaro baki gyara yana can cikin manya mata yan duniya yana ganin mata kala kala a bariki,
Ni,ma matan tsoho amma gani nan kullun dole a cikin gyara nake kin san mazan yanzu sunfi son mace mai gyara,
Daki ,jiki abinci da kuma uwa uba can gurin aikin,
Murmushi kawai nai mata tare da dan dukar da kai na,
Asmau tana gama shanye kunun zakin ta tamike tana cewa zata gidan su Shemau kawar ta, don basu da nisa sosai,,
Fitar Asmau dakin yaba anty Zarah damar fara yi min magana acikin sake jiki kamar haka,
Yanzu ke Aisha inba abinki ba wake zama wanan zamanin haka dip babu wani motsi,
Wallahi mazan yanzu sai a,slowa don basu da tabbas indai maza ne, komai dadin ki da miji sai ya cusa maki irin nashi kalar tsiyan shiya,sa kikaga mata a wanan zamanin a tsaye suke kem akan maza jen su don kada a samu matsala,.
Anty Zarah ni to yaya nadsn zanyi tunda ba tare da wata,nake wace zata koya min wanan abubuwan,
Don kinga a gidan mu al,amarin sai a,slow amma a kwanaki da baban mu baida lafiya mukaje gaidashi naji su Anty suna hira,
Anty zarah tai shiru tana sauraren abinda zan fada mata, amma sai taji shiru,
May kikaji suna fadi shiru nayi again ba amsa tace baki fada min sai nake cewa wallahi anty kunya nake ji don akan kwanciyar mace da namiji ne wanda ni Anty Sam ban masan da cewa akwai wanan abin ba ai,
Dariya sosai Zarah tayi tana cewa wai yanzu Aisha kina nufin cewa ke haka kike dip dama ?
Amma ko abin da mamaki ace wai yar yau wace tadan yi boko bata,san wani abuba akan zancen kwanciya da miji,
Sannu a hankali take ce wa saurara kiji abinda zan fada maki kinga,duk da mijina ba yaro bane amma wallahi dole na zage damtse a gurin kyautawa a, makwancin mu, wanda har takai yanzu wallahi shi da bakin shi yakan fada min cewa yana matsuwa ranan girkina yazo ya kwashi garan da,Allah yai min,
kinga inda kina tare da mijin ki mussaman ke din ma da kike ke kadaice a gurin mijin ki,
Na farko ki tabbatar da cewa kin fara tsabtace jikin ki,
Dakin kwanan ku sai uwa uba shimfidar ku wanda duk yadda zakiyi ki dinga kulawa da sake bedshet,
Kamshi adakin ki duk lokacin da kikasan cewa mijin ki zai kasance a cikin dakin koda bawai wani abin zakuyi ba, yadai kasance dakin na bada kamshin dadi,
Shiru nayi ina,sauraren ta tace, sai kuma nau,in abinci duk wai nasan cewa mu gidan mu ba,wani gidane mai wadatacen abinci ba irin na zamani,
To amma kada ya kasance kice kullun sai tuwo zaki dinga bashi nasan cewa idan kin mai magana ya,sayo maku abu kaza a,,asirce zai sawo ki girka batare da,Umma tasan cewa kece kika ce asayo maku ba,
Na kara gyara zama tace kinga indan kin hada wanan kin fara hada kanki ke nan,
Sai ki koma a gurin nauin kwanciya wanda ko wani lokaci zaki kasance mai zuwa mai da,sabon sallo na dubarun mata,
Nan tafara min bayani yadda zan kwanta da miji ba kunya ba wani jin nauyi tun ina dukar da idanuwa har na,sake jikina ina tambayan ta da cewa Anty kina ganin zai yarda kuwa,
Ke ai abinda maza ke bukata ke nan mace taita sarrafa,su kamar masa a cikin tanda suya,,
Hmmmm Anty ni ai duk na shiga tunane yaya zan iya tunkarar yayana da wanan irin akidar tace to zauna Aisha
Idan yazo maki da tsarabar yar jami,a ai zaki gane kuren ki,
Nace ai da na,shiga uku anty sai dai na koma gida gurin Ummi na ke nan,
Allah ya rabaki inji Zarah abinda na,fada maki su zaki yi kokari ki rike su koda ba dukka,
Nace ai anty zance ne fa na kudi kinga ni dake zaune futis saidai an bani ina zan samu kudin yin wasu abubuwa haka,
Tace yo ke zaman zakiyi tayi bazaki koyi dan sana,a ko na ciki gida ba yara na shigowa saye,
Mijin ta ne ya,shigo dakin wanda ranan ne zance na tantance shi da kyau dan dattijo mai dan farin saje a fuskan shi sai dai ba,wai tsoho bane can don bai kai shekarun mijin su Ummina ba,
A,gabana suke dan wasan soyayyan su amma na fatan baki tana wani dan kararaiya a gaban shi take cewa daga dan wani kwanciya datayi tana wani dago gaba,
Alhaji dama ina son kiran ka matar Yaya Hamza nane naje son akirawa maikitso mu da kumshi tai mata kudin da,zan sallamau ta nake son kadan bani,
Yadan ja mata hanci yana cewa shine kike wani dan marairaicewa
Ya saka hannu a cikin aljihun shi ya dauko kudi yana mai mika mata,
Kudine wanda bazance ga yawan su ba yake cewa sai ki sallamay ta aciki dayani ai zasu isheki ko,?
