Showing 135001 words to 138000 words out of 299981 words

Chapter 46 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17641

nuna ta da yatsa tana cewa wallahi a,hir dinki da kiran dan uwana mijinki don Allah ya raba mu da hadawa da mace shu,uma irin ki a rayuwar mu,
Ke ki iya bakin ki don ban da time din irin ku saboda ba gurin ki muka zo ba,
Wanan zance shiya kara tunzura Umma wace dama take a kule da su, take cewa wallahi ahir dinku da zuria ta don ban haifi dana donku ba wai ku wasu irin mayun mata, ne haka wai da bakin nacin tsiya
Murmushi sukayi a tare tare da wani yin har da idanuwan su sai ita Lima ce tace mama kiyi hakkuri son dan ki nakeyi tsakani da Allah
Ke rufa muna baki kinji macuciya wazaki yaudara haka ake so ko bala,i inji mama hafsi, Umma tace,
Yadda Allah ya kwato min dana,daga,sherin ki da makircinki Allah bai kara baki sa,a a kan sa,insha Allahu,
Kiyi hakkuri mama ni mai son dankine ba,wai sheri ba, zakiji dadin zaman mu dashi nan gaba,
Abinda su umma basu lura dashi ba shine cewa, Lima daga gurin da take tsaye tana wani saddabaru ne,
Nice nafara hango yadda take saka hannu a hand bag take yarfa abu a tsakar gidan mu daidai saman hanya da,zai shiga da mutum gurin da dakunan mu, suke a jere,
Ashe mama ta gani daga inda take tsaye zata kara na uku mama hafsi ta nuna ta da hannu tana fadin dakata hakana don idan kika kara wallahi sai kin gane kurenki a gidan nan,
Tsintsiya da Parker na dauko batare da nai magana,ba baki ina karanta lai,la ha, illah anta subbahanika in,ni kuntu minal zalimin,
Nafara tatara daidai gurin da ta yarfa ruwan magani a gaban mu nai hanyar toilet dashi, suna kallo na,
Ibrahim suka,shigo shida abokan shi akai masu tas don kiris ya rage a bugesu a gidan,
Sai cewa suke wallahi tunda mijinta ne dole a bari su gan shi saboda itama ai tana da hakki a kan sa,
Fitina yai fita ancika sunga rashin mutunci a filin Allah haka ya,saka su barin gidan takalmi a hannu don sunga ruwan bala,i saboda matasan shiya sunce sai sun kashe su sai dai su ma a kashe su tunda sun zo har cikin gida yiwa mutane rainin wayyo,
Rikici yafi wani rikicin cikin tashin hankali suka bar uguwan don ganin dandazon jama,a yadda suke karuwa a kan su,
Suna barin uguwar Bicky tace wayyo Allah na yau mun ketare rijiya ta baya aida mun fada a jikin mu,,
Don wallahi wa yan nan katai indan sun dake mu sun daki banza wallahi,
Dayar Mary tace nikan ba zan sake zuwa irin wanan risky din life dina ba,saboda wanan village people, sun fimu hauka,
Ke da kikaga kina iyawa zaki iya zuwa for your own, risk ba dai dani ba again, gaskiya,,
Sai lokacin Lima tace, hmmm ni duk ba wanan ba wai kun kula da yadda wanan yar ficikan yariyar tawani canza gaba daya kamar bata a cikin wani case haka,,
Kina nufin matar Hamza din tace eh ita mana Mary tace wace daga ciki ?
Wanan da tazo ta kwashi abu a gaban mu da Parker mana abinda na zuba ne fa wai wanan yarinyar tagani take kwashewa a gabana,
Ki duba irin kudin dana kashe kafin na,samu a hada min wanan magani amma duk da haka nasan cewa, dole za,a samu wani da zaiyi amfani a gurin,
Muddin Hamza ya bi gurin dole maganin nan yayi aiki a kan shi,
Kawai ni bukatana shine yabi gurin kawai koda sau daya ne,
Amma ashe matar yarinyace haka karama gata kuma tana da kyau wallahi sosai,
