Showing 114001 words to 117000 words out of 299981 words

Chapter 39 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17676

nan dama ai can sherin kune kuka,dauki tsana kusawa yar mutane,
Ummi dake dakin ta taji abin yaki karewa ta fito tana cewa haba malam haba kubar wanan zancen haka dan Allah,
Hakan ba girman ku bane dakai da yaya ko ina duniya ko bana nan Aisha yar kuce don gaba dayan ku bazamu manta da halarcin da kukai mata ba na zaman ta gurin ku,
Ta juya gurin mama saude tace Yaya don Allah ki bar maganar nan aishi maso habaici dama maso fada ne,
Atika daga kofan kitchen tace nidai na fadi gaskiya don dama daci ne gare shi,
Da kyat Ummi ta rarashi mamata shiga dakin ya a cikin bacin rai don zancen atika da mijin su ya bata mata rai sosai,
****** ********** ******
Gidan yai muna tsauri saboda ga,damana tai nisa duk kudin Hamza ya watsa su a gona yana duban abinda zai girba idan lokaci yayi,
Don kwanciyar Umma ya jawo masu rashi kudi a hannun su,
Mun wayi gari dan kamun da zamu dama kunu a gidan yadan buwaye mu,
Gashi babu abincin da zan dafa muna da rana muci,
Hamza ya shiga dakin gurin Umma yana tambayar ta ko akwai dan kudi a hannun ta sai ta ara, mashi, har ya,samu ya mayar mata,
Amma sai Umma ta kyankyashe kasa tace batada ko kobo a hannun ta ya tafi gurin matar shi ai tana sana,a ta ara mashi,
Cikin dan marairaice murya yace Umma bata dashi ne dana karba a gurin ta ai,
Wani kallo Umma ta watso mai mai nuna owo kana goyon bayan matar ka ko,?
Cikin daga harshe Umma tace duk sana,an da take a gidan nan za,a ce wai bata da kudi a gurin ta,
Hamza ya kara cewa bata dashi ne Umma ni na san da hakan,
Daidai nan mama tafitowa daga dakinta taji wanan hayaniyan takaraso zuwa gurin,
Hamza yace Umma wallahi duk kudin danai ta amfani dasu a,sibitii gurin Humaira na karbe su,
Sai duk suka watso mai idanuwan su yace, wallahi mama a,gurin ta nai ta karba don su sauran yan uwana, sun ce min bazan samu ko sisi a gurin su, ba
Duk wanda ma na tambaya bana jin mai dadi a,gurin shi,
Shiru Umma din tayi don jin dan nata ya rantse cewa a,gurina ya karbi kudaden da ya kashe asibiti,
Juyawa tayi sai mama tace duk kudaden da akasamu a asibiti fa yaya ?
Bazaki bayar a rufa asiri dashi ba may ye amfanin samu a gida,
Daki, tashiga ta dauko dari biyar ta miko mashi a wullakance,
Yakarba yana godiya, yace zai je ya samo dan abinda za,a karya dashi,
Bai fita ba daki ya shigo ya zauna da dari biyar din a hannun shi yana dan juyawa a hankali,
Nafahinci cewa bazasu ishe shiba shiyasa ya rasa yadda zaiyi da daribiyar din, na hannun shi,
Dubu dayan da ya rage min a dakin dama kayan zobo zan saya dasu nadauko na mika mai nace ga wanan sai ka kara ko,
Yadago idanuwan shi da,su kai ja ya sauke su a kaina yana cewa cikin wani sanyin murya,
Wanan kuma fa nace cinikin da nasamu ne jiya da wanda ke a,gurina dama kayan zobo naso saye dasu,
Idan kin bani ke damay zaki hada zobon naki dashi ?
Tunda ba,wasu kudi a hannun ki,
Nace Alkah zai rufa min asiri insha Allahu na samu nayi ko da kadan ne,
Ya karbi kudin daga hannuna badon ya so ba ya mike yana ce min bari nadan fita nagani Humaira,
Zuwa wani lokaci yadawo da leda ya auno yar shimkafa a ciki da cefane yakawo min yana cewa nayi na rana kafin anjima yagani ko za,a samu na yamma
Acikin dabaran mu na mata nai tuwon shikafa na hada da saurwn gari na daure sai yakai muna har da na yamma,
Haka rayuwan wanan damanan tazo muna sai na,dan kulla cinikin dan zobon da kakaran nonon da nakeyi mu sai wasu abubuwa don har shagon namu ya kare,
Kubura tazo gida yini taba da kudi a,sayo mata idomie ta dafa don wai bazata iya cin abincin da aka,dafa a gida ba,shinkafa da wake,
Anya kuwa za,a samu abu a shagwan Hamza din nan don duk kwanakin nan duk abinda aka aika sai suce babu shi ina ga sun lashe,
Tawani juywa tana kallon mama din tace wallahi mun ta aikawa hatta maggi cewa suke wai babu shi,
Tsiya takai tsiya ke nan tunda har shagon ya kare ai nasan karya ta kare ke nan,
Ita yar agwai din fa to mama ?