Tace nagode a cikin wani dan tausa muryan tare da cewa asayo muna dan abin tabawa in an fita,
Yadan kara nufota nidai kaina yana kasa sai yar kara naji tayi na,wasa tana cewa wallahi kada matar ka taji kasan ta da kishin tsiya,
Yace cikin dan nufar kofar fita daga dakin taji, mana ke dai kinyi arzikin bakuwar ki kawai,
Mamaki abin ya bani yadda dattijo kamar wanan yake wasan soyayya irin haka
Sabanin ni da ko kadan banga fuska ba daga ni har mijin ba,wanda ya iya wanan abin,
Kamar yadda tace din haka akayi mai kitson su da kunshi tazo tai min da yake sana,ar matar ne nan danan aka gama nin duk da kitson sunyi yan yiri,yiri sosai,
Asamau koda ta dawo tasamu ana min kwalliya don haka dole ta jirani duk da korafin da take tayi,
Ni damuwa na,shine yadda yau zamu sha fada a,gurin Umma agida sai faman dada kitson da kumshi sukeyi,
Duk sun kidimay ganin gashina yadda ya,sauko anty tace Aisha ga ki da,gashi kitso mai kyau haka,,
Zaki bari ya lalace a banza,
Aisha idan kin gyara wallahi nina fada maki sai Yayana yasan cewa yayi dacen mata a duniya,
Anty dama da take cewa wai an hada Yaya hamza da yarinya wata kala can,
Ai ko ita yanzu inhar tazo zatai mamakin ganiki haka
Mai kitson ke cewa inane gidan ta zan diga zuwa intana bukata nai mata,
Nadago kai inace mata ai banda kudin biyan irin wanan kitson mijina tallakkane fa,
Allah ya kawo yayan mu yaga wanan gyaran irin haka shi da kan shi zai dan dinga bada kudi ai ai maki,
Inda Asamau ke cewa ai kafin ya shigo har kitson ya tsufa,ko, kilama har ki canza wani,
Tsab na fito a cikin wasu kayan anty Zarah data bani nasaka bayan nai wanka inda takara hada min yan kayan gyaran mata tai min bayanin yadda zan yi amfani dasu,
Ni kaina nasan cewa na canza ranan don na dubi madubin dakin nata naga irin yadda na sake lokaci guda,,
****** ********* ******
Kubura inda sabo yanzu ta saba da halin Nuran ta, don haka zaman nasu yake ba dadi ba kuma zafi,
Sai dai hakkuri kawai takeyi don yadda Mana tai alkawarin zasu san abinyi akai din tayi,
Don yanzu yakan dan shiga bayan dan kwana biyu haka su kasance a tare,
Sai dai ta gane cewa aduk lokacin da ya kwana da ita wanan halin na kiyayyan nashi yakan taso mai yai ta tsaki har gari ya,waye su kwana a wahalce,
Duk yadda takai korafi a gida mama takan ce Kubura na fada maki kije kiyi zaman hakkuri,
Kada kiyi sake ki watsar da daman da Allah ya baki, don kinga duk yan uwanki babu mai aure acikin irin daular dakike,
Kubura takance mama daula babu kwanciyar hankali tayaya zan uya kwantar da hankalina har inga wanan daular da kike nufi,
Sai ki tatake ki watsar da daman naki tunda baki jin magana,
Kubura takan zauna tayi kuka don tasan cewa duk wanda tafadawa damuwar ta shawara daya ce zai bata irin na mahaifiyar ta cewa tayi hakkuri kawai,
Mama tace ki tashi ki koma dakin ki tun mutanen gidan nan basu fahinci irin halin da kike ciki ba,suyi muna dariya,
Haka uwar kan lalashe ta har tabar kukan ta samu ta koma dakin ta baki alaikum,
Ki matsa yadda kikaga abokiyar zaman ki tana tarairayar mijinku kema ki kama
Ita ko uwar gidan Jamila da,suke ganin laifin ta a banza tana iya kokarin ta gurin ganin cewa ta sasanta zama a tsakanin mijin nasu da Kubura,
Duk da bawai sanin may ya shiga tsakanin su tayi ba amma tana iyakar kokarinta gurin fadakar dashi akan hakkin da ya wajaba akan shi,
****** ********* ******
Wasgegari na tashi da,aikin gyaran daki da,duk wasu yan abubuwa na dake bukatan wankewa,
Umma tunda ta kyala ido da,safe taga irin gyaran da yar ta,tasaka akai min sai cewa tayi,
Ashe ku dawiniya kuka kai wa yar uwar taku haka wansn irin gyara haka kamar wata yar Arab,
Komai sai dana gyara ranan a dakina tare da karawa dakina mazaune na canza kayan daga gurin da sukr zuwa wani position,
A take dakin ya koma tsab kamar ba,shi ba har kofan dakin Umma tazo tadaga labulen dakin tana cewa,
Ganin gidan su Zarah ne yatayar maki hankali haka aishiyasa ban son ana,shiga gidajen masu kudi kada mutum ya dauko wahala,
Acikin dan marairaicewa nake cewa Umma ba hakana bane dakin ne yai min kura shine na ke gyara,
Kannen mijina duk wanda ya shigo sai yai min sherin cewa halan yayan mu zai zo ne wanan gyara irin haka,
Murmushi nakan yi nace ai ko bai zo ba ku kun isar mashi ai tun da kun gani
Haka muka,auni dasu munata barkwance har zuwa yamma inda na gama muna girkin dare wanda ba wani abinci bane mai wuya dan kullun ne nadada mune,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Don girman Allah ku rike min amana novel dina kamar kullun don Allah nagode da hadin kan ku a gareniπππ
π SARAUTAR MATA π
1β£6β£
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Kamar kullun yau ma aikina da na,saba yi shine, nake duk da wani irin kasala da nake ji amma haka,na daure na karasa aiyukan nawa,
Sai na koma daga cikin dakina,wanda ni kaina yanzu yana,bani sha,awa, kallo,saboda tsab yake ta ko ina ,
Umma wace