Showing 63001 words to 66000 words out of 299981 words

Chapter 22 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17645

Matar,shi tace wallahi ta bani sha,awa sosai tana da kamun kai ba irin yaran yanzuba da sunyi aure sun fara rawan kai ke nan su ga matan aure,
Nadawo daki na bar yar dattijuwar a,waje tana ta,saka min albarka tare da muna fatan alheri,
Abinda yasani jin dadi dama ace nima haka nake zaune da umma danafi kowa jin dadi wallahi,
Yan mintina kadan Hamza ya mike yana cewa tau madam ni zan tafi zan barki da bakuwa sai anjima zan dawo na dauke ta,
Tace amma na gode kuwa sai ka dawo din a gaida gida,
Ya juya inda yake yana ce min tau zan tafi sai nadawo ke nan
Allah ya tsare nai mashi cikin dan sanyi magana
Suna fita take ce min wai yaya sunan ki ne ?
Nace mata a hankali Aisha,
Tace ni kuma suna na Hindatu nake amma anfi kirana da hindu, yara na biyu, ta farkon tana gurin mahaifiyata don ban yaye taba na,samu cikin Abba shine mahaifiyata ta dauke ta,
Allah sarki ita kuma mayne sunan ta,?
Tace Hadiza take ,
Tau,fa, sunan Anty nace na bata amsa da fadar hakan,
Muna zaune sai dan jana da hira take a hankali ina dan bata amsa a cikin hikima take dan fahinta a hankali duk da wai naga ina boye mata sirina,
Haba Abba kabari na dan tashi naje na wanke kanyan ka gasu can a jike tun da safe a ruwa,
Sai kuka yaron yake ta faman yi gwanin ban tausayi idan mutum na kallon sa,
Tace bari dai na kara ma magani nagani ko zaka samu barci kayi haka ta mike zuwa uwar dakin ta don dauko maganin,
Mikewa nayi na fita daga dakin zuwa waje inda famfon su yake ta jika kayan yaron a cikin baho mai dan fadi,
Na gyara hijab dina ba tare dana cire ba na,soma wanke kayan yaron da nata a hankali,
Har sai da na kusa kamalawa sai ga Hindatu tafito daga dakin goye da goyon yaron ta Abba a bayan shi
Lah Aisha yanzun ashe wankin kike yi ni ina ce kina nan zaune a,waje ke da mama,
Ashe kina nan kina wanki ne ke haba Aisha idan mijinki yazo ya,samay ki a haka fa,
Muryan mama ne daga bayan mu take cewa yar albarka ke nan,
Tarbiyan da ta samu daga gidan su ne haka in bashi ba ai da tun shigowar ta zaki gane,
Kyakyawan tarbiya wa da,gwada kan shi yake batare da mutum yasan Yana yi ba,
Mansur ne ya shigo gidan yake jin Hindatu nace na bari ta kara sauran da kanta,
Ikon Allah amaryan kece kuma ke wanki da kanki suke cewa ai shine ake magana a kai,
Mama tace ku barta halinta na alheri ne ke nuna kan sa,
Ledan kayan cefane ne yashigo dashi a hannun shi wanda inda Hindatu ta karbi ledan tana mashi sannu da zuwa,
Suna dan wasa da junan su a gaban mahaifiyar shi itako uwar sai murmushi takeyi tana nuna jin dadin ta a fili,
Mansur din ya,shiga daki yake cewa takai mai ruwa yai wanka,
Dakin su ta shiga da ruwan ina dan satan kallon su nace a raina kun huta da,sa ido duk da dai uwar mijin ba ruwan ta,
Amma ni wani lokacin ma Umma zata zo ta tsaya a bakin bayi da,asuba tace tana son kewayawa ne,,
Dole na fito a gagauce na bata guri tashiga tana bina da kallo,
Haka aikin girkin kusan nice na karasa wa Hindatun shi saboda yaron yaki yarda sai kuka yake hankalin uwar duk ya tashi,
A cikin wani turen silver ta zuba muna abinci a tare inda ta zuba nama da yawa duk ya rufe shikafan take ce min don Allah inci abinci in sake jikina don a gida nake ai,
Yaron ta ya samu barci don haka itama ta,samu ta dan shiga wanka ta gyara jikin ta tafito banci abincin ba duk da ina son ci amma kunya bai bari naci don kunya nake ji sosai,

