Showing 90001 words to 93000 words out of 299981 words

Chapter 31 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17678

ko na amsa da eh mama,
Inda flask din yake na nufa don na dauka sai Umma ke cewa rike min flask da kyau kar ki mayar dani baya tun flask din haihuwan autana nane nake maneji da abina,
Sai na mayar da flask din nace bari na dauko cup na juye muna,
Mama hafsi tace tafi dashi mana ki rike mata shi da kyau ,
Hamza yace bari ta juye mama zaifi ta dauki flask din ai,
Ni dai ba zan yarda a fasa min abuba don maneji nakeyi dashi gaba dayan wurin shiru mukayi,
Don haka sai nabi umurnin hamza na juya na koma na dauko cup na juye ruwan zafi aciki,
Banji haushin Umma ba don nasan cewa a gidan mu banzo da wasu kayan amfani ba, ai irin na aiyukan mata,
Kwaliya na taiwa Hamza kyau sosai sai bina yake da kallon sha,awa,
Suna zaune shi da su Umma inda suke hira da mama hafsi Umma na daga gefe take cewa,
Dama ina jiran zuwan kane, don naji shawaran da zaka bayar,
Kaga an raba gadon mu gidan da aka bar muna an sayar abawa kowa kudin shi da yan sauran kaddarorin da aka bar muna, baki daya ,
Shine na hado kudin nazo dasu nan don mu san abinda za,ayi dasu,
Banda kowa a duniya yanzu sai ku da yar nan guda da Allah ya bani ita kuma kaga shi Alhaji ba mahaifita bane ga mijinta dan kwaya ne ita kuma ba lafiyayya bace don haka ba dama na,sakar mai kudi su lalace a banza,
Shiru sukayi baki dayan su mamata ce yanzu tun da Alkah ya,dawo da kai kaga sai ka ba da,shawaran yadda za,ayi da kudin nan,
Zama Hamza ya dan gyara tare da,dan numfasawa yace,
Mama kin san shi kudin gado wani abune mai nauyi da karfi,
Don haka yanzu abinda za,a yi shine asamu gida ko fili a,saya maku dashi a je a matsayin kaddara wanda ake gani,
Don ajiyan su a haka ba zaiyi ba don aje kudi masu yawa kasa dane babba,
Mama Hafsi tace a,a Hamza ba zaa sayi gida ko fili ba dasu ni a nawa shawaran may zai hana ka,karbi kudin ka,fara dan juya su kana kasuwanci da su, har zuwa lokacin da zaka samu naka sai ka biya na dai idan kudin suna gurin ka ko ibrahim wallahi hankali na a kwance suke Hamza,
Murmushi Hamza din ya,dan sake yace a,gaskiya mama nagode da karamcin da kika nuna min amma gaskiya na Allah bazan karbi ko kwandala daga kudin ki na juyawa ba,
Don kin san yadda kudi na amana kuma na gado suke da saurin samu kaddara, don haka shawaran da na bayar shine kawai abin dubuwa da mafita,
Amma gaskiya ban so ka musaya min shawarata ba Hamza na sanka tun kana karamin ka na san halin ku zaku iya rike wanan amana, kai da dan uwan ka,
Hamza yace mama yanzu abinda za,a yi sai nayi shawara zan san abinda za,a yi da kudin don ci gaban su,
Nan suka dauko zancen tsohon mijin nata wanda ya rasu tai mashi wanka da irin taimakon da yai masu a lokacin da suke da bukatan hakan,
Har zuwa wani lokaci ya mike zuwa waje don ya gana da mutanen shi ,
A kofan gida ya hangi Baba Mudi ya karasa su ka gaisa yake tambayan shi cikin murnan yaushe garin yake bashi amsa da cewa jiya da yamma ya shigo,
Ya tambaye shi karatun shi da kuma yadda ya samu mutanen gida,

