Showing 12001 words to 15000 words out of 299981 words

Chapter 5 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17619

cewa a gidan sune ma zata shiga abokan hiran shi suke matc a sheri haka,
Allah ya shirya ku yace yaci gaba da aikin shi don yasan ba,bari zasuyi ba,
Da,sallama ta shiga gidan Umma Rabi din tare da ganin tana shara duk da saura kadan amma,sai da Aisha ta karba ta kara mata ta kwashe ,
Ganin ba alamar Kubura a gidan yasa Aisha jan bakinta ta tsuke tai shiru abinta,
Tana gama zubar da shara daidai Umma tana fitowa daga daki take cewa Umma ni zan tafi,
A,a Aisha har zaki tafi ke nan ai ina ce zaki tsaya ne don yau ba karatu ai,
Tace aa Umma dama na shigone na gaida ke da wuni an aikeni ne sayar kalanzir nashigo nan,
Kai aiko na gode kwarai Allah yai maki albarka gashi harda shara na,samu anyi min ai nagode sam barka,
Shigar Aisha gida takecewa mama saude na fada mata tana tafe na samu tana taya Umma aikine,
Dadi sosai ya shiga ran mama saude ganin yar ta yanzu ta fara sanin ya kamata a rayuwa,
Sai dai gaban ta,sai faduwa yake don gudu kasa asirin karyan da tayi ya tonu,,

