Showing 66001 words to 69000 words out of 299981 words
su ba, tun suna yara kanana suke wanan noman a gidan su,
Mu tayaya ma,zamu iya wanan aiki da Hamza yake shi da yan uwan shi, su da,suka tashi tun suna yara suke aikin karfi,
Rayuwan Baba mudi ya baci inda yai masu kaca kaca akan su dage su tashi tasaye su nemi na kansu don in shine yau gobe ba,shi bane,
Ganin yadda rayuwan shi ya baci dasu yasa suka fahinci cewa fada ne yake masu na kwarai a lokacin,
Boka ya bata matasa yanzu har takai basu iya,sana,ar hannu ko kadan ,
Abinda sauran diyan yan kudu sukafi matasan arewa dashi kenan,
Don su basu dogara da boko ba kawai ace sai aikin gwaunati,
A na son duk uba ko uwar da ya san kan shi yadan koya wa danshi sana,ar hannu ko ta karfi wanda zai iya tallafawa rayunwan shi ,
Domin mutum in shine yau tau bashine gobe ba saboda mutuwa,a koda yaushe zata iya daukan bawa tabar iyalin shi inda idan ba mataimaka,masu karfi sai zama liability ga,sauran dangi,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
👑 SARAUTAR MATA 👑
1⃣8⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Gurbin karatun da,aka,samo min zanyi heka ka dawo ne ba a,can zan zauna ba,
Umma tai masifa tai jidali, tayi jinini amma Ibrahim yace sai ta barni natafi tun da mijina yana,ra,ayi haka,
Shekara uku zan dauka ina karatun a makarantar koyon aikin ungwazo ma dake a cikin garin Jega ta jahar kebbi,
Wanan karatun da zanyi ya jawo surutu sosai ga mutanen uguwar mu yan daukan wa kai nauyi,
Inda duk Umma tafita,a can sukr zugata cewa yanzu ace mutum da auren ta bazata zauna a gida ba,sai tai tafita wai zuwa wani makaran ta can,
Da,surutun shiya ya ishi Ummi na,sai ta,bukaci ganina gidan amma bata tsawala,min ba don cewa tayi anytime na,dan samu daman zuwa tana magana dani,
Aiken ta,da kwana,biyu ranan Asabar na fadawa Umma cewa ina,son na,shiga gidan mu nagai dasu,
Allah ya bani sa,an ta na samu ta barni na tafi don Hamza ya fada mata cewa idan har gidan mu zan shiga ko zan tafi gurin yan uwan shi a barni na tafi koda baya gari
Don haka ba bata lokaci na,shirya tsab dani na,shiga gidan na mu,
Suna a tsakar gida kamar kullun kowa tana aiyukan gaban ta,nai masu sallama,
Inda na bisu daya bayan daya ina gaida su a cikin ladabi kai ba,sai anfada maka cewa irin kallon da mama Saude da Atika suke min na hassada ne ba,
A cikin rashi sakin fuska kamar kullun suke amsa min gaisuwan nawa sai dai tankar ban fahince su ba,
Atika ce dan ta tsinkani take cewa, ke Aisha kullun da hijjab guda kike fitane, wai ?
Nai murmushi tare da dan kara kallon hijjab din nawa nake cewa, ai wanan sabone mama don baki sanni dashi cikin wanda yaya ya,saya min ne da zai tafi din nan don shiga makaranta,
Sai na gan shi kamar kullun dashi kike shigowa gidan nan ai idan zaki zo,
Dakin mahaifiyata na nufa inda na,samau ta a dakin ta tana jiran karasowa na,
Zaune take a bakin gadon ta tana nade kayan wanki da na samu tana kwasa dana shigo, gidan,
Har kasa nakai ina cewa Ummi ina wuni a cikin ladabi da girmamawa,,
Nace Ummi yaya,su yaya yusuf da su yan biyu take cewa,duk suna lafiya cikin dan ci gaba da abinda takeyi, batare da ta dakatar ba,
Na ce Umma an fada min sakon ki shine yau nace bari na, shigo naji,
Ta dan dago kanta kadan tare da dan kallo na cikin dan kura min idanuwan ta nadan wani lokaci sai kuma taci gaba da abinda takeyi,
Sai take cewa dama kiran ki nayi don naji gaskiyan zancen karatun nan da akace wai kin matsawa yaron nan sai ya mayar dake karatu,
Nan da nan naji wani bacin rai idanuwa na suka ciciko da hawaye inda Ummi takecewa Atika tashigo muna da zancen da,bai muna dadi ba,a gidan nan don haka nace kizo naji daga gare ki,
