Sarautar Mata

Chapter 47 of 94

mashi,
Ya dawo gida jiki da sanyi baida wani kuzari duk hankalin shi a tashe,ya rasa mafita yadda zaiyi,
Mama hafsi tace ya sayar da wanan kangon gidan daya saya mata a,baya ya samu kudi yai abinda zaiyi dasu,
Sam bai sha,awan taba hakkin marayu da sunan zai juya su don yasan yakan karye a kan mutum lokaci guda duk su ruguje baki daya,
Haka ne ya dan nuna wa mama cewa tabari har a samu mai saye,
Sam bai san cewa ina da kudi a hannu na ba sai dai duk maganan da suke ina jin su daga inda nake a zaune,
Bayan ya shigo daki yana zaune abin duniya yakai mashi ko ina don ko magana na lura da baya,son yi sosai,
Ance tsakanin miji da mata sai Allah tsab na mike na sauke akwatina na inda na boye kudin da aka,sayar min da wake na kirga kudin na miko mashi gurin da yake zaune,
Cikin mamaki yake kallo na yana kallon kudin, cikin nuna mamaki yake tambaya na kudin maye wanan Humaira,
Nakai zaune a hankali daga inda nake tsaye nace kudi nane wanan yaya,
Kudin ki ?
Ya tambaya cikin tsureni da idanuwan shi yana son jin amsar tambayan da yai min,
Nake ce mai eh na wane kudin da na,sayar da,wanke dana saya a gurin kane,
Sai naga ya dukar da kanshi cikin dan jin nauyi da kunya sai kuma ya dan dago kai yana mai kallona a cikin jin nauyi,
Nace a hankali idan zasu ishe ka sai ka fara dasu mu gani,
Cikin wani murya mai ban tausayi yace Humaira kina ganin ba matsala idan nai haka ban tauye ki ba,ashe,?
Nagirgiza kaina nace ba matsalan komai dama fridge naso na canza dashi don wanan da nake amfani dashi ya fara tsufa yana son canzawa,
Amma zan ta maneji dashi har zuwa lokacin da Allah zai hore min na,sai, wani kuma,
Ajiyan zuciya naji yayi mai karfi tare da fadi a fili Allah nagode maka,
Yadda kika taimaka min kema Allah ya taimake ki Humaira nagode,
Haba yaya ai abina abinka ne basai kai min godiya ba a kan shi don nima da taimakon ka na samu haka ai,
Wasu kudin zasu kai goma sha biyar na kara mika mashi again,
Da sauri ya kara tambaya na sukuma wa yan nan na maye kuma nace nakane ,
Nawa ?
Ya tambaya a cikin mamaki yana kallon kudin batare da ya karba ba,
Nace eh ka manta kudin da kasamu a gurin gasar amfani gona kace nabar wa yan nan a guri na har ka tambaya,
Ido ya zaro yana mamaki tare da nuna kudin yana cewa kina nufin duk tsawonokacin nan kudin nan su a jeye a hannun ki, har yanzu,
Nace eh mana ba cewa kayi na aje ma,su ba har ka tambaya,
Shiru yayi yana tunane a ranshi cewa wanan yarinyar wata iri ne ita, kudi kusan shekara biyu da rabi zuwa uku tana ta faman boyon su haka ba tare da ta kashe su ba,
O ni Hamza Allah nagode maka da,wanan baiwar da, rufin asiri da kai min a cikin dakina,
Ya kara juyowa inda nake yana cewa Humaira na gode nagode da wanan rufin asirin da kikai min bazan taba mancewa da irin wanan halarcin da kikai min ba a duniyar nan,
Mikewa tsam yayi da kudin zuwa waje gurin iyayyen shi ina jin shi yana masu bayani dalla dalla ,
Zan iya cewa yaune rana na farko a,rayuwan zamana a gidan su Hamza danaji Umma ta bude baki tana sa min albarka kamar yadda ko wace uwa takewa dan ta,
Naji dadin wanan adduan da suke min don har da fatan Allah ya bamu zuria masu albarka tai muna,
Sai naji a raina a gaskiya nima yanzu ina bukatan haihuwa a rayuwana
Don Hindatu tace min idan har na haihu kila kiyayyana da Umma zai dan rage don albarkacin abinda na haifa,