****** ********* ******
Dakin mahaifiyarta ta,shiga tanq kokarin cire hijjab a wuyan ta,sai dai idanuwanta suna a kan mahaifiyar nata,
Wace ayanzu tausayi take bata ganin irin yadda take wahala akan cikin dake a jikin ta a lokacin,
Sannu Ummi Aisha tacewa uwar tare da dan kashe da idanuwa a cikin tausayawa take cewa
Ko na shimfida maki tabarma a,waje zaifi iska acan din,
Ki barshi don nan din ma yayi ai inji Fatima dake cije bakinta don wahalan nauyin cikin dake a jikin ta,
Tace mama kije asibiti ma ko da sau daya ne don su dan baki magani su duba ki,
Aisha ke nan tace a cikin dan sake murmushi danawa zanje asibiti adubani,
Kedai bari Aallah da ya bani wanan cikin shi tasan yadda zaiyi dani insha Allah,
Gurin dan kantan da kayan ta,suke yarinyar ta nufa ita kam Fatima sai taci gaba da dan fitaran da ttake da mafefecin kaba daje a hannun ta,
Muryan uwar taji tana cewa halan baki samu Kubura a gidan Uwar Hamza ba,
Tadan juyo daga gurfanen datake tana tonon kayan ta tace a hankali bata gidan,
May kika fadawa uwar ta to tace nace tana tafe aiki take taya Umma din a gidan,
Yadaifi maki ga sherin Kubura don bake ba har ni uwar ki yau sai tai muna zari ina fama da kaina,
Kudine tafito dasu daga cikin kayan ta tazo gaban uwar tana kara gyara shirya su da kyau,
Da sauri take cewa ina kika fito da wanan kudi haka Aisha,?
Umma wallahi kudina ne danake tarawa dama nace idan kin haihu sai na baki ki yi hidimar suna dasu,
Kudin ki a ina kika samau su ka take tambayan diyar nata acikin tashin hankali,
Ummi kudin break fast dinane da Baba ke bamu bani kashewa ina tarawa sai kuma kudin da mama Rahana ta bani idan naje gashe ta,
Wanan kuma,wasu sabbin kudi masu dan yawa zasuka dari uku tace na barka da sallah nane na boye,
Murmushi uwar tasake tace haba Aisha may kike ci a makaranta idan kin tafi,
Mama idan munsha koko a gida sai sauran tuwon da ake gyara muna shi nake ci har na dawo gida,
Rai uwar ta bata taje cewa gaskiya ban yarda kina zama da yunwa ba haka,
Idan wani ciwo ya kamaki fa na yunwa ya kike son nayi gashi ban da kudi ni,
Wazai kaiki asibiti kindai san wanan Baban naku bazai damu da ciwon ki ba,
Murmushi Aisha tayi tanacewa insha Allahu mama zan dan dinga kashewa tana mikewa tsaye bayan ta hada kudin ta mikawa uwar nata take cewa,
Ai Ummi ban iya cin abinci a makaranta sai naga kamar kowa ni yake kallo idan ina ci,
Dariya ta sa uwar nata tace kai kedai Aisha bafillatan gaskiya ce wallahi,
Juyowa tayi tace wa uwar wai da gaske Ummi ni bafillata ce dama kamar yadda ake ce min din,
Take ran uwar ya baci ta tsuke fuska da sauri Aisha ta juya don ita ma zance subul da baka yazo mata,
Kiyi hakkuri don Allah Ummi idan na bata maki rai ne bazan sake ba,
Yusuf dan Fatima na farko shine ya,shigo dakin da,sallama jikin shi yana saye da kayan aikin kanikawan da yakeyi,
Idanuwan shi a kan kudin da suke aje a gaban mahaifiyar tasu yace Ummi wanan kudin fa haka ?
Kai ko gaisuwa baka iya ba har yanzu babangida kasancewa sunan mahaifin mijin su ke ga yaron,
Ummi ya jiki yace cikin dan zaunawa daga gefen ta yana kokarin ciro dan kunshin naman da ya sayo mata da kudin da,aka,sallamay shi a gurin aiki na yinin ranan,
Ta karba tare da,sawa dan nata albarka inda tai masu jam,in gaba dayan su da kuma sauran diyan musulmai baki daya kamar yadda sunna ya koyar akan kyakyawan adduan don ta karbu da sauri a gurin Allah,
Tana kokarin bude takardan naman ne take cewa yar uwar kace tabani su yanzu wai naje asibiti gobe a dubani don wahalan yai min yawa,
Inda Aisha take tana mayar da kayan ta ga jakar ta,
Ina ta samay su haka ita kuma ?
Fatima tacee nima ai tambayan da nai mata ke nan yanzu haka,
Sai uwar take fada mai bayanin da Aisha din tai mata akan kudin,
Kudin yaron ya kara dubawa yake cewa ai wanan basu isheki ba bari na,dauko wanda nake tarawa nasayi keke dashi,
A,a Babangida kabar shi kawai naje da,wanan din ai zai isheni sayan kati, dashi,
Shima gurin kayan shi ya nufa ya ciro nashi kudin ya kirga ya mika mata ta raba kudin biyu
Ta mayar mai da,saura tana mai sawa yaran albarka ,
Tace wa Aisha ta miko mata plate tasawa kishiyoyin ta dan naman da,yaron ya sayo mata taci,
Haba mama dan wanan abin shine zaki raba ke may zakici a ciki abinda baida yawa,
Bari dai na basu ai suma suna bamu idan sun samu,
Haka al,adan gidan nasu yake duk wanda yadan samu abu komai zaman shi kasan sai yabawa sauran abokan zama sun sa albarka su ma,
Hakane yaje dan kara kawo masu zaman lafiya a gidan don suna kokari ganin sun danne kishin su,
Daga waje aka daga labulen dakin maigidan ne a tsaye yana,saye da wando sai babban riga da ya aza a sama kawai babu yar ciki,
Lokaci daya ya kare masu kallon yana mamakin irin yadda ko yaushe take zama da diyan ta kamar abokan ta ,
Ya kika kara jin jikin naki ?
Ya tambaye ta a cikin yanayin son kulawa gare ta ,
Ta amsa a cikin dan matse fuska iri yadda mace maiciki idan tana da kishiya take amsawa,
Daga gurin da Aisha take, zaune gefen uwar take cewa Baba sannu da,dawowa,
A,dakile ya ansa mata batare da,wani sakin fuska ba ,
Daga gefe Yusuf ke ce mai Baba sannu da,dawowa,
A,a Babangida andawo yaya shagon naku ba matsalan komai ko ?
Yaron yadan gyara,yana cewa ba komai Baba kuma,muna,samun aiki sosai a gurin,
Tau ka,dai mayar da hankali ga,aikin ka,don ka,samu ka iya,abinda ya kai ka,
Yana kokarin sake labulen dakin ne Fatima ke cewa malam,
Gobe idan Allah ya kaimu ina son zuwa asibiti awo ,
Awo Fati gaskiya ban da kudin zuwa asibiti don kinga yanzu ba,wani Kasuwa sosai karfin hali kawai nake ina maneji,
Kabar kudin ka izzinin ka kawai nake nema ni,
Yace Allah ya kaimu gobe lafiya yajuya yafita daga dakin ,
Summa suka bishi da kallo kowa da irin abinda yake kiyastawa a ran shi daga,cikin su,,,

