Showing 96001 words to 99000 words out of 299981 words

Chapter 33 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17636

ki akan komai a,gidan nan,
A hankali na furta insha Allahu yaya zan kiyayye hakan daka ce,
Ki barta da,mama don nasan zaman su da mama zai kawo mata sauyi a cikin rayuwa sosai,
Don haka idan har munyi hakkuri komai zai zo ya,wuce tankar ba,a yi shi ba a gidan nan,
Nace a hankali cikin sauke ajiyan zuciya insha Allahu yaya zan yi kamar yadda kace to amma kuma zancen haihuwan da Umma da,su Asmau suke fadi duk har nawa nake da za,a matsa min da zancen haihuwa,
Ga su anty kubura nan babu wanda ya ya damu da zancen haihuwan su saini ce kawai xa a sakawa ido don ba,a so na a gidan,
Hmmm waya fada maki ba,a sonki a gidan nan Humaira,?
Ni dai kin san ina son ki zarah tana sonki haka ma Ibrahim ga kuma mama da tazo,
Kai kowa ma kin san yana sonki gidan nan gar Umma din, don haka kar na kara jin ko ganin kin bata ranki a banza,
Na kara amsawa da fadar insha Allahu a sanyayaye inda ya sa hannayen shi ya rugumoni a jikin shi tare da matse ni gam cikin jikin shi kamar wani zai kwace ni gare shi,,,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
👑 SARAUTAR MATA 👑
2⃣7⃣

GAIRUN MAGGALUDBI ALAIHIM WALLAD,DDALI,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA


Satin su Hamza biyu yau da dawo daga ma karanta, ke nan,
Mukuma sai fama da exam mukeyi inda karatu ya sha min kai don yanzu haka da taimako mama hafsi dake gidan na ke dan samun time din karatun mu,
Sai kuma sa,ar dana samu yaya Hamza yana gari yana kara wayar min da kai a inda yai min zafi,,
Yau na samu mun gama exam don pepper daya mukayi muka fito tun twelve,
Nadawo gida da gajiya a,tare da ni don haka na watsa ruwa don naji sanyi a jikina,
Nafito na shirya a cikin wasu kaya nawa masu kalar baki da zanen farin flawer a jikin shi ko ina,
Buje da riga ne nai kasan bujen fish tail, ya dan baje daga kasa daga sama na ya tsuke ni,
Sai dinki rigar kayan mai umbrella yasha dan tattara yai min kyau sosai,
Na dan shafa kamshi na gyara dakina tsab wanda dama a koda yaushe a cikin gyara yake, duk da ba komai a dakin, sai rufin asirin Allah,
Ina daura dan kwali naji sallama har ta kofan dakin mu muryan kuma bazan sheda shi ba,
Na amsa yayin da naji Mama Hafsi tana kara amsa masu,
Mun fito kusan a,tare da Mama Hafsi din a lokaci guda daga dakunan mu,
Wasu yan mata ne ko mata zance manya guda biyu farare masu kiba don ko wacen su zata iya goyani bata san cewa ta goyani ba,,
Sannun ku da zuwa sai wani shan kamshi suke muna suna karewa gidan mu kallo suna tauna chewing gun kas kas kas,
Mama ce tace bayin Allah bamu ko gane ku ba ?
Dayar tace O eh gaskiya naku san mu ba don Allah maman Hamze muke ke nema please,
Waye kuma Hamze, ina
Tau inji mama tana binsu da wani kallo ita ma sai nice nace ku shigo daga ciki, ko,
Dakin Umma na nufa dasu tana ciki zaune tana dan gyara wani abu a leda nace cikin yar sanyin murya na Umma ga baki,
Gaba dayan su suka bi junar su da kallo cikin jin murya na da kuma yanayin tafiya ta,
Suka shiga dakin da,sallaman su tare da dan tsugunawa suna cewa Umma sannu da gida,
Cikin mamaki sukewa dakin Umma din kallo suna dan tabe baki dayar tace Umma mu bakine daga Zuru mun zone mu gaida ke dama,
Guri guda muke karatu da Hamze na gidan nan shine mukace bari mu shigo mu gaida ku,
Lokacin na kawo masu ruwa da zobon gora masu sanyi nace masu ga ruwa kusha,
Na dauko tabarma daga can cikin kuryan dakin Umma din na,shimfida masu suka zauna a kai,
Mama hafsi tace wanan itace Aisha matar Hamza din da kuka zo gayarwa,
Sai duk suka kara dagowa suna kallona nikan na juya nafita sai dai kuma naji wani irin faduwan gaba ya sauka min,
Dakina na,shiga na zauna saman kujera na a hankali ina tunanrn cewa su wan yan nan din su waye,
Kamar an jefo shi sai gashi ya shigo gidan naji muryan shi yana cewa mama inda mama Hamsi din ta karba tace naam dan mama ka dawo yace eh ,
Sai ya nufi dakin mu yana,son aje takardan da ya,shigo dasu, a hannun shi,
Mama tace idan ka fito kana da baki gasu nan dakin yaya,
Baki ya juya yana tambaya da mamaki hannun shi daya rike da labulen mu,
Sannu da zuwa nake mai ya kara juyowa gurina yana kallona yace Humaira har kun fito exam din ne nace eh,
Dakin ya,shigo yana aje takardan yake tambayana su waye suka zo Humaira,
Nace a dakile wasu matane suka shigo su biyu suke neman ka koda yake sun ce Umma,suka zo gayarwa,
Yafita zuwa dakin Umma din na mike na dauke takardan na adana mai, a jakar kayan shi,
Turus yayi yana kallon su a cikin mamaki,,Halima kune a gidan mu ?
