Showing 60001 words to 63000 words out of 299981 words
Anty Rahima ta samu tai shiru take bata shawaran cewa ta samu lokaci ta tambaye shi,
Indan ma har wani abinne to ki bashi hakkuri dan Allah ance dukawa wa wada,ba gazawa bane mijikine zaki iya bashi hakkuri yadda ya dace,
In Allah ya karba muna sai kiga ya,sauko yayi hakkuri k7n fahinci junar ku Kubura ta amsa mata da to, anty insha Allahu zanyi yadda kika ce din, idan ya dawo,
Taso fadawa anty zance fitan daren da Nura yake sai taga rashin dacewan haka tace a ranta ko banza sirin mijinta ne wanan,
Yanzun dai ta samu ta gyara zaman su tukun don shine wajibi,
****** ********** ******
Tun zuwa na gidan Umma Umma bata taba tayar dani sallah asuba ba,
Amma sai gashi yau muna cikin wani irin barci mai dadi don rugumay muke da junan mu a lokacin,
Karan yadda take bugun kofan tana cewa a cikin daga,murya gari har yai haske haka ace baku bude kofa ba,
Dalilin mikewar mu ke nan a cikin sauri ina kokarin zare jikina daga na shi naji ya rike ni gam a jikin shi,
A hankali ya rada min cewa, kyale ta har ta tafi sai ki tashi, kara lafewa nayi yayin da nake jin hannayen shi a jikina yana yawo,
Muryan Umma daga kofa tana cewa wanan wani irin sabon halin rayuwane,
Ace anyi sallah mutum yana kwace like da mace awa chewing gun ,
Mugun rayuwan nan na diyan fillani daji da nake gudu shine za,a fara kawo min shi a gidana,
A hankali na dan rutse idanuwa har takai na dan sauke ajiyan zuciya bashiri,
Muryan shi naji kamar mai rada yana ce min kada ki sa zancen Umma aran ki don ba,wurin ramawa bane,
Da ace wanine yai wanan maganan ni da kaina yau zan bashi amsa da kaina,
Bayan tafiyan Umma da dan mintoci naji ya,sake ni yana kokarin mikewa daga zaune,
Inda na dan lumshe idanuwa saboda bazan iya kallon idanuwan shi ba a lokacin,
Don abubuwan da yafaru a tsakanin yana dan dawo min a zuciyata a hankali,
Umma tana a tsakar gida a bakin murhu tana kokarin kunna wuta a murhun wai zata sa wutan dama koko
Taji motsin bude kofar dakin mu a lokacin tadan juyo tare da dan dagowa daga duken da take,
Hamza dan tane daure da,wani sabon zani na a jikin shi sai butan da ya rika a dayan hannun shi,
Yanzu Hamza wani sabon rayuwa kake son tsiro dashi a gidan nan a ce ana sallah mutum yana kwance har rana haka,
Kada ka bari yarinyar nan ta canza maka rayuwan kafa, don ni bani son ganin haka,
Bai yi magana ba ya nufi bandaki sai dai bai karasa shiga ba yaji muryan Ibrahim yana cewa wai Umma wani irin haline kumw haka kike so ki tsirowa kanki ne,
Gaskiya gaskiyan hakan sam bai dace ba gaskiya ace mutum da matar shi kuma bazasu sake ba a gida,
Baki Umma ta bude tana kallon mara kunyan dan ta Ibrahim tace to ubana yi min fada,
Ai sai kayi nasan cewa ka isa mara kunya kawai kabari kajira lokacin naka din,
Gaskiya dai hakan bai dace ba Umma bakiga laifin danki ba,sai na diyan mutane kawai,
Ya fice gidan yana jinini tare da kada kanshi a cikin nuna bacin rai,
Cikin daurewa na fito daga dakin tare da dan tafiya kamar mai sanda na,shiga bandakin nai wanka,
Ina fitowa tana a bakin randa tana diban ruwa a cikin tukunya na kawar da kaina na,shige,
Sai da na shirya tsab nafito don karban aikin a hannun ta ta shige tabarni ba tare da ta tanka min ba,
Ina kamalawa nakai mata daki a cikin roban gaba daya don ta raba muna,
Sai a lokacin nai mata ina kwana Ummma,?
