Showing 99001 words to 102000 words out of 299981 words
Nura yanzu duk ta sauke wanan mugun hali ta koma bi, da, rarashin kawai,
Wani jiji da kai da basarwan da take a gidan duk ta,sauke su don ba wani wanda ya damu da ita kowa ya fahinci halinta tun farko an kama kai da ita,
Dole badon taso ba ta sauke fadin rai din yau Jamila tana zaune a falon gidan nasu tana kallon wani Indian film, sai ga Kubura din tafito saye da wani don riga baki ta daura dankwalin shi a,kanta,
Jamila tana ganin futowan ta kamar kullun taja mata irin addu,oin da ta,sabayi akan Kubura din kamar haka,
La,illah haillah mohammadan rasullillah, sau uku,
A,uzu bi kalamatillahi tamatati min sherin min halaq,
Muryan Kubura ne ya ratsa kunnuwan ta tana cewa yau India aka i muna,
Ta dan dago kanta tankar a lokacin ta ga,fitowan ta daga dakin ta, tace eh wani film nake kallo a tashan,
Kubura ta kai zaune tana cewa ni ban faye son tashan irin haka,ba nafi son na kallli hausa ko yaya yake,
Don baki saba dasu bane aida bazaki barsu ba don suma,suna fadakarwa a ciki ai,
Nura ne ya,shigo gidan wanda dawowan shi ke nan a lokacin don bai kwana a,gida ba,
Yana rataye da couth din shi a kafada ya,dan sasauta nicktie din wuyan shi, kadan,
Kallon mamaki yake masu gaba dayan su don bai taba tsanmanin ganin su a haka,ba, ya kalli wancan ya juya ya,dubi waccan,
Cikin rashi sakin fuska Jamila tace sannu da dawo,
Kubura wace take zaune a gefe guda ko kallon shi bata yi ba tace mai ina kwana kawai,
Ya dan shiga da yan min tina Jamila wace ita ce da girki a ranan ta dan mike dingis dingis zuwa dakin shi ,
Idan ba kunnuwan ta ke mata karaya ba zata iya cewa fada tadan ji Jamila din tanawa maigidan nasu, don tafahinci akan dawowan shi lokacin take magana daashi,
Mikewa tayi zuwa dakinta don rashin ganin dacewan hakan, don zamata a,gurin tana sauraren sirin su tankar wani abinda bai dace ba take yi,
Kwance take tana nazarin abinda taji suna fada wa junan su,
Yanzu Nura ya dace ace mutum mai iyali kamar ka dai yanzu zai dawo gida cikin iyalin shi,
Yace cikin irin halin shi na,dakawa mace tsawa wani ya turo ki kimin fada ko kuwa,
Jamila tace amma kasan hakan baidace ba ace namiji mai iyali baya kwana cikin italin shi yana can yana bariki sai lokacin da yaga dama ya,dawo don kan shi,
Tun yaranka basu da,wayo har yanzu sun fara fahintar halinka cewa a can ka kwana ko,
Yau Amira dagewa,tayi wai bata zuwa school idan bakai zaka kai su kullun ko wani yaro baban shi ke kai su,
Yace look ki fita ki bani guri ina bukatan hutawa kin zo kin cikani da surutun tsiya haka,
Sai ka tafi ka,wullakanta kan ka a,duniya ka dawo gida kana wa mutane cika da batsewa,
Jin motsin ta yasa Kubura shawaran komawa daga cikin dakin ta
Tambayan ta anan shine ina Nura ke zuwa haka wanda duk dare sai ya tafi,
Kardai ace neman mata yake haka har yai muni kada fa ya jawo masu matsala ko wani mugun cuta ya saka masu,
A hankali ta furta cewa Allah gamu gare ka ka kare mu daga mugun ciwon zamani, a rayuwan mu,
Mirginawa tayi tanamai jin haushin kanta akan rashin kwantar da hankalinta tun shigowan ta gidan ta fahinci mai gidan ke ciki,
Ta dauki fadin rai ta saka a ranta tana ta wahala tsayin shekara da,watanni,
Gashi yau yau da,fara kwantar da kanta tafara fahintar wani abu a gidan,
Lalai sai tasan ko may mijin nasu yakeyi wata,sana,a ce yakeyi irin haka har yake hadasu fada da Jamila mata mai hakkuri, kamar ta,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
👑 SARAUTAR MATA 👑
2⃣9⃣
RABBANA, LA TUZIGH QULUBANA, BA,DA, IDDZZI, HADAITANA , WA HAB LANA MIN LADUNKA RAHMATAN INNAKA ANT AL WAHHAB,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
DON ALLAH YAN UWA INA BARAN ADDU,A AGARE KU KU TAIMAKENI KU TAYANI ROKON ALLAH AKAN ABINDA NAKE BUKATA A GURIN UBANGIJIN MU ALLAH SUBBAHANAHU WATA,ALLAH,,,,