A hankali nakai hannu na a cikina karo na farko ina mai adduan nima Allah ya bani haihuwa hakana,
Don ko Kubura da na riga aure duk da tafini cika yanzu tana da tsohon ciki a jikin ta haihuwa ko yau ko gobe,

****** ********** ******
Noma haikan Hamza ya fara da dan kudin daya samu a hannu na,sai dai da yake noman yanzu kudi yake bukata sai gashi tun ba a kai ko ina ba kudin duk sun shige ga a aikin noman,
Fada nan fada can haka har Allah ya taimaka gonan ya samu tsayuwa,sosai, komai yai kyau yadda yake bukatan gani sai da muce Allah ya albarkaci gonan ta mu kawai yanzu,
Ranan na dawo da gajiya,daga makaranta don yanzu muna rubuta final exam din mu ne a school din, mu,
Ban samu abinci ba don yanzu dama ba ko yaushe muke girki ba a gidan kamar baya, can,
Ina zaune daga kofana ina dama yar furar da na shigo da ita a cikin jakata don yanzu wani kwazaban shan fura ne yazo min sosai,
Ga yunwar da nake ji don haka nake sauri na dama ko zai rage min yuwan da nakeji don ji nake kamar banda hanji a cikina don yunwa,
Muryan mama sa,a ce ta,shigo tana sallama daga kofa ,
Daga inda nake zaune na karba mata tare da gaishe ta a cikin ladabi a matsayinta na,sarakuwana itama,
Take tambayana bayan ta karba gaisuwa na da cewa Umma fa tana cikine ,
Nace eh amma tadan kewaya yanzu zata fito namike nakawo mata kujera don ta zauna,
A lokacin itama Umma din tafito daga bandaki hannun ta dauke da butan data kewaya dashi,
Daga inda mama Sa,a take a zaune sai bingidan da kallo da dan yatsunan da takeyi,
Tun daga nesa Umma ke mata sannu da,shigowa tana cewa ashe har kin karaso yanzu nake cewa kindan taushe hannu kada rana yai muna don da kafa kikace zamu tafi,
Tace eh nadan tsaya ne balaraba ce ta shigo shine yasa na dan taushe hannu kin san halin dakaren mijin nata mai hali baya barin halin sa,
Ni kashe auren zan yi kowa ya huta don bazan iya ba ace aure ba,wani karuwa sai dan banzan fitina, don iskanci har ya,fara zagin iyayye,
Umma tace ai sha anin yaran ne yanzu sai hakkuri Sa,a don abinda kai kake hango masu su basu ganewa sam,
Tamike tana cewa ga gidan naku shiru mana kodaya ke dama ku haka gidan yake ba,wani karuwan yara sai dai aci akaiwa masai kawai amma anki aje muna dan kama hannu mu rika mu samu dan rakiya zuwa uguwa,
Take Umma ta tabe baki tace bari kedai Sa,a ni wanan abin ya kai min inda yakai wallahi ace gida shiru kamar gidan bariki,
Can kuma tace umm bari dai nai shiru duk da yake dai baka ganin naka a cikin cutarwa ka kyale shi dole ne kafada mai gaskiya,
Wani irin dimm naji a raina sai da cikina yadan bada kara kulululu don nasan sabon fitina mama sa,a ta jawo min kuma,
A cikin karfin hali nai masu adawo lafiya ban tsanmani Umma ta amsa min ba suka fice,
Furan da nake dokin sha sai naji duk yafita min a rai annurin fuskana duk ta gushe a lokaci guda,
Sai nake tuhumar kaina da kodai ina da matsalanr dasu suke ganin laifin nawa ne ni kadai bada Hamza din ba,
Sai nice kawai abin zargi a kullun laifina kawai suke ganin naki daukan wanan cikin,
Na mike tare da,daukan furan nakai cikin fridge na je batare da nasha ba,
Ina zaune ina hadiyan bakinciki mama hafsi tashigo gidan tun daga karban sallaman da nai mata ta,fahinci ina cikin damuwa,
Tun daga tsaye take tambayana may akayi halan Aisha ?
