Showing 57001 words to 60000 words out of 299981 words

Chapter 20 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17681

shigowan ta ke nan daga zuwa gurin barka da ta tafi,
Jin muryan shigowar umma gidan yasani fitowa ina mata sannu da dawowa,
A,a Aisha har kin gama aikin ne naga kin shige daki kin kwanta abinki,
Nace acikin sanyin murya Umma na karasa ne yanzun na,shiga daga ciki,
Ledan dake hannun ta take kokarin miko min yayin da na karaso gare ta ina mika hannaye na don karban ledan,
Umma ke cewa karbi ki dan kwaba min latus ne nagani a hanya na,sayo muna,
Na juya zuwa gurin da muke aje kwanonin wanke wanken mu don na dauko kwanon da zan sa a ciki,,
Umm take cewa bari ta shiga daga ciki ta duba, guntun man gyadan da ta ajiye, a dakin nata,
Sai ganin akuya nayi tafito daga dakin dagudu inda umma ke ta masifa daga ciki tana zage zagen masu kiwon dabbobin da basu iya killance su a guri daya
Takara dan fitowa dauke da kwanon da mai ke a ciki tana ce min na karba na,gyara,mata dashi,
Ina gyara ganyen Umma,na zaune a saman kujera daga gefe guda tana kallo na,
Sai kiyasta yadda nake gyaran ganyen a cikin kwancinyan hankali nake wanda ita Umma din take ganin sanyin jiki ne ke gari ni hakan,
Haba Aisha don Allah ki motsar jiki ki gyara min latus din nan yunwa na kwaso ke kuma,, sai sanyi jiki kike simay simay hakan nan,
Maganar ta bai sana fasa aikin da nakeyi ba,sai juyawa nake a hankali kamar yadda na saba,,
Muryan Umma naji tana cewa waiko ranan kun kai wa Zarah sakon da na baku ku kai mata,
Gabana ne ya fadi don tuna cewa,sakon yana a gurina nadawo dashi Zarah ta ce na dauka tabar min,
Nace Umma mun bata har tana cewa idan zamu dawo zata bamu sako mu kawo maki sai kuma ta manta,
Murmushi tayi har hakoranta suka baiyyanq tana cewa hoo yar nema tasan kan sakon ke nan shiya sa take zance bada abu a kawo min,
Jin abinda Umma ta fada yasani sanin cewa abune mai muhinmanci a cikin abin,
Don haka,na kudur ta cewa,a,raina da zaran nashiga,daki zan bude ledan don inga abinda ke a cikin sa,
Na kamalla na aje gaba daya ganye agaban inda na debo mata ruwa a randa na girke a gaban ta,
Daki na,shige inda na jawo ledar tawa gurin da na boye ta na dinga ciro su daya bayan daya ina dan dandanawa,
Don ko wani yana da bayani a cikin shi naji dadin wanan abin don zaki gare shi sosai,
Na mayar na,boye gurin da nai masu ma,adanan boyewa,
Umma ta na a gurin dan barta taci ta koshi sai gyatsa take tana dan sakatan hakorin ta,da tsinken tsintsiya a hankali,
Na koma bakin murhu don na tsabtace gurin saboda hakan ka,idatace kafin na dora girkin sai na gyara gurin aikin nawa tsab na tsbtace shi da kyau,
.
****** ********* ******
Daga,gurin da nake aikina naji sallama a bayana abinda yasani juyawa baya ke nan don na duba ,
Muryan Umma ne kafin na katasa juyowa take cewa a,a ikon Allah Hamza kai ne tafe ashe,
Sannu da zuwa lalai marhabin da mutanen sokoto ashe kana hanya tafe,
Yadan shafa kai tare da dan cewa Umma sannu da gida ,
Daga guri da nake a tsaye nace sannu da zuwa yaya ,
Yadago ya duban inda nake tsaye ina kokarin goge hannaye na da ragan dana,tana da don aikin kitchen dashi,
Saye yake a cikin wasu kananan kaya suyi matukar mashi kyau kayan sun fitar mai da kurciyan shi na asali,
Wata t,shirt ne baka anyi rubutu da jan kala manyan haruffa an rubuta,
EASY LIFE,
Sai wando irin na,samari velvet, brown color mai laushi takalman kafan shi irin ta maza budadu,
Alokaci guda duk na kallace kayan jikin shi tsab,
Ya amsa gaisuwa na acikin dan sake fuska yana cewa,, sannu da aiki,
Umma tace a, a Hamza wai dama ashe ana,dawowa gida ba,sai hutu ba?
