Showing 15001 words to 18000 words out of 299981 words

Chapter 6 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17635

hulu hulu alamar kuka da tayi sun baiyyana a fuskan ta kadan,
ina kika shiga nace hakan,
A hankali tace gidan mama Rahana na tafi amma ban dade ba acan,
Ki shiga ki dauko abincin ki a daki kici kada yai sanyi da yawa ,
Har zata shiga dakin take cewa Mama tace tana tafe dan anjima,

****** ********* ******
Yana fitowa daga daki dauke da yar ledar gyada soyayya a hannun shi don ya bata sai yaga bata gurin ta tafi ko,
Umma tace ai ta tafi bazata karba ba indai Ai ce narasa gane irin rayuwar yarinyar nan don bata da sabo,
Hamza dake kokarin zamma a kasa cikin turbanya yace rayuwan ta daban ne dana,sauran yaran gidan duk da kuwa a cikin su ta tashi amma sam bata irin halaiyan yaran,
Dan jingina jikin shi yayi da,bango yayin da,Umma tazo ta shige ta gaban shi zuwa cikin dakin ta,
Tafito dauke da kwanon abinci wanda ta dafa masu shimkafa da wake da mai da yaji, acikin sa,
Tace a lokacin da take zama, daga kofan ta, ai ni ina,son hali irin na,yaro wandda yasan darajan kashi tun yana katami ammaa kaga ita,ta gurin nan naka sai munyi daga da ita sosai a gidan nan,
Murmushi yayi don jin dadin furucin ta a akan cewa KUBURA ta gurin shi ce,
Umma ai duk yanzu kurciya ne bari zatayi nan gaba ai,
Uhummm Allah dai ya kyauta dan nan amma gaskiya babana yarinyar nan al,amarin ta ya fara bani tsoro,
Hamza yadan lumshe idanuwan shi a hankali tare tare da dan tunanen wasu abubuwa a,ranshi,
Mama Rahana kamar yadda tai alkawari ta shigon gurin yar uwar nata don ji daga,bakin ta,
Cikin daga hankali Fatima take bawa yar uwar ta bayanin da likita yai mata a kan cikin ta da take dauke dashi wanda,ake zargin ya,samu matsala,
Mama Rahana tace Allah ya sauwa ka yanzu ki kwantar da hankalinki sai muje wani asibitin muji may zasu ce a akkai,,
Don haka ki kwantar da hankali kin ga hankalin Aisha duk a tashe yake tana zaton wani abu,
Ta amsa a hanakali da cewa tau, yaya insha Allah zan bar komai a gurin Allah tace dadai yafi maki,