****** ********** ******
Ina dakina zaune bayan na dora muna abincin rana sai nake jin sallaman daga kofa, muryan mamana Rahana nake ji,
Nafito daga dakina a cikin murna da yar tsalena na tare ta nai mata sannu da zuwa na karbi abinda ta shigo dashi a cikin wani dan buhu,
Sai take ce min ki rike da kyau don akwai abin fashewa a cikin sa,
Gurin Umma taje suka gaisa dasu tare da maso godiya da rike mata 'ya da,suke yi,
Suna tare na,wani lokaci ta mike tana cewa bari su gaisa da ni a dakina,
Mun gaisa da Mamana na,rasa ina zan sakata dan murnan ganin ta yau gida na,
Mama ta aika ka,sayo mata ruwan masu sanyi takawo mata har dakina,
Nan nake nuna mama ga mama Rahana nace kaunar Umma ce ta dawo zama damu,
Ta jajan ta mata akan rasuwan mijin ta da kuma yi mata godiya,
Bayan fitan Mamane Mama Rahana take tambayana cewa tana fatan ba wani matsala dai ko, a zaman mu,
Nai yar dariya nace babu komai mamana lafiya muke da kowa a gidan,
Sai naga tana sance habar zanin ta kudi tafito dasu take cewa na tafi gida Aisha har gurin yan uwan mahaifin ki na tafi, ganin su tinda kin san yan uwan mune,
Tsit nayi ina sauraren ta don jin ta ambaci yan uwan mahaifina, da tayi don ni sai nake gani basu kaunana na ko da yake basu da laifi wanda ma ya haifeni bai damu dani ba balle yan uwan shi,
Muryan Mama ke cewa sune suka hada wanan kudin suka ce na kawo maki kya,samu ki dan sayi wani abin sana,a kina dan juyawa,
Kudin da ta ciro a zanin ta ta miko min a,gaskiya kudin suna da dan yawa don za su kai dubu talati da yan kai,
Sunce kudin gadon mahaifinki ne da,aka,sayar da gonan su na gado nashi kason suka dan baki daga ciki,
A hankali na,dago idanuwa na,da,sukai ja nace har yanzu Mama ba asan inda Baba yake ba ke nan,?
Tace haka,suke fada min amma,wai wani mutum yace ya ga,wani a kasar Niger ko shi ne bai sani ba,
Nace cikin murya mai rauni Allah ya baiyanar dashi duk inda yake in har yana raye,
Mama tace min Amin nakaiwa mahaifiyar ki kudin shine tace na zo maki dasu nan ki gani, ko akwai abinda zakiyi dasu,
Mama ni kan ai banda ta cewa duk yadda kukayi min dasu daidai ne ba matsala shawaran ku itace tawa nima,
Mama Rahana tace ni da,shawaran da nayi shine a dan saya maki dan ijimin nika ko dan fridge, kina dan sana,a kudi na shigo maki basai kin dogara ga miji ya baki ba kullun,
Tajawo dan buhun da ta shigo dashi tace daga ciki mukai maki wanan sayayyan tun a sokoto,
Tafara jawo kayan zanin gadone flask ban san lokacin da nace wayyo Allah na ba mama na gode wallahi,
Kinga yau din nan Umma tai min gorin flask a gidan nan sai idanuwa na,suka ciciko da hawaye,
Sai kuka nafara yi ina hawaye mama tace ki bar kuka ki fada min may ke faruwa ne ni uwar ki ce baki da wanda zaki fadawa damuwar ki sai ni,
Mama abinda Umma take min a gidan nan yai min yawa mama saukina zuwan mama hafsi,
Nan nake fada mata zancen haihuwan da ta fara bijiro min dashi da kuma yawan gorin ban da komai a dakina sai tsiya,
Hmmm duniya yanzu ita Rabi har ta manta da irin halarcin da,akai masu kika fitar da dan ta daga dariyan shiya,
Idan ba aure nufin Allah ba har may zai zaunar da ke a gidan ta ko don basu san asalinki ba ,
Duk da yan uwan mu a kauye suke zaune ai muna cikin rufin asirin mu gwargwadon hali,
Idan ta matsa maki ni zan fito na fada mata,gaskiya wallahi don ba,rasa mai so kikayi ba ko don mun kyale kawai don malam Mudi,
Ganin da takewa uwar ki a gidan mijin ta haka ai rayuwan aure ne yakawo hakan,
Taci gaba da fitar da kayan ledan kasa sabo spoon, plate sai saitin kula na abinci mijina mai kyau,
Mama taso ta lissafa min kudin kayan amma sai nace cikin shagwaba haba mama haba mi zaki lissafa min ni wallahi na gode ,
Tace akwai bahohi da uan sauran tarkace za,a kawo maki daga gurin Fatima idan an sayo maki nace na gode mama,
Muryan Hamza ne ya shigo gidan cikin sallama daga kofan su Umma mukaji muryan shi,
Mama hafsi ce ke fada mashi shigowan Mamana Rahana,a zaton shi mamana Fatima,
Sai da ya,shigo yaga mama Rahana ce tazo muna, yace,
A,a mama sannu da zuwa idanuwan shi a kan kayan dake baje a tsakiyan dakin gaban mu,
Nan mama tai mashi bayani, akan komai da tazo dashi sai a lokacin yake cewa mama mahaifin Aisha baya gari ne cikin mamaki yake tambayan,
Tace baka sani bane Hamzs nan take dan mashi bayani tare da kara bashi bayani har da wanda ma ni ban sani ba,
Yace Allah ubangiji ya baiyanar muna dashi lafiya idan yana raye,
Mama hafsi ya fita yana fada mata tare da nuna mata kudin sai gata tashigo dakin tana cewa,
Ashe alheri akazo muna dashi haka ?
Mun gode Allah ya sa ta amfana da abinta muka ce amin ni da mamana,
Umma shiru tayi kamar ruwa ya cita don taga isharan Allah taga rashin amfanin yiwa mutum gori a lokaci guda,
Tun mamana tana tsaye mama Hafsi ke cewa sai a sai fridge zaifi samun karbuwa,
Don ko samarin nan masu zama kofan shago ai za,a samu ciniki a gurin su,
Mamana tai muna sallama inda fitan ta bada dadewa ba sakon sauran kayan suka samay ni nai murna kwarai,