Wasa wasa yanzu anfi sati Umma tana kwance masasaran yaki tsayawa har ya kaita a kwance, sosai,
Yar uwar ta mama hafsi ke faman dawainiya da rashin lafiyan Umma din, sai ni dake faman dafe dafe a gidan
Naka shiga dakin fiye da a kirga don na gaida Umma na Kuma duba lafiyan yata, nakuma wanke kayan da tai amfani dasu,
Ranan da ta cika sati Daya a ranan na shiga daki na Sami duk yaran Umma suna a kanta, tana cewa sanyi take ji su rufa mata bargo, sai rawan dari take daga kwance,
In tsaye daga gurin da nake ina nazarin abinda ke damuwar ta gashi sai faman dirka mata magani akeyi
Ina mai kura mata ido, sai naji suna cewa wai, za a Kira Mai chemist yai mata allura,
Ni ko na fahinci wani abu a jikin nata sai dai Ina tsoron magana suce ban San komai ba, na jawa uwar su mugun ciwo nake mata fata,
Daga inda nake tsaye daga bayan su nace amma yaya da kiran wanan mutumin ai da kawai akai Umma asibiti gurin doctor ya dubata zai fi wanan, kaura da kai din da ake tayi a gida da ita,
Duk kan su suka juyo inda nake suna masu sako min idanuwan su, gaba dayan su
Kaji malamar asibiti fa aida sai ki dubata idan har kin gane wani abune, jibrin ne yai wanan magana,
Mama da Yaya hamza suke cewa tun da kukaji Aisha tai wanan maganan akwai abinda take hasashe ke nan,
Ibrahim yake cewa, cikin, tambayana Aisha don Allah kokin fahici wani abin ne suna masu sako idanuwan su a kaina,
Cikin harshe turanci wanda zance duk gidan nan ko shi Hamza din bai taba sani na iya turan ci ba haka nake masu bayani, komai,
Don ina gudun yi da hausa Umma taji tace ina mata mugun fata ne,
Jikin su gaba daya yai la,asar suke cewa gaskiya ya kamata subi shawara na don bai kamata ace sun aje ta a gida ana magani daban ciwo daban,
Fita Hamza din yayi zuwa wani dan lokaci sai gashi ya shigo gidan a cikin, saurin shi tun a kofa yake kiran mama,
Duk muka yo waje don son jin may zai fada tunda kowa a tashe hankalin mu yake,
Ance mai baki bai iya ciwo ba don Umma ta wani koma ragwab da ita duk tafita hayacin ta, sai nishi take daya daya
Mama ga mota a,waje mu tafi ko?
Ina shiga dakin naga yadda idanuwan ta suka juye sukai, weak a lokaci guda,
Da sauri har ina ture Ibrahim na karasa bakin gadon a gaban Umma na kamo hannun ta ina dan massage din hannun nata a hankali har wani dan lokaci,
Sai naji tai wani irin ajiyan zuciya a hankali sai da kowa yaji a,dakin,
Duk sai suka kara rudewa hankalin su ya tashi,
Nace Mama ku kamata a tafi sai dai aiwa driver magana ya tuka ta a hankali don Allah saboda tana bukayar resting sosai,, saboda jikin ta is already been weak,
Hankalin su gaba daya ya tashi sai wasu suka fara kuka suna cewa wayyo Umman mu Umma don Allah kada ki mutu ki barmu,
Cikin tsawa mama take masu fadan wani mugun fatane haka sukeyi ai ciwo ba mutuwa bane,
Ke Humaira dauko hijjab dinki mu tafi asibitin a tare zaifi,
Ba musu na shiga daki kamar yadda ya umurce ni na dauko hijjab dina a tare muka tafi,
Ni da mama muka zauna a baya tare da Umma ina dan mata masage yadda ya dace ce,
Mun shiga inda duk wani abinda ya dace ayi na ganin likita tare da Yaya Hamza mukayi kasancewa akwai yan makarantar mu da su kazo practical a gurin,
Sosai zuwana ya taimaka nan da nan muka shiga gurin likita don bada bayani, abinda ke damun ta,
Likita ya tambaye, ta ta kasa magana kamar maijin tsoron shi, dole ban san lokacin da na bude baki nafara yiwa likita bayanin yadda Umma din tafara ji har zuwa yanzu da abin ke son zama mata blood pressure,
Tambayana yayi wasu irin medication mukai mata a gida nan ma tirya tiryan nai mai bayani har zuwan mu asibiti ,
Yadan bugi taburin gaba shi yace she is, very luck dat you are around if not she will die or be in critical condition,,
Umma tana rike a hannuna sai nishi take guda,guda, tana kara kamay wa,cikin tashin hankali,
Are you a student ?