****** ********* ******
Zaune KUBURA take a saman gadon mahaifiyar ta tana karatun wanni littafin hausa mai sunna wayasan gobe wallafan wata shahararra marubuciyar littafin hausa SAFIYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA,
Yar gurin Atika ce ta shigo dakin tana cewa Kubura Hamza yana waje wai na kiraki,
Tadago kai fuska a,yatsune take cewa yana ina ?
Yarinyar ta amsa mata da cewa yana daga kofan gidan nan,
Jeki ce mai ban samun fitowa tace, cikin jan yar guntuwar tsoki,,
Yarinyar ta juya ta,fita jim kadan sai gata ta,dawo tace wai yace nace kizo don Allah sako ne zai baki kawai,
Ai sai tai wani hargago yarinyar da wani irin daga murya inda tai wuf ta,fice daga dakin,
A zaure suka hadu da malam Mudi yake cewa kin fada mata yaron yana waje, ko,
Yarinyar ta take mayar mai da cewa, ai takoreni da ihu wai na bata guri na bace mata da gani,
A harzuke ya shiga cikin gidan tare da kwadawa Kubura kira cikin tashin hankkali,
Ita ma din dai a gigice ta fito daga dakin tana cewa na,am Baba,
Ba,a fada maki cewa yaron nan Hamza yana kofa yana jiran ki ba,,
Ciciki ta amsa da an fada min Malam Mudi ya ce to sai kika shanya shiko,
Shiru tayi yace zaki wuce ki fata, tun ranki bai baci ba yanzu,
Daki ta koma inda ta saka kuka wai ita bazata fita ba gurin Hamza din,
Mama Saude wace shigowan ta ke nan daga bandaki, ta soma cewa ke may yafarune wai may akai maki,
Tace ba Baba bane yake son takura min cewa wai sai na tafi gurin Hamza a waje,
Ni wallahi mama banyin wanan hadin da Baba ke son yi min nidai na fadi wallahi bazan yi ba
Bari na fita na gayawa Hamza din daga yau kadda ya kara zuwa gurina da sunan wai yana sona,
Haka ta saka hijjab din ta zuwa gurin da Hamza din yake zaune saman dan dakalin da ke kofan gidan,
Hamza yana zaune yana dan bubuga kafan shi a kasa a hankali saboda irin yadda yake dan ji a ranshi,
Tafito fuuu da ita tana cewa kai wake ne ma Hamza ne ko wa,
Da maki yadago kai yana kallon ta don jin abinda tace mai,
Yadan murmusa tare da dan dago kan shi ya dan kalleta yace tau fa yau kuma sunana ma baki sani ba Kubura,
Hamza din dai nake ba wani ba
Ranki shi dade barka da fitowa
Tana tsaye kerere a gaban sa tace ai ba fitowan arziki nayi ba tace a zuci,
Idan da sabo yaci a ce hamza din ya saba i yanzu don haka din yanzu shine halaiyar ta gare shi,
Sam bata kallon shi da dara bata nuna mai wani almar kauna ko kadan,
Sam duk wanan abin da takeyi sai ya dan saka Hamza dan murmushi,
Don yasan cewa dama can a rashin ji ta tashi daga kurciyar ta,
Don haka yasan cewa wanan irin halaiyar nata idan sunyi aure duk daina su zata yi,
Don haka hankalin shi a kwance yake don ya riga da ya nasa a ranshi cewa zai mata, tarbiya irin wanda shima mahaifiyar shi tai masu,
Fuska a daure tace malam nazone naji lafiyan kirana da kakeyi wai,
Yace ba ko gaisuwa Khadija, tace gaisuwa a nawa za,a yita ,?
Hmmm Khadija da ki gaishe ni da kada ki gaisheni duk daya a gareni ,
Don watarana muna tare dake a daki daya don haka kinga bazan damu da gaisuwan a yanzu ba,
Ta dago idanuwanta ta re da kara tabe fuskanta ta dube shi tace cikin wata murya ,
Au dama kazo ne ka karanta min wanan,
Idan har wanan ya kawo ka zan koma daga ciki don ina da abinyi aciki,
Mikewa yayi daga gurin da yake a zaune da farko yace dama zuwa nayi naga lafiyar amarya ta kawai kuma na gani tunda kina lafiya Alhamdullahi zaki iya shigewa, ai,
Ta dan gyara tsayuwar ta tace kana so yin wasa dani Hamza,
To tsaya kaji idan ma har mafarki kake to ka farka don ni,
Nafi karfin dan talkawa irin ka,wallahi kaje can ka,nemi daidai da kai zaifi maka alheri,
Don idan har kai rigimar kai kan ka idan ba kaiba ka zata kwabewa,
Don ni KUBURA nafi karfi dan tallaka iri ka don tsayawa dakai a,gareni barnan suna ne sosai,
So dan Allah malam daga yau ka da ka kara zuwa kofan gidan nan da sunan wai kazo gurina,
Dubeka kalle ni kasan ai sawun rakumi yafi karfin na yaro
Gyara tsayuwar shi yayi dakayau ya,dan tako kadan yana cewa
Koma dai mai zaki fada don ni nasan cewa duk zaki daina ne wata ran,
Dan harara ta,watsa mai tana cewa dubeka ji wai a hakan kake nufin cewa na aure ka din,
Kai kan ka,ka,dubeni sama da kasa kasan nafi karfin ka wallahi,
Idan zaka tafi naiman daidai dakai tallaka irin ka tun dare bai maka ba zai fi maka alheri,,
Tankar a mafarki yau Hamza ke jin irin wanan mugun kalaman daga yarinyar da ya,dade ya reno da dan taro da,sisi shi,
Ya murmusa tare da dan tokare habar shi da hannayen shi yace Kubura ki iya bakin ki da zaifi maki alheri ina gani,
Ta ja,wani dogon tsuki tare da kara watsa mai harara tana cewa idan ban iya ba ai sai kai ka iya ko,
Daga haka ta juya ta,shige warta cikin gida inda ta barshi nan inda yake a tsaye har nawani dan lokaci yana mamakin irin fitsaran Kubura,
Wanda bai taba tsanmanin cewa har abin yakai haka ba a rayuwan ta,
Mamaki ya hanashi ko da dagawa nan da can wai yau Kuburace take fada mai magana irin haka,
Sam ta ma manta da irin mutunci da zumuncin dake tsakanin gidajen su biyun,
Sannu a hankali jiki ba karfi ya juya zuwa bakin shagon sa bai wani dadeba a ranan ya kwashe kayan shi zuwa cikin gida,
Bai iya,fadawa Umma wanan labarin va don sanin da yayi bazata iya hakkurewa wanan cin mutuncin da Kubura tai mashi yau,
,A dakin shi ma yana kwance muryan ta ne ke mashi yawo a kunnuwan shi yana mamakin yadda ta rufe idanuwanta tai mai wanan cin mutunci,