****** ********** ******
Kubura tana ganin Hamza da Aisha taji wani irin haushi da takaici ya tokare mata zuciyan ts,
Tana shiga gida ta samu mutanen gidan duk a tsakar gida kowace tana aikin gaban ta,
Yanayinta kawai ya isar wa mutanen gidan cewa yau ba dadi sosai,
Lafiya ke kuwa Atikace ke wanan tambayan a cikin gwazai irin nata don ita ko yaushe nuna take bata,son Ummi ta rabu da Mama Saude,
Don kada a,samu alheri ace su raba tare da ita ko ta shigo tace zatafita iyawa,
Kin ganta da wani kamane na alamar rashin lafiya tarr da ita ?
Mama Saude ce ke tambayan Atika din cikin hasala,
A,a naga kamar baya da dain raine da ta shigo kawai shiyasa na tambaya inji Atika,
Daga inda Ummi take tadan murmusa don tasan cewa ramin karya kurara ce,
Ita dai badon wani abu take tare dasu ba duk da cewan da,suke diyan su na,aure a gidan wada ta da hutu,
To amma ina amfanin dukiya babu kwanciyan hakali a tare da yarinya,
Kubura tana zaune a saman kujera kanta sama tana kallon tsohon silin din dakin mahaifiyar na ta,
Mama Saude ta shigo dakin tana cewa yau ma kunyi tsiyan naku ko,
Wai may yasa baki daukan shawara ne Kubura kowa ya fada maki cewa kije kiyi hakkuri,
Kamar jira take uwar ta,shigo da zancen sai kuka ta fara acikin daga sautin maganan ta tana cewa,
Mama ni bazan kara komawa gidan wanan macucin mutumin ba,
Duk mai ganin laifina sai dai ya gani amma bazan koma gidan Nura ba na barshi har abada,
Cikintakaici uwar ke cewa yanzu da kike kukan nan haka so kike ataru muna a kai asan halin da kike ciki a gidan mijin ki har yaushe akai auren nan ne wai
Kubura ta kara sautin kukan ta batare da ta tsaya,sauraren uwar ta dake cewa ta tausa muryan ta ba,
Abin da yakara jawo hankalin mutanen gidan ke nan suka dan tsaya sauraren may ke faruwa a dakin,
Yanzu Kubura wanan abin da kike yi ai baidace ba yaushe akai wanan auren, dazaki zowa mutane da wanan zancen,
Atika ce kamar wace take a labe a kofan dakin tun farko ta fado masu daki,
Shekaran jiya fa mijinki yazo kofan gidan nan ya aikomuna da abin arzikin
Dago kai Kubura tayi tana kallon Atika cikin dakatar da kukan ta,
Tace kinji mugu ko azzalumi macuci kawai yana can yana gwada min boni yanzu yazo nan yana gyara kan shi,
Duk zancen da sukeyi Kubura bata saurare su sai magan ganu take fadi mara dadi a kan mijin ta,
Mama saude da ranta ya baci tafito waje inda ta samu Ummi tana aikin ta a hankali kwance,
Kubura na ta kuka tana tujara har lokacin da Ummi ta gama abinci ta zuba mata nata da kanta ta,shiga dakin Mama Saude dauke da abincin don ta kai mata,
Ummi tayi wankan ta kafin ya fara rabon abincin don ka,idar tane yin haka bata zama rabon abinci sai ta tsabtace jikin ta tukun na,
Kubura na kwance ta kifa ciki a saman gadon mahaifiyar ta inda Ummi ta shiga dakin da sallaman ta,
Haba Kubura maynene yai farko baiyo karshe ba yanzu kina ganin kin kyauta ke nan kizo kina tayarwa mahaifiyar ki da hankali haka,
Kusa da ita ta zauna tana mai kara dan bata hakuri a cikin tatausan lafazi mai kwantar da hankalin macen da,ranta ya baci
Dan tsakaita kukan ta takeyi can ta nisa tana cewa wallahi Ummi abin Nura ya isheni ne duk abinda kike tunanen zanyi mai na ban hakkuri nai mashi amma kamar kara tunzura shi nake yi ,
Hakuri zaki karayi Kubura kinji kinga ai kowa zaman hakuri yakeyi yanzu idan kince bazaki koma ba sai mutane su fara fadin abinda bashinr ba alhalin ke kikasan abinda ya hada ku dashi,
Kiyi hakkuri kiji Kubura mace bata gajiya da hakkuri wata rana shi da kan shi zai gane cewa bai kyauta maki a rayuwa,
Kiyi hakkuri kinji Kubura kitashi kici abinci ki watsa dan ruwa ko zaki dan watsake sai kiji zuciyan ki yai sanyi kikai wa Allah kukanki da kan ki Allah maiji rokon bawansa ne musan man ma bawan da ya roka da kan
Tashi kinji ki dan watsa ruwa kiji sanyin jikin ki sai kici abinci kinji, muje na zuba maki ruwa kiyi wanka,
Ga mamakin Ummi sai taga Kubura din ta mike zaune daga kwancen da take da farko,
Kiyi hakkuri kinji Kubura tashi muje kiyi wanka ki karasa hakkuri a zuciyar ki insha Allahu komai zai wuce,
Cikin wani sanyin murya kamar ba nata ba tace nagode Ummi nagode insha Allahu zanyi yadda kikace, din,
Mama Saude ta shigo dakin taji dadin ganin Ummi ta rarashi diyar nata ta daina kuka,
Tace wallahi Fatima yarinyar nan bata daukan shawara na fada mata ba yau ba inda bai son tane ai ba zai zauna da ita ba,
Abar zance kawai yaya tashi kijr kiyi wanka kin san mazan nan halin su ne sai hakkuri wallahi kinga kuma ita yarinya ce ba wai komaine yanzu zata iya shayewa ba,
Amma idan anbi abin a sannu zakiga komai ya wuce an manta,
Kubura ta mike tanufi waje Ummi tabita ta bata ruwan wanka tashiga,
A lokacin ne Ummi ke cewa yaya don Allah idan yaro yazo da zancen ce shi acikin taushin lafazi za,a bashi magana yadda zai fahinta tunda hankalin da saura,
Mama tace Fatima na gode don wallahi yau badon ke ban san ya zanyi da wanan yarinyar ba a gidan nan,
Ummi tace hakkuri za,ayi yayabita a,sannu har gano inda matsalar yake kinga sai a magance mata shi,