Idan har wanan karatun ba,dole bane kiyi hakkuri ki zamn ki a dakin ki shi ya fiye maki, daraja,
Don kin ga,surutu yai yawa ga wanan zancen karatun naki
Uwar mijin ki tana yada magana wanda ni dai da, wasu ma mun san cewa ba gaskiya bane,
Don haka ni dai ba,wai na yarda bane don nasan halinki nasan ko ke wacece,
Amma idan ita Umma Rabin yanzu tafadi zance a kanki mutane zasu dauka ne su zaci da gaske ne tunda ita ce ke zama da ke, yanzu,
Take naji jikina yai sanyi da jin maganganu Ummina da ake fadi a kaina cikin uguwa,
Hawaye yadan fara silalowa,daga idanuwa tace min dakata mana don kuka bazai fishe mu ba ki fada min gaskiya shin ke ce kika matsawa mijinki cewa sai ya mayar dake makaranta ko kuwa ra,ayin shi ne hakan,
A hankali na dan girgiza kaina ina ce mata ina wallahi ban san komai a kan zancen karatun nan ba asalima dai ni shine yazo min da zancen,
Ummi ki san halina kin san abinda zan iya da,wanda ba,zan iya yin sa ba,
Tsawon lokaci Ummi tana min nasiha tare da kara lurar dani zaman duniya da mutanen ta,
A karshe take ce min kada ki biyewa halin sararkuwar ki ki ci gaba da hakuri da kowa yadda kika saba yi,
Don haka in har kika bi magan ganun da na fada maki zaki samu rayuwa ingan tace a karshen rayuwan ki don zaman lafiya da mutane shine azikin bawa a,duniya,
Ganin yadda yau muka samu dan lokaci da mahaifiyata yasa na,dan fada mata kadan daga cikin halin Umma da nake fama dashi har diyan nata ma,
Amma,sai Ummi ta katse ni da cewa ko yaya halinta yake mahaifiyar mijiki ce don haka sai ki bita da halinta ku zauna lafiya
Hakan kuma zai kara maki daraja da marta a idon mijinki koda taushe don yasan hakkurin da kike yi a gidan ai tunda a gaban shi ake komai,
Jeki idan kina,da abinyi a gida don kada, na tsayar dake da surutu kiyi laifi,
Zan daga take cewa mijinki ya kawo muna,amfanin gonan da ya,samu a gidan nan duk da dai ance ya rabawa mutanen uguwa da,dama,
Sai a lokacin nai dan murmushi ina cewa ai ina ga kamar zakka ne ya rabawa mutane,
Muryan mama Saude ce daga kofa take cewa matar sarkin noma sai ga sako daga maigidanki gudan mai yawa haka,
Murmushi nayi kawai banyi magana,ba,fon kawaici wa iyayye,
Ance kin matsawa mijinki wai sai ya mayar dake makaranta Yar Agwai,?
Atika ce ta,dago labulen dakin Ummi na tana tsaye daga bayan mama Saude wace ta rigata shigowa daga ciki kadan,
Haba Atika wai may yasa kike magana itin haka ne,
Ke yanzu ko wani kikaji yana fadan wanan maganan a gabanki bazaki tare zancen ba akan sanin halin yarinyar nan da kikayi,
Ni bani son irin haka gaskiya mama saude ce ke magana a dan hasale ta juya batare da kara fadan wani abuba,
Itama Atika ta mara mata baya suka bar kofan dakin ummi din,
Shiru mukayi a,dakin Ummi tace min tashi kije rayuwa ce wata rana sai labari ke dai ki ta hakkuri kinji,
Har na mike nake cewa Ummi don Allah gobe lahadi ki turo min su yan biyu suyi min yini muyi hira dasu,
Ba,wai ban son zuwan su gurin ki bane Uwar mijinki ce nake gudun anyi ance din ta a uguwa,
Ummi har da yan uwana sai tace kuma kada su zo gurina haba dai Ummi don Allah ki bari su zo din kinji Ummi,
Tace cikin dan guntun murmushi Allah ya kaimu gobe din zasu zo,
****** ********* ******
A makarantar da nake zuwa hijjab nake sakawa har kasa idan zan fita da nikaf, sai zan shiga get din school nake cirewa,
Ban yarda nayi kawaye irin na zamani ba kamar yadda Ummi na tai min gargadi ga yin haka,
Tace min yin kawayen da,suka fi karfin a jina zai iya jawo min matsalar rayuwa,
Mussaman idan ina kallon irin rayuwan da wasu keyi yau da,gobe zance na dauka,