****** ********** ******
Likita,yayi mata duk wani awo da zaiyi don ya fahinci kan cikin,
Bayan ya gwaje gwajen da likita yai matane ya rubuta result din duban ya masu bayani cewa zasu dan bata magani amma sai bayan sati biyu zata dawo yagani,
Idan still abinyana on briged dole hakkuri zakiyi muyi mamaki tiyata, mu fitar da dan,
Sun dawo gida inda sun samu Aisha ta,gyara ko ina na dakin ta,saka ka kamahi,
Ga abincin su data, aje masu ta sai ruwa masu sanyi da ta kawo masu,
Ganin Aisha a,daki ya hana su yin zance don kara ta kara tayar da Ahankalinta irin na farko,




Ba yawa yau muyi maneji da shi haka please nagode


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
👑SARAUTAR MATA👑
0⃣6⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

RABBI INNI, LI MA ANZALTA ILAYYA MIN KHAIYRIN FAQIR,,,,👏👏


Asalamu Alaikum yan uwa musulmai, ina son in kara maku tuni akan cewa duk wace bata biya ba don Allah kada ta katanta don gudun shiga hakkin wasu,
Wanan littafin Amana ce a tsakani na da wanda ya,biya ya shiga group,
Duk wanda ke acikin group na hada shi da darajan Allah da Annabi kada maishi ya fitar min da novel ga out siders, don darajan Annabin rahama,
Don haka wace duk tasan darajan Allah da Annabi idan har bata biya ba kada ta karanta wanan novel don Amana ce mai karafi, akai,, karshe dai kenan ba a yafe ma wace tafitar ba haka kuma ba a yafewa wanda ke turawa ba, har yakai ga wanda bai biya hakki ba,,,


Tun Faruwan wanan al,amarin Hamza ya dauke kafan shi daga zuwa gurin Kubura da sunan hira,
Sai dai hakan bai hana shi aika masu da alherin da ya,saba aika masu a koda yaushe ,
Yanzu lokacin aikin gona ne hankan yasa shi kara mayar da hankalin shi zuwa gonan shi ,
Wanda yai sanadiya mutane basu fahinci irin halin da Hamza da Kubura suke ciki ba,
Abu guda ne ke ci mashi rayuwa wanda ya kasa fitar da zancen a ranshi,
Da Kubura take ce mai wai shi dan matsiyata yan tara tara masu jiran na rabbana su saka a,bakin su,,,
Idan ya tuna yakan dan lumshe idanuwan shi yace Allah ka,bamu karka bashe mu ya Allah,
Aike sosai Hamza kewa Kubura kuma tana karbe abinta,
Idan ma bai kai ba mahaifiyar ta ce ke aikowa da kanta cewa suna bukatan abu kaza,
Wasu lokuta Atika ta kan so suyi gulma da Fatima akan abinda ke gudana a gidan,
Amma sai Fatima ta jayewa zance badon komai ba sai ganin cewa Uwargidan tasu bata bar su da komai ba a gurin kyautatawan rayuwan zaman takewan su a tare,
Shi kan shi mai gidan bai zama a gari anytime yana zuwa gona ko gurin wasu tsabgogin shi hakan yasa bai fahinci da akwai matsala a tsakanin su ba,