****** ********* ******
A cikin wata irin kasalaliyar murya mai nuna yanayin shi ya canza yake magana a lookacin,
Haba baby ki bari mu dan kara time mana tun yanzu zaki ce zaki wuce gida ni da na zaci cewa zamuyi till down ne a gurin party,
Cikin bude baki a cikin sauri take cewa Haba sweetie na baka son na kara fitowa ne yau din ma fa,dabara nayi a gida don ba,ranan zuwa islamiya bane,
Badon yaso ba yaja motan zuwa wani shago inda yai mata sayayyan abubuwan tabaa alashe ,
A hankali yake jan motan kamar wanda nai son yin tuki,
Hannun shi guda ya mika zuwa jikin ta inda ya dan fara shafan ta
Da sauri ta dago kai tana cewa haba sweetie kabari mana don Allah kaga kana tuki ne fa,
Au to na tsayar da tukin ke nan ko ya ce a cikin wata irin murya irin na mayaudaran maza,
Ganin yana son yai galaba a kanta yasa Kubura sauri dan ture shi daga jikin ta tana cewa haba dear ban son haka gaskiya kaga wani yana iya ganin mu a hakan a fadawa mahaifana,
Fushi yayi yanu baiji dadin hakan ba da tai mashi,
Har suka kawo gurin da ya,dauke ta ya tsayar da motar a gurin,
Sai a lokacin ya furzar da iskan takaici daga bakin shi yace a kasalance sai yaushe kuma ke nan baby na, ?
Tace a lokacin da take kokarin bude motar ta,sako kafan ta daya daga waje,
Tace sai wani lokacin tamikaa,hannun ta tajawo hijjab din ta daga bayann motan shi ta zumbula abinta kamar wata ustaziya,
Tajuyo inda yake zaune yana akallon ta acikin wani yanayi tace zan tafi sai mun kara haduwa kuma,
Nan ta bude motar tafita zuciyar ta fes dashi don ta hada abubuwa da dama,
Ta samu saurayi kamar mansur gashi kuma sunje gun fati ,sun cashe kamar yadda take so, gakuma kayan kwadai da,ak,siya mata,

A daidai shiga daga cikin gida suka hade da mahaifinta wanda yabita da kallo yana cewa Gwagona sai yanzu akadawo ne ko,
Murmushi tayi daga can ta,cikin gida muryan mahaifiyarta ce ke cewa ai na tura Aishi ta,kirata tadawo tana cewa ai tasamu tana that's
Uwar Hamza aiki shiyasa bata,dawo ba tun dazun,
Sosai yaji dadi hakan inda yake saka mata albarka ta,shige ciki simi simi da ita,
Bayan tashiga mahaifiyar ta take tambayan ta mutanen gidaan take cewa duk suna lafiya,
Tafaki idon uwar nata ta kwabe kayan jikinta don gudun kada tafahinci irin kaya da ta, fita dasu
Shi,
Hamza wanda yake zaune daga shagon shi ya hango dawowan Kubura a lokacin,
Cikin mamakin inda tafito a wanan lokacin da daren nan haka,
Bayan yan mintina ya aika kiranta sai ta aiko mashi da cewa a gajiye take bazata fito ba,
Sam ya rasa may yasa Kuburan ta canza mai yanzu don kwata kwata, bata da lokacin shi,
Abu gudane idan ya aika mata da abin makulasa zata karba ta lashe ko kuma idan tana son wani abin kwadayi zata iya aiko mashi, da bukatun ta,
Abin ya fara damun shi a,rayuwa saboda ya fara dan tuhumar ta,don ganin iri sauyin rayuwan dake tare da ita,
Saboda ta waye irin wayen da baza,a ce diyar gidan malam mudi bace ita,
Shidai yasan ada can baya bata da wani suturu irin haka amma yanzu ta zama wata yar gayu gaba daya,
Gashi ta nuna a fili cewa ita yanzu tafi karffn shi don bata da lokacin shi samm,
Ya tunkari Umma Rabi da zancen abinda ke damun shi a rai indz take cewa ita ma ta gane wanan sauyi ga KUBURA din,
Uwar shi tafi kowa bukatan akan aiyi wanan hadin tsakanin yan gidan mala.
Don haka ta,samu mahaifan Hamza ta turasu zuwa zancen don a,tsayar masu da,matsaya,
Kamar yadda malam Mudi yayi alkawari hakan akayi don anyi baiko a tsakkanim su kowa ya sheda cewa Kubura ta a matsayin kamay Hamza ne a garri,,
Wanan baikon shi ya tayarwa Kubura da hankali sosai inda har ta kasa boye bacin ranta ta ,soma nunawa a fili wai bata son Hamza yanzu,
A gareta abin kunyane a ce kamarr ta wai zata auri Hamza dan gidan tallakawa talas,
Marasa galihu agari da gurin dagi tallakawa masu neman abinda zasu ci wa ran su a rana,
Ganin tanuna bata so ita kuma mama Saude yanzu irin abin duniya da yar nata ke shigo dasu gida yafara bude mata idanuwan ta,
Don haka tafara goyawa yar ta baya akan bata son wanan hadin itama don yanzu Kubura ba matar Hamza bace,
Kubar ba matar tallaka bace kalman da mama saude take yawan fada ke nan a tsakar gida a gaban su Fatima da Atika kishiyoyin ta,
Shiko malam Mudi ya dage akan cewa sai anyi wanan auren ko basu so
Don shi haka kawai Allah ya,dora mai son wanan yaron Hamza a ranshi don irin kwazon shi,,,



