Showing 84001 words to 87000 words out of 299981 words

Chapter 29 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17686

yanzu,
Al,amarin Umma nima ina,rokon mata Allah ya,yaye mata wanan halin nata,
A lokacin da nake karami akwai abubuwan da,suke faruwa a tsakanin ta da mahaifin mu da ma yan uwan shi amma ban fahinta ba sai yanzu nake fahintar wasu abubuwan,
Cikin sakin Fuska nace Umma fa nima uwata ce don haka duk abin da take min tana da dakilin yin haka don haka kada ka,damu da wanan,
Abinda na cire daga kedojin niya ne na dan dauko mashi amma,sai yace na barsu nayi amfani dasu kawai,

****** ********** ******
Kubura tun bayan komawan ta gida tunane duk ya damay ta tana matukar mamakin yadda ta ga,Aisha yau din,
Aisha yar Agwai da ta,sani ce yau tai wani fresh da ita zaka ce ko wani gidan dadi take aure ga kwanciyan hakali a tare da ita karara, ta hango a danuwa na,
Tsuki taja tana cewa kanta to damuwar may zan yi bayan nasan irin gidan da take a zaune ko kwatan irin rayuwan dadin da take ciki babu
Kwanciyan hankali da soyayyar mijine bata da shi gaba daya,
To amma wanan kaya da Aisha din ta saka a jikin ta ai sai take ganin sunfi karfita ,
Tajuya kwanciyar ta tana cewa kai akwai dai don gaskiya abin ya daure mata kai,
Ita dai tasan cewa Hamza bai taba kama kafan mijin ta don haka sai dai aita karya amma ba aziki ba,
Ta ja tsuki tace to wai ma ina ruwana da wata banza can wai yar agwai may zata zama balle don dan wanan shigar da tayi ya razana ta,
Har barci ya dauke ta bata daina wanan tunanen ba a ranta,
Da,safe ko da ta,tashi bata ji motsin kowa ba a,gidan don haka kawai ta, fito zuwa kitchen don ta,samu abinda zata gyara taci,
Jamila tafito daga dakin ta a cikin dan dingisawa inda ta hango Kubura din,
Cikin Murmushi tare da,sakin fuska take cewa aa, amarya yanzu nake cewa banji motsin ki ba ko duk ganiyan jiyane,
Batare da ta juyo ta kalli Jamilar ba take cewa ai kin san ban taba buki ba dole wanan bukin yasani gajiya,
Har may akayi a gurin da zai sani gajiya ko a,zaton ki naga wani abin birgewa ne,
Tsaye Jamila din tayi sororo tana kallon ta a cikin mamaki don ita har ga Allah maganan girma da azikine tai mata,
Amma sai take mayar mata da irin wanan magana cikin gatse,
Cikin dakewa Jamilan ta tsaya yau ta fuskanci Kubura tana cewa wai je wata irin yarinya ce mara kunya da baki san zaman arziki ba,
Au ai na ma manta cewa ke yar gidan Sarki ne ba,a gwada maki komai,
Kubura ta juyo a hasale abin kaddara tana nufo Jamila din maigidan nasu yana shigowa gidan,
Jikin shi a,saye da farar shadda mai maiko an mashi dinkin half gown na maza,
Ke ke, may haka may zakiyi mata a hankaki tafara dan ja baya baya kadan da nufin komawa kitchen,
Dakata yace mata inda taja guri guda ta tsaya daga inda take, tsaye,
Yadan tako zuwa gare ta a hannkali annurin fuskan shi ta canza gaba daya,
Sai da yazo gab da ita ya ja ya tsaya yana mata wani irin kallon cikin tsana,
Yace ashe abin naki har ya,wuce yadda nake tsan mani a gidan nan,
Look ban auro ki na kawo ki gidan nan ba don ban son matata,
Kinga ta nan wallahi duk ranan da kikai gigin taba lafiyan jikin ta a gidannan sai ya kada hayen shi suka ba da sauti alamar gwali gwali ke nan (wuya)
Yace kingata na idan kince bazaki zauna lafiya da ita ba a,gidan nan kina tare da tarin wahala,
Don ban san cewa a haka kike ba koda yake ba abin mamaki bane idan nai la,akari da inda na,fara haduwa dake,
Da sauri ta dago kai tana kallon shi don jin mai yace,
Yace ina maki kashedi da ki raba kanki da,wahala ki bari ku zauna lafiya shine dan saukin ki a gidan nan,
Idan kuwa kiki zaki yi mamaki na sosai a,rayuwan ko dan sai na muzan ta maki,
Sam ban san cewa rayuwar rashin tarbiyan naki har yakai haka ba,
To amma mu zuba ki gani idan kin ki,
Iyalina ba abin wullakan tawa bane a gurinnki don ni banga wanan macen ba tukun,
Ganin yadda yake warning din ta da kakausar murya yasa ta natsuwa,don tana ganin kamar zai kai mata bugu ne,
Ya juya fuu ya,shige dakin shi bayare da ya tsaya duban wani ba a gurin,
Kubura ta dago ksi ta kalli Jamila wace take zaune a lokacin itama din ita take kallo,
Wani haushi ya kara kumay ta yau a kan gurguwa ake mata wanan wullakanci haka wani abukuwa,sai aure,