Amma idan har naci gaba da normal life dina batare da yawan mu,amula da kawayen zamani ba zanci gaba da,rayuwa a cikin dadin rai babu kunci a cikin sa,
Wanan magan na Ummi ne ya tsaya min a,rai nake ta taka tsantsan da komai da nakeyi a makarantan daga gurin lecture sai masallaci sai na,fito zuwa gida,
Duk wanda,aka fadawa cewa ni matar aure ce sai kuji mutane suna mussawa cewa wai yar karama dani za,ace nai aure,
Da yake Allah ya taimakeni tun ina primary three akai promotion dina zuwa primary five kan wani devet da mukayi da wani makaranta nai sanadiyar cin wanan gasar a makarantar mu,
Shine dalilin gama karatuna dawuri ina da karamin shekaru a lokacin
Da,nadawo karfe biyar zan dora girkin abincin gida da,nakeyi kullun,
Wanda karatu bai kawo sauyi akan duk wani aiki da nake a,gidan ba a baya,
Kowa zai kwanta ya barni ina aiki a cikin dare don gudun makara da,safe zuwa makaranta na,
Dalilin da yasa Umma ta kasa samun wani dalili ko hujjan da zata kawo suka na akan fita na zuwa makaranta da bata so,
Don ina matukar yin taka tsatsan da halin Umma din don gudun abinda za,a jimu da ita,
Sai da sati ya,zagayo ne su yan biyu suka zo min wuni kamar yadsa Ummi tai min alkawarin zuwan su din,
Don wancan satin basu samu zuwa din ba saboda hassan ya,tashi da gudawa, a ranan,
Nai murna kwarai da zuwan yan kannen nawa wanda yar gurin Atika ce yar matashiya takawo min su,
Ko da yaran suka zo Umma bata a gida tafita uguwa zuwa buga bugan ta na yau da kullun don yanzu har da dan dillanci take hadawa,
Sun samu daman ina girki na gama na zubs a kwano tare da,su muka shiga daga cikin dakina muna ci muna hira ina dariya wanda mutum zai iya cewa tun shigowa na gidan ba,a taba jin dariyana irin haka ba,
Umma,wace dawowan ta ke nan daga uguwar da ta tafi,
Take jin dariya na da,surutun mu mamaki take yau may ke faruwa yayin da take dan kara karasowa cikin gidan zuwa kofan dakina,
Sai da,tazo gab da kofa tai sallama tare da dan tsayawa kamar mai shigowa,
Ganin ta yasani cewa,a,aUmma sannu da,dawowa ina,mikewa yayin da nake nufar kofar don karban ledar dake a hannun ta,
Idanuwan Umna kyam a,cikin kwanon da nake cin abinci da yan uwa na da,sukajo har yar gurin Atika,din,
Au yaran gidan malam Mudine suka, shigo ashe gaske nake jin muryan ki tun a kofan gida,
Murmushi nayi tare da karban ledan hanu bibiyu take cewa su yan biyu kyautar Allah,
Abinci kowa an zuba mai mai isarsa, ko don kada wani yace min bai koshi ba, daga baya,
Nai mamakin jin tambayan da Umma din tai min kan abinci don haka nake cewa, Umma kowa ya,samu,
Bude kwanon abincin nata tayi tana dan dubawa komay ta gani sai ta,rufe tana cewa Allah ya kyauta,
Na koma gurin yan uwa muna ta shirmay mu a daki sai dai yawan kiran da Umma take min ya,fara isat, aamma haka na daure i ta ta al,amurana,
Sai zuwa yamma,nai masu wanka tare da gyara masu jiki don lokaci ankusa shiga islamiya,
Cikin irin tsaraban da Hamza ke kawo min na boys nadan basu na ce su gayar min da Ummina,
Kafin Umma tafito daga bayi yaran sun tafi batare da taga may na basu ba,
Idan Hamza yana gari nakan danji dadin zuwa karatuna,dan yakan rage min hanya akan yar mashin din da ya,siya
Wani lokaci kuma Ibrahim ne kan rufe shago ya kaini har bakin get ya juyo abinsa,
****** ********** ******
Ranan ina gida muna hutu ban fita ba ina tsaye a gurin randar ruwan mu ina wankewa naji sallama,
Anty Hindatu ce da dan ta Abba sun yi gayen su suyi matukar kyau dasu ,
Cikin yar fara,ata na nufe ta da murna na abinda ya jawo hankalin mutanen gidan mu ke nan don gani wacece nagani nake wanan murnan haka,
Anty Hindatu ta,dan gwauce tana cewa ja can mara,zumunci ai wallahi fushi nake dake,
Yar dariya,na kara,yi tare kama bakina ina fadin kiyi hakkuri Anty wallahi karatune ya rike ni,