Na karaso na karbi yar bakar jakar da ya rataya mai igiya, a kafadar shi,
Gurin amsan jakar hannuwan mu suka dan hade idanuwan Umma su na,akan mu, yayin da,kowan mu yadan ji re,action
Gaban Umma ya karasa ya durkusa yana gaishe ta tare da tambayan ta bayan rabo,
A zuciyan shi sai mamakin ganin yadda a lokaci guda Aisha ta canza mashi,
A yadda ya barta a kwanaki yanzu ta,sake mai gaba daya, ta murje tayi wani irin kyau a fuska ga kumshi da yaga anzana mata sai sheki takeyi,
Gaban ta sun dan ciciko mata, girma ya kara dan baiyyana mata,
Ruwa na dauko a cikin jug duk da basu da sanyi sosai amma yasha ruwan sosai,
Najuya zan wuce yake ce min ki taimaka min da,ruwa na watsa nadan ji sanyi,
Juyawa nayi zuwa inda nake aje bokitina na,dauka na debi ruwa a randa nakai mai ban daki, soso da sabulu na kara juyawa na kai,,
Yamike ya nufi dakin ina a ciki zan fito da zanin da zai daura don kewayawa, dashi,
Shigo dakin namu inda yaga wani sabon sauyi danai wa dakin
Murya kasa kasa naji yace Aisha na,dan dago ksi muka hada ido dashi sai naga ya kara min wani kwarjini,
Sai na,dan sunkuyar da kaina kasa ina cewa yaya hanya yaya,?
Yace kina kuwa kewana wanan irin kyau da kika kara haka,
Wani irin dadin yabon da yai min naji har cikin raina muryan Umma ne daga waje tana cewa Aisha zuki mai da hankali ki dora girkin nan ya,samu yadan ci wani abu,
Yan uwan shi duk wanda ya,shigo da murnan ganin dan uwan su zai shigo suna matukar kaunar junan su sosai,
Yafito a cikin wani shiga guntun wandon crazy ce asshr color, wanan karon ya wuce gwiwar shi tare da riga,mai kalar brown, mai zanen layi layi,
Kayan zance sufi na farko yi mashi kyau yace wa Umma zai dan fita bakin shago ya gaisa da mutane,
Mutum na farko da ya fara gani a,waje shine Baba Mudi,
A cikin ladabi ya isa inda baba yake zaune saman tabarman shi da aka shimfida mai,
Ladabin yaron yana matukar burge baba akoda yaushe gashi yanzu yafa ya zama mai wani dan birni, sosai,
Yai wa Baba jajen accident din da yayi baya gari tare da,adduan Allah ya tsare,
Baba yake tambayan shi yaya karatun da jama,an su na can da ya baro,
Abokan shi sun ji dadin ganin shi don sunyi kewan abokin nasu sosai,
Nan aka zauna ana hiran yaushe rabo don watan shi biyu da kwanaki rabon shi da can,
Anan ya,shiga shagon su yana dan bincika abubuwa a yadda ya bar su,
Mutane duk wanda ya,wuce zai mashi sannu da zuwa tare da tambaya karatun shi,

****** ********* ******
Dakina kamshi yake na turaren wutan da Anty Zarah ta,bani ranan,
Duk bayanin da tai min da wanda naji su Antyna,suyi a,gida yana a raina don yau ina,son na gwada sa,a ta,
Tunda yamma nake fakon idon Umma nake kewayawa da ruwan dumi ina tsarki dashi,
Kayan hakin da na samu wurin anty Zarah na kara damawa nasha,
A dan wasu awani nafara jin wani yanayi a cikin jikina, wanda na kasa fahintar shi,
Hira Umma ke jan shi dashi yayin da take sani aiki jefi jefi, a gidan,
Sai da hankalin shi yana a,gareni bayan yadan jini shiru gashi yana,son shiga gurina daki ga kuma Umma ta tare shi da firan yan uwan su ,
Dole yafara mata dan gyangyadin karya kamar maijin barci,
Tai magana tai magana taji shiru hakan yasa ta fahintar cewa a gajiye dan nata yake,
Hamza ai da ka shiga daga ciki kadan huta zaifi maka don ka kwaso gajiya dayawa, ka kwanta ka huta kaji sai da safe,
Hamza yadan mike zaune da kyau yana cewa a cikin muryan yanayin mai barci wallahi duk na gaji barci nake ji,
Tashi kaje ka kwanta kaji ka huta hakana gobe ka tashi da,wuri tunda kace zaka,tafi gona ka zagayo,
Ya dan mike tare da yin mika ya na hamma take cewa o,o duk ka gaji to ba hutu ana ta karatu koda yaushe,