Tambayan da yajefo mi ke nan lokacin da nake kokari gyarawa Umma zanin ta daya rankafo,
Nabashi amsa cikin gyada kai da cewa yes,
Where are you schooling ?
Health and technology nabashi amsa a takaice tare da mikewa ina kokarin jan Umma gurin gadon da yace tahau,
Sai yace, interested,,,
Yakamata ace parents naki nursing suka kaiki ba health ba,
Don you are very intelligent gaskiya yakamata ace nursing kika tafi,
Maigida na nan yake son nayi karatu shiyasa na tafi can din,
Naba shi amsa a daidai lokacin da nake gyarawa Umma kwamciya,
Na juya nafita nan na barsu da Yaya Hamza ina fita na samu har su yaya Ibrahim da su Jibrin duk sun shigo asibitin mama tana masu fadan an watse anbar gida babu kowa, su Asmau, su koma gida,
Amma sai sukai banza da zancen ta kamar basu ji ta ba,
An dan dauki lokaci yaya yafito yana cewa an bamu gado za,a kwantar da ita,
Nan muka shiga kuma dawainiyar kwantar da umma wace daga zuwa akai mata allurai masu karfi da kara lafiya sai drips da akai setting za,a kara mata,
Ganin komay ya dan kammala nace zan koma gida don nai mu na abinci da za,a kawo asibitin,
Tuwon masara,nai masu da miyar kuka,da nama,a cikin sa kamshi kayan yaji da daddawa yana tashi daga cikin miyar,,
Ranan ni kadai ce a gida sai ban samu komawa,asibitin ba ina fama da,aikin gida, da yai min yawa,
Sai dare sosai ina daki banyi barci ba a lokacin don tsoro nake ji sosai saboda ni kadai ce a gida, duk suna,asibiti gaba dayan su gidan,
Ya,shigo gidan inda shima tun a,waje yaga gidan yai mai wani fadi fayau,
Ya shigo da yar mashin din shi daga ciki ya kaita kofan mama inda yake ajewa ya kulle,
Sannan ya juyo zuwa dakin mu cikin takon shi na, natsuwa,
Zaune nake saman kujera na idanuwa na,a kan kofan shigowa,
Yana shigowa na gyara zama na mike sosai ina cewa sannu da zuwa Yaya ?
Ya dan rugumoni daga gefe tare da shafan dan kumci na yana cewa cikin harshen turanci ni ban son kiran yayan nan da ake min fa,,
Murmushi nayi nace anfitar dani a cikin kannen ke nan ko kuwa,
Kafin ya kai ga bani amsa sai nace ya kabaro jikin Umma din da sauki yanzu ko?
Ya ce da sauki don tana ta barci ne har yanzu sai ruwan ake kara mata nace shine lafiyan ta,
Abinci na gabatar mai tare da mikewa nake cewa ga ruwan wanka, zan kai ma bayi,
Har na kai ruwan wankan bayi na dawo yana zaune inda na barshi yayi tagumi da hannayen shi, dukka biyu,
Lafiya dai yaya ? Natambaya cikin son jin may yasaka shi tagumi haka,
Ya sauke yar ajiyar zuciya yace Humaira dole ne ki ganni haka don ban da kudi a hannuna duk na zubasu a gona gashi dan kudin mama da ta ban na saya mata kangon gida dashi,
Ga kuma lalurar asibitin nan yataso komai na kudi ne yanzu asibitocin mu ba tausayi a cikin su,
Kudin zasu kai nawa, ? Natambaya cikin son jin yawan abinda zai bukata na kudin,
Sai daya dan sa hannun shi a bakin shi ya busar da wata iska mai nuna bak8n ciki
Yace na, dai rike koda goma ne don test test din da ake yawan yi mata, su ne ke cin kudin,
Nace akwai kudin da mama ta bani na bawa Ummi na daga ciki sai na,sana,ata dana tara a asusuna zan fasa naga may ke a ciki,
Yace kinga kuma ga abinci don duk da,asibiti gurin jinya ne amma yan sa ido na gurin suna kallon kalar abincin da ake kawo wa mutum daga gidan shi,
Wanan matsalar su ce don wani ma idan ka rabu da shi har abada,bazaku kara haduwa dashi ba,
Yace hakane Hummaira amma ya kamata na samo dan shinkafa da,sauran abubuwan da,za,ayi amfani da,su,
Nace dare yana yi ruwan wankan ka yana a cikin bayi kada yai sanyi ko wani shedani ya taba ma,
Yana fita na dauko a susu na nafasa nazauna kasa dirsha nafara kidaya kudin dake ciki na,samu shauku da dari takwas, cif,
Yana shigowa da ruwa a jikin shi yana daure da zani na da ya daura da zai shiga wanka,
Na ce mai ga kudin na fasa asusu sha uku ne da dari takwas na samu a cikin sa,
Yakai zaune bakin gado yana mamaki yace duk da wanan sana,an kika tara wanan kudin haka?