Wanan mai gadon zurfin cikin aibazata taba fadin komai ba ita,
Sai dai taita wahala a ciki takare haka na a wahalce,
Wai shine da Baba yaso turani cikin wanan wahalan boni yaci har na lalace,
Ai har yanzi shi bai san da haka ba don kwanaki yadan bada Omo akawo muna shine munafukar nan kecewa wai suna kina,aure gidan mai kudine amma yar Agwai tafiki sa,an daki da kwanciyan hankali,
Halan maman Aina ko ?
Ta tambaya cikin canza fuskanta tare kufulowa,
Ita mana dawa zaiyi wanan zance in ba itaba mai kwarmaton banza,
Wallahi mama sai nayi maganin wanan munufukar matan agidan nan don bazan kara bata fuska ba dani take zancen,
Tamike tare da yafa dan yalalon gyalen da ta yafo a kanta tana cewa ina zuwa,
Zaune nake ina raba abinci shimkafa da wake da mai da yaji nadafa sai kamshi man dana,soya yake tashi naji sallaman Kubura,
A zatona ta shigo gaida Umma ce taji labarin bata da lafiya nai mata iso a cikin washe bakin naga yar uwata,
Nace tazo su gaisa da Umma tana kwance daga kofan dakin ta,
Cikin wani yatsuna duk da ta ramay ta fada yangan nan da kaudi irin nata yana nan kamar baya,
Mun koma dakina da ita,na gabatar mata da abinci na aje mata zobo da ruwan sanyi,
Nai mamaki kwarai danaga ta sake jiki ta kwashi abincin dana saka mata din,
Tana shan zobo Hamza ya shigo cikin daga labule yana ganin ta ya dan daure yace a kubura kece a gidan namu tace eh,
Nashigo ne naga yar Agwai tunda ka hanata zuwa gurina,
Ban hanata ba idan tace zata ai zan barta ko na kaita,
So kada kiga laifina bani na hana taba,
Ta kurbe zobon ta mike tana cewa zata koma tana gida sai da yamma zaya tafi don yini ta,shigo nai mataalkawarin insha Allahi zan shigo gurin ta,
Tana shiga gida mama ke cewa ke ina kuma kika,shige tun dazun,
Tai gyatsa tace gidan su yar Agwai na shiga naci abinci,
Kai amma Kubura baki san kunya ba a rayuwan ki wallahi da hat zaki shiga kici abinci a gidan wanan kaskantatun mutanen,,,




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
.SARAUTAR MATA THE STORY JUST BEGINNING,,

Haka rayuwa tai muna tsauri da wanan damanan ta wanan shekarar, inda mace batakai zuciyan ta nesa ba kullun za,a ji ta da maigida don abin ya kai lahaula tako ina,
Duk sai ince da dan sa,na,a ta muke cima a gidan don Umma taja bakin aljihun ta ta tsuke wai bazata bayar ba,
Niko abinka mata da miji d zaran na gan shi a cikin damuwa yanzu zan jawo dan asusu na a fasa a debe kudin sai muyi amfani dashi,
Gashi Allah ya albarkaci sana,an tawa sosai don mutane suna son zobona da kunun ayya da yar kankarar nonon danake kulawa,
Hamza ya koma makaranta sai dai baiwani dade ba ya dawo don cire amfanin gonan daza ai mai,
Wani sabon aikine kuma yazo min don nice a tsaye gurin aikin saboda mama Hafsi bata nan tai tafiya duba yar ta da aka aiko bata da lafiya wai mijin ta yasa mata ciwon tari,
Ni kadaice atsaye kyam ke faman gyara kayan da duk aka,shigo dasu gidan,
Na ramay nai baki na koma wata irin bagidajiya dani,
Koda su Asmau suna gida basu iya tayani komai sai suce wai ai kayan mijina ne idan naga dama na tatala ko na barshi ya lalace,
Ranan sai akan kunnen Hamza wanda zai shigo ke nan yaji Asmau dake a saman turmi zaune tanw min zari,
Yarinya baki isa aure bakin nace ke zakiyi yanzu gashi kullun a cikin aiki kike ba hutu ba tausayawa duk kin kanjamay kin ramay kamar wata tsohuwa,
Nace cikin yar dariya Asmau kin taba jin mutum ya wuce kaddaranshi ce ni tawa kaddarance aure da wuri kuma ban raina da hakan saboda Allah yasan dalilin yin aure na,
