Showing 165001 words to 168000 words out of 299981 words

Chapter 56 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17615

yaji nama sai dafa duka yaji kayan hadi cikin sa, sai kamshi ke tashi ga ruwan masu sanyi,
Ranan Umma ta saka sabin tufafi ajikin ta sai faman washe baki take tana murna da farin ciki, wai
Dan ta ya samu sakin wawa ko haihuwa bata tabayi ba gidan da ta fito ya aura,
Wata abokiyar wasan su ta gurin Uba take cewa, sakin wawa ko dai sakin mai wayo amarya haka tsatsaye da ita shine har za a ce wai sakin wawa,,
Sakin mai wayo dai,,
Nan dai su kai ta shammatan junan su muna daga dakina muna sauraren su,
Sai yamma lis aka watse yan yinin buki sai mu yan gida aka bari,kawai a gidan
Rabon Hamza da gidan tun da safe da yai wanka yafita bai shigo ba duk taron nan da akayi a gidan,
Idan antambaya ina angon Umma ce mai bada amsa tace yana can tare da abokan shi sun taron buki,
Duk taron da ake raina a bace yake watau idan badon Allah ya,rufa min asiri ba da sai dai yau naji kunyan da zanji amma shi babu ruwan shi da damuwa ta,
Ina daga kofa naiwa su mama Rahana rakiya saboda tace ba, zata tsaya har a kawo amarya ba,
A kofa ya samay mu tsaye da mamana tana kara bani hakkuri tare da kwantar min da hankali,
Yashigo gidan da sallaman shi fuskan shi dauke da murmushi a sake ya tsaya yana gaida mamana Rahana,
Kai da ganin sa kin sa bai cikin damuwa ko kadan sha sa,wasu sabbin shadda dinkin babban riga a jikin shi mai ruwan milk ban san lokacin daya dinka su ba kuma ban san a ina ya saka su a jikin shi ba,
Mama tana ganin sa itama a cikin fara,a ta gaida shi tare da mashi ya taron jama,a take ce mai sai yai ta hakkuri da kuma adalci yake cewa ba matsala insha Allahu,
Da kyat na iya bude bakina daga inda nake tsaye nai mashi sannu da zuwa,
Ya amsa min da cewa yyawa ya taro sai a lokacin na dan ga kiban da Hamza ya kara ,
Mama tai min sai anjima alokacin shi har ya fara tafiya zuwa cikin gida, ko,
A daidai kofan Umma suke tsaye dashi da Zarah daganin su wani maganan siri suke a tsakanin su,
Suna ganin zan shiga dakina sai naga duk sun juyo suna kallo na,
Zan shiga daki naji zarah tana cewa Aisha zo nan dan Allah sai da nai dan jimm sai kuma na juyo zuwa inda suke tsaye,
Wa8 idan ankawo amarya ba ana bada tukwaici ba tambayan da zarah ta jefoni dashi ke nan ina isa gurin su,
Eh kawai na iya ce mata saboda da takaici to ni bazan bayar ba na fada maki zara komai tun da akafara bukin nan cikin kawo dai kawo dai ake min da may zanji ne please,
Nikan ina fadin haka naja kafafuna na koma dakina inda na samu wasu abokan karatuna su biyu da sukazo min kara sun zauna har a kawo amarya sai su wuce,
Sai dai gaskiya maganan da Zarah ta tambayeni yai min ciwo sosai don rainin hankali nice ma za,a tambaya zancen kawo amarya,
Banda yadda zan yi kada kawaye na su gane dole sai hakkuri nayi don haka Allah ya nufe ni da gani,,

****** ********** ******
Maggariban farko muka ji gudan yan kawo amarya, sai yaran unguwa suka dauki ihu da shewa suna fadi ayyuriri amarya kekikace kina so dabakice kina soba da ba,a baki shi ba,
Mairabo mairabo , mairabo ya samu mara rabo yana can ya manne da bango,
Innalillahi wa inna alaihim raj,un nake fadi a bakina sai kuma,
La illah ha illah anta subbahanaka ini kuntun minal zalimin,
Wallahu galibun ala amarrihi Hamza, Sadiya Umma Rabi,
Sai ga anty Hindatu sun dawo kamar an jefo su daga sama tana shigowa take cewa dama nasan yan iskan nan zasu iyayin haka tunda kamar a gagauce suke da,auren nan,
Anna magariba wai ana kawo amarya tace kamar masu uzuri a gaban su basu ko iya tsayawa har zuwa anjima sukawo ta,
