Sarautar Mata

Chapter 49 of 94

nr cif na bude baki don ganin suyi yawa tare da juyawa gurin mama ina cewa mama har fa dubu uku ne kudin,
Kodai zan rage na mayar mai da kudin ne don suyi yawa wallahi,
An ma kinji abinda mijinki yace yace ya rantse ko kin mayar bazai karba ,
Nace cikin jin kunya na gode na cire dubu daya nabawa su Umma su raba ita da mama din,
Kamar nai fushi naki zuwa gurin sunan sai dai, na daure kawai na tafi don gudun zargin rashin shiga na,
Aiko na,samu an kwasa za,a tafi gidan su Kubura a gagauce na shiga gurin Ummina ta hauni da fadan rashin zuwa da,wuri da banyi ba,
Naimata bayani yadda duk mukayi tave to al,amarin mazane sai hakkuri don haka idan dai kin san bai barki ba ki koma gida kawai ban son fitina,
Nace a maraice da idanuwa da suka kawo kwalla shi ya barni da kan shi ai yanzu din,
Jin ana kirana,waje nazo mu dauki kayan da za,a tafi gidan Kubura dasu yasa nabar dakin da sauri na,samu yan uwana muka kwasa sai gidan maijego tare da kayan arziki niki niki, irin su masa, guguru, dibbila, su man gyada shimkafa, maggi kifi albasa, da sauran su,,
Mun samu gidan sunan da yan uwan miji Kubura makil sai ita da kawayen ta duk da basu da yawa a dakin ta,
Nan ta fara muna korafin rashin zuwan wasun mu mu zauna da ita take cewa tundai ke yar Agwai na zaci ko banga kowa ba ke zanganki kinzo zama dani,
Murmushi nayi kawai ina bata hakkuri din banda abincewa saboda nima gaskiya haka na so nai mata nazo na zauna da ita tun safe sai hakan bai samu ba,
Nan aka,shiga sha,anin suna yarinya,ansa mata,suna Fatima wai sunan yar maigidan ke nan,
Ashe anty Hindatu tana gidan ban sani ba,sai da ta leko dakkin tana nemana nan muka fita muna hiran yaushe rabo da ita,
Can take ce min wai yaya alkar mu da Kubura yake sai nake fada mata yadda muke,
Tace mijin ta dan iska ne baida mutunci saida iyayyen su sukai mai tas yau da safe wai baiyi murnan da haihuwan ya mace da tayi mashi ba,
Kin san ance wanzan bai so a jikin sa yana gudun a rama abinda yakewa diyan mutane a yar shi,
Aiko ita yar uwar taki ance cafkeshi tayi don yaso ya yaudare ta ya gudu da farko da yake ita yar duniya ce itama sai ta kamashi,
A raina nace ko ina kuma suka samu wanan labarin haka kai mutane a kwai tsegumi,
Take ce min ai kila bata,san halin dan iska bane har ta yarda ya aure, ta,
Dan cacane fa kuma ga kalwanci da yakewa manyan gari yana daukar masu mata ana,bashi kudi da manyan motoci,
Da sauri nace Subbahanallahi shi Alhaji Nura din tace shi mana ai bata rasa sanin halin shi ita,
Ko ita uwargidan nashi yar uwar namu ai don tana da dan nakasa aka hada su dashi hakkuri take da dan iska sam baida hali baida mutunci, ko kadan,
Itace ma takai karan shi yau da safe wai yaki yiwa maijegon da yarta sayayyan komai na suna,
Takr naji tausayin Kubura ya kamani har cikin raina na tausaya mata matuka,
Nace mata cikin muryan tausyi kin ko san da itace zata auri yaya Hamza ana gobe a saka ta a lalai taki yarda tasa baba kuka ganin baba yana kuka nace ni a daura dani,
Ta tambaya a gagauce da cewa ke ki bari dan Allah dai Aisha ?
Nan na dan bata labarin yadda abin ya kaya tace kinga ikon Allah ko,
Gashi tayi zaben tumun dare tafada gurin dan caca kuma kalwani,,,