Tana,saye a cikin wasu lace pink color tayi buje da riga hannun rigar ya dan wuce gwiwar hannu, kadan,
Ta,yafa farin gyale a iya,wuyan ta tare da jakar hannu fari a gefen kafadar ta,
Sai danta Abba shima,ashiga irin ta yara maza na,wando da riga mai dogon hannu da belt,
Ganin Umma yasa ta nufi gurin su tana gaida Umma din sai dai ganin Umma din bata gane taba yasani fada ma Umma,cewa,
Umma Anty hindatu ce matar abokin karatun Yaya Hamza da,suke tare a can,
Au to Allah sarki inji Umma karaso mana ku shigo daga ciki, sai Anty hindatu ta dan zauna daga waje saman wani kujerar yar tsuguno na mata yar karama da ita,
Nan suka gaisa umma tana haba haba da ita don jin cewa daga fanin dan ta bakuwar take,
Inda na koma dakina kafin ta taso na dan kara gyara dakin yadda ya kamata ai mai,
Ta mike zuwa dakina tana tafiya tana fadin wallahi badon ki nazo ba,sai don Hamza bawan Allah na shigo,
Umma take cewa ta,sakawa ranta,wahala wai karatu take bata da hutun kanta yanzu,
Hindatu tai dan murmushi tana cewa cikin da tsayawa wallahi Umma karatun yana da amfani sosai yinsa don mutun wata rana yana iya cin ribar sa ta inda ba,a zata ba,
Mun shiga daki wanda shigar Anty Hindatu na farko daki na ke nan,
Duk ganin ta yasa na,dan rude,sai dan kamay kamay nake acikin rudewa,
A bakin gado ta zauna,tunda banda kujera a,dak8n nawa na zama sai tabarman dake shimfide a kasa,
Na koma na dauko ma su ruwa a,cup dina na,silver na aje a gaban ta ,
Nai mamaki ganin ta,dauki ruwan ta dan kurba ta aje cup din shima dan ta tadan bashi amma ya kawar da kan shi wai bazai sha ba,,
Muka kara gaisawa da ita take ce min anko takawo min na bukin
gidan su,
Ido waje nace anko Anty ni da,ban sana,a ina zan samu judin anko ,
Ta saka hannu a hand bag din ta taciro wani turmin zani ta miko min tana cewa ga,ashoben ki nan don har an dika maki buki on 27 ne dis month,
Na karba a cikin mama na mike don zuwa nunawa Umma tace umm,umm Ausha dakata,
Ba,wai komaine zaki nuna wa Umma,ba ki dan rika boye wani sirin ki ga cikin ki,
Don dan shigowan nn nawa na fahinci wani abu a gidan nan naku, ki kula da kanki kiji kaunata,
Ta dan daga kai tana karewa dakina kallo a hankali take cewa may yasa kika shimfida wanan bedshet din Aisha ya tsufa da yawa,
Murmushi nai mata ba tare da na bata amsa ba sai cewa tayi ai kamata yayi ko mijinki baya gari dakin ki ya dinga zama neat don gudun kar kiyi baki,
Don kinsan wani idan ya,shigo gurin ka daga tsakar gidan ka zai fara gane tsabta ka,
Sai kuma dakin ki ki da gurin girkin ki don sau dayawa sai kiga mace tsab a waje a waje amma idan kazo gidan ta,sai ka raina mata wayo ga kazan ta,
Amma ke ga komai naki neat wallahi kamar ba a gidan yawa kike ba,
Asmau ce tashigo dakin da,sallama tana dauke da pure water leda a cikin wani kwano take cewa Umma tace na kawo mata ruwa,
Hindatu tace ayya ai munsha ruwa wallahi Aisha ta bamu ruwa mun sha,
Sai ta dauki ruwan ta fita dashi zuwa waje inda ta fito murmushi naga hindatun tayi tana cewa wanan ma kaunar Hamza din ne ko,?
Nace mata eh uana da kanne yan mata su biyu suna nan gida biyu sunyi aure,
Tau kiyi ta hakkuri kinji Aisha zama da yan uwan miji sai an daure idan ba a dace ba,
Kafin tai shiru jibrin yashigo daga waje yake cewa Aisha akwai sauran miya ki zuba min da abokina zamuci abinci,
Nacd mai wallahi ba miya duk akaraba yace naki fa kin ci ki kara min daga ciki,
Nace tau bari na,dauko ma na dauko mai miyan dake cikin wani dan karami kula na bashi gaba daya,
Mikewa naga hindatun tayi tana cewa mu zamu tafi har takai kofa taja ta tsaya tasa hannu a jakar ta ta dauko kudi, tamiko min zasu