Nace cikin kakaro murmushi ba komai mama , inadan dariyan yake,
Halan Sa,a ta shigo gidan nan yau ko,?
Nabata amsa da eh mama yanzu suka fita zuwa uguwa,
Wanan bakar makiran mace yaya taki gane halinta har yanzu duk irin abinda tai mata a gidan nan kan zance yaron nan amma wai shine yanzu suka kara dinkewa kuma,,
Haka mama taita mita bata daki bata waje har yamma da,su Umma suka,dawo,
Don tasan cewa zataji ko maye a gurin Umma tunda ni naki fada mata komai,

Ai ko suna zaune ana hira kowa na gida bayan
isha,i yan gidan mu suka shigo suna cewa, Kubura ta haihu da yamman nan su Ummi suna can sun tafi dauko ta wai,
Nifa hakkurina akan rashin haihuwan yaran nan yasoma kai karshe ace aure kusan shekara uku har wanda sukayi aure a,bayan su sun haihu suko shiru kakeji haka,
To tunda kina da ja da al,amarin ubangiji ai sai kiyi yadda zakiyi su haihu din ko,
Mamace ta bata amsa da haka daga inda take zaune tana cin abinci,
Tace ni wai har yaushe ne za,a ce yaran nan sun wani jima basu haihu ba har ana batun tayar da jijiya akai
Nifa nasan Allah ne mai bayarwa idan lokaci yayi bawai sai mutum yaso ba,
Dole na na fadi hafsatu don wanan abin ya fara damuwa na,arai ace gida haka shiru babu hayaniyar yara da mutum zaiji yaji dadi a ran shi,
Kin san kowa da irin bayan shi wasu guntun baya garesu wasu dogon baya ne dasu sai andauki lokaci mai tsawo,
Don haka kibar wanan zancen haka yaya duk fa yadda akeyi yarinyar nan tana yin shi a gidan nan,
Tau ai bance batayi ba,shi maganan haihuwa wani magana ce ta daban don kowa nason yaga nashi a cikin karuwa dashi da ita ai ina son ganin kowa ya samu karuwa,
To sai kici gaba dayi tunda ki fi bukatar ganin su a cikin tashin hankali, ko yaushe don zancen ki tayar masu da hankali kawai yake a gidan nan,

****** ********** ******
Da kwana biyu Hamza ya dawo don yanzu bai dadewa bai shigo ba tunda mansur yana da mota kuma ba,wani nisane tsakanin sokoto da mu ba,
Wajajen shidda na yamma suka shigo don yin weekend, kamar yadda suka,saba, yi muna,
Na tare shi da murna ina fada mashi zancen haihuwan Kubura azatona shima murna zaiyi sosai jin kubura ta haihu don ko banza ai an zama daya yanzu,
Sai naji yana cewa aiyya ashe ciki gare ta,
Yadda ya amsa min sai banji dadi ba sai dai nabi bayan shi da kallo kawai cikin mamakin irin yadda ya amsa min,
Can yadan leko daga waje yana ce min kikai min ruwa na,watsa na cire wanan kayan na jikina,
Ban tsaya ba namike zuwa ksi mai ruwan kamar yadda ya umurta nakai masa,
Zandawo nake jin Umma na cewa da zuwan ka an tare ka da zancen haihuwan wata can kai ba,a baka labarin maidadi na gidan ka ba,
Nikan gaskiya dole asan abinyi don wanan shirun yai yawa haka a gidan nan gida kamar gidan GRA ba wani hayani a cikin sa,
Sai lokacin jin yadda Umma ta ke sake zancen ta yasa shi yin yake kadan yace Umma itama idan lokaci yayi ai zata samu din lokacine kawai bai yi ba,
Daga haka yai shegewan shi bandaki ya barta tana ci gaba da mita ita sai dai mutum yai taci yana kaiwa masa kullun ba wani karuwa a kai,