****** ********** ******
Na gyara dakina da sabon ledan kasan da aka sayo mun, tare da yan sauran abubuwan amfanin da mama ta saya min,
An samu fridge dan madaidaici da kayan hadin shi sauran kudin da ya rage min yaya, Hamza yace zai cika ya sayo min dan maidaidai cin kujeran zama maicin mutum, biyu,
Hakan yasa dakin namu yakara wani kyau, gwanin ban sha,awa na idar da,sallah ina zaune na karewa dakin kallo naji wani dadi ya kumay ni a,raina,
Ina kallon dakin yadda ya sake min kamar ba dakina ba ga dan fridge dina,yana aiki sosai don nayi sa,a samun lafiyeyen fridge yana aiki sosai,
Ruwan farko da nafara sakawa,har gidan mu na aikawa wasu Ummina da abokan zaman ta dashi su sa min albarka,
Hamza da ya dawo yasamu yadda na gyara muna daki ranan bakin shi har kunne yake don dadi,
Wata sabowa inji yan caca don Umma ta saka dan ta daki akan cewa bata yarda cewa bashi ya bada kudin da akai min wanan sayayyan ba dasu,
Ai ba,a tashi sayo min ba sai da yazo gari kuma sai da tai min maganan flask ai,
Wanan sabon maganan da tazo dashi ne daga gidan aminiyan ta, da taje ta fada mata cewa iyayyena,sun kawo min alheri,
Sai take mayar mata,da yadda akayi da zancen flask din ranan,
Tace amma Rabi gaki kamar mai wayo ashe baki dashi ,
Yanzu yara kanana ne zasu yi maki wayo mai yasa ba,a tashi saye ba,sai yanzu da yazo gari,
Aikuwa take hankalin Umma ya tashi inda tahau zancen mama Sa,a ta zauna a kai,
Kamar an ce nazo gurin taga Umma daukan kwano sai naji Umma din nacewa ko sau nawa zaka rantse min cewa,bakai kaba da kudin wannan sayayan ba zan yarda ba,
Cikin ladabi naji yana,cewa Umma baki mamakin ina zan samu kudi haka masu yawa nai mata wanan sayayyan,
Ai duk inda zaka samo ka,sani tunda kayi niyar gyarawa matar ka,rai don nai mata gori,
Innalillahi wallahi Umma ko kur,ani za,a kawo na dafa wallahi na yarda Umma bani na,saya mata ba,
Tace tashi ka bari guri tunda ka zama dan bi bawan mata sai yadda karamar yarinya tayi da kai waikai gaka dan soyayya ko ?
Da,sauri nabar gurin gudun kada wani ya shigo ya samay ni azaci ko labe nake masu duk da na, yi dan laben, ai
Innalillahi nake uya furtawa a zuciya ya ina fadin na shiga uku da Umma a gidan nan,
Take zuciyana ya raya,min cewa fitan da tayi zuwa gidan mama, Sa,a ta dawo da wanan sabon zancen, a gidan,
Hakalin na yai matukar tashi a gurguje na,samu na karasa aikina ina waje naga fitowan Hamza din dakin mahaifiyan nashi rai a bace kamar zaiyi kuka,
Kofan gida ya nufa cikin bacin rai nan ya hadu da mama Sa,a wace dawowanta ke nan ta,shiga cikin gari,
Ganin yanayin shi ta matsa mai da tambaya sai da ya fada mata abinda ya faru tsakanin shi da mahaifiyar shi,
O Allah jama,a wai ina yaya ta,samo wanan halin daga sama haka ?
Don dai a da can baya,ban san ta,da,wanan halin ba sai yanzu,
Duk zama da wanan bakar aminiyar nata wace bata kaunar ta da,alheri amma ita,bata gane ba har yanzu,
Wannan matar, da tana da hali, ko, ku, diyanta, da tarabaku da ita don kalaman ta babu na alheri daga cikin sa,
Nan dai mama tace gabar zance kada ya,sa a ran shi ya,wahala, don Umma yanzu addu a ya kamata muyi mata don Allah ya yaye mata,wanan matsalar,
Maganan Mama yasa shi dan jin sasauci ga zuciyan shi har ya dan dawo normal,
Ina karasawa na koma dakina ina kwance saman sabon kujera ina,shan iska daga kofan dakina,
Yaro ya shigo yana cewa wai a bashi, ruwan sanyi ya saya, amma sai Umma take cewa ba,a sayar da ruwa ya fita ya damay ta,
Yaron sukayi kicibis da mama take tambayan shi ko may ke faruwa may yake so ne,?
Yaron yace na zo sayan ruwa ne ance wai ba a sayarwa a gidan nan ,
Zo kawai tace mai suka shigo tare inajin duk abinda ke wakana,
Labulen dakina ta daga take cewa tashi kibawa yaro ruwa ya,saya,namike nafara sayar da ruwana sana an da tazo min a cikin sa,a,
Umma tana jin mu amma takumay tankar bata jin mau kewa kana a gidan, har ruwan hamsin yaron ya saya ya fita,
Mutane suna shigowa saye abamu ruwa a ba mu ruwan sanyi,
Ibrahim yace min na dan yi zobo ko za,a saye ya aje min a shagwan shi,
Shi da,kan shi ya,sayo min abin hadin zobon da gorunonin da zan zuba a ciki idan nayi,
Take na,dan fara tara taro sisi na kaina daga kudin fridge dina da aka,saya min da kudin mahaifina,
Kishi karara da kyashi da hassada Umma ta nuna duk da tana wai kokarin taushe zuciyar ta,
Hamza ya fara zanceb noman shi duk ya manta da zancen fitinan Umma,
Don idan ya fita da safe sai da yamma,zai dawo gidan ,
Haka yasa fitina yanzu shi da Umma ba lokacin hin hakan saboda bai zauna ba balle suyi,
Ina zuwa school ina,sana,ata ga kuma hidimar mutanen gida da ta Hamza,
Ina zaune a baki kofana ina kokarin hada zobo ga girki kuma da,nake a dayan bangare,
Umma wace shigowan ta ke nan gidan ta,soma cewa aaa wanan wutan fa na may yenewa haka kamar za a dafa
Nai saurin daga kai ina kallon gurin da akaice wai ancika wuta a murhun,
Tsam namike nabar abinda nakeyi zuwa guri girkina na jaye iccen kamar yadda, tace nabar gurin zan koma,



