Showing 120001 words to 123000 words out of 299981 words

Chapter 41 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17632

shi idan amarya ta shigo kada ki dauki raini run farko daga gurin kishiya,
Duk abinda akafara kin san yana da wuyan bari da sauri,
Amma idan an shigo gidan ki an samay ki akan kan bun sarautar ki komai naki a daidai yake tafiya kishiya ko da may tazo dole ta barki,
A lokscin zaki kara gyara mu,amular ki da maigida dama yan uwan shi,
Don zasu shigewa amarya suna ganin cewa ai sabuwace tana saman amarci komai dan uwan su zai iya masu a dalilin ta,
Gyara yaranki, gidan ki dake kanki hakan zai kara daga martaban ki uwar gida,
Sai kuma kikara kokarin ganin kingyara tallennki, girki ke nan don kar a barki a baya,
Idan har zamu rike hakan duk abinda wata zata shigo dashi dole ta barki ke ma,
Idanuwa na a,duke suke ina dan juya cibin dake hannuna acikin shikafa ni banci ba ban kuma,bar wasa da cibin ba,
Na dago kai sai ga,hawaye duk ya ciko min a fuska wanda na kasa controlling din su
Kinga ita Umma yanzu abin zai mata dadi ne idan taji ko taga kin tayar da hankali ga dan ta,
Don haka duk abinda zaiyi Aisha don Allah ki daure ke dai ki dage wurin kaiwa Allah kukannki,
Kuma ki fadawa mahaifiyar ki itama,ta tayaki addu,a don adduan iyayye a gare mu taki ne,
Kiyi hakkuri kiji Aisha gaskiya abinda zafi sosai amma idan kinyi tunane sai kiga mungaji ganin haka,ga iyayyen mu,
Don haka,share hawaten ki, tankar ba abinda ya faru ki koma normal, don kinga man ya shedi hamza cewa bai neman mata kuma bai zina,
Ai na namijin dake zina yafi tayar da hankali tunda bakasan da,wace irin mace yake taraiya ba,
Mai lafiyace ko mara lafiya musulmata ko kafira ce,
Nadago da,sauri nace Anty bana fada maki labarin matan da sukazo gidan mu kwanaki gurin shi,
Tace cikin girgiza kai baki fada,min ba Aisha,
Nan na,bata labarin zuwan su Lima gidan mu da abinda sukacewa Umma ya kawo su,
Babban magana ashe makin san da zancen ko har nake maki boye boye da,farko,
Gaskiya Aisha sai kin jajirce kin hana idanuwan ki barci gurin neman mafita akan zancen nan,
Don jiya Man yana bani labari yace, Hamza ya canza a cikin dan lokaci guda kuma matar ba yarinya bace tsohuwa ce sosai,
Innalillahi Anty na,shiga uku, nace cikin dan kuka haba dakata baki shiga uku ba kinji,
Allah baibari ki wulakanta Aisha don shi da bakin shi Hamza yazo nan yana,fada muna irin halarcin da kukai mai keda iyayyen ki,
Don haka tunda tun yanzu harkin samu sheda a,gur8n shi duk abinda kika,sani wanda kikeyi na kyautata mashi kira saman wanda kike yi ki nuna ta kar baki fahinci may yake ciki ba,
Sai inshi yafito maki da zance saiki ce Allah yasa alheri ne hakan ya,raba ku daga haka kada ki kara tayar da zance kuma,
Nan taita kawo min musalai masu yawa har na gamsu ban iya cin abincin ba,daurewa nayi namike nace zan tafi,
Har kofan gida ta biyo ni tana kara ja min kune akan na,daure na danne fushi na kar na,bari a fahimci halin da nake ciki,
Mukai sallama na hau mashin zuwa gida na makara amma,ban samu Umma a gida ba sai mama don har ta kusa kare girki a ranan ,
Nai mata sannu da gida tace na,dauki abincina na shiga dashi ban mussaba na dauka zuwa dakina duk da nasan ba ci zan yi ba ma,
Da magariba naba almajiri sadaka lokacin babu kowa a wajen gidan,

****** ********** ******
Sosai Hamza kan ya kamu da soyayyan lima da,tarkon da take dana mai
Abinci lafiyaye zata dafo mai yanzu baida matsalan abinci ko kadan,
Ga,drinks kala kala tana kawo mai ga kudin kashi akai akai tana bashi, don ya yiyadda ran shi ke so dasu,
Duk inda zaka gansu a tare suke kamar tip da taya, tun mutane basu fahinta har takai yanzu kowa yasan may ye a tsakanin su,