Duk lokacin da naga wanan yarinyar nakan ji matukar bala,in kishin ta ya kama min zuciyana sosai,
Duk yadda zan raba shi da wanan yarinyar zanyi na shiga tsakanin su muje zuwa suna wasa dani wallahi,,
Shiru sauran sukayi don su abin yafara basu haushi sosai don dai sun san suna samun biyan bukatan su ga,alhazawa masu kudi balle wanan yaro karami
Da baida ko sisi inba jikin shi da take moraba basuga abinda take mora a gare shi ba,
Suna fita mama Hafsi tace a zuba fitsari da ruwan tsami yadda asiri zai kare, a duk gurin da,suka bi suka zuba maganin,,
Ina tsaye imani da tsoron duniya duk ya kamani yau naga mai abu ja mara abu ja a filin Allah yadda mace tazo ba kunya tana duban idon mutane tana cewa wanda ba,a,san yadda suka daura aure ba wai mijin ta mijin auren ta,
To ni ma,wai yanzu a wani matsayi nake da auren shi da ke a kaina, ne don banga alamar wanan matar zata bar min mijina ba don babu kunya babu tsoron Allah a tare da ita, ko kadan,
Ina gurin banyi aune ba sai ji nayi kamar numfashina zai tsaya min don irin bacin ran da nake ji, atare dani,
Da kyat na,samu na nemo natsuwana ina fadin innalillahi, wa,inna alaihim rajji,un,
Sannan na dan samu natsuwa a tare dani, duk kace nacen da mutane keyi ban iya cewa uffan ba don mamaki,
Gaba daya ji na nake kamar ta kwace min miji ko, don may zan gane wa mutumin da ke mu,amula da mace irin wanan matar,
Mace ga jiki ga haske ga sutura na alfarma, ga kayan karau ko yaushe da take dazawa,a jikin ta,
Nasan kowaye hamza gwarzon namiji a cikin mazaje yabiyo tarihin mai sunan gurin karfi da hazakan nema,
Nasan bako wace mace ce zata mallakeshi ta bari ya shige mata kai tsaye ba, batare, da wani jayyaya ba,,
Haka naja kafana da kyat zuwa dakina inda na,fada saman gadona na fara wani sabon kukan gwanin ban tausayi dani,
Ganin ba sarki sai Allah ni daya a cikin daki sai na,fara jero tasbihi inayi tare da neman sauki a gurin Allah ubangiji subbahanahu wata Allah,,
Don wanan masifa yai muni saboda yadda suka shigo muna a cikin fitsara babu burbushin kunya a idanuwan su ko kadan,
Wai mijina take kira mijinta a gaban bainan jama,a ina ji ina gani don rainin wayyon da take min, ta daukeni ni da banza duk daya,
Haka nake kwance ni kaidai a daki sai juyi danake a saman gado ga tunanen kala, kala da ya addabi zuciya ta,
Don sai nake kiyasta irin rayuwan sha, shanci da tambadewan da su kayi tare dashi a idanuwana,
Na kara rintse idanuwana raina yana ci gaba da baci don zafin kishin da nake ji ban taba sanin cewa na iya kishi ba sai a wanan ranan da naiwa Lima kallon tsab,
Take idanuwana suka kade sukai jawur dasu tankar anyi min duka nake jin yanayin jikina a lokaci guda,
Sai ji nake rayuwan gaba daya baida dadi kwata kwata ya fita raina kamar babu wani sauran dadin da ya rage min a duniyar nan kuma,
Allah mai rahama maijin kan bayinsa nan cikin wanan halin barci mai nauyi ya,daukeni duk da mafarkine barkatai marasa dadi nake amma na jima ina wanan barcin,
Ban farkaba sai gab da la,asar na samu tashi jikina kamar anmin duka,
Tabbas naji dadin wanan barcin don dana farka duk wani kunci da nakeji yafita min a raina,
Nafito na debi ruwa na watsa don na kara jin dadin jikin nawa,
Na samu zarah tai girki don ganin ban cikin dadin rai a ranan,
Haka na tutura abinci ba wai don jin cin sa ba ban ci wani mai yawa ba na barshi ,