To Umma sai da safe ke nan nashiga nadan samu na huta duk a gajiye nake,
Ya,wuce zuwa ciki inda tabi bayan shi da kallon tausayi irin na da da mahaifin shi,
Tana cewa a hankali Allah yasa wanan yarinyar dai tayi barci ita ma ko da yake dakariyar bawai wayon wani abu ta iya ba gida humar banza,
Bari nima nashige hakana don na tashi da wuri zuwa nemo mashi dan wani abin da za a gyara mai yaci,
Tamike tsaye da dan tsuki taso ta kira Aisha don ta kwashe kayan dake waje amms tana gudun ta tayar da ita kuma wani abu yace zai shiga tsakanin ta da dan ta wanda ke bukatar hutu na barci a yanzu,,
A da can idan zamu kwanta nakan saka riga da kuma hijjab a jikina,
Amma a yau zancen yadan banbanta don hudubar anty zarah zata fara aiwatar wa,
Tsab nake don ina jin jikina ni kaina yau din da banbanci sosai a rayuwa na da can baya,
Motsin shigowan shi dakin naji wanda hakan yadan sani kara dan lafewa a saman dan gadon mu,
Ganina kwance saman gado sabanin da can da nake kwantawa a kasan tabarba da filo sai yai ta faman kirana akan nazo inda yake,
Buta naji ya dauka yafita zuwa bandaki don yadan kewaya da alamar kila ruwa zai watsa don naji yana cire rigar shi,
Da Umma sukayi kicibis tana kawar da yan sauran kayan da ban kawar ba a tsakar gida don bamu barin komai a wajen gida don gudun shedanun dare dake wa masu sakaci da barin kayan amfani a bude,
Too ashe baka kwanta ba Umma take tambayan shi yake ce mata zandan kewaya ne ,
Koda ya fito bata wajen ya shige dakin tare da rufo kofar mu da addua,
Ban san may ya ke a cikin jakar da ya,shigo da ita ba sai daga baya na fahinci turare ne ya fesa don kamshin shi daya zo a hanci na,
A hankali naji ya tako bakin gado inda nake a kwance yadan zauna a bakin gado a hankali,
Kara lafewa nayi a inda nake tankar mai barci sai naji hannuwan shi a,saman bayana a hankali ya fara dan shafawa,
A hankali yake shafa bayan nawa wanda yai sanadiyar sauke numfashina a hankali na bude idanuwana,
Na dan juya na gyara kwanciyana wanda hakan ya dan sa kirjina dan fitowa fili, da kyau,
Aisha, nayi missing din ki sosai ina fatan yadda naji ke ma hakan kikaji,
Banyi magana ba,sai dan kara kwantar da kaina da nayi a,saman filon da nake a kwance,
Ya kara kai hannun shi a,saman jikina yana,dan son yi yadda muke a da can baya,
A hankali cikin wani kwarin gwiwa na kai nawa hannuwan saman jikin shi a hankali,
Take wasan dakin ya canza sallo bisa ga,wanda muka,saba,aiwatarwa da farko,
So sai na matse shi a,jikina inda na,shiga shafan shi ta inda ma bai zata ba,
Ba fanka ko AC ke gare mu ba, a dakin don haka baka,jin motsin komai sai sautin nishi da gurananin mu ke tashi a,dakin abin kurciya kowan mu ya,shiga,wani sabon yanayi,
Irin wanda tun auren mu bamu san cewa akwaishi ba a cikin rayuwar aure da mukayi,
Sosai mu ka murji junan mu a,ranan kamar ba gobe gare mu, don da Umma zata ga dan ta da take cewa a gajiye yake da zata sha mamaki ranan,
Sai da,muka raba dare a cikin wanan sabom yanayin sanan muka sahirtawa junan muka kwanta ba,don mun so ba,
Numfashi muke mayarwa,a hankali daga inda kowar mu yake kwance,
Muryan shi data zama mai rauni yake cewa A,isha,,,
May ke faruwa ne wai ?
Nima a cikin wata sanyayar murya nake cewa a ina Yaya,?
Kin canza min Aisha ta ko ina wallahi duk kin rikita min kwakwalwana gaba daya,
Waya koya maki wanan abubuaan please ?
Wasu abubuwa ke nan yaya ?
Hmmmm ,
Ina kika,fita,zuwa lokacin da ban gida,
Gidan mu kawai na shiga lokacin da Baba yasamu accident,
Sai kuma , ina yace a gagauce, ?
Mun tafi gidan Anty Zarah mu da,su Asmau, shekaran jiya,
Ok hmmm, Zarah ce ko ?
Tai may yaya ?
Tai maki darasi ko ?