Sam Hamza baijin kunya ko nauyin abinda,jama,a suke cewa akan su shi dai ya haukace akan son Lima,
Da,farko taso gwada sa,anta akan ya yarde mata sukoma yan addinin ta,
Ranan ta gane bata da wayo a rayuwan ta don yai mata cin mutuncin da bata taba tunanen shi ba a,gare ta,
Sai da ta dawo tana lalashin shi tare da turo mashi kawayen ta yan duniya suna bashi hakkuri,
Sai cika yake yana batsewa yace ai ya zaci kaunar gaskiya take mai da ya yarda da ita ,ashe ita da wani manufa tazo mashi,
Sai da kyat ta samu ya,sauka akan daga ranan bazata kara yi mai zance a kan addinin shi ba,
Wanan abin ya tayar da hankalin Lima sosai don a gaskiya ita bata jin zata iya musulunta a,rayuwan ta, da tuni ta musuluntar amma ga dan karamin yaro yazo yana son garata saboda Allah ya jarabeta da matukar kaunan Hamza din,
Haka tai hakkuri takara kokarin ganin ta kara kaimi wajen kara kamashi da,asirai da kuma abin hannun ta,
Sun fara zancen aure wasa wasa dashi, har abin ya fara tasiri a zuciyar hamza inda yake ganin cewa yanzu a shirye yake zai iya auren Lima din don ba wanda ya isa ya hana shi auren ta din,
Sai sake sake yake a zuciyan shi na yadda abubuwa zasu kasance masu,
Yaya ma za,ayi ya zauna da Lima a cikin gidan su haka, gata ga su Umma, da yan uwan shi,
Sam a rayuwan shi ya manta da zancen wai wata Aisha,
Yakan dan tuna ta idan asiri yadan fita a kan shi kadan sai kuma yani kai Aishan may ga babban mace ya samu inda zai morewa komai, na rayuwan shi ya huta,
Yagama yanke shawaran abinda zaiyi don haka bai tsaya shakka ko shamakin komai ba ya shirya zuwa gida,

****** ********** ******
Na idar da sallah bayan na dawo daga school na zauna a gurin yayin da nadan dage labulen kofan dakina saboda iska ya dan shigo min don ba,wutan an dauke NEPER ,
Sallama shi mukaji daga sama don ba wanda yai tsanmanin zuwan shi a wanan lokacin
Murna sosai naji yan gidan suna yi suna mashi sannu da zuwa, gurin su Umma ya nufa inda suke a zaune, ya zauna,
Namike a hankalo baki daukr da addu,a kamar yadda Ummi ta koya min ,
Kalman shahada na fito dakin dashi inda Allah ya ban sa,a mukai ido biyu dashi a lokacin da nake karatawa,
Wani irin yaji a ranshi lokacin da ya ganni, nauyi kunya duk sun tsirga mai a lokaci guda,
Nakaraso ina,saye da hijjab din dana kare sallah dashi,
Nace Yaya sannu da zuwa ya amsa cikin dan kara dago kai yana kallona da cewa, yauwa sannu Humaira mun samay ku lafiya,
Alhamdullahi nace inda na juya zuwa daki don na dauko mai ruwan sha saboda naga shi tare da iyayyen shi,
Na tafi ina tunane sam jikin shi ba,alamar wani, wahalan karatu yadda muke zato yayi kiban shi ya haska gwanin ban sha,awa dashi,
Nadora ruwa guda biyu tare da goran zobo mai sanyi sama,
Har kasa na,durkusa a gaban shi inda yake a zaune yayin da kamshi jikina da ya dade baiji ba ya daki hancin shi,
Yadan lumshe idanuwan shi don tuna abubuwa da,dama a hakan,
Yasha ruwan sosai tare da,zobon suna hira yana shan a hankali,
Umma ce tace yaya akayi ka dade haka baba bayan ba haka kake muna,ba da farko,
Gaskiya rashin ziyarar da bakayi muna kaman baya ya saka,mu a cikin damuwa,
Yace Umma ai in kaji shiru lafiya ne karatune ya rike ni tare da,wasu yan abubuwan da su ke agabana,,
Daki na koma inda na,dan kara kimtsawa kamar yadda mace zata tari maigidan da yai tafiya ya kwana biyu,
Ya dauki lokaci a,gurin su Umma da mama suna dan hiran yaushe rabo a tsakanin su,
Can ya mike yana cewa,bari yadan watsa ruwa, ko zai danji dadi a jikin shi,
Wani balai, sam Lima taki bari yazo da kayan jikin shi koda kwara,dayane ita hikimar ta nayin haka shine kada yazo ya ce zai kwana, biyu tare da ni,
Ya,shigo dakin da,sallama a lokacin ina kokarin fitowa don na dauko mar abincin shi,