Ina jin Umma don haka nai shigewa ta dakina ina dan kata kimtsa guri don samun hilin daki,
Da dare nace zan shiga gidan mu na gaidasu kafin da safe naje gidan Kubura don ance mijin yaki yarda ta,dawo gida,
Kamar ba zai amsa min ba can dai yace min sai kin dawo kawai,
Banyi fushi ba jiki ba karfi nai sallama dasu Umma na tafi gidan mu don nai masu barka,
Na dan dade gurin mama,saude nafito zuwa gurin Ummina bayan na gaida maman Aina,
A dakin mun gaisa da Ummina shine nake fada mata irin sakani gaba da Umma tayi ita da kawar ta,
Dariya Ummi tayi tana cewa kai Rabi ho ita yanzu har yaushe kike da zata wani matsa haka wai baki haihu ba har yanzu,
Ta manta cewa koda akai auren ki bawai wani shekaru ne masu yawa akanki ba,
Nace cikin nunadamuwa nikan Ummi har abin ya fara damuna a rai don yanzu nafara saka abin a raina wallahi,
Ji nan Aisha ke dai ba jahila bace don gwargwado kin san addini yanzu,
Mutum baiyiwa kanshi abinda Allah bai tashii mashi ba,
Ki dinga dogaro da Allah domin shine mai bayarwa kuma,shine mai hanawa,
Idan kin biyewa jahilcin Rabi kika cutarwa kanki ke kika,sani don ni ba ruwa na,
Ban iya hauka irin na sarakuwar ki ba mutum yana girma yana kara cin kasa saboda jahilci,
Shiru nayi ina kallon zanen tabarman da nake zaune akai ina sauraren Ummi din,
Tai min nasiha mai kashe jiki nai sallama dasu nafito zuwa gida tare da masu sallama,
Washegari da zai fita na roki zuwa gidan Kubura don na dibata da jaririyar ta,,
Bai hanani ba sai adawo lafiyan da,yai min inda na,shirya cikin wasu atamfa zani da riga na,sa hijjab dina wanda ya sauka min har kusan kasa,
Mashin na hau don gidan yana da nisa da uguwar mu don haka ban dade ba na isa gidan nasu, wanda zuwana nabiyu ke nan,
Tundaga wajenake jin hayaniyan mata agidan wanda nakarasa ciki naga gidan dam da mata sai dai zan iya cewa bakin fuskane a gare mu don ba yan uwan mu bane,
Na gaishesu na karasa dakin Kubura din tana zaune bakin gado rugumay da yarta wace tai kashi ta rasa yadda zatayi don tace min bata jin dadin jikin ta,
Mun gaisa sama sama da ita take ce min cikin dakiya, na samu ruwa na,wankewa yarinyar jiki duk ta bata da kashi,
Nafita na samo ruwan na karbi yar na wa ke mata tare da dan dauraye ta tsab nan naga kayan su da,suka bata anjibgesu a gurin famfon gidan,
Bayan na mayar da yarinyar nakoma na,wanke kayan tsab inajin matan falon suna gulmana suna cewa wai kila ni yar uwar ta ce,
Amma in bashiba ita watake taimakawa da za,a taimake ta idan taje gidan mutane tana masu kalkon raini wayo kamar diyar wani attajiri,
Na gyara mata har dakinta nafita na,sayo turaren wuta na,sa a,dakin take dakin yafara kamshi jego kamar na kowa,
Ni ce nai ta bata abin sha tana,sha har take ce min tai matukar jin dadin jikin ta ranan,
Ina gida har bayan sallah la,asar sannan nai mata sallama na tafi gida, tana tayi min godiya,
Ban shiga gida ba sai dana tafi gidan mu nai masu magana akan a samu wanda zai kula da kubura don tana bukatar tai mako,