Muna daga dakina muna jin irin yadda suke ta sake magana dama mutanen mu sun iya irin wanan sakewa uwargida zance,
Badi war haka muzo sunan yan uku,
Yau sai gado ya kare gobe muzo gyara nai
Yau hamza kada karaga ma,shegiya kai mata har dozen,
Ku cika buta da ruwan zafi don wagga yar banzan amaryan bata,bari abokai su kawo shi,
Haka dai suke ta faman yadda magana a tsakar gida muna jin duk abinda suke fadi,
Hindatu ce ta katse shirun da mukayi a dakin kowa da irin yadda rayuwan shi ke suya a lokacin,
Yakamata ace kina da kayan kallo a daki Aisha don zai rage maki zafi da kewan idan kina kallo,
Sai dayar ke cewa gaskiya nima tundazu nai wanan tunanen nace ga daki ya hadu dama ace tana da kayan kallo ne a,saka da,sai dakin yafi nan kyau,
Sallaman su mukaji zasu shigo dakina a lokacin
Dangin Sadiya Amarya ne suka kawota daki na kamar yadda akeyi a al,ada,
Basu san da gyaran da,Hindatu taimin ba,sai kawai suka fara raraba idanuwan su a cikin mamaki don jiya ba haka dakin nawa yake ba ai,
Gurin zama aka basu ina zaune a bakin gadona wanda yasha gyara cikin sabbin zannuwan gado masu kyau da tsada dasu,
Daya daga cukin matan tace tau Aisha ga amaryan ki nan yau Allah ya nufa mun kawo ta gidan ku,
Don haka ku zauna lafiya a tsakanin ku tunda dama kowa yasan kowa a tsakanin ku don zance kusan a tare aka tashi tunda a unguwa daya aka tashi,
Zo mu zauna zo mu saba don haka aita hakkuri da juna ku zauna lafiya,
Sai wata tace shi kishi dama ansan dole ayi ahi idan yazo sai hakkuri don mutum bai lokacin shi yayi na,wani,
Carraf hindatu ta bata amsa da cewa balle ita mace ance lokacinta kalilan ne kinga tunda amaryan ta girmay ma Aisha dole ai zama na hakkuri saboda shekaru ba daya ba,
Haba nan fa guri ya dan so kaurewa da fitina saida manya suka tsawata akai shiru tare da kara rokon a zauna lafiya banda daukan jita jita a tsakani,
Suka dauki amaryan su suka tafi suna guna guni wai hindatu ta gasa masu magana,

Suna shiga daki Sadiya ta kware munafukin mayafin da ta yafa tana fafin bura uban nan yaushe yarinyar nan ta sake kayan daki haka banda labari,
Bar muna fuki, shi yai mata in anyi magana yace wai baida kudi idan bashi da kudi ina ta samu kudin da ta sai wanan kayan haka wanan matsiyaciya may take dashi ita,
Daya bayan daya mutane sukai ta,watsewa akabar mu mu yan gida kawai a cikin gidan su Hindatu sukai min sai da safe tare da kara bani shawara,
Na koma na dauki buta nai alwala tare da kawar da sauran kayana dake waje na shige tare da kullo kofan dakina kawai,
Bayan na idar da sallah na dade a gurin ina,addua na mike na haye sabon gadona don sai nake ganin kamar dakin ba nawa bane yau,
Cikin ikon Allah sai ga barci mai dadi ya kwashe ni ban farka ba,sai karfe biyar da rabi na,asubahi,
Namike don gudun kada na makara ga,sallah nai suri buta,sai ban daki na fada, nai alawala nakoma dakina,
Sau daya na daga idona na kalli kofan Sadiya amarya na kawar da kaina da idona da sauri ban tsaya jiran komai ba shige daki,
Ida nai sallah nake zaune ina adduoin safe kamar yadda na,saba yi a baya, nan barci ya,kwasheni ban sani ba,saboda akwai wuta fanka ya na kadawa a hankali,
Muryan Umma ne dake kwada min kira cikin tashin hankali ya,sani farkawa daga barcin safen da ya daukeni mai dadi,
Naji ta tana cewa Aisha may yai zafi da bazaki fito kiba mijinki da,abokiyar zaman ki abi karyawa ba har rana yayi haka,
Nafito tare da kokarin gyara hannun hijjab dina ina cewa wallahi ban ma,san barci ya daukeni ba haka,
Ina kwana Umma bata karba min ba,sai cewan da tayi don Allah ji inda rana yakai amma baki sa wuta ba,
Hamza ne yafito daga ban daki yana,saye da babban rigar dana gan shi saye da ita jiya ya wani nade jikin shi a cikin ta dakin Sadiya ya nufa a lokacin,
