Showing 138001 words to 141000 words out of 299981 words

Chapter 47 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17654

hankalin sa,
Wasu suka ce bazasu zo ba amma sai wasu suka biyo bayan shi mansur din cikin tashin hankali,
Sun samu Hamza dafe da kan shi sai wasu hawaye yake fitarwa kamar fanfo,
Man may ke faruwa ne haka wai da,safen nan duk ka wani zo ka tayarwa mutane da hankali irin haka,?
Maimakon Hamza yayi magana sai kara dafe goshin shi da yakeyi tare da murdewa guri daya tankar zai mutu,
Daya daga cikin su dake tsaye daga kofa ya ce kai mu kaishi asibiti fa kada, yazo ya mutu muna a gida haka,
Mansur dake duke gap dashi ya dago kai yana sauke numfashi yake cewa, wanan ba zancen zuwa asibiti bane Yusuf akawai wani bakon al,amari da yazo wa guy din nan don haka muyi kokari muga cewa mun taimaka mai kowa ya karato mai abinda ya sauwaka daga cikin alkurani maigirma don ya ida samun sa,id,
Sihiri ne da alamar yake fita daga jikin shi a cikin wahala hakan nan,
Don rayuwa na ya bani cewa, zuwan da brother din shi yayi ya koma something serious zai
faru a kan shi,
Nan suka taru kowa da irin ayar da yake ja a bakin shi suna tofawa, cikin tashin hankali suke gaba dayan su don ganin irin yadda yake wahala a lokacin,
Cikin ikon Allah bowayi gagara musalin sai suka ga ya fara barci a hankali barci ya soma daukan shi yana rufe idanuwan shi da sukai mai ja jajir kamar garwashin wuta,
Gaba dayan su suka fita daga dakin zuwa waje, shawara sukeyi don sun san cewa Allah ne ya kubutar da Hamza daga kaidin shu,uma Lima,
Sun yake shawaran daukan shi zuwa wani gida gidan wani dan uwan yusuf malami su gani hakan sukayi suka dauke shi daga gidan zzuwa wani gida na daban inda maigidan yai masu alkawar8n taimakawa Hamza din,
Suka dawo gida kowa ya kama shirin shi zakace wani abu bai faru ba da su,,

****** ********** ******
Gap da Mansur zai fita saboda yayi late sai ga,su lima ita da Bicky sun zo rai a bace masu, ko gaisuwa babu suka shigo gidan ,
Mansur wanda ke waje yana kokarin bude motar shi zai shiga ya,watsa masu harara cikin kawar da kai,
Lima ce tace mai cikin dakatar da kai, malam ina mijina yake,
Wani kallon banza Mansur ya,watsa mata yace mijin ki ko farkan ki ?
Naji koma may yake ina yake don nasan babu inda zai tafi dai nan gurin ka ,
Dayake nine Uban shi ko uwar shi ba zaki ce baida gurin zuwa,
Yadda Mansur yake masu magana cikin tsauri yasa duk wani shirin iskancin da suka zo suyi mai yai sanyi sosai,
Gaskiya tunda safe nake neman shi ban san ina ne ya shiga ba ta fada in a angry voice,
Bayan kin raba shi da mu kina tsan manin cewa zai shigo wajen mune again,
Suka juya cikin sanyi jiki ba wani kwarin gwiwa tare da su,
Har sukai kofa zasu fice daga compound din gidan sai taji muryan Mansur din yana cewa,
Ke Mansur din ya nuna ta da key din motar dake hannun shi yana cewa,
Indan ma har kin san cewa kin mai wani abune kike wani boyewa mutane,
To zaki kuka da kan ki wallahi,
Wani kallon ta watso mai ita ma cikin kai a suwa kuma tare da jan tsaki tasa kai tafice,
Bayan ta tayar da motar ta take cewa, Bicky wallahi iam scared kada fa ace wanan guy din ya salwanta ,
Dana shiga uku a garin nan da yaya zanyi ga wanan dan rainin wayon har ya fara zargina cewa wai nice nai mai wani abu,