Tun a gurin maman Aina take ce min gaskiya ita bazata ba don da tai ciwo kwanaki ta tafi mijin bai kawo masu shayi sai dai wanda aka hada gaba daya na gida,
Ummina ce take cewa idan malam ya dawo zata roke shi ta tafi dama tana gudun taje ne maman Aina tace tai mata cin layi,
Nai masu sallama na tafi gida duk da yamma yayi na samu komai ba,ai min ba don mama Hafsi bata nan ta tafi tallan kayan gwanjo da take sarowa kasuwa don samu rufin asirin ta,
Tun a,waje na aje hijjab dina na soma tara kayan wanke wanke nakuma yi shara tare da dora girkin dare,
Allah ya taimake ni nagama komai da wuri kafin duhu yayi don tuwon masara nayi da miyar kuka,
Nabawa kowa nashi na,debi ruwan wanka na watsa don naji sanyi a raina sai dai ziciyata fam take da tunanen halin da na riski Kubura acikin sa,
Ina tunanen cewa watau dai haka rayuwan auren yake ko ina ko wani gida da kalar tasu matsalar rayuwa ke nan,
Allah dai ya karawa ma,aurata daraja da rufin asiiri juna duniya da lahira,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA YAR UWA DON HAKKIN WASU NE, BA,A YAFE BA ,,,


Haka Ummina ta dage taita kokari da Kubura da jaririyar ta wanda a,dan wanan zaman Ummi ta fahinci halin mijin su Kubura din,,
Haka yasa ta dinga kwantar mata da hankali tana mata nasiha gwargwadon yadda duk uwa ya dace taiwa yar ta nasiha, akan zaman aure,
Dafarkon zuwan Ummi sai ta lura cewa Kubura din tana wa yar ta wulakanci saboda laifin ubanta da ya shafe ta,
Ummi ta shigo gidan sun dan gaisa da Kubura din yan min tina kadan sai yar jaririyar ta,soma kuka,
Amma,sai Kubura tai biris da ita kamar bata jin may take yi,
A,a gyara mana ki bata nono tasha Ummi take cewa Kubura din,
Barta, tai tayi kawai Ummi idan ta gaji zatayi shiru ai,
Ummi tace auzu billahi may yai zafi kuma haka kubura da zaki horar da yar malaukar Allah da bata san momai ba a,rayuwa,,
Juyawa Ummi da yar jaririyar baya tayi yayin da jaririyar ke ta faman tsala ihu,,
Jamila ce kishiyar Kubura taji ihun yai yawa ta leko dakin don duba,yarinyar, turus taja ta tsaya, don ganin Ummi a dakin,
Gani yarinyar a hannun Ummi yasa ta cewa ai ina ce ba kowa adakin ne ta juya tana kallon Kubura wace ta kwanta ta,bada baya,
Ta gaida Ummi wace ke kokarin ba wa yarinya ruwa ta,sha,
Jamila take cewa kin gane ta mama bata son bawa yarinyar nan nono ko may zatayi dashi oho,
Ummi ta juya gurin da Kubura take kwance ta basu baya take cewa a fusace,
Tashi ki bata nono nace kamar ba,zata juyo ba sai can komay ta tuna sai ta dan dago daga kwancen a hankali,
Idanuwan ta da,Ummi ta dan kalla taga sunyi wani irin hulu hulu da su alaman tayi kuka,,
Mika mata yar Ummi tayi inda ta dan mike ta gyara mata rikon yar sai kawai ta kama zukar nono kamar mayunwaciya,
Ganin yarinyar tana shan nono yasa kishiyar tata,juyawa tafita tabar dakin,
Tana fita Kubura ta zare nonon daga bakin yarinyar ta kokari azata saman gado,
Idanuwa a,waje alamar tsoro Ummi tace lafiyar ki kuwa,Kubura,
Ta,dan dago kai ta kalli Ummi kadan ta danyi tsuki tare da

Download complete TXT · Novel page