Sai ga sadiya din itama tafito ta dauki buta zuwa ban daki har ta danyi nisa naji Umma tana cewa ko ruwan wa ka,bako kaiwa amaryan taki ba saboda kishi ko,
Murmushi kawai nayi naje na fara hasa wutan a bin karyan da zan muna,
Ina aiki ina tunanen sai yanzu karfe takwas da wani abu suka bude kofa ko may ake nufi ne wai,
An dan dauki lokaci naga fitowan Hamza ya fito zuwa kofan gida,
Sai gashi dauke da leda breadi ne da kayan shayi a cikin sa ya,sayo a waje,
Dakin Sadiya ya nufa dasu a gefen idanuwa na nabishi da kallon mamaki har ya shige ciki,
Sai ga Sadiya da Cup inda nake batun yin gudajin kunu a tukunya tabude ta debi ruwan zafi batare da tace min uffan ba,
Ta juya ta wuce abinta zuwa dakinta nima ban tanka mata ba duk da dai raina ya baci amma sai kawai na,dake abina,
Ina gama kunu nace Sa,an Umma ta karbo min inda zan zuba masu Sadiya da angon ta kunu ,
Sai ga Sa,a ta dawo tana fadin wai tace nabarshi ita ta karya ko,
Na zuba nawa tare da kai sauran gurin Umma don ita mama bata damu da kunu ba,sau sauran tuwo,
Na koma na,gyara dakina nafito har wajen dakin, mama hafsi dake makwabtaka dani sai dana,share shi tas sanan na debi ruwa naje na,watsa a jikina,
Na dauko dinkin shaddan da mama Rahana tai min na saka a jikina,
Na zauna na gyara fuskana yai kyau, sai lokacin na tuna cewa ban karya ba fa,
Kayan tea din da Naga Hamza ya shigo dasu dazun suka,fado min a,rai mamaki ne ya kamani yadda Hamza ya iya wuce wa da kayan tea a gaban idona kuma sun hada tea din basu bani ba,,
Shida yake cewa ba zai iya cin abinda ba,zaibawa su Umma da yan uwan shi ba,
Yau sai gashi an sha tea ba,a bawa kowa ba,sai su kadai suka sha abinsu,
Ina nan zaunr na saka kunu a gabana sai binsa nake da kallo ya shigo dakina da sallama a bakin shi,
Kunnun dake gabana a cikin cup ban shaba yadan kalla sai ya kawar da kanshi gurin kayan shi ya nufa cikin daurewa nai mashi ina kwana,
Ya amsa min da an tashi lafiya ?
Alhamdullahi nace a hankali yazo ya wuce ni zuwa waje batare da ya ce min uffan ba again,
A hankali na sauke ajiyan zuciya ina mai gyara zamana da cewa Allah ka tai make ni
Muryan Sadiya naji daga waje tana cewa Hamza kada ka dade fa dear,
A hankali na lumshe idanuwa don wani abu na ji alokacin ya ratsa kunnuwana har cikin zuciyana,
Shiko sai naji ya amsa da cewa yanzu zan dawo bazan dade ba, ai
Murmushi ne ya,subbuce min daga fuska na ni kadai a cikin daki,
Mamaki nake yau yau da farawa na,fara ganin sabbin rayuwa a gurin Hamza,
Shiru shiru zata fito dora girki kamar yadda amare zawarawa keyi amma sai mukaji shiru nikan ga kunun dana dama da safe ma na kasa shan shi kuma bana jin yunwa,
Aina ce ta tayar dani daga barcin da ya fara dauka take cewa mamanta tace a kawo min dan wake da mai da yaji data dafa masu agida,
Naji dadin wanan dan waken dayajin shi yaji tafar nuwa sosai naci nasha Aina tana zaune tana min hiran jiya da dare take cewa wai kin sani ne anty yar agwai,
Jiyafa da kyat amarya tayarda zata zo dakin ki wai cewa tayi baki isa taje dakin ki ba,sai dai ke akiraki dakin ta,
Murmshi nayi Aina tana tabani labarin abubuwan da mutanen Sadiya sukai ta fadi a kaina,
Tace wai Sadiya tace wata biyu tabani a gidan Hamza sai na fita na barya dashi,
Wai dama ta dade tana son Hamza a ranta Allah bai nufa ta aure shi ba shine ni na tashi na,aure shi yanzu gashi Allah ya,sa ta aure shi ita wallahi bazata iya zama da dashi da wata mace ba,
Murmushi nayi a fili duk da a cikin zuciyata naji wani iri nacewa Aina wace sai yanzu na fahinci kawo dan waken da mamata tabayar takawo mi nagane ma,anan haka,