Kamar bazata tanka min ba sai naji ta ansa a kausashe,
Zan juya take cewa dauko inda za,a zubawa mijin ki nashi,
Cup din silver mai marfi nadauko tare da ludayin shi,
Bayan ta zuba ina tsaye sai naga ta ja cup din zuwa wani side din dakin ta mannin bango ta aje haka yasani juyawa fon nasan bazata bani na kai mai a dakin mu ba ke nan,,
Sai da ya gama duk wani abinda yake a dakin ina,waje zaune don ina tsoron na,shiga dakin tace min jaraba ya kaini,dakin,
Ina a zaune gurin yafito saye a cikin shigar wando da riga na wani farin yadi, ya rikide ya koma saurayin shi tsab,
Ganina zaune a kofa cikin yar damuwa ya,sashim dan tsayawa a kaina yana tambayana ko may yafaru,
Dariyan yake nayi ina cewa ina son na karasa aikin dake gabanane da,safen nan,
Ibrahim ne ya shigo yake cewa Amarya may zamu karya dashi,ne tunda yau muna da bako a gidan,
Nace kunu, ne Yaya Ibrahim kuma yana dakin Umma a can zaka karba idan zaka sha,
Dakin Umma din ya nufa inda ya samu dan uwanshi a Umma tana miko mai cup din kunnun shi a gaban shi,
Yace ba dai a nan zaka zauna karyawan ba matarka tana can a takure waje,
Wanan, wanan anyi dakaren da a gidan nan idan ya tsaya yasha anan wani abin ne ko kuwa, ?
Ita Aisha din ce takure a waje ina take ta samo kofi na zuba mata nata kokon mana,
Baka ji matsala ba yaushe kuma wace tai aikin za,a ce wai za,a, zuba mata wanda zata sha, kuma,
Batare da ta kula ibrahim din ba ta fara kwalamin kira nazo da cup dina a zuba min kunu,
Simi simi nazo da kofina inda ta zuba min rabin kofi ta ce nadauka na juya nabar dakin ,
Hamza yana daga gefe cup din shi cike da kunu ga kosai a cikin wani, kwanon silver mai dan fadi,
Bina yayi da kallo baiji dadin yadda yaga Umma tai min ba a lokacin,
Tsab ya mike tsaye yana daukan kwanon kosai dake a gefen shi,
A,a,a ya haka kumar ina kuma zaka ne wai karyawan ka tsaya guri guda kanatsu mana,
Yace Umma zan koma daki ne can mu karya don naga bata,samu kosai ba ita,
Towoo,
To aje min dama kosai dagani sai kai na,sayawa ban saye da kowa,ba don haka idan ya ishe kane sai ka barmin ni na ci,
Yace to Umma zanci nabar yar mutane batacu ba ita alhalin tagani,
Ibrahim yace koma bata gani ba hakkin cin da kayi batayi ba yana a kan ka ai,
Murmushi yayi yabar kwanon kosai a gurin yadauki kunun shi zuwa dakin,
Umma tabishi da harara tana cewa to lalai yaron nan kana son zance,
Yo ni ina zan iya wanan haka na ciyar da ita wani koko da kosai can,
Dakin ya,shigo da sallama ina zaune a saman ledan kasa da kofin koko a hannu sha nake a hankali,
Muna hada ido yake cewa ki aje wanan ki sha wanan sai ni kibar min wancan din,
Ina dan in, in niya nace a,a kabar shi wanan din ma ya isheni ai,
Sautin murmushin sa naji yana cewa Allah ya buda muna watarana sai labari ai,
Idan na samu sarari ai sai na dinga sayo abinda zaki girka naki na kanki kici,
Nace a cikin sauri kabar shi kawai yaya ai nagidan ma yana isa na,
Yace cikin dan lushe idanuwan shi, ke dai Allah yai muna budi kawai,
Na karba mai da fadar Ameen ,tare da danci gaba da kurban dan kunun dake a cikin cup din dake rike a hannu na,
Wata ajiyar zuciya ya sauke gami da fesar da iska daga bakin shi ,
Wani irin balain tausayin shi ya kamani a lokaci guda,
Don nasan cewa shi mutum ne mai hakkuri da sanin ya kamata ga hangen nesa gare shi,
Ranan idanuwar Umma a kaina kamar wace ke son fahintar wani abu a gu na,
Na kammala,duk wani aiki dake a gabana kamar yadda Anty Zarah ta,fada min ,
Wanka nayi nasaka wanan kayan da Anty Zarah ta bani don kayan sun matukar bugeni don ina,son su sosai saboda suna fitar min da sura na waje tsab,
Ibrahim ya,fara shigowa sai yake cewa wanan kadafa ki hana mijin naki komawa fa,
Hamza ya shigo wanda da alaman dawowan shi ke nan daga uguwa a lokacin,
Wani kallon yake min inda nake mai sannu da,zuwa ya dan sake lalausara murmushi alamar a,lama ansawa,
Ya is,gurin da,Umma take a kofan dakin ta yana mata,snnnu' da,gida,
Inda ya juya take cewa abinci fa yake ce mata shi zan je naci ,
Ai ga abincin anan bari na,dauko ma kaci ko,?