Nacd cikin murya kamar mai shirin kuka waini shagwaba darasin may kuma yaya,
Murmushi naji yayi yayin da hannuwan shi yake a,saman kaina yana wasa da kitson da ke kaina a hankali,

****** ********* ******
Abin duniya yana damuwar ta a rai nafarko mijin da ta aura ba zaman lafiya a tsakanin su,
Nabiyu kuma yara fahintar irin sana,ar da Alhaji Nura din ke yi wanda sauda dama tayi tunanen wanqn wani irin sana,a ne zai fitar da mutum gida a cikin dare haka,
Sai na uku ta,rasa yadda zata danne zancen Jamila uwar gida a gidan don maigidan shi bai da kamar Jamila dayaran ta,a duniya,
Komi ya,samu yace yaran shi idan magana yake yace jamila, dai jamila dai,
Jamilan nan kuma aure ne na hadi akai masu a tsakanin su don akwai zumunnci tsakani sosai,
Gashi ta dauki watanin tana batun shekarewa amma abubuwa sun ki sauki yadda take so a tsakanin su,
Gashi a duk lokacin da tasamu ya shigo dakin ta ya kwana da ita tana dan samun natsuwa amma shi kuma zai ta da tsohuwar gaba a tsakanin su, ya dinga tsuki yana hattaran ta gashi kuma ya kasa sakinta kamar yadda ya kudur ta da farko,
Kubura ta kasa hakkurewa wanan karon kamar yadda ta,saba, saboda duk ta bi ta rame ta wani susuce sai kace ba itace Kubura yar kwalisa ba,,
Ta,rasa may ke mata dadi a rayuwan ta don kwata kwata tafita cikin hayacin ta, har takai yanzu bata iya boyewa don duk wanda ya santa a baya ya ganta yanzu sai ya tambaye ta may ke damun ta,
Gashi tana ganin cewa tayi auren gidan mai kudi yadda zata, huta sai gashi bubu jinbdadi babu kwanciyan hankali ko kadan a,tare da ita,
Yar ta anty Rahima ta shigo gidan ganin ta tana kwance tana tunane taji ana,sallama ta, tashi tana karba sallaman
Ganin Rahima yasa ta,saurin sake dan ihu cewa wayyo anty kece tafe da ranan nan sannu da zuwa duk ta rasa inda zata aje bakuwar nata,
Itako sai faman kallon yadda duk yar uwar nata ta canza kama takeyi ,
Bayan sun gaisa ne ta gabatar mata da abinsha wanda suke dashi a cikin fridge ko da yaushe,
Ta dawo gefen kujera da yar nata take zaune ta zauna tana cewa,
Anty kamar kin san cewa dama ina son ganin ki wallahi ido rufe,
Lafiya dai ko Kubura ?
Anty Rahima ta tambaya da sauri tare da dakatar da cup din lemon da zata kai a bakin ta,
Tana mai kurawa yar uwar nata don jin may zata ce inda take kara ganin lalacewa ta a idanuwan ta,
Gaban anty ya yanke ya,fadi da,taga Kubura din tana hawaye,tana furta cewa lafiya anty,
Anty Rahima tace ina babu lafiya dubi fa yadda duk kika ramae kin wani susuce haka ,
Kuka Kubura ke ta mata inda ta kasa mata bayanin komai sai she,shekar kuka,
Haba Kubura ki daina wanan kukan ki min bayani nasan halin da kike ciki,
A cikin kukan Kubura ke cewa, Anty wallahi ina matsala kunci yai min yawa a,rayuwa na,
Don tun shigowata gidan nan ni nasan irin halin da nake ciki a gidan nan,
Oya yanzun ki natsu ki share hawayen ki kifada min halin da kike ciki don mu san abin yi, a kai,
Kubura ta dakatar da kukan ta da kyat bayan dan rarashinta da anty din tayi sanan ta fara bayani haka,
Cikin sanyin murya Kubura ta fara magana da yar nata tana cewa,
Anty da farko na,dauka cewa aure a gidan mai kudi shine kwanciyan hankalin diya mace,
Murmushi yar uwatayi tana cewa idan har an dace haka din ne ai,
Kubura tace to ni Anty zan iya ce maki ban dace din ba gaskiya,
Subbahanallahi, inji yar uwar nata inda ta kara maida hankalin ta sosai ga kaunar nata,
Anty tsakani na da Nura ba zaman lafiya ko kadan asalima sai nake gani yanq,min daukan mazinaciya tun a,wajr,
Subbahanallahi shi Nura din kuma ?
Sam anty ba ruwan shi da al,amari ina kallon yadda yake tarairayan matar shi da yaran ta amma ni kamar an aje mai ni dole a gida yake kallo na,
Kubura ta rushe da wani kuka mai tsuma zuciya tana fadawa yar uwar ta irin mugun tsana da kiyayyan da mijin nasu ke gwada mata wanda bata fahince shiba,
Nan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login