Don naji duk wani labarin daban sani ba agurin yarta tunda su ba halin su shigo gidan mu agansu,
Nace wa Aina kyaleta kawai kaunata Allah yafita yafi sherin ta idan ban mata sheri ba tazo tai min Allah bai bata sa,a,
Muna ciki ni da Aina har wani lokaci muna hiran mu wanda a gaskiya naji dadin shigowan Aina din don ta debe min kewa sosai a gidan,
Sister din Hindatu ce tashigo take ce min hindatu tace takawo min wani ledan vacco da kayan tea da kuma su taliya da miya mai yawa a cikin sa,
Nai godiya nai mata raki take ce min ai zata dawo in an kwana biyu, ta dubani,
Wai yau gidan nan baza ai muna girki bane ko kuwa yaya akayi ne wai,
Muryqn Ummane tsaye a tsakar gida tana tambaya tare da duban kofan dakina,
Nikan banda yunwa na ci dan wake nasha zobona mai sanyi na kwanta ina,sauraren wa,azi a cikin wayana bayan fitan Aina,
Jin muryan Umma gap da kofana tana maimaita tambayan ta yasani fitowa daga dakin nawa,
Umma aikin san yau banice zan muna girki bs shiyasa ban dora muna ba,
Wa zai muna take tambayana cikin kafe ni da idanuwan ta,
Sadiya ce ai da girki don haka ne ban fita ba kada taga nai mata katsalandan
Kwarai kuwa inji zarah daga bayan Umma inda budurwa ce kinga sai a koya mata yadda za,ayi na yau ta gani,
Tau bazan yi girki ba sai lokacin da na ga daman karba kokuwa Sadiya ce daga kofan ta ta daga labulen dakin tana kallon mu,
Banyi magana ba sai kawai na juya zuwa cikin dakina na kyalesu dole zarah ce tai girkin rana kowa yaci har ita Sadiyan nikan ance wai nakawo guri a,zuba min nace na koshi,
Da yamma dole nice nafito na dora girkin dare na kwashe nabawa kowa nashi,
Ina ganin yadda ranan Hamza yake shige da fita a gidan amma kamar bai san da zamana ba a lokacin,
Bayan na idar da girkin nai wankq na,shige daki ban fito waje ba,sai zuwa dare bayan ishai, ina kwance rigingine a kasan carpet din dakina kafafuwana,a,sama kujerana,
Naga shi ya shigo dakin wayana yana a hannu na ina,sauraren kira,a tare da bin kira,an a hankali,
Dakin nawa yake bi da kallon sai da ya kewaye ko ina da idanuwan shi kamar bako sai yake cewa kizo ki samay ni a waje yanzu,
Namike tare da gyara hijjab din dake a kaina nadan saka silfers dina a kafa na tabarma nagani an shimfida a kofan Umma da mama suna zaune akai sai na nufi gurin nima na zauna suna daki muna jiran fitowan su shiru shiru sai da mama tace kodai yaron nan ya manta da ya,tara mu nan ne,
Can sai gasu fitowa dagani sun sha,soyayyan su ne don fuskan su yana dauke da murmushi sake fayau,
Kamar zata shige mai a jiki irin yadda suka zauna a tabarman,
Shine yafara magana tare da cewa tau da farko dai ina son na godewa Allah daya kawo mu wanan lokacin msi albarka,
Yanzu mun kara samun karuwa a gidan don haka nake son na ja maku kunne akan ku zauna lafiya da junan ku ,
Ban son nani wani hayaniya ko tashin hankali daga dayan ku ko wacece zan batawa maishi rai,
Ga iyayyena nan suma ina son a basu girman su don bazan yarda a wullakanta mi uwaye ba ko kadan,
Sai zancen girki ku tsara yadda kuke son yi a tsakani ku don na sani saboda ni yanzu kunga matafiyi ne,
Shiru ne ya dan fito baya ba,wanda yai magana a cikin mu daga cikin duhu ina iya ganin yadda take wani dan lalaban shi daga bayan shi,
Zamuyi kwana daya daya don ni haka naga kamar yafi min sauki,
Umma tace girkin kwana daya may zaku gane a cikin sa kwana biyu dai zakuyi shi yafi,
Ni kwana daya na tsara zamuyi don haka ne yafi min saukin aiki,
Sadiyq ce ta furtawa Umma din haka yayin da gaba daya muke kallon ta da mamaki ,
Ibrahim wanda tun fara zancen ya shigo gida yana zaune yana cin abinci ya kada bakin shi,
Ke mu fa gidan nan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login