But yashigo gidan kallo guda gaiwa Mau tashige dakin uwar su simi simi don kallon da yai mata kawai yasa ta sanin cewa duk yaji zancen ta,
Sai faman bakacen masara nake ina gyara tare da zubawa a buhu,
Sannu da zuwa nai mashi tare da mikewa don zuwa dauko mai ruwa yace barshi Humaira na hutar dake Allah yai maki albarka,
Wani irin dadi naji ya kumay man zuciyata tare da farin ciki,
Yace kiyi hakkuri munyi waya da mama tace min zata dawo zuwa gobe insha Allahu,
Kin ga sai ta taimaka maki don aikin nan yai yawa maki,
Murmushi nayi na daga fuskana da yai, futufutu da kurar masara nace mashi aiki indai na,samun ladan aure na ne, bazan taba gajiya ko kasawa da,shi ba insha Allahu,
Ya dan dauki lokaci tsaye yana kallon yadda nake aiki,
Sai kuma naji ya,furza iska sama yana cewa lalai dole na canzawa yaran nan
Yanzu nabar gona da bacin ran Jibri na,shigo gida kuma,na,samu na Asmau,
Nace hakkuri zakayi don su ai dole da kai suke takama, duk fadin duniyan nan,
Bakomai yace a fili dole zanyi maganin iskancin nan nasu in ba haka, ba bazasu gane may ake cikiba,
Ya shige daki yana ta mita leda biyu na ruwan sanyi ya zuka yafito don daukan abincin da na gama tun shabiyun rana zai kaiwa yan aiki a gona,
Nan kuma ya tsaya yana dan kama,min wasu yan gyare gyaren masaran dake watse a kasa,
Tausayi nake matukar bashi don yasan cewa lalai sai aure zai sani hakan duk da auren ma da ganin dama,
Don da Kubura ce daga shi har aik8n shi yasan cewa basu isheta kallo ba balle wani zancen gyaran kayan gona,
Umma ce ta leko daga dakin ta don zuwa zagayawa ban daki tagan shi tsugune yana tsintar masara a kasa tace,
Lah yanzu baba baka tafi kaiwa bayin Allah can dake daji abinci ba katsaya yin shiririta a nan har sai sun tagaiyara,
Ya mike zubur da sauri yana fadin Umma yanzu zan tafi naga masara a kasa ne nake tsuncewa,
Yamike tare da,wawuran fantekar da abinci yake a cikin sa ya nufi kofan gida, dashi,
Mama ta dawo kusan a tare muka kammala aikin da ita, don tana da kuzari sosai,
Ikon Allah dama tazowa mutane da haske don duk wanda yai shuka farkon damana ya samu amfanin gona fiye da tsan manin maikaratu,
Hamza yana daga cikin irin manoman nan da Allah ya albrkata da yawan amfanin gona a wanan shekaran,
Wanan dalilin yasa sunan Hamza ya daga sosai a gari aka fara zancen albarkan gonan da ya samu din,
Bai koma ba sai da ya tsaya fitar da zakka kamar yadda sheri,a ta kindaya a kai,
Bayan yayi yadda aka sharianta sai kuma yai ta,aikawa a cikin uguwa yana badawa sadaka don asa mashi albarka,
Duk gidajen da aka kai Umma batai magana ba,sai da za,a kai na gidan mu sai tace Sa,a datu ta tsaya a rage yawan shi,
Cikin dan bacin rai yana daga duke ya dago kai yana cewa haba Umma yawan may kuma a nan
Kusan fa tare da yar su muka kayi duk wahalan nan Umma sai naga aiko don Humaira za,a basu wanda yafi nan ma,
Cikin daure fuska tace haka naga daman basu ko kana da jane yace a ahankali a,a Umma a rage din,
Amma wanda ta,aikawa mama Sa,a aminiyarta yakai biyun na gidan mu kowa yana kallo ba,wanda yace uffan,
Har gida Baba Mudi yazo da kan shi yai masu godiya tare da fatan Allah yasa badi afi nan samu,
Shine mutum na farko da ya sallama yai godiya haka yasa mama,hafsi cewa kaga wanda ya san darajan alheri gashi ana kaiwa yazo godiya,
Umma dake zaune saman kujera yar tsuguno tace ba dole yazo ba kila dama shi ake jira a ci,
Innalillahi Umma wa ?