Ina muna fatan fara azumi lafiya Allah ya hada mu da rahamomin sa dake cikin wanan wata mai albarka,
Sai dai muyi hakkuri da juna don idan azumi ya kama ba kullun ne zaku dinga jina ba sai a hankali, zandinga post idan na samu time insha Allahu,
Masu fitar min da novel waje zuwa wani group na bar su da Allah ya isar min da isar sa,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA,,
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE

Wanan karban haihuwa danayi a cikin shiyan mu shi ya taimaka min sunana ya samu daukuwa ga mutanen uguwar mu har suka fahinci na yi karatin health nasan wani abu,
Yanzu mutane suna dan shigowa guri na don neman taimako,
Yaran su dama su kan su matan sai suke ganin sun samu hanyan sauki ba sai sunje asibiti ba,
Idan naga abin yafi karfina,saina turasu su tafi asibiti don ban yarda nai kasadan dubu ciwon da,bazan iya treating din sa ba na jawa kaina matsala,
Don duk bakin ciki da hassadan su Umma ya kai min ko ina yanzu sosai ban jin dadin irin yadda Umma take yawan, nuna min hassada akan wanan ci gaban da na,samu,
Don duk wace tai sallama da zaran Umma ta fahinci cewa mace tazo ne don gani na yanzu zata bata ran ta ta,shiga yadda magana ke nan a tsakar gida kamar yarinya karama,
Sannu sanu har ankai ga cire amfanin gona yanzu mutane sai aikin gona ake ko ina ana faman cire amfanin da,aka saka,a gona, duk da dai daman ta bana ta dan zo wa mutane da yar gardama,don duk wanda bai yi shuka,da wuri ba ya samu dan matsalan fari na ruwa da,akayi a karshen damana,
Shi ya kawo lalacewan gonakin mutane sai ba a,samu anfanin gona wadattace ba, sosai,
Duk da wanan korafin na jama a mu dai zamu iya cewa Alhamdullahi don gaskiya mun samu ci gaba sosai don shi kan Hamza ya samu amfanin gona mazu yawa, a gonan shi har ma yadda bai taba tsan mani ba,
Ranan da yazo yana zancen yadda ya samu albarkan gona kowa na murna da farin ciki, a gidan sai mama Hafsi kawai ta kada baki tace,
Gaskiya hannun Aisha yana da kyau don a gaskiya da badon taba da bazamu san yadda zamuyi ba har ma da ace a wajen wani aka karbi kudin nan ba lalai bane a samu amfani mai yalwa irin haka don wani hannun ribas gare shi,
Koda anyi amfani da abin shi sai kaga komai na mutum ya tafi ya lalace kamar yadda gara take cinye duk abinda yai karo dashi,
Azatona Umma zata ji dadin abinda mama ta fadi a kai na ,
Amma abin mamaki sai naga daga ita har dan ta kamar ba wanda yaji dadin zancen don ita umma cewa tayi
Wanan ai ba yin wani bane hannun wanda ya dafa abin ne kawai da albarka,
Shi ko Hamza ji nayi yace hmmm mama ke nan ai wanan abin ba haka yake ba,
Zataci gaba da magana amma sai Umma ta saka wa mama waigi da cewa don Allah hafsi kibar wanan zance
Ina wanan taimako ne tsakanin mata da miji bawai abin wani zance bane,
Mikewa Hamza yayi don yasan cewa yanzu uwayen nashi suna iya kaurewa,akan wanan zance,,
Duk da banji dadi ba yadda Umma ta zage tana wa yar uwar ta akan dan maganan da baikai ya kawo ba, don kawai ta yaba zance na, ta rufe ido tai mata tas tadai shige daki ta bar ta nan,