Mune inji wace ya kira da Halima din tana wani murmushi tace mun shigo gaida Umma ne ai,
Ruwan sanyi da zobon dana aje a gaban su ya,dan kalla yasan bazasu sha ba ya juya yana cewa ina,zuwa ,
Can yadawo gidan dauke da kwalaben drinks masu sanyi d,biscuits a,cikin wani leda,
Ya shigo dakin yana cewa bani cups Humaira nakai masu na mike daga inda nake na,dauko wasu cup din tangaran dina ,
Yajuyya fuuu ya fita zuwa, dakin Umma din gurin bakin nashi,
Ina zaune ina kallon yadda ake dawainiya da bakin sai mama Hafsi ce tafito daga waje ta zauna a saman wani kujera ta mude fuskan ta,
Abin fitara Umma ta miko masu tana cewa karba ku dan fita akwai zafi wallahi,
Halima din ta daga kai tana kallon tsohon rufin dakin Umma din tana cewa,
Umma ya kamata a saka maki fanka a dak8n nan don zafin zai maki yawa, ai, idan ba fanka,
Umma tace yar nan mu marayun Allah ta fanka mukeyi muna ta abin da zamu ci,
Umma tace aida kun koma daga can dakin Aisha ku zauna zafi nan din dan shan iska ai,
Kibarshi kawai Umma ai nan din ma yayi muna zamu zauna a hakana,
Dan kadan suka sha drinks din tace Yau gamu a gidan ku yau dai munga Umma,
Kullun kana muna hiran Umma Umma dai ,
Umma taji dadi har a cikin zuciyar ta najin dan ta ya damu da ita a makaranta har zancen ta yake yi,
Hamza yace a daidai lokacin da na fito don dauraye plate naji yana cewa,
Kun ga wife dina Aisha Humaira ko ?
Dayar tace mun ganta da muka,shigo ina itace yar yarinyar da muka gani kamar under ege, ko ?
Yai yar dariya yace aiko ta girma yanzu don gashi har tana batun shiga two hundre a health and technology,
Ita wanan karamar yarinyar din ?
Suna a zaune sai hira suke suna dariya a tsakanin su Umma daga gefen su sai washe baki takeyi,
Sallama akai ma Hamza din ya fito daga dakin zuwa gurin da,ake neman shi a waje,
Ina duke ina,wanke gorunan zobona yazo ya gitta ta gabana ban ko dago kai na dube shi ba,
Sam baiji dadin hakan ba don yasan ban taba mai haka ba a rayuwan zamana a gidan, su, sai yau din nan,
Yana magana da bakon shi da ya kawo mai maganin feshi amma zuciyar shi na ga yadda nai mai ko in kula,( kishi)
Ledar da suka shigo da shine daya daga cikin su ta aje a gaban Umma tana cewa Umma baida yawa dama mun ce bari dai muzo mu gayar da ke, ne
A,a,a duk wanan ni kadai wanan ai yayi yawa ga,zuwan da kukayi ga kuma,dawainiya haka mai yawa,
Angode Allah sa albarka nagode nagode kunji sai dayar tace Umma wanan ce Halima itace dama suke tare da Hamza a can makaranta tana yawan taimaka mashi da abubuwa da dama shine tace ya kamata muzo mu gaida ke don ki san da ita, itama,
Tau taufa Umma ta dago kai da sauri ta dubi maimaganan tace wani irin magana ne wanan kuma yaran nan,?
Tace to may zamu boyewa Umma tunda da aure take son ka ita ?
Aure inji Umma ?