****** ********** ******
Kikan yi amfani da kayan mu na mata na baki Aisha,?
Muryan Hindatu ce daga uwar dakin take jefo mata tambayan nan,
Dan dariya nayi kawai bance komai ba tace to baki so ke nan,
Nace ina so mana tace to amma fa bana cusawa zan baki ba don shi yana wa mace illa sosai a jiki,
Nai shiru ban bata amsa ba tafito dauke da,wani bukitin roba a hannun ta tana kokarin budewa,
Duk wanda ta bude sai ta,lasa ta min bayani ta,daure ,
Tana dariya tace kin san fa mu mata ne sai da dan gyara dole don dan guntun lokaci gare mu a,rayuwa,
Amma fa,sai kin hada da ladabi da biyayya da kwarkwasa ,
Duk da,a,gida guda kuke da uwar mijin ki rufe idon ki ki kama mijin ki ki mashi abinda ya,dace kafin wata tazo tana mai kina kallo,
Don mu matan hausawa kin san bamu da tabbacin cewa ba,ai muna kishiya,
Kada ma kiyi mamaki idan anyo wata sai ya nuna,aike baki taba mashi komaiba duk zaman ki dashi,
Don kin a wanan zamanin maza suna son suga ana kula,su ana tarairaya idan ba hakaba,sai suje su aro wacce suka ga zata iya kula dasu yadda suke so duk da wahalan da akasha dake a baya sai a fita batun ki ki zama hoto a gefe,
Tace Aisha wallahi ai hakan ma yafi faruwa yanzu ka,wahala da namiji idan dadi yazo yace aike baki iya ci ba,
Don Allah Aisha ki cire kunya ki kama mijin ki ki kula da abinki kin ji gaki yarinya karama,
Wanan abin da zan baki kiyi amfani dasu zasu taimaka maki sosai sai wasu kwalabe da ta bani guda biyu ruwane kamar turare a ciki tafada min yadda,zan yi amfani dadu,
Sai a lokacin na nuta da wanda gwagona ta taba bani a baya lokacin ina amarya,
Inata mata godiya tana jin dadi yadda nake ta bata girma
Ta hada min da bed shet sabo da kuma room fresh masu kamshi da man kitso dana,wanke gashi,
Sai yamma lis yazo muka tafi gida da ledana fam shake da kayan tsaraba inda ta,rufewa Umma baki shine sabulai da man shafa babba vasilen tace nabawa umma don yanzu sarakai kyauymta,suke so,
Muka,rabu muna ji tankar kada mu rabu da juna don dan sabon da mukayi da ita da,sararkuwar ta mai kirki tabani turaren wuta da yan abubuwan amfani,