Na,dan kauce mai a hanya yashige a zuwa cikin dakin mu,
Sannun na kara mai tare da nuna ba komai a raina akan shi,
Sai naji ya jawoni zuwa jikin shi ya wani kankamay ni kamar wace za,a kwace mai yana wani sauke numfashi,
Sai kuma naga ya,wani sakeni da sauri kamar andaka mai tsawa ko umurnin ya sake ni,
Bakin gado ya zauna ya sauke wani irin numfashi tare da,dan dafe kan shi kamar mai jin ciwon kan,
A,uzu,bikallamatil,lahi tammah,,
Shi na fadi a zuciya na nabar dakin gaba na,sai faduwa yake nasan da magana ke nan,
Ya kai wani lokaci kwance rairai kan shi dafe da dayan hannun shi,
Murya na kamar kullun, nake cewa yaya ka tashi lokaci sallah ya kusa yai firgigit ya tashi sai naji banji yai salati irin yadda ya,saba yi ba idan ya farka da barci,
Har yamma ta karasa hakane nace eh ga ruwan alwala can a waje, a aje ma,
Yana fita na jawo ruwa a leda na tsiyaya ruwan jug din da zan sa a tire din abincin shi,,
Nadurkusa gurin sai da na karanta bissimilahi, kafa dari da sha uku a cikin ruwan,
Na mayar da marfin na rufe na girke ruwan a ture naci gaba da aiyukana,
Duk da tare suka ci abinci da Ibrahim ban yi wa i fargaban shan ruwan da yayi badon dama addu,a ce ta kara asiri kawai, hakan,
Daga inda suka ci abinci naji guri yai tsit hakan ya nuna min alamar akwai wani magana mai muhin manci da sukeyi,
Sai ko naji murya Umma tana cewa in banda shirmay irin naka don zaka yi jarabawar karshe, shine zaka zo kace zaka kwashe muna abinci mu may zamuci,, badi idan rai ya kai da may zaka noma wani,
Gaskiya haka bazaiyuyu ba don bazaka bar mu da yunwa ba ka,arcewar ka,
Mama wanan abin fa nawa ne ni ke,da abina ba ina nema shawara ko yadda bane,
Haka nake son yi da abina idanuwan shi kawai zaka kalla kasan cewa gaba daya Hamza ya can za, kamar wani zarare,
Babana kan ka daya kuwa, yau Mama may kika gani kike cewa hakan kaina daya mana nazo daukan abinane ya zama kudi,
Kawai sai naji Umma ta saka kuka tamike ta shiga daki ikon Allah inji Hamza yanzu saboda Allah mama maye abin kuka a nan,
Abinane kuma bukata ta taso ina son inyi amfani dashi don na biya wa kaina bukata,,
Allah buwayi gagara,mussali mama tace a,fili,
Ta gyara zama suna kallon juna da Hamza din tace, amma kamar da alaman wani abu mai muhinmanci zakayi da kudin nan ko,?
Shiru yayi yasada kan shi a kasa don kukan da Umma ta shiga dashi dako yasa jikin shi yin la,asar,
Ina daga dakina hankalina yai matukar tashi don dai iya sani na da,Hamza tun ina karama ina shigowa gidan ban taba ganin suna sa insa da ,Umma ba sai yau,
Mama ta rarasheshi cewa ya bar zancen har da safe sai asan abin yi akai tunda yanzu Umma tayi fushi da yawa haka,
Bai fita kofan gida gurin abokan shi ba yadda ya saba sai ya,dawo daki ya zauna a bakin gado yai tagumi da hannu bibiyu,
Ban ce mai komai ba ina ,zaune ina gyara ayyan da zanyi kunun zaki dàshi,
Ina jin muryan, Umma a dakin ta tana kuka tana magana har dakin mu kana jin muryan ta,
Sai da na gama aikina tsab na kwashe kayan zuwa inda nake boyewa nagyara gurin da nai aikin tsab, nafita nadan wanke hannayena da kawar da sauran kayan waje,
Wanan karon da na shigo na samay a tsaye ya jingina,jikin shi a,bangon dakin mu,
Kafan daya shi na tokare, ta baya a,bangon dakin namu sai hannun shi da ya dan riko habar shi da shi, sai da na shirya tsab na cire hijjab din dake kaina,
Matsawa nayi jikin shi a hankali, na jingina kaina a saman kirjin shi,
Ajiyan zuciya naji ya sauke mai sanyi, hannaye na,nasa na zagayo tabayan kunkumin shi dasu,
Ya dago idanun shi da,suka canza kala ya kalle ni dasu cikin murya mai kaushi yake ce min Humaira ina cikin matsala a rayuwata,
Na kara dan matse shi a jikina na dan ce hummm, Yaya Hamza,nace cikin natsuwa,