Bicky dake zaune daga gefe tace so annoyed dama duk irin abubuwa nan ina maka gudun su Helina,
Yanzu gashi wani masifa yana so ya kuno kai sabuwa,
Ajiyan zuciya ta sauke a cikin firrigita, take cewa na shiga damuwa sosai Bicky,,
Ban tsan mani cewa My zai iya min wanan abin ba haka irin yadda na daure shi sosai
Kin manta cewa yana da parents yana kuma da mata a gida ga kuma abokan arziki iri shi wanan guy din,
Helina, ban san abinda ya rude ki ba haka da yawa kike ta cewa wai ke sai kinyi zaman aure da guy din na ,
Bayan kin san cewa ba age mate dinki bane kuma kuma wai wani mai hali bane balle a ce don kudin shi kike son shi,
Shiru tayi tana ci gaba da driving idanuwan ta na a gefen titi tana kallo ko zata hango Hamza din,
Can tace Bicky bazaki gane ba ke ina fada maki ni na,san dalilin da yasa na ke son guy din nan,
Yanzu ma nafara son shi a rayuwa na,saboda ban taba haduwa da namijin dake da skills irin na,wanan guy din ba yana satisfy dina yadda nake so ,
Baki Bicky ta tabe tace nasgi dai kike ji shiyasa kika ce haka amma ai akwai maza masu abubuwa da dama da zaki bukata,
Har cikin school suke suna tambayan ko akwai wanda yaga masu Hamza amma shiru,
Sai sun wuce mutane suce killa ya gudu ne ya gaji da,wahala ko wani abu, dai maka mancin hakan,
Har yamma ba Hamza ba labarinsa hankalin Lima yai matukar tashi dole aka bata shawara a kan ta fara dubawa a garin su ko ya tafi can ne,
Wani iri taji idan ta tafi may zatace wa iyayyen shi bayan sun san cewa ta raba su dashi na tsawon lokaci sai yanzu zata fara cigiyar shi,
Gashi saboda kishi ta hana shi amfani da waya, wai don kada ya dinga kiran matar shi dashi,
Ga Mansur sun fara mata barazanan zasu karanta sai ta fito masu da dan uwan su don kowa yasan a gurin ta yake, zaune,
Wasa wasa sai ga case har a police station an aje cewa za,a tafi gidan su Hamza din a gani ko yana can gida,

****** ********** ******
Barci nake sai dai ba mai dadi ba duk da ban wani nisa da yin barcin nawa ba, amma kuma mafarki yazo min a,wahala lokacin,
Sai juye juye nake a fili ashe har da,sambatu nake wanda daga inda Mama Hafsi take zaune tana nafila tajiyo ihu na,.
Hamza ne na gani wani naman daji mai mumunar suffa yana na binshi da gudu sai faman gudu yake, dabban tana bin sa baki a bude kamar zata cafke, shi,
Saura kiris ya rage ya dabban ta cafke shi ya tuma ya haye wani tsauni da wata mace ke tsaye a kai wanan matar ba kowa bace ashe mama Hafsi ce ta rogumo shi suka gudu, tumar da yayi na,saura kiris dabban ta cafke shi yasani Ihu wanda har na baiyanar a fili su mama sukaji ina cewa Innallilahi da karfi Hamza,,,,
Da sauri suka fito daga dakunan su ina kwace a kasa girin dana idar da sallah barci ya kwashe ni naji muryan mama da Umma suna cewa
AIsha, Aisha, Aisha da karfi suke kiran sunan nawa abinda yasani farkawa duk nayi zufa ga hawaye yana fita daga idanuwa na,
Da sauri na bude kofa na nufi bayan mama hafsi din na boye sai kuma kukan da na,saka a cikin kwanciyan hankali don tunawa da nayi da mafarkin nawa,
Sai kuka nake suma hankali a tashe suke tambayana,
Nan nake fada masu irin abinda na gani a mafarki abinda yasa Umma ta suri buta zuwa bandaki ke nan,
Tsoro ya kama su mama sai nanata kalman innallilahi suke yi, a cikin tashin hankali,.