****** ********** ******
Alhamdullahi don komai ya kammala ancire albarkan gona gashi kuma Hamza ya kammala karatun shi lafiya yanzu yana zaune a gida suna jiran sakamako,
Wanan dalili yasa ya fara sana,a haikan wanda cikin yarda Allah sai abin nasa ya fara bunkasa, mai,
Sannu sannu ya fara shiga kauyuka ya na,sayo hatsi yana kawowa birni ya na,sayar wa,
Inda ni kuma ina dan buga bugana a gida ina samun dan abin rufin asiri ga yar sana,ata,
Dan maganin ciwon kai maleria, ulcer, pain relief da,sauran yan magani duk ana shigowa gurina sayen su, don haka na,rage wasu yan bukatuna,
Ganin yana samu akai akai, yasa mutane ganin ai Hamza ya dan samu ci gaba a irin kudin mutanen kauye,
Nidai tunda aka cire amfanin, gona bai min zancen kudin da ya karba a guri na ba balle nayi zance canza sabon fridge da nake son yi ba,
Haka yasani dan kokarin kukutawa gurin tara dan kudina don na,sai wani sbon fridge din don ina da niyan yin hakan,
Da kyat da taimakon Allah da mutanen arzikina na sayo sabon fridge dina LG mai saurin yin sayi da kuma kankara,
Aikuwa sayen wanan fridge din ya kara jawo min bakin jina sai umma take gani dan tane ya bani wanan kudin na,sayo fridge din,
Ranan da,nake kwana biyar da,sayen fridge din sana,an tawa naji Umma ta tutse dan ta yana ta mata rantsuwar kan cewa wallahi ba shine ya saya min ba asailima bai san da cewa zan sayi fridge shi,
Amma ina sam Umma bata yarda ba,sai cewa take gasu da lalurar auren Asmau a gaban su, amma shine zai kwashi kudi don tsoron bacin raina ya sayo min fridge dashi,
Idan bashi ya saya min ba wa nake dashi da zai sayo min wanan dalele fridge haka,
Ya marairai ce murya yana cewa wallahi Umma bani na saya mata ba ki yarda yadda kika gan shi nima haka nagan shi a gidan nan,
Amma sam Umma bata yarda da rantsuwar shi ba sai fada take zazaga mashi tace sai fa ya mayar ko ya,sayowa Asma,u abubuwan da ta bukata ya sayo wa yar ta mai shirin aure,
Don haka ita yanzu tunda ta fahinci cewa duk neman kudin shi a kaina yake karewa zata dauki mataki a kai,
Daga inda mama take tsaye tai min nuni da na kyale kada na tanka, don haka ma nai shigewa na daki kawai,
Can naji yafito yana cewa zata iya bincikawa taji in har shi yasaya min ta dauki matakin da tace din,
Nan ya shigo daki rai a bace ban kula shi naji har zai fita ya juyo yana ce min,
Humaira kina son ki hadani fada da mahaifiyata a gidan don ta kasa fahintar cewa bani ne nake saya maki wa yan nan abubuwan ba,
Duk da nasan cewa kokarin ki kike kina sayan abubuwan ki amma ya kamata ki san yadda kike abubuwan ki don gudun jefa zargi a zuciyar umma,