Gaskiya sana,a tana da amfani sosai shiyasa akace zaman banza baida amfani a rayuwa,
Yanzu gashi zamu ci albarkacin sana,ar cikin gida a gurin ki,
Yakarbi kudin yana cewa Allah ya bani ikon biyan ki su a cik8n dadin rai kamar yadda ya dace duk wani wanda ya dauki bashi ya fadi,
Ranan ba wani abinda ya shiga tsakani na da Hamza don ya kwana ya na juyi saboda damuwan ciwon mahaifiyar shi,dake a rayuwan shi,
Washegari tun da asuba na tashi na,dora ruwan kunu da sauran aiyu ka don nasan bawanda zai taimaka min da aiyukan, tunda mama bata gidan tana asibiti a can ta kwana tana jinyar yar uwar ta,
Ranan bani na samu kaina ba sai kusan karfe daya alokacin komai da ya kamata nayi nayi nagama na gyara gidan fes ta ko ina,
Nai wanka na sa wasu atamfana wax masu ruwan blue color,
Shigowan shi gida don daukan abinci ya samu na shirya nima sai dai ban yarda mun fita ba sai da na zaunar dashi a cikin dubara ya danci wani abin sannan muka rufo kofan gidan zuwa asibiti,
Kofan gida zamu hau mashi muka hadu da Baba Mudu wanda ya fito daga cikin gari,
Hamza ya sauka ya nufe shi acikin alkunyar sarakuta kamar kullun suke gaisawa,
Nan Hamza ke fada mashi Umma ce aka kwantar a sibiti ba lafiya,
Ba ya dago kai gurin da nake a tsaye da kullan abincin dana kulle ga wani dan kwalina, yake cewa,
Kin aika cikin gida a fadawa iyayyen ki kuwa Aisha ?
Nace Baba ban samu yaro ba yau duk su Aina basu shigo guri na ba,
Yace kin san yau ana zuwa boko babu kowa duk sun tafi makaranta ku isa insha Allahu yanzu zan karaso nima insha Allahu,
Mun samu ba laifi Umma ta samu lafiya don tana zaune saman gadon ta tana magana da kishiyoyin Anty Zarau,
Mun gaisa da,su nai masu yaya maijiki suka karba min da,Alhamdullahi,
Na aje kwanonin abincin daga can inda naga kayan abin karin safe dana aiko masu dasu,
Na lura Umma sai da kyat take amsa min gaisuwa na ina zaune ruwan dake manne a,jikinta ya kare sai ake kira nurse on duty ta cire mata take cewa tana aiki gata tafe,
Ganin ruwan ya kare zai iya fara dan sinking din blood din ta yasa na mike daga gurin da nake na nufi inda cotton yake na debo na wuce direct gurin ruwan na cire na mayar da canular din na,rufe mata
Ke Aisha kada kije rigima ki ja min matsala a ce sai an sake yi min allura, ko wani abu don walle duk na gaji da soke soken nan,
Umma ce ke fadin haka cikin maganan ta na yanayin mara lafiya, take maganan da kyat,
Lokacin ne nurse din ta iso gurin don cirewa Umma ruwan bayan mintinoni da na cire mata ganin ancire anyi komai yadda ya dace yasa ta dan fara waige waige tana cewa wacece ta cire maki ruwan, ?
Cikin sauri Umma take cewa dama ai na fadi rigimar yarinyar nan kada ya jawo min matsala,
Gata nan waje sallonta, ta cire min shi, ina cewa tabari amma sai da tacire, saboda iyayi,
To ai tayi daidai don ni ban zaci ruwan ya kare haka ba gaba daya ina ce kadan ya saura suka kirani, kin kuru da yaja jinin ki badon tana gurin ba,,,
Inda nake nurse din ta juya tana cewa, amma kina karatune ko,?
Nadan bata amsa cikin gyada kai tare da cewa eh ,
Wani school kike karatu nace