Umma tana fitowa ta jawo kujera takai zaune saboda kafafuwan ta basu daukan ta tana cewa Hafsi akwai matsala ke nan maigirma,
Mama Hafsi tace akwai shi mana yaya Allah dai ya kyauta ya kwato muna wanan yaro aduk inda yake,
Amma insha Allahu da safe zan koma gurin liman don na fada mai wanan mafarki,
Yanzu ke Aisha taso mu shiga daga dakin ki na taya ki kwana da safe sai mu san abinyi,
Tare da mama hafsi muka kwana a,ranan tana ta kwantar min da hankali,
Har akai kiran sallah farko inda muka,futo muka kara yin alwala da gabatarda nafilfilu,,
Ita ma Umma a ranan cikin tashin hankali ta kwana tare da yaranta a daki don sai kiyasta wani irin halin rayuwa dan nata yake a ciki,
Nan dai muka karya a tsatsaye ba wai don rai yana so ba,
Fitan mama hausi a dakina ya bani damar samun lokaci nai kuka yadda raina ke so,
Ban san cewa mama ta tafi gurin mama Rahana ba sai ga ni su mukayi atare sun zo nan suka taru a kaina har Umma suna min nasiha ,,
Barcin da ban samu ba da dare bashin shi yake a kaina, shine ya sace ni a bayan mamana nake kwance saman tabarma,
Sallama matan da,suka shigo ya,sa su mama mayar da hankalinsu a garesu,
Cikin tuna inda suka san su sai mama hafsi ce bayan sun zauna take cewa yau kuma kin biyo mu har gida ne bayan sace hankalin dan mu da kikayi yabar mu har abada,
Sai wani nuna,sarakuta sukeyi kan su mama da umma,
Murmushi Bicky tayi tana cewa haba mama bashi ya kawo mu ba,
Mu alheri ne ya kawo mu gare ku don yanzu mu da ku mun zama daya ko,
Zuwa mu kayi mu gaida ku mukuma, ji idan har Hamze ya samu shigowa don muyi zai shigo kafin mu zo,
Tau bai shigo ba mama hafsi ta basu amsa a cikin gatse, shiru sukayi suna kallon junan su wanda alamar, ke nuna shock a fuskan su,
Gurin yadan yi tsit sai mama ce tace amma boyar Allah kiji tsoron Allah don baki da tsoron Allah shine zaki raba yaro da u
Iyayen shi har na tsawon wani lokaci yanzu don baki da kunya zaki shigo muna kice wai kinzo kina zaton ya iso,
Mama ki fahince mu mufa bamu son rashin mutunci daku don dan ku amma don may zaki fara gaya muna zance haka,
Nan bakaken maganganu ya fara tashi a tsakani su da mama, abinda ya farka dani daga barci ke nan,
Sai ganin su nayi suna mikewa zasu tafi cikin wasu dogayen riguna irin ta yan gayu ga manya duwawunan su sun fito daga cikin rigar,
Cak ta tsaya tana mai kura min idanuwan ta, duk zancen da Bicky ke yi da mama ita bata samu bakin magana ba sai kafe ni da idanuwan ta da tayi,
A take nace mata La,illaha illa anta subbahanaka inni,kuntu minal zalimin,
Wallahu galibun Ala,amrihi,
Sai naga ta,wani kawar da kai tana cewa mama kuyi hakkuri abin ba haka yake ba zamu tafi sai mun kara shigowa,
Waye mamaki sai dai idan ke ce mamata ai don ni kin haifeni ma,
Mama hafsi taba ta amsa da hakan tare da tafa hannayen ta tai masu yas suka fita jiki ba kwari don rayukan su a cakushe yake lokacin,
You see, what you course for us matan kauye suna zuba muna magana akan jarabar ki,
Bicky take fadawa Lima din haja wace sai a lokacin ta sauke ajiyan zuciya tana cewa,
Kin faye shirmay Bicky mai zaki tsayawa fada a wayannan yan kauyen dan sune dai na kwace sai dai su haifi wani kuma amma ba Hamze ba,
Helin yanzu ke baki hango tarin fitina a idanuwan wanan matar ba ne wai sai fa kin san yarda zakiyi da ita don kin manta ki hada da ita a dafa maki ita,
Bicky forget about her, ni ba wanan ba wanan yarinyar nake matukar bakin ciki a rayuwana wallahi dana sani kawai a batar min da ita kwata kwata a,rayuwan mu,
Amma bar su kawai zan san yadda zan yi dasu gaba dayan su,
Sai ta ce for god sake where this guy hide,
Bicky abin ya fara bani tsoro fa wallahi kin ga bai zo gida ba ke nan,
Tau shi kuma ina ne ya shige wai haka abu wasa wasa tun jiya,,,,

****** ********** ******
A hankali daga inda yake kwance ya bude idanuwan shi da sukai mashi nauyi,
Dakin daya ke kwance a ciki yake bi da kallo sannu a hakali sam bai iya tuna ko ina ne wanan gurin haka,