****** ********* ******
Alhamdullahi yanzu jikin Ummi yayi kyau sosai ta samu lafiya, don ta,watsake daga irin ramar da tayi a baya,
Duk da akwai abinci a gidan malam Mudi din amma tana,bukatan irin wanda zai gina mata jikine sosai,
Don haka Yusuf danta ya dage gurin dan sayo mata dan lemo kankana ayaba da,kwai ko ba yawa yakan dan sayo mata,subata a boye taci,
Inda ita kuma Aisha take bata kyakyawan kulawa yadda ya dace,
Da yake yanzu anyi hutu hakan yasa bata aikin komai sai Aisha din ce mai yin aiyukan uwar tasu,
Yau ma kamar kullun daga inda Fatima take zaune take kallon yadda kayan su ya taru suna bukatan wanki,
Daga gurin takira,Aisha wace ke waje suna aikin girki da mama Saude,
Ta shigo dakin don jin bukatar uwar nata, tace cikin dan murda baki, ki daga pillow din can akwai ashiri a cikin shi ki sayo omo ki dan wanke min wanan tsumakaran da nake daurawa ,
Aisha ta nufi guri, pillow sai dai ba taga komai ba a gurin duk iya duban ta babu komai a gurin,
Ummi ban gashi ba fa Aisha ce ke fadawa uwar tasu haka a lokacin da ta duba ko ina bata gan sh ba a gurin pillow,
Ajiyan zuciya uwar tayi tana cewa bari Nasir ya dawo don shi ya,tafi gurin wai yana neman karfen keken shi,
Aisha ta juya zuwa waje tabar uwar a zaune a inda ta samay ta da farkon shigowar ta,
Hijjab din ta,dake a saman window din dakin su taja zuwa kofar gida,
Zuciyar ta fam da tunane yadda zatayi indan ta fita, har ta fara tunanen ta juya kawai don bata ga alaman mutum a,ahagon ba ma,
Sai tajiya a yan mata lafita,dai ko ? Kinzo kuma zaki koma mana,
Dan murmushi ta kakaro a fuskanta tana cewa a,a dama nazo kuma dai a barshi kawai,
May kike so ya tambaya in a serious voice ?
Bata san lokacin da tace omo zanyi wanki ne idan Yusuf ya dawo zan karbo kudin na kawo ma tafada idanuwan ta a kasa,
Batare da yai magana ba ya juya zuwa cikin shagon omo sabulun wanki sabulun wanka har da man shafi kaman yasa mansu ya kare Baba kuma bai sayo ba tukun,
Ya miko mata yana cewa kice wa Ummi abar kudin baku nayi tasaka min albarka,
Cikin yar murya tace mun gode yaya Hamza kalman da tai mashi dadi ke nan a,rai don ko kannen shi basu kiran shi da yaya,
Ko da ta,shiga gida ta samu Ummi tayi barci a lokacin don haka,sai kawai takwashi kayan wankin zuwa bakin rijiya ta,soma wanki abinta,
Sai zuwa gab da ta karasa wankin ne Ummi ta farka daga barcin da ta,samu tayi,
Inda ta hagon kayan ta a,shanye ko ina na gidan cikin mamaki take kallon aikin yar nata,
Shigowan Aisha dakin don aje wasu kayan da suka fara bushewa take tambayan ta ida ta samo omon da tai wanki dashi,
Aisha bata boye mata komai inda a take Ummi tai cikin ta da, fada kancewa ta rufa mata asiri kada Kubura da uwar ta suji suce ai ba yau suka fara zuwa karban abu a gurin shi ba
Hakkuri Aishsn tabawa uwar ta akan cewa bazata karaba insha Allahu,

****** ********** ******
KUBURA yanzu sai abinda yai gaba sosai don idanuwan ta ya kara budewa,sosai,
Ta murje tayi wani irin kyau da ita,saboda duk masu zuwa gurin ta suna da dan abin hannun su,
Kamar yadda take bukatan ganin rayuwan ta zaka ganta tana ciye ciye da taune taunen chewing gun, a bakinta,
Yau ma sallama ake da Kubura din a kofan gida inda yaron da yazo yake cewa wani mai mota yace a sallamo mai Kubura,
Dama tana daki tana sauraren kida a,dan wani rediyon ta tadan gyara fuskan ta tafito zuwa gun da ake ne manta a,wajen,
Munsur ne yadawo daga gurin tafiyan da ya tafi kwatano gurin sayen motoci,
Tana fitowa Hamza yana a bakin shagon shi tare da abokan hiran shi, idanuwan su fam a kofan gidan,
Zaune mansur din yake kafan shi daya yana daga waje yana duban wasu takardu a cikin motar,
Tun daga nesa ta,washe masa baki bata damu da duk wani wanda yake a gurin ba don yanzu ta bushe fitillan ta akan bata son Hamza din,
Mansur yafito daga cikin mota shima yana washe baki saboda farin cikin ganin masoyiyar tashi,
Yana cewa, Khadijatul Kubura my baby kinko ga yadda nai missing din ki kuwa ?
Wani murmushi tayi tana dan gyara gyalen da ta yafa a kanta,
Cikin yar siririyar murya take mashi sannu da zuwa tare sa wani yi mai far da idanuwan ta,
Yace mata ya take tana lafiya dai ko,?
Tace kallau acikin wani tsigar jan hankalin maza cikin kashe murya take cewa ka tafi ka barni zakace wai ina lafiya ?
Murmushi Mansur din yayi yana,mai ce mata ashe tare zamu dinga zuwa ke nan next ta wani zaro idanuwan ta tana cewa wace ni
Yace oright kina ce ina wasa ne ko,
Yanzu dai ga tsaraban ki nan nakawo maki sai ki samu yara su shiga maki dasu gida,
Ledoji ne farare manya guda uku abarba lemo Apple da,sauran su irin tsaraban yan kurmi,
Daga inda su Hamza suke a tsaye suna kallon su

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login