Don Allah muyi hakkuri da,wanan ba yawa sai mun hadu a na gaba da fatan za,a rike min amanata kamar kullu na gode da taimakon ku a gareni,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU👑SARAUTAR MATA👑
0⃣5⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

RABBIG GAFIRLI WAL WALIDAYYA WAHARHAMHU KAMA RABBA YANIY SAGEERAH 👏👏


Tun daqon Ummin ta daga asibiti hankalin Aisha yake a tashe don jin irin bayanin da Fatima take wa maigidan ta,
Akan cewa da likita yayi wai sai tayi scanning a cikin don tantance lafitan baby saboda suna ganin kamar a gilmay cikin yake mata,
Don inhar tunanen su gaskiya ne to bazata iya haihuwa da kanta ba kenan sai sun mata aiki,
Gaba daya yarinyar duk da karancin shekarunta ta,fahinci may hakan yake nufi ga zancen,
Sulale jiki tayi daga gidan zuwa gidan mama Rahana yar maahaifiyar nata, tafiya take a cikin tashin hankali bata ko ganin gaban ta,
Ta isa gidan acikin tashin hankali don Mama Rahana tana ganin ta take cewa lafiya dai nagan ki a haka kuka ?
Dakin ta tafada tazube a kasa gefen kujera ta fara rusa kuka a hankali,
Abinda yai matukar tayarwa mama Rahana da hankali ke nan,
Acikin dan daga murya take cewa ki daina wanan kukan ki fada min may ke faruwa ne wai ?
Ki natsu kifada min kukan may kike haka wai,
Aisha bata boye mata komai ba take fada mata irin abin da taji Ummin ta tana fadawa maigidan ta akan zancen cikin dake a jikin ta,,
Shiru Mama Rahana tayi, inda ta dago kai tana kallon Aishan acikin tausayawa,,
Tace cikin sanyi murya tauki daina wanan kukan haka don idan har kin tayar da hankalin ki Ummin ki zata kara shiga tashin hankali ne sosai,
Don kinga kowa da irin tashi kaddaran rayuwa, wanan ba,wani zancen tayar da hankali bane don su likitocin ai sun san irin dabara da zasuyi mata,
Kuma ta haife shi lafiya da yardan Allah don haka maza ki share hawayen ki ki shiga yi mata addua, Allah ya sauke ta lafiya,
A hankali taji sanyin maganan da mama Rahana tai mata don haka tafara dan share hawayen dake a fuskan ta da habar hijab din ta,
Nan mama Rahana tashiga kwantarwa da Aisha hankali da kawo mata yan musalai daidai fahintar ta,
Batai wani dadewa ba tai sallama da mama Rahana inda mama Rahanan take ce mata zata shigo gidan taji yadda za,ayi zancen zuwa asibitin,

****** ********** ******
Daida shiga gidajen su ta hango Hamza dake dawowa daga gona yana dauke da buhu da wasu, yan kayayyaki,
Da sauri ta nufi gurinshi ta karbi dan kullin buhun dake a hannun shi,
Duk da kokarin hana yarinyar da yayi amma,sai daa ta karba
Tana shiga gidan ta samu Umma Rabi tana wanke wanken kwanonin abincin su ,
Sallaman ta yasa Umma Rabi din saurin dago kanta tana kallon Aisha din,
A,a kece ?
Karaso mana
Kofan dakin Umma Rabi tanufa ta aje buhun dake a hannun nata,
Taso ta karbi aikin amma,sai taga cewa har ta karasa din saura kadan shi kuma take daurayewa,
Ta gaida Umma din ta juya ta fita a kofan shigowa suka hade da HAMZA yana kokarin aje yar keken shi a gefen ginan daki,
Yace tau Ai na gode kin ji da ki tsaya na baki akwai sauran rake yana nan a,daki,
Cikin murmushi wanda yadan sa dimple din ta dan lotsawa kadan tace haba kabar shi kawai na gode bata tsaya ba tafita ta nufi gidan su,

Shigowan ta gida yai daidai da Uwar nata ta,dan fito waje, tun a kofa ta kafe yarinyar da idanuwa don son fahintar wani abu daga idanuwan ta,,
Hawaye ne suka kara ciko mata a idanuwan ta Fatima ta kawar da kanta tankar bata gan ta ba,
Ina kika shige ne haka wai Aisha ?
Idanun yarinyar taga sunyi dan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login