Shigowan mai gidan dauke da wani kwarya dauke a hannun shi sabo ya sashi dan kokarin mikewa zaune,
Mutumin yace a bawan Allah ka farka ashe da kai Hamza ya bashi amsa sai ya samu guri daga gurin kafafuwan Hamza din ya zauna a hankali,
Kwarya ya mika mai yana cewa karbi wanan ka shaye duk kaji, kayi bissimillah,
Ba mussu Hamza din ya mike zaune ya karba inda ya kwan kwade gaba daya ruwan rubutun sai mutumin ke ce mashi karage kadan kashafa a fuskan ka da kafan ka,
Yadda aka umurce shi haka din yayi ya shanye ya shafa saura a fuskan shi da kafa,
Haka suke ta mashi har hankalin shi ya dawo daidai ya fara tuna wasu abubuwan da zai iya tunawa a baya,
Umman shi da matar shi Aisha yake matukar son gani a rayuwan shi tare da yan uwan shi da mama hafsi,
Kewan gida yake sosai a ranshi har abin ya fara damuwar shi,
Gashi duk wa yan nsn mutanen bai san su ba,sai yusuf ne dakan zo jefi jefi ziyaran shi a kauyen,
Nan Yusuf ya ke kwantar mashi da hankali akan ya kara hakkuri har komai ya koma dai,
Don an balain saka masu ido ga duk wani movement din su ,
Yayin da su ma a nasu bangaren su hasawa Lima wutan cewa sai ta fito masu da dan uwan su,
Tun Lima na daukan abinda wasa har gashi yau sati daya cif da batan Hamza a gurin ta,
Har can garin su ta saka in secret a duba mata ko yana garin amma ba labari,
Ranan da Ibrahim yazo muna da labarin batan Hamza da wani abokin karatun su ya fada mashi anga tashin hankali a gidan mu,
Tsaye nake ban san lokacin dana fadi ba kasa sai dai bude idanuwana nayi naga matan gidan mu tsaye a kaina, har da Ummina sai mama saude da mama Rahana da suke min hitara,
Ranan ne mutune gari suka san irin halin rayuwan da muke ciki wata takwas ke nan rabon Hanza da gida muna ta hadiyan bakin ciki a ran mu,
Sosai aka tausaya muna munga yan uwa da abokan arziki masu zuwa muna jaje da Allah ya kawo shi ya baiyanar dashi lafiya,
Anty Hindatu tazo da cikin ta wanda ya fito sosai alokacin muna dakina zaune tare da ita mama da Ummi duk muna ciki zaune,
Bayan mun gaisa sun gaisa da su Ummi take muna jaje sai ta ke kara bamu labari yadda batan yazo yadda sukaji labari,
Wayan ta touching ta ciro daga jakarta takira mijinta mansur take fada mashi cewa, gata a guri na yace ta bani waya,
Nakarba da kyat jiki babu kwari, nace cikin muryana da yai sanyi nake cewa,,
Hello, yaya ina wuni ya amsa a bangaren shi da lafiyan Aisha sannu ya hakkuri idanuwa na suka kawo hawaye na amsa a muryan kuka da Alhamdullahi,
Yace kuna da yawa a gurin ne ina son magana da ke ne nace, ni da mamana ne sai anty yace, good,
Kina ji Aisha banson kitayar da hankalinki ki ji ki kwatar da hankalinki lafiya Hamza yake bana,son ko da wasa ki fadawa wani zancen don haka ki kwantar da hankalinki kinji ,,
Nace tau yaya na gode hakan kawai daya fadi naji sanyi a raina, tare da tunane barkatai na akwai wani abu a boye ke nan killa,
Don haka sai nayi kamar yadda yace din ina daga kai muka hada ido da Anty Hindatu sai ta daga min kai alamar be strong nace mata tau a hankali,
Ayarin wasu mata da suka shigo ba wanda yasan su sun dai shigo ne da sunan yi muna jaje,
Daya daga cikin su ce ke cewa ina matar tashi aka nuna masu dakina suka shigo muka gaisa dasu sai daya daga cikin su take cewa,
Wai yakamata nai shirin takaba kada na zauna ba mayafi a kaina, don killa baida rayuwa gani ban shirya ba,
Anty Hindatu tace haba boyar Allah wanan wani irin fatane haka,
Daga bayan su suka ji mama na cewa aniya makomiya, bamu cikin takaba yanzu a gidan nan insha Allahu
Allah baki hakkuri ni dama naga kamar ya dace tayi hakane,
Suka mike suka tafi mamatana masu bakar magana,
Nan suka tafi sukka barmu a cikin bacin rai kowa da abinda ke yawo azuciyar shi,
Hankalina ya daga da zancen matan nan don sai ina gani zancen su gaskiya ne,
Anty hindatu ce ta dan zungure ni da kafa abinda yasani saurin dawowa daga nisan tunanen da na,shiga ke nan,
Tace cikin harshen turanci nadaina takurawa kaina dayawa haka nabarwa Allah komai,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login