Yace zan turo Aisha ta daukan min acan zanci don akwai abinda zanyi a dakin,
Kamar zatai magana amma kuma sai taja bakin ta tai shiru sai dai bataji dadin nisanta ta da danta da akeson yi mata ba,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
👑 SARAUTAR MATA 👑
1⃣7⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Tun a cikin dare Yaya Hamza yace min washegari na shirya zamu tafi uguwa gidan wani, abokin karatun shi,
Naji wani iri a raina don nasan cewa wanan fitan namu zai iya jawo muna matsala ga Umma,
Amma banda halin mussawa don haka naja baki na nai shiru inga yadda zamu kwashe da ita,
Kamar kullun washegari na kamala yan aiyukan da ya dace nayi duk da Umma ta ban wanki nayi masu, amma sai na kammala da wuri kafin ya shigo gida,
Girki ma da, wuri na dora har Umma tana masifa wai don may zan dora girki da,wuri ya huce yai sanyi kafin a ci,
Hamza ya,dawo gida da dan saurin shi ya shigo inda ya samu nayi wanka ina shiryawa,
Wata farar atamfa mai adon gashin dawisu na saka tare da kara dan gyara fuska na da kyau,
Daga daki ina jin muryan Umma tana cewa Hamza wai may kake son komawa ne ne?
Yanzu don rashin kunya matar taka zaka dauka darana tsaka kufita kowa na ganin ku kana nunawa mutane ku gaku marasa ta ido ko ?
Hamza yace Umma ba hakana bane naga cewa shi wanan abokin nawa matar shi danta baida lafiya shiyasa mukazo tare dashi ya bani lift,
Kinga bai dace ace mun koma batare da taje taiwa yaron sannu ba,
Too,wooo sai kuma akace kuje da ranan nan kiri kiri kowa na ganin ku haka ko ?
Umma ba hakana bane kin san yanayin garin shi yasa zamu tafi yanzu ta dan yini masu,
O ashe ma,sai da ka gama ashirin ka shine kazo fada min kai ga mai mata ko ?
Umma kiyi hakkuri nayi kuskure bazamu kara ba ko yanzu don na riga na,aro mashin din Hadi ne da mun fasa to har na,zubawa mashin din mai ne,
Shiru tayi tana,dan kada kai tana nuna alamar cewa akwai magana gaskiya,
To ji nan idan zaku fita ka tabbatar da cewa kun bi ta baya da ita don ban son abin nuna rashi kunya,
Tau Umma mun gode sai mun dawo ai gidan ba nisane da namu ba can kasan layin suke gurin sabbin gidajen da akeyi,
Kai ka,sani kana,wani rawan kafa wai kai mai mata ko har ina matar take abu haka yar fayau da ita,
Wani iri Hamza yaji a rayuwan shi don dai shi a ganin shi wanan yarinyar bataci a dinga mata muzanci haka a gidan nan ba don ta taimaki rayuwan shi sosai yadda ita Umma din bata iya ganewa, sai shi kadai,
Daki ya,shigo ya,samay ni zaune, a bakin gado yanayin yadda ya samay yasa shi cewa may kuma ya faru duk da yasan cewa naji abinda Umma ke fadi,
Cikin dan marairaice murya nake cewa Yya idan har fitan zai sa ran Umma baci mu fasa mana,
Idan kin shirya ki tashi mu tafi kawai amsan da ya bani ke nan a takaice,
Namike tare da kokarin jawo dakina don awakin mutane da ke shigo muna,
Dakin Umma na nufa tana zaune ta mike kafafuwan ta don zafi ake ranan tana shan iska,
Nace a cikin sanyin murya irin nawa Umma zamu tafi a dakile tace min adawo lafiya,
Sai da muka fitane naga ashe a saman babur zamu yi tafiyan ya shiga shagon shi yafito da leda baka da abu a cikin shi yana mika min,
Ibrahim ya dan leko daga shago a lokacin na hau mashin din yake cewa yau ta daure an samu saki ke nan, adawo lafiya,
Nsi dan murmushi kawai don ban iya bashi amsa saboda ina ganin girman shi har yanzu kunyan su nake ji sosai,