Mamakin zancen shine ya kamani a zuciyana kwarai da gaske, don ban san may ma zan ce mai ba sai binshi da kallon mamaki danayi a lokacin da yake fita daga dakin ,
Zuwa rana Zarah ta,shigo gidan inda tazo kamar yadda take zuwa kwana bibiyu don duba mahaifiyar ta da yan uwan ta,
Nan suka gaisa ina jin su harda mama wace tafito daga dakin ta don ranan bata fita ba tana gida,
Don yanzu har da,su turamayn zanuwa take dan daukowa ta sayar wa mata bashi ,
Nafito muka gaisa da zarah wace ke zaune saman kujera dan tsuguno tana shan raken da ta saya a hanya da zata zo,
Na juya zan tafi naji tana cewa Aisha ashe kin samu dauko fridge din dazun Karimay ta shigo take ce muna kin karasa biyan ta kudin har kin dauka,
Amma gaskiya kinyi kokari dan nai maki murna kinga shawaran dana baki yayi don ita karimay bata da matsala indai kana bata kudi ko kadan kadan ne sai ta tara ma har lokacinda ka gama,
Balle ke ta yaba kwarai da yadda kikai mata biyan kudin tace duk kika dan samu kike kai mata ko baida yawa,
Murmushi kawai nayi na wuce zuwa aikina, don nasan zata fadawa mahaifiyarta yadda na samu na sai fridge din da takewa wa bakin ciki duk kwanakin nan,
Aiko banko yi nisa ba naji Umma na cewa ta,saye ko aka sai mata ai duk na gane wayon yaran nan don sun mayar dani yar kauye wai nice zasuyiwa wayau ko,
Zarah tace haba Umma kamar yaya yanzu fa ta kai wata hudu tana kokarin sayen fridge din nan nice ma nasa yaya taiwa kaunar ta Karimay magana a gurin ta ta,saya,
Yanzu ke Umma hakan ba dadin ki bane yau ace sarakuwar ki matar dan ki tasai abin karuwa a gidan ku,
Wallahi baki ga yadda ake yabon ku ba kan wanan abin ,
Baki Umma ta tabe tana cewa, ke dallah matsa min can ke may kika sani ke ,
Ina zata samu kudin sayen wanan fridge in ba shi yabata ba ta,saye don sun raina wa mutane da hankali,
Yanzu in ba itaba ba mai cin abin yaron nan sai dai kagan ta tana yadda take so,
Ina duke na fara wanke tukunya,wani yaro ya shigo yana cewa ance a bani maganin ciwon kai dana ulcer,
Tace ummu jifa mai sanan chemist za ace wai ina ya samu kudi, haka ga karban haihuwa da take dan yi, don Alkah Umna kibar wanan zargin wallahi ita ce ta,sai abinta da kanta,
Umma dai bawai ta yarda da bayanin zarah bane sai ma fita zancen da tayi,
Da yamma sai ga mama Sa,a wai tashigo ganin fridge da taji ana na saye yana kankara ,
Tana gani suka koma daki da Umma sai abinda suka rage a gurin zagina da kuma dan ta
Wai inba aure ya kara ba Umma bazata taba gane kan dan taba don nariga na asirce mata shine, sai abinda nace,