****** ********* ******
Da dare ana zaune bayan duk liman yaji bayanin da su Umma suke mai ya kada kai tare da nisawa
Yace lalai wanan matar takai fitsarara don rashin mutunci zata shigo har cikin gidan nan tanawa mutane wanan irin fitsara haka,
Dayan mutumin yace ku barmu da ita kwata kwata zata ji ko zancen shi bata kaunan ta ji a,rayuwan ta,
Indan ita tsafine nata mu muna karya tsafine da ayar Allah maigirma, a lokaci guda,
Mutumin ne yace ni yanzu shawaran da zan bayar shine a yi kokari a auna shi don tabbatar da lafiyan jikin shi, saboda gudun jefa matar shi a cikin halaka ita ma,
Umma hankalin ta yai matukar tashi don jin abinda ake zargin hamza dan ta dashi,
Sai kawai ta fasa kuka tana cewa Allah ya isar mata ga wanan bakar mace mai muguwar hali da ta jefa mata da a cikin bala,i,
Gaskiya idan haka ya kasance sai dai su zauna kotu da Lima don bazata yarda ba ta kashe mata da haka kawai,
Hakalin Umma da yai balain tashi tunda safe washe gari sai gata a gidan liman ita da mama,
Bayan sun gaisa da mutanen gidan ne sukaiwa malam bayanin suna son ganawa da Hamza din,
Malam ya nuna masu masaukin inda Hamza yake zaune,,
Sunsamay shi zaune yana karatun kur,ani inda ya yakai aya ya tsaya su gaisa da su,
Umma kan tana ganin yadda danta ya koma alokaci guda kamar ba hamzan ta ba,
Sai duk ta rude ta,shiga damuwa da kyat mama ta,samu ta,shiga natsuwa,
Magana suke dashi kamar baison yin maganan don da kyat yaje bude baki ya basu amsa,
Don shi kadai yasan irin halin da yake jin kansa aciki
Yajuya inda mama take yana tambayan ta lafiyan matar shi Aisha da sauran yan uwan shi,
Umma tace mai kaji zancen gwajin da ake son ai makako don gudun jefa ita Aisha acikin wani hali,
Wani irin ba dadi yaji a ranshi take ranshi tmya baci yanajin kowa na mashi kallon mazinaci ke nan a rayuwa,
Cikin dakiya yake, cewa indon wanan ne ba matsala Umma Allah zaikare ni daga duk wani sherin wanan matan,
Sai dai sun boye mai zancen zuwan su Lima din don kada hankalin shi ya kara tashi,
Yai shiru yana jinjina maganan a ranshi wai yau shine za,ai wa gwajin HIV don zargin zina ,
Ganin ya shiga damuwa ne yasa mama cewa kada kasa damuwa zamu taya ka,rokon Allah insha Allahu hakan bazai faru da kai, ba,,,
Sun dan dauki lokaci a tare da su suna dan hira sake wanan kama wancan har sai da suka ga hankalin shi yadan kwanta,
Sukai mai sallama tare da mashi alkawari kara,dawowa su ziyarce shi don suga lafiyan shi, zakuma,suci gaba,da taya shi addua insha Allahu,
Bayan tafiyan su saiya koma wani iri damuwa da shakku suka saka shi a gaba suna addaban shi,
Damuwar shi shine yadda mutane zasu fahince shi a,zarge shi akan abinda bai taba tunanen aikata su ba a rayuwan shi,
Tausayin Aisha Humairan shi ce ya kama shi don a gaskiya idan har yakamu da,wani mugun ciwo bazai iya yafe wa kan shi ba don yasan da ya cuta wa wanan yarinyar, mai,
Mutunci karamci kamala sanin ya kamata,da,sauran su uwa uba ga hakkuri,
Bai san lokacin da hawaye ya fara digo mashi daga idanuwan shi,
Yana kokarin sharewa ne sai ga bakon nan da yazo dashi ya shigo dakin idanuwan shi akan Hamza yake tambayan shi ko may yafaru yaga yana kuka,
Guri ya,samu ya zauna yana daga gefe shi yana fuskantan
Hamza bai boye mai komai ba akan irin zanman da mukeyi tsakanin mu yai ma banin komai,
Malam.ya ke cewa sai ka mayar da hankali sosai ga ibadan ka ka kuma daina kwanciya da najasa a jikin ka,
Ka dinga addua kafin kafita gida ko ka kwanta, da gurin cin abinci komai kankantan shi ka karata bissimillah kafin ka,saka a bakin ka,
Hamza yana saurare inda yasan cewa duk wanan abubuwan yana da matukar sakaci a kan su
Amma yanzu insha Allahu zai yi kokari ya gyara wannan kurakuren da ya tafka a baya inda a nan ne shedan da shedanu suke samun shiga jikin bawa da sauri