Daida zamu dan sha kwana fita daga lungun mu mai mashi ya goyo Kubura wace ta bi mu da kallon kamar tana mamaki,
****** ********* ******
A kofan wani gida mai alamar dan hali a gidan dan ginan zamani muka tsaya da matshin din,
Yake ce min na,sauko daga bayan shi da nake zaunr ina,sauka ya gyara tsaguwar mashin din nasa da kyau yake min iso da cewa na,shiga nayi sallama na tambaya idan Mansur yana ciki ana mashi sallama ,
Gaba,na yana faduwa na shiga gidan inda nake jin wani iri a raina don ban saba shiga gida je ba,
Sallama nakeyi inda naga daki mai alamar akwai mutane a cikin sa don ga takalma a kofan dakin,
Sai dai karan tv yana tashi daga cikin dakin inda na kara dan matsawa ina daga murya na a,sallama,
Wata mata fara ce ta leko, daga dakin tana rike da yaro a kafadan ta da gani yar boko ce ta na min kallon mamaki,
Nace Ina wuni ta amsa da lafiya nace wai idan maigidan ya ciki ana mai sallama a waje,
Juyawa tayi hannunta yana rike da labule tana cewa kai akewa sallama,
Inda naji mijin yana tambayan waye ?
Tace wata yarinyace ban san ta ba ina gani ba yar shiyan nan bace,
Mijin yafito babu riga a jikin shi abinda yasani saurin kawar da kaina gefe ina cewa ina wuni ya amsa da lafiya nace wai ana ma sallama waje,
Rigar shi matar ta miko mai yana sawa inda yadan fito ni kuma ina tsaye a inda nake ya dan zo ya wuce ni ,
Ganin ina tsaye ban bi shi ba ya matar cikin dan kallon kallon da mukewa juna cewa shigo mana daga ciki,
Na shiga da sallamana dakine mai adon zamani TV, da DVD sai kayan kida ga kujeru manya set a,falon,,
Muka kara gausawa tana ce min ban ko gane ki ba na dan yi murmushi tare da dukar da kaina,
Muryan mijin ne ya shigo yana ce mata daga waje ashe matar Hamza ce fa,
Tace Hamza wani Hamza ke nan dear ?
Hamza course mate dina danake baki labari mun hadu a,school dashi,
Tacd OK wanan da kace tare kuka shigo dashi ke nan ?
Tambayan ta nayi da cewa Yaya maijikin da sauki ko tace gashi ai ya samu lafiya dama kyandace sai dai bata fito mai sosai ba ya samu lafiya sosai,
Na mika hannu na karbi yaron take cewa wanan dan kiwar ai ba zai zo ba don baida yarda, sam,
Yaron kuwa ya kara lafewa a jikin uwar shi tare da dan sako min idanuwan shi da yake lumshewa,
Hamza da maigidan suka shigo tare inda yai mai iso har cikin falon matar inda matar ta,shiga dakin ta soko riga don dama bata da riga a jikin ta,
Dariya suke yana cewa wallahi in ba yau dana gani ba banyarda cewa kana da mata ba,
Kai kai kai Hamza wanan ai sai ace kaunar kace ta rako ka,
Shima yaima matar ya yaro maijiki tare da mai fatan Allah ya,bashi lafiya ya tsare gaba,
Muna daga zaune nake jin magana irin ta manyan mata daga bayan tagar su ana cewa, baki kukayi ne,
Matar dakin ce ta bada amsa da cewa eh mama abokin karatun dear ne su kazo gaida Abba, da jiki, shi da matar shi
Tace Allah sarki sannun ku da zuwa kunji mun gode ai yaji sauki yanzu bisa ga shekaran jiya
Sosai naji mamaki a rai na yadda bata jin kunyan kiran mijin ta da,dear a cikin mutane haka,
Matar ce take ce mu na mama ce maman dear take gaishe ku jin haka na
Mikewa zuwa waje don in gaida matar da,akace mahaifiyar maigidan ce da muka zo,
Ina Fita Mansur ke cewa matarka karamar yarinya mai hankali ba irin yaran yanzu ba, yaushe kukai aure ne wai ?
Hanza ya ba da ansa da cewa almost eight months kenan
Kai ashe ma baku wani dade da ita ba,sosai, kace dai kai ango ne,