****** ********** ******
Duk sha anin bukin da ake ina zuwa yi wa hindu kara acukin shigana na tufafin da akaimin don shiga mutanen arzikine,
Tun Umma tana kyalewa har sai da hakkurin ta ya kure inda ranan da za ai yinin buki na wankin amare shigana yasa Umma yin magana,
Cikin fushi Umma ke cewa yanzu Hamza ashe har zaka iya hada baki da matar ka ku yaudare ni a gidan nan,
Kamar Aisha ce zaka ce ka fifita akan mu har kai mata wanan irin tufafin don kawai fitan bukin da ba dangin iya bana baba,
Hamza cikin dan marairaice murya yace Umma yarinyar nan fa ko laife ba a yi mata ba amma bata taba nuna bacin ran ta ba akai,
Wanan kayan ma da kike magana a kan su kusan zance maki bani nai mata ba,
Masur ne idan yaje yiwa matar shi sayaya,sai ya dauko da Aisha din,
Rufa min baki ka, mara kunya ka mayar da kanka wani solobiyo sai abinda tace kake wa mutane a gida
Tausayi shi ya kamani yadda Umma ta tsayar da shi tana mashi masifa a kai,
Ranan saboda abunuwa sunyiwa Hindu yawa shi ya kaini gurin bukin da kan shi,
Muna tafe kowa rai a bace sai jefi jefi nake sako dan hira don ya,wayance zancen a ran shi,
Har Allah ya taimakeni yadan saje ranshi yana min hiran wani babban shago da muka gani a hanya mai suna B,L,K
Yana,ajeni ya,juyawashi shi,@³ inda na shiga cikin gidan hankalina duk yana ga tunanen zan can Umma a gare ne,
Haka na, shiga mutane duk da bawani sabawa nayi da mutane sosai ba amma haka akai ta,al,amari buki dani,
Na lura,da yadsa naga Kubura tana bin abokiyar zaman ta duk da ba a cikin sake jiki take ba amma a tare zaka gan su sabanin ranan farko dana,fara ganin su,
Zan iya cewa wanan ne karo na farko dana,fara,shiga mutane akai al,amarin harka buki dani har na,dan san wani abu tare da,samun experience din mata kala kala,
An kamala bukin lafiya na,dawo gida a cikin tsarabab buki kala kala,wanda aka raba a gurin buki,
Ban shiga gida ba,sai da na samu yaro na,aikawa Ummina da abokiyar zaman ta da,wani abu daga cikin abubuwan da aka bani ,
Kwanan Hamza biyu suka kwasa,suka koma school inda a,lokacin sun samu lecture yai nisa haka sukai ta kokarin covery din inda aka wuce su,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
👑 SARAUTAR MATA 👑
2⃣4⃣