Yaya dakai da,Umma duk zancen ku a kwai gaskiya a cikin sa,
Nafarko kai kana da bukata da abinka na biyu kuma ita Umma tana hangen abinda kaje ya dawo a gidan nan, ne
Kasan cewa kaine mafi darajan mutum a idon Umma da yan uwanka yau zaka zo masu da zancen sayar da abincin dake gare ku a gida,
Kasan dole Umma taji wani iri a,rayuwan ta saboda kune abin alfaharin ta duniya da lahira,
Kasameta ku shirya a cikin kwanciyan hankali yadda zata fahince ka sai ku sasanta da ita yafi wanan kai ruwa ranan da kukeyi a tsakanin ku,
Zubo idanuwan shi yayi a kan fuskana kamar yana son gano wani abu tsawon dan wani lokaci sai naji ya nisa,
Gyara tsayuwar shi yayi yadan rugumoni jikin shi, cikin murya mai sanyi ya soma magana
Humaira nasan zaki fahince ni akan irin rayuwan da na tsunci kaina a cikin sa,
Da sauri na dago kaina na dan kalle shi ido da ido sai kuma na dukar da kan nawa,
Na dan kara shigewa jikin shi a hankali ina cewa idan har aka bi al,amarin a sannu zaku iya fahintar juna da Umma don zancen ai itama ya shafe ta, koma may ye tunda zancen tane,
Sai nake ganin zaka iya samun ta ku shirya a cikin sauki tare da fahintar junan ku don wanan abin baikai na har ka bari Umma tana zubar ma da hawayen akan abinda kake son ganin haske a cikin sa,ba,
Da sauri naji ya matse ni gam ajikin shi yana wani irin sauke ajiyan zuciya da kyat ya iya bude bakin shi ya na fadin Humaira nagode nagode da irin fahintar halin da nake aciki da kikai min batare da kin kara min pressure ba ke ma,
Nan ya jani muka zauna a bakin gado yafara min magana kamar haka,
Hummaira ba sai na rantse maki ba ko insa ki yarda dani dole, ba
Nidai wallahi ban dan yadda ake zinaba kuma ban taba anyana yinsa a rayuwa na ba,
Da sauri nace mai subbahanallahi wanda nai zaton a cikin raina na fada ashe nafada har a fili,
A raina nace lalai an samu matsala maigirma a cikin wanan al,amari amma ban yarda na nuna mai damuwa na,a,fili ba sai daurewa nayi nace Allah yai muna abinda yafi zama alheri a rayuwan mu,
Ya amsa min da amin Humaira na gode ya mike tsaye naga ya fara cire bottom din rigar shi a hankali,
Mai makon inga abinda nai tsanmani kwanciya yayi ya juya min baya fuskan shi a,sama yana tunane,
Ban nuna damuwa na ba ko kadan sai karasa aiyuka,na da nayi ,
Nadawo daga gefen shi cikin kumci na kwanta tankar ba wani abindake damuna, dashi,

Kamar yadda na bashi shawara hakan yayi washegari da safe ya shiga gurin Umma ya bata, hakkuri tare da dan mata bayani akan zancen auren da yake son yi,
Umma ta kira mama take sheda mata zancen da danta yazo dashi,
Cikin taushin murya mama tace Dan nan matarka tai maka wani abune da zaka kara aure yanzu yace babu komai a tsakani da Humaira mama,
Auren dai ne yin sa yazo min a yanzu ai ba wani abin damuwa bane don ba,a nan zan zauna da ita ba,
Zata zauna a Birnin kebbi ne ko sokoto ita ita kuma Humaira tana nan tare da ku,
Umma dake cikin nazari tace sam batayarda da wanan tsarin ba inda har wace zaka aura bazata zo nan inda muke ba ta zauna to sai dai a fasa zancen,
Mama take ce mai to matar ka tasan da zancen karin auren naka?
Mama Humaira ba matsala bace yanzu yardan ku kawai shine fatana,
Sallama akai mashi yafita kafin su kai ga matsaya da su Umma nan zancen ya tsaya har wani lokaci,
Umma ta yafa tafita zuwa, gidan mama Sa,a don ta fada mata zancen da ake ciki a lokacin,,
Fitan Umma naga mama Hafsi tana min wani kallo a cikin tausayawa,
Naga can tafita daga kofan gida ta dan leka sai kuma ta dawo inda nake duke a bakin randan ruwa tace Aisha na, dago daga abinda nakeyi ina cewa na,am mama,
Aisha ina sonki bazan iya ganin abinda zai cuta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login