ZAlINAB IDRISMAKAWA

SeEENABU
👑 SARAUTAR MATA 👑
2⃣5⃣


I,HHIDINAS SIRRATAL MUS,TTAQIN,,,,,


ZAINAB IDRIS MAKAWA



Matakin da mama ta daukar min a gidan ya kawo muna sauyi a cikin gidan don, sosai
Don a nawa bangare bana yarda abu ya hadani wanda zai kawo cin fuska a tsakanina da kannen mijina duk da sun girmayni sa,adatuce kawai zan iya cewa na girma acikin su,
Don haka suma suke taka tsantsan da ni don gudun fadan mama hafsi dake zaune da mu a gidan yanzu,
Ba,wai ba a magana ta bace kawai dai an daina min irin yadda ake min a baya can,
Don haka samun sasaucin da nayi yasa ni kara kyautatawa uwayen mijina, don kawar da komai,
Haka kawai na tashi ina son na gyara dakina don ba,zan shiga school sai Monday,
Ganin ina,wanan aiki mama hafsi da,suke zaune da Umma a kofan su suna shan iska sun gama cin dumamay da na kawo masu,,
Mama Hafsi tace a,a sarakuwana ko dan nawa zai shigo gari ne naga yau kin tashi da gyaran daki,
Daga gurin da,nake tsaye nsi murmushi, kawai,
Muryan Umma ce take fadin aikin san dan naki tunda kikaga tana gyara, zai iya fada, maya yana tafe,
Haba yaya ko ya,fada mata ai ba laifi bane yanzu bagashi tana gyara ba,
Tsab na dan kara,sanfarin dakin nawa washegari kuma nai kitso da kumshi, a gidan inda,na,kira wata,budurwa,mai sana,an kitso da kumshi tazo tai min,
Washegari ,ban da aikin komai, kasancewa duk na gama aiyukana da wuri ranan,
Don haka na dauko littafaina ina dan dubuwa don kara fahinta,
Wani yaron makwabtan mu Aliyu ya shigo gidan da,wasu leda guda biyu a hannun shi bakin shi dauke da,sallama, ya shigo gidan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login