Gaskiya yarinya kin zo da sabon zance Hamza marayane bamu da kowa sai Allah kinga yar matan shi da muke maneji a gidan tare da ita,
Ina muka ga kudin auren irin ki a gidan nan ko ainda zamu aje irinki ai mu bamu dashi,
Dariya sukayi Umma wanan ai mai sauki ne a gare mu mu kawai yarda ki muke nema ki bamu baki ya aure ta,
Don shi mun rasa gane kan shi bai bata hadin kai yadda muke so,
Kuma wallahi a tsakani da Allah take son ta aure shi ita,
Kafin Umma tai magana mama Hafsi ta,shigo dakin tana cewa,
Ku da kata don Allah wani irin magana kukazo dashi, gidan nan,
Yanzu ku don baku da kunya shine zaku shigo muna da wanan zancen haka ba kuyan bajin wani nauyi, a idanuwan ku,,
Hafsi ki barsu su fadi abinda ya,kawo su aiji ba aiki bane, dashi dole don haka ki barsu muji shakuwan su ko,
Shiru sukayi don jin mai matan gidan suke fadi inda Mama Hafsi tace duk cikin ku wacece sa,ar auren hamza din ,
Don haka na roke ku da kubar min yaro na ya zauna lafiya da iyalin shi kada ku kawo muna,sabon fitina a,gida,
Boyar Alkah dakata ki ji mu bawai munzo ne akan zancen yanzu yanzu ba
Mun dai zo ne dan mu nuna kan mu asan da zancen a gida,
Hummm,ummm
Ikon Allah,
Allah ka kawo mu zamani kuma ,
Ba wai hakana bane mama kawai dai kada ace ana abu baku da labarin komai,
Sai zuwa wani dan lokaci a na zaune dasu zugun zugun tsakanin su da su Umma nikan sai sintirina nake ina aiyukana a tsakar gidan,
Ya shigo yana cewa sorry Halima na barku a zaune ko,
Kuzo ku gaisa da madam dina mana din ta san ku itama,
No kabarshi idan mun fita zamuyi sallama da ita ai,
Sai ta juya gurin Umma cikin dan kashe murya suna cewa,
Umma da,fatan zaki duba zancen mu da idon basira ki fahince manufan mu a gare ku,
Wani kallon mamaki yakewa bakin nashi don bai fahinci akan may suke magana ba,
Don bai taba tsan manin cewa zasu iya fadawa Umma zance maka man cin haka ba a,gaban ta,
Jin ana kiran sallah ko ina yasa su dagawa suna cewa,
Yanzu zamu koma sai wani lokaci ta juya inda Hamza yake a tsaye tana cewa dear na zamu, koma amma ga wanan ,
Tafara kokarin sa hannu a jakkanta tana ciro kudi tace a,sayawa Umma fanka a saka mata a,daki, ko,
Ke Halima baki gajiya da yin dawainiya ko yaushe sai kinyi hidima a mutum,
Umma itace fa ta aiko da kayan kwaliya kwanaki nakawo wasu Asma,u da sa,a,
Yafada cikin yar fara,ar shi batare da fahintar komai ba, a zuciyan shi,
Ina a zaune duk zancen da,ake ina jin abinda ake fada dama tun farkon fitowa na mama tai min signal da na kyale na kada kaina kawai ban ce komai ba,
Sun futo ana yan dararaku tsakanin su sunayiwa Umma sai watarana,da godiya ita dayar mai suna Bicky tana cewa Umma a diba muna zancen mu dan Allah,
Wai wani zance ne wanan kuke ta magana a kan shi Hamza din yake tambayan su don son jin maganan,
Babu ruwanka Bicky din ta fada maganar ce da maman mu,ai,
Sun mikawa Mama Hafsi kudi tace ku barshi in kunzo ne don ku saye mu ku cuci dan mu toni ba haka nake ba,
A,a mama wanan ba haka bane kawai munzo ne don mu gaida da ku kuma ku san mu,
Har zasu fita ya sake cewa baku gaida wife dina ba fa tana ciki dakin ta,
Dole suka,shigo dakin namu ina zaune na idar da sallah a lokacin na karba masu fuska ba yabo ba fallasa
Sun wani zauna suna kallon dakin dawaini irin karkada kafafuwan su,
Mikewa sukayi suna cewa zamu tafi sai wani lokaci mun kara haduwa,
Nace, sannun ku mun gode da kulawar ku gare mu,
Dariyan yake sukeyi suka ce ai ba komai, sai anjima ko,
Rakasu na yi zuwa kofa na yadda shari,a tace kaiwa bakon ka,rakiya ladane,
Daga nan nai masu Allah ya tsare hanya na koma ciki,
Zama nayi zuciya na tana wani harbawa don sai a lokacin nai masu kallon tsab don zan iya cewa sun haife ni dukkan su don ba yara bane gyarane kawai ya rufe shekarun su,
Suna ficewa gidan mama hausi tafara fada tana sababin inda take shiga ba nan take fita ba, ba wanda ya tanka mata
Abin duniya duk ya,sha min kai ko magana ban samu yi ba,
Don ita Umma sai farin ciki take tana cire kayan da,aka,kawo mata,sai faman yabawa take tana sa albarka,
Turumin zani ne sabulai, man shafa, turare da takalma silifas mai kyau,
Ya kai wani lokaci a,waje bai shigo gidan ba,sai zuwa yamma liss ya shigo ya samay ni a bakin murhu ina kwasan abinci,,
Sannu da,zuwan da nai mashi batare da na,dago kaina kona juyo in dubi shigowan shi ba,,
Buta,ya,sura zuwa,ban daki yafito ya zauna ya na son daura alwala,
Umma ce ta shigo gidan da ledan kayan da ta tafi nuwa,makwabciyar ta, aminiyar ta,
Ganin Hamza a gida yasa ta dan tsaya,gurin shi bata karasa isa gareshi ba,
Tace ashe ka,dawo sun tafi ko,?