****** ********* ******
Tunda muka dawo umma tadan fara shan kamshi amma ina bata tsaraba tare da,fada mata sakon Hindatu cewa zata shigo su gaisa sai ta shiga washe baki,
Tana cewa yar albarka ke nan ince yaron dai ya samu sauki,
Nace to da dama dai za,ace tace ai zance Hamza ya kaini na dubo shi kafin ya tafi,
Na,shiga dakina na,samu guri na boye tsarabata yadda ba mai gani inda,suke,
Umma tana min tayin abinci nace mata na koshi munci abinci acan,
Tace yar nema anciwo dadi ke nan yau ba,a yayin talen umma ko ?
Tun a ranan nafara amfani da abinda anty Hindatu tabani inda take ce min na daina yawan karban abinda Anty Zarah take bani don ko banza matar dan uwanane don duk yadda akayi zatafu son dan uwanta dani,
Wata rana ma Uwar ta zata iya bata wani abu a cuta min ta wanan ha yan don haka nai taka tsantsan da dangin miji don ba abin yarda bane sunfi son dan uwan su da matar dan uwan su,
Ranan Hamza ya kasa daurewa sai da ya nuna min iya zakuwar shi a kaina sai zance yake sakewa yana tambayana wai may ke faruwa ne haka da yawa yaga fa gaba daya na canza mai sallo da tako wanda bai sanni dasu ada can baya,
Kwanan su hudu da mansur suka kwasa suka koma ba tare da ransu yasobba kamar yadda duk wani dan makaranta mai iyali ke komawa yabar matar shi cikin rashi son barin ta

****** ********* ******

Dama ta sauka mai albarka inda mutane sai gona suke kaida kawon zuwa saboda lokaci ne na noma yanzu,
Kudin da Hamza ya bani ajiya ya karbi rabin rabi daga ciki ya nufi harka noma dashi,
Idan yana makaranta Ibrahim ne mai kula,da harkan noman shi da,sauran abubuwan gida
Inda sukan kwashi yan kallo da da Umma su hau sama su fado amma ibrahim yace shi sam bazai yarda ba,
Saukin ta sai idan Hamza ya shigo gari takkan dan samu irin yadda take so a gare shi,
Shuka sunyi lab lab dasu acikin daji tankar an shimfida Carpet ne a fili, gwanin ban sha,awa dasu,
Mutane suka zance a kan noman hamza din inda suke mamakin wanan hikamata karamin yaro kama shi har zai yi irin wana shukan babban gona haka,,
Baba Mudi yana daga cikin masu farin ciki da irin wanan ci gaban da karamin yaro kamar hamza ya samu akan amfanin gona,
Sun shiga hutun dogon zango inda dalibai su kan dade a gida suna shan hutu kowa da irin abinda yake a wanan lokaci,
Wani ranan asabar da hantsi ina sauri na kamala aikin abincin masu zuwa gona,
Wanda duk yawan shi babu daya daga cikin yan matan Umma dasuke tayani wanan aikin mai wahala,
Ganin yadda nakw ta faman aiki ni daya Ibrahim yake tambayan ina,su Asmau su taya ni,
Umma da ke daga daki take cewa to dan na iya bazasu fito ba ina aikin mijinta takeyi ita,
Ibrahim yace su kuma aikin yayan su ko do duk abinda aka,samu aidasu ake ci,
Hamza din yana daga kofa yana jin zancen da akeyi amma bai ce masu uffan ba don tsakanin Umma da,Ibrahim ba a shiga tsakanin, su,
Hakana Umma ta rufe shi da fada ta inda take shiga bata nan take fita take cewa taga kamar ana son a shiga tsakanin ta da diyan ta a raba ta adasu abinda bazata taba yarda da shiba ke nan a rayuwan ta,
A karshe Hamza ne ya shiga bata hakkuri inda da kyat ya samu tai shiru a kan zancen,
Daga haka Hamza din ya samu ya ja Ibrahim suka fita zuwa gona don gudun kada ya kara jawo wani zance,
Suna hanya ne a,saman yar tsohuwar babur din da Hamza ya,saya mazu don rage zirga zirga ata haya,
Hamza yake cewa ina son kafin na karasa karatun nan Aisha ta koma makaranta itama ta karasa nata karatu ,
Sai dai Umma taki yarda da hakan ban san may isa bata son zancen Aisha ba a rayuwan ta,
Ibrahim yace idan har kana,ra ayin haka kada ka,fada mata,sai ka kan mala komi yadda ya,dace sai ka sanar da ita zance tafiyan kawai shine fatin ka ka kuma fada mata a lokacin da nake a gurin,
Sosai Hamza ya ji dadin wanan zancen na dan uwan shi inda ya,sa aran shi cewa da zaran ya koma zai fara nema min gurbin karatu a inda ya dace,

****** ********* ******
Yanzu ace duk yawan ku yaran nan kun kasa ko da rabin aikin da yaran gi
dan Rabi mai gyada suke,
Yanzu ku diba kusan mu goma sha amm gona daya karama ta gagare mu nomawa,
Audine ke cewa Baba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login