****** ********* ******
Wani abokin shi yabashi shawaran yafara sana,an kai hatsin shi kurmi ya gani don akwai ci sosai,
Sana,an mahaifin shi ke nan shiga kasan kurmi dama don haka ya shawarci Umma
Da farko taso takiya mashi amma daga baya sai ta yarda ta barshi inda ya dan kara kulla jarin shi ya,saro kaya masu yawa ya fara zuwa lagos kai wa,
Sannu sannu tafiya tafa kyau dan idan zai dawo sai yadan sayo yan abubuwan da za,a samu karuwa dashi a nan arewa, ga kuma tsaraba da yakan dan sayo muna mu ma,
Ai kuwa take abin nashi ya fara bunkasa don ya kara bude idon shi sosai a harkan business din yanzu,
Shine Kano shine har kasar Niger yake zuwa dauko kaya yanzu,
Ya sai mashin irin na matasa idan yana gari ita yake hawa zuwa yawo ga suturu wanda ke nuna mutum yai lafiya,
Nidai saukina dashi shine yabarni ina yan sana,ata bai matsa min akan harkokina kamar yadda Umma takan so yai min,

Diyar mama sa,a data fito daga gidan mijinta takan yawan shigowa gidan mu idan Hamza yana gari da,safe ko da yamma,
Zatai wanka tashigo takan dan yi wasan kaunar miji dani wai ita kaunar Hamza ce itama,
Amna yanzu sai naga idan ta shigo zatai wani fuske min ko ina mata wasa irin yadda muka saba sai naji ta mayar min da mai zafi,
Mama Hafsi ce ta jiyo a gurin tallan ta cewa wai Hamza ne yake neman ta yanzu,
Ranan da mama take fada min na so na tayar da hankalina amma sau ta kwantar min da hankali da cewa,
Akan may zaki daga hankalinki haka Aisha bar su ai yanzu za,aji kan su akan wanan hadin da suke son yi,
Don Allah ba azzalumin kowa bane ba sunce wai sakin wawa bane basu san cewa sakin mai wayyo bane,
A gaskiya bayanin mama bai kwantar min da hankali ba don sai naga ai cin amana ne wanan,
Rasa wace za a aura mashi sai Sadiya wace tasan komai na gidan mu tasan ciki da baidin komai namu,
Gidan mamana Rahana naje da rana ina kuka ina fada mata abinda mama ta fada min,
Saida na gama fada mata sai naji tanisa tace amma kuwa Rabi ba mutumiyar arziki bace ashe,?
Yanzu ita sakaiyan da zata bimu dashi ke nan duk irin wanan halarcin da mukai mata,
Nace cikin kuka mama ni inda ma,watace ba wai Sadiya diyar mama Sa,a ba da suke kamar tip da taya da Umma,
Shiru mamana tayi tana kada kai tace duk abinda tayi ita da Allah ai don dai in bakici amanan su ba sai Allah ya fitar maki da amanan ki,
Don irin wanan aure ba,a kai ko ina yake watsewa saboda badon Allah akayi shi ba,
Yanzu abinda nake son ki da shi, shine ki kwantar da hankalin ki Aisha kada ki tayar da hankalinki,
Don kinga shi aure nufin Allah ne matar mutum kabarin sa,
Idan Allah yayi akwai aure a tsakanin su ba makawa sai sunyi shi don haka kada ki bari aji komai daga gurin ki,
Ki koma dakinki ki kwantar da hankalinki kici gaba dayin komai irin yadda kika saba,
Yanzu ya kamata ki kara zage damtsenki gurin kokarin kyautata mashi ke har ma da sauran jama,an gidan,
Kuma ai shi Hamza din bai nuna maki wani alaman cewa suna tare da ita yarinyar ba ko ya nuna maki hakan ne,?
Na hade miyau da kyat tare da girgiza kaina alaman a,a tace to kin gani idan ma hakane aiki barsu kawai mu ga iya gudun su,
Nace cikin sanyi murya da to mama insha Allahu zan yi yadda kikace din ,
Tace madallah yar albarka, hakanake so dake don kinga ba yadda zamuyi saboda shi dama namiji ne mijin mace hudu,
Dole ne a matsayinki na matar shi ta farko sai kinyi hakkuri da abubuwan rayuwa da dama don ke ce uwargida duk wani auren da zai kara ko diyar waye kece dai matar shi tafarko da kowa ya sani yakuma sanki dashi,,
Na dan kai wani lokaci a tare da mamana har kishiyar mama din ta gama girki takawo min amma sai na kasa cin koda cibi uku saboda damuwan da nake dashi,
Naima mamana sallama bayan takara kwantar min da hankali tare da min tuni cewa na dage da yin addu,a tare da sadaka don Allah ya bani rinjaye akan koma wace ce zata shigo min,
Tace duk safe na ambaci sunan Hamza da ita nace wallahu galibun Hamza da Sadiya sai na,shafa a fuska na,
Na kuma dage da fadan Subbahanallahi wallahamdullahi, Allahu akbar,,,

****** ********* ******
Ina zaune a bakin gado yana tsaye yafito wanka yasa tufafi a jikin shi yana fesa turare,
Sai binshi

Download complete TXT · Novel page