Yace ai tun fitar mu suka tafi dama daga Birnin kebbi suka karaso nan, din,
Tace kaga,abinda ta zo min dashi ko ?
Gasu nan, na tafi nunawa Sa,ade tagani itama ta samasu albarka,
Kaya kuma ita Halima,din ta,za maki dasu mama,bafa musulmai bane kin san halin kiristan din nan da son shigewa,mutane,
Kirsta,kuma inji Umma ta fada a gagauce cikin mamaki,
Umma kina,mamaki ne, kin san su yan zuru ba, a gane musulman su sosai don kirstocin shigar musulmai suke harda hijjab da,gyale suna yafawa,
Cudan yan su gida guda da musulmai da kiristocin yasa kowa ya iya aladan wani,
Zaki shiga gida guda komai a,tare akeyin sa,amma,kowa da,addininsa uwa daya Uba daya
Daga daki mama hafsi take fitowa tace haba biri yai kama da mutum ai, yanzu yaran nan kafirai ne suka zo muna da,wani zancen banza a gida wai yaya ta bada baki ta bari ka auri dayar matar,
Mama su suka,fadi hakan da kan su mama tace aiga yaya nan gurin ta,wai, su kazo suna neman hadin kan ta ta,yarda ka,auri mai sonka din,
Wallahi mama sam, ni ban san da wanan zancen ba,don wani makamancin irin wanan zancen bai taba,shiga tsakani na dasu ba,
Sai dai harka kawai na karatu saboda likewar da tai min yan ajimu ke cewa,wai ni kanin Halima ce, haka yasa muke mutunci da ita amma ba zancen soyayya a,tsakanin mu,,
Sai a lokacin ne ya,daga kan shi yana kallon guri da,nake na mike zan kwashe kayan abincin da,na,raba,
Yake cewa a,ranshi amma halima,yau ta cutar danin ta,zubar min da mutinci na a,gurin yan uwana,
Ya kara dago kan shi kara na,biyu ya,bini sa kallo fuska kawai ya nuna mai canjin yanayi a tare dani,
Umma tana kokarin nuna mai kayan ya fara alwala yana cewa, Umma bari kawai zan ciwa wanan matar mutunci ne don kada ta kawo min iskanci har a gida,
Ina wanan zancen ya fito haka har take kulla min sheri, haka har a gidan mu zata zo tana irin wanan maganan kamar wace ta samu tabin hankali,
Wallahi mama ni a zatona ko zuwa sukayi don zumunci kawai,su san gidan mu,
Kayan da bai duba ba ke nan yai, alwala ya fita abinshi kawai ya bar Umma rugumay da kayan a hannuwan ta

****** ********** ******
Duk yadda mutum yai tsan manin rayuwan kubura yan zu abin ya,wuce nan,
Gashi mahaifinta ya saka mata dokan cewa duk tafara ta kashe auren ta ba dai gidan shi ba,
Don ya fahince ta ita da uwar ta,so suke ta kashe auren ta ta,dawo gida tana mashi iya,shege cikin iyalin shi,
Haka yasa dole ta koma dakin ta, tazauna tana hadiyan hakkurin ta ita,daya,
Wani iskanci da iya,shegen da tai dammaran yin shi a gidan Alhaji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login