IYYAKA NA, ABBUD WA,IYYA,KA NAS,TA, INN,,,


ZAINB IDRIS MAKAWA


Yau gari wani irin zafi ake ga rana, yana kuda wanda hakan ne ya sa mutane shiga wani hali,
Rana yana kudan kai da kafafunan mutane sai fama da zufa sukeyi,
Cikin nan zafin ranan nake tafe sai kishin ruwa da yuwan dake damuna,
Ruwa nake son na isa na dan watsa a jikina ko zan dan ji saida a raina,
Gun a kofa kamar yadda na saba idan zan shigo gidan nake ta kwada sallama amma babu wanda ya amsa min sai yar hayaniya su nake ji daga ciki,
Na isa har kofar Umma din na kara sallama ina cewa Umma sannu da gida,
Dayar mata nace wa ina suni tace cikin yar fara,a lafiya,
Ko sarakuwar tawace wanan ?
Itace kin san wai karatun boko takeyi don ya mayar da kanshi bai san ciwon kanshi ba,
Matar tace haba yaya ai zamani ne mu yanzu fa yaran garin mu har wani gari suke barin mazan su su tafi karatu kuma su dawo lafiya,
Allah ya kyauta nikan ai naga abu macen aure ace kullun fita daga dakin ta wai wani karatu,
Na juya zan wuce naji Umma na cewa ga kaunata nan tazo daga garin mu ganin mu,
Na juya da sauri da dan murmushina ce a, mama sannu da zuwa,
Ya mutanen gida,?
Itama a cikin fara,a take ce min duk lafiyan su kalau,,
Nazo ai ina tambayan ki ake ce min kin fita, bakyanan ashe karatu kike ,na amsa da cewa eh mama,
Gurin da muke aje abincin mu na nufan na dan in dauki nawa naci,
Muryan Umma ce take cewa, ai ba abincin don shine nabawa hafsi da tazo,
Bakuwar tace ai akwai abincin don ban ci ba ma amma sai Umma take cewa a,a barshi kawai ki ci anjima,
Fuska a sake na ce tau Umma na juya zuwa dakina,
Sai dai a cikin zuciya ta wani iri nake ji ba dadi don haka ina shiga na debi ruwa zuwa bandaki dan na dan watsa naji dadi,
Ina watsa ruwan a jikina naji wasu hawaye na biyo min fuska a hankali, ina dan watsa ruwan ina goge hawayen , a hankali tare da tausayin kaina a irin rayuwan da na tsinci kaina a ciki,

Ibrahim ne ya,shigo gidan shima murnan ganin mama Hafsi yake cikin jin dadi da farin ciki
Daga gurin da,Umna take a zaune take ce ma Ibrahim ga abincin shi ta miko mashi ne,
Yace Umma a koshe nake wallahi don yanzu aka kawo wa sule abinci mukaci tare,
Sai ta mayar da kwanon inda ta dauko da,farko ta aje tana juyowa,
Mama hafsi tace ai sai aba wanan yarinyar da tadawo bata samu abincin ba taci ko,
Wata yarinya ke nan Mama hafsi tace matar dan uwanka yanzu ta dawo bata samu abincin ba ance ya kare,
Wani irin kallo ne na mamaki Ibrahim din yaiwa Umma yayi wani huci wanda gaba dayan su dakin sunji,
Amma,sai Umma tace ai bata rasa abinda zataci a dakin ta,
Haba Umma Aisha fa may zataci may ta,aje banda abincin gida wace bata wani sana,a,
Kai rufe min bakin ka ban son maganan bazan don kai baka,da kunya kana nufin karya mukayi ,
Mikewa yayi yabar dakin ya fice gaba daya daga gidan,
Mama hafsi ta kalli Umma tace haba yaya wanan abin baidace ba gare ki ace matar da ka kuma ba,a bata abinci taci ba
A ina ake son ta samu taci tinda ba shi ke gare ta ba a,dakin,
Shi ke hadani dake hafsi son kawo wa mutum Allah kamar kinfi kowa tsoron Allah,
Ni wallahi nasan abinda nakeyi don bazan yarda ace nayi sakaci yarinya takawo min wasu akidoji na,daban a,gidan nan bayan na gama gina gidana da tubali irin wanda nake so,
Mikewa mama hafsi tayi ta dauki kwanon abincin da Ibrahim yace bazai ci ba ta nufi dakina dashi,
Sun hade da Ibrahim wanda ya shigo dauke da bakar leda a hannuwan shi,
Lemon kwalbane da breadi acikin ledan sai kosai mai zafi da ya,hado dashi,
Ya tsaya daga kofa yana cewa Aisha ga wanan ki dan ci ko,
Abinda yasa Umma lekowa daga dakin ta ke nan,
Mama Hafsi ce ta karbi ledan daga hannun shi ta karasa shiga dakin dashi,
Ina zaunr inda na sallamay sallah anan nake zaunrena dan jingina kaina da gadona kafafuna na,suna a tokare a kasa, sai dan kada su nakeyi,
Ganin Mama a dakin da,sallamata ga leda ga kwanon abincin a dayan hannun yasani saurin dagowa ina cewa mama ai da ki, kirani nazo na dauka da kaina,
Tai murmushi tamiko min kwanon da nake mika hannu na karba,
Tace wanan ledan ibrahima ne ya kawo maki yanzu shine nakarbo na shigo maki dashi,
Nakarba nace mama nagode,
Daga haka ta fita daga dakin ta koma dakin Umma,
Na bude ledan don ganin abinda ke a ciki sai na ga a binda ya sayo min, mai yunwa taga abinci ba bata lokaci na,hauci hannu baka hannu ga leda,
Sai da na koshi kat nai gyatsar lemon da nasha nan nai hamdala nagodewa Allah Ubangiji,na,
Sai a lokacin na bude kwanon sai naga abincin yai min wani duhu yafita raina,duk dani na dafa shi, duk da,nice na dafa abincin amma sai naga abincin yai min duhu a fuskas,