Don Allah kuyi hakkuri da,rashin jina kwana biyu da bakuyi ba, nagode,


ZAINAB IDRIS MAKAWA,
SEENABU
IDAN BAKI BIYA,BA KADA KI KARANTA HAKKIN WANI PLEASE,,,,

Kiran sallah da ake a ko ina cikin uguwa ne ya tayar dashi sallah kamar yadda ya saba,a baya kiran farko zai farka ya fara, alwala da nafiloli,
Zubur ya mike zaune yana wa kansa tambayoyin yadda akayi ya gan shi a nan haka ya waiga da kyau Lima tana kwace shirif da ita kusan duk rabin jikin ta yana waje,
Tambayoyi ya fara jerowa kan shi kafin kiran sallah ya kara tunatar dashi,
Zubur ya mike daga kan gadon da sauri sai yake jin shi daga shi sai boxer a jikin shi,
Duban ya ayin shi yayi sai yaji wani irin kunya da nauyi sun gama shi,
Ji yake tankar duk duniya suna kallin abinda ya aikata, a lokacin,
Ruwan da ke a gidan sai yake jin kyamar amfani dasu gurin tsabtace jikin shi,
Ruwan ledan pure water da su ke a jingine da yawa gefe daya su ya diba yashiga bayi da su,
Wanka yake amma ziciyar shi fam da tunane kala kala a cikin ta,
Yafito inda yaga yar bag din shi ya nufa ya dauki wasu kaya nashi daya gani a goge, ya dauko ya,saka ajikin shi don su yake gani suna da tsarki,
Har ya bude gida ya fita zuwa inda yake jin ana kiran sallah bata farka ba sai nasari take kwa kwa kwa, duk ta ruda guri da,sautin nasarin,
Daga masallaci ya dade zaune yana azzakar har rana ya hudo sosai, ya mike duk zuciyar shi har lokacin a cakushe yake fam,
Direct inda zai samu Nape da zata sada shi da inda su Mansur yake ya,shiga watau hostel din su ke nan da suke zama a ciki ko ince inda mansur ne ya kama gurin gida ne babba sai suka dan hada kudi suka biya sai dai share din mansur din yafi yawa a ciki,gidan,

****** ********** ******
Cikin barci taje ta dan rungumo shi amma,sai taji kamar wayau, takara labawa tare da wani mika sai taga baya sama gadon,
Bude idanuwan ta tayi cikin sauri sai yaum ta gani a gurin baya kwance a kusa da ita,
A zaton ta yana cikin bathroom, don haka takara lumshe idanuwan ta, don a zaton ta yana acikin bayi,
Shiru ba shi har takai ga fara, kiran sunan shi tana cewa my my har yanzu kana ciki ne ,
Jin shiru yasa ta saurin mikewa zaune tayi ta bi dakin da idanuwan ta a hankali sai ta hango wandon boxes din shi daya cire yashe daga kofan fita, bayi,
Da sauri ta kai tsaye tana cewa ina kuma ka,shigane wai haka,
Bayi ta leka duk da gurin da yai wankan ya,sha iska amma alaman ya nuna yai wanka,
Da sauri ta leka falon su baya ciki nan ma kofa a,bude yake ya dai dan saya mata shi,
Har wajen gidan ta leka bai gurin sai mutanen shiya dake zirga zirga jefi jefi, a layin,
Ta juya zuwa, cikin again nan ta lura cewa, ya yamotse jakar kayan shi dake dakin a jiye,
Juses, tace da karfi tare da cewa yau na,shiga uku ina guy din nan ya shiga haka tun da safen nan,
Mutumin da bamu tashi barci sai after nine muke tashi amma yau gashi ya tashi as early as possible haka, nan,
Takai zaune a saman gado tana dan tunane a hankali can kamar wace a ka tsikara ta mike tsaye da sauri ta nufi wardrobe din ta,
Cikin sauri take daga kayan dake a ciki tana binciken wani abu sai dai da gani wani abune mai muhin manci take ne ma acikin wardrobe din nata,
Wani leda ta jawo mai kauri baki tana kokarin sance ledan a cikin rawan jiki,
Wani kashine, lailaiye da jan kyalle acikin ledan an nade shi kamar gawa,,
Tana duban kamshi hankalin ta yai matukar tashi don tasan ba haka ta barshi ba,saboda duk maskin da ke a jikin kamshi wanda har ya fita daga jikin kyalen,
Da sauri ta mayar da kashin cikin ledan da ta boye shi sai faduwa gaban ta ke matukar yi,
Hankalin ta idan yai dubu ya tashi a lokacin don sam bata taba tsan manin irin haka ba ma da,sauri a rayuwan ta,
Kwatakwatama bata taba zaton wanan kashin zai iya bushewa ba irin haka da sauri,,

****** ********* ******
Shirin shiga school yakeyi don suna da test gobe don haka yake son shiga da wuri yadan taba karatu,
Jin ana nocking din kofan falon shi a lokacin yasa shi dakatar da abinda yakeyi ya nufi kofan don ya bude
Abin mamaki don Hamza ne ya gani a tsaye daga kofan cikin dan yanayin damuwa tare da shi,
Hamza ya ambata da karfi a cikin mamaki sai Hamza din ya amsa a cikin wani yanayi na ban tsoro,
Ya dan jaye mai ya fada dakin inda ya samu kujeran three seater ya zauna tare da dafe kan shi wanda tun asuba yake mai wani irin ciwo,
Fita Mansur yayi zuwa dayan dakunan da yan uwan su suke a ciki suna barci ya kira su yake sheda masu suzo Hamza ne yazo acikin wani irin jalin rayuwa,da ya tayar mai da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login