Malam Mudi din wallahi karya haramun don ko shekaran jiya buhun dangote naga an shiga mashi dasu,
Kai Umma ma dai mutanen da a dacen suke kawo muna abinci duk cikin uguwar nan nifa ban matawa da duk wanda yai min alheri,
Ibrahim wanda ya shigo da ledan breadi da kosai yana ci ke wanan maganan,
Mama Hafsi tace to itakan yaya ta manta don , har hana akai masu ma wanda babana yazuba akai tayi,
Ibrahim yace kai Umma amma wallahi k8na da saurin mantuwa, malam Mudi fa,
Tun baba na da rai naga ko tafiya zaiyi yakan ce idan wani abu ya faru a fada wa mudi kafin ya dawo,
Ibrahim, Ibrahim shin haihuwana kayi ko ,a,a wallahi kafita idona tun ban bata maka rai ba,
To amma Umma yaya za,a ce wai an rage na malam mudi,
Ga kawar ki da kika aika mata zan wuce ta gidan su naji tana cewa wai duk amfanin gonan da kuka samu sai dan wanan abin zaki aika mata dashi,
Wallahi kamar na,shiga na bata amsa sai nace ai kun fi kusa bari na barku ammq sai na fada maki idan tai musu zan fada mata da wacce naji ta hiran ita da yawale ki hira a soron gidan su,
Murmushi naga Hamza yayi yace wai kai baka,barin zancen hakana tunda angama,
Wallahi yayan mu matar nan Sa,a munafuka ce Umma dai ne bata gane halinta ba duk zancen gidan mu itace ke yadda shi a gari,
Nan Umma ta shiga fadan borin kunya dashi shidai yafita yabar gidan bayan ya shiga dakina ya dauko ledan pure water biyu ya kora,
A kofan gida Hamza ya samu dan uwan nashi suka kara tataunawa akan halin Umma din, yace su dai yi hakkuri da ita su samu su rabu lafiya saboda uwace mahaifiya ba abin wasa bace,

****** ********** ******
Duk suna zaune yake lissafo mata yadda zaiyi da hatsin da ya samu din, dakuma wanda zai fitar a gyara na cin gida saboda shi zai koma makaranta ranan lahadi mai zuwa,
Yace zanbawa Humaira wake, buhu daya sai shimkafa biyu,
Kafin ya karasa Umma tace a bisa wani dalili za,a bata,
Umma kada ki manta cewa nakarbi kudin ta tunfarko munyi lalurar asibiti dashi,
Sai kuma wanda nake karba muna,,,,,
Cewa tayi sai kabiyata ko may don ban fahince kaba yanzu don ka karbi abin matar ka kayi amfani dashi shine za,a ce sai kabiyata da wanan abubuwan haka,
To ban yarda ba kaji na fada maka banyarda ba ikon Allah tun ba,aje ko ina ba ina zaune yarinya karama zatai maka wayo ina kallo,
May nene abin wayau anan yaya duk abinda yabata ida tasaye da kudin ta daya karba aida yanzu kudin su ya wuce man,
Mama hafsi ke bata amsa da fadar haka
Nadai ce ban yarda ba kaji na fada maka lalai ashe akwai magana ke nan,
Yanzu yaya yaro na son sauke nauyin yarinyar nan dake kan shi amma har kike hanawa ,
Ina daga dakina duk zancen su ina ji duk da banji dadi a raina ba haka na hade bacin raina nafito don daukan kayan dana wanke nakai daga cikin daki,
Ganina bai hana Umma sake maganan da takeyi ba har lokacin da taga dama don kanta ta kyale ita daya,
Ya shigo daki ina zaune da hand out dina ina dan dubawa don ina da test, yake cewa,
Kada zancen Umma ya tayar maki da hankali Humaira zan san yadda na biyaki kudin ki,
Cikin nuna rashin jin dadina nake cewa haba yaya ai Umma tana da gaskiya don ka karbi kudina zaka ce sai ka biyani,
Humaira hakkin kine fa dole na baki abinki don ba kyauta kika bani ba nace ni abina nakane ai,
Shirin shi yayi tsab na komawa school don ya dan so ya makara ma saboda aikin da ya tsaya yi, na gona,
Haka rayuwana yake ci gaba a gidan banda wani freedom din kaina ko ruwan sanyi nasha a gaban Umma yanzu zatace masu abu ku kayin yadda ranku yaso,
Ko naji marmarin abu sai dai idan na fadawa mama a boye ta sayo tabani inci a gaban Umma shine samun lafiyana,
Don ban isa na dora dan tukunyan idomie ko taliya ba ince zance ranan kila da sai na kwana gidan mu don fitina,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login