****** ********** ******
Zan iya cewa zuwan Mama hafsi a gidan mu ya kawo min saukin rayuwa sosai,
Don tana kama min aiyuka da dama nagida, duk da Umma ta hana mama hafsi yin aiyuka,amma sai mama hafsi tace mata ai ita idan batai aiki ba jikinta ciwo yake mata,
Dole Umna na kallo kusan aiyuka,mama hafsi ce mai yin su tun ranan da tazo washegari da safe zan tafi school taga ina,aiki take cewa ba zaki bokon bane yau,
Nace zan tafi mama sai nagama aiki nakan tafi, ai tace haba Yaya ga yaran nan basu komai a gida aikamata yayi su taimaka mata har ta dawo da yamma sai ta dora inda suka tsaya,
Umma tace cikin jin haushin zancen yar uwar ta ai ita ta daukawa kanta karatu don haka bazan takura wa yara ba akan nata bukatan,
Ganin yadda tabata amsa yasa Umma hafsi sanin irin rayuwan kuncin da nake fuskan ta a gurin Umma,sarakuwata, don haka taja bakin ta tai shiru,
Sai dai ita da kanta ta mike tana taimaka min da aiyuka masu dama daga sharan gida wanda takeyi da ta sallamay sallah,
Sai kuma wanke wanke, wani lokaci idan nai rana zatace na tafi nabar mata girkin tai min zata karasa da kanta,
Umma tun tana jin haushi har takawo ido ta,sa ma mama hafsi din suka zauna lafiya, don mama hafsi macece mai zumunci ita kanta Umma tana jin dadin zama da ita,
Hakan ba karamin dadi yai min ba don zan iya cewa tun lokacin da nai aure wanan takin ne na samu kwanyan hankali da ragwamay aiyukan da ke a kaina a gidan,
Haka yasa dan haske ya fara,dan dawo min nafara dan yin magurjin jiki,
Karatuna yana tafiya a,daidai, don irin baiwar da Allah yai min ta hazaka,
Shine sauki na da madogara na gurin rafe expensive din makaranta ba,sai anbi a gwada mi gata,ba da kudi da kwakwalwata nake karatuna,
Kawar Umma kum aminiyar ta da basu wanka,su bushe suna tare a kowani lokaci,
Watau mama, Sa,a da ta saba zuwa gidan mu wace duk zuwan ta bai zama min alheri a rayuwata, sai sheri,,
Yau ma kamar kullun da yake weekend ne ina gida don ban faye shiga school Saturday ba,
Naji muryan mama,Sa,a ta bayan na gaishe ta ta karba min a yatsune,ta,wani juya a hautsane tana cewa au kina gida ashe?
Nai mata yaya yar ta bintu wace itace auta a,gurin ta,
Rabi naga yarinyar nan tai min wani dan fari a idanuwa na har da dan jiki ta kara, nace kodai alheri ya samu ne a gidan,
Da sauri Umma Rabi takai idanuwanta gareni tana cewa kin ga alama ne ke ?
Mama Sa,a tace cikin wani dan washe baki Aisha Humaira mai babban suna yaki nan,
Har nakai kofa najuyo fon kiran da tai min don ni ban fahinci komai a kan zancen su ba
Tace cikin washe bakin da goro ya mayar mata da hakora ja
Nace kodai kinyi batar wata ne ko don naga dan canji a gare ki,
Nace canji mama sai na fara dan dube duben jikina,
Tai wani dan shake murya tace nace ko baki ga al,adan ki bane a bin arziki ya samu watau k8n samu ciki,
Idanuwan Umma tai saurin kakafe ni dasu don son jin may zan furta,
Nai saurin girgiza kai nace mama banda komai fa ni ko sallah banayi ina fashin sallah ne yanzu haka,
Kut, inji mama Sa,a tace cikin wani kawar dakai a razane,
Umma Rabi tai wani yarfar da hannayen tace ai na sani dama wanan ai kiwon hayan masai ne,
Daga taci sai takai masai ta zubar da shi can bata gaji arziki ba balle ta,aje shi,
Haba yaya haba, haba, ina wanan zancen yafito daga bakin ki haka sai kace ba musulma ba,
Kafira nake ko baki sani bane hafsi,?
Nikan jin haka na juya simi simi zuwa dakina jiki ba karfi, don nasan yau kuma mama sa,a ta banbaro min wani sabon fitina a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login