Showing 168001 words to 171000 words out of 299981 words
duk abinda Umma ta ce shine muke bi don haka ku barshi a kwana bibiyun da tace din,
Wanan kuma ai ba hakkin kowa bane hakkin mune mu masu auren shi inji Sadiya tana ba Ibrahim din amsa,
Kwana biyun da Umma tace abarshi a haka inji Hamza wanda tun farko bai ce uffan ba a kan zancen,
Mikewa Sadiya tayi zuwa dakin ta wanda hakan ke nuna tayi fushi ke nan zuwa dan wani lokaci Hamza ya mike zuwa dakin,
Muna gurin a zaune na wasu yan mintina ba wanda yai magana, Allah ya kyauta inji mama hafsi ta mike zuwa dakin ta nima mikewa nayi ina cewa a hankali sai da safen ku nabarsu a gurin inda naji Ibrahim yana cewa yanzu aka fara ai indai wanan fitsararan yarinyace da kuka kwaso wa kan ku,
Narufe kofana nai shigewa na daki bankara fitowa ba sai safe yau ma kamar jiya don basu fito ba sai da rana ya take, sosai,
Ina daga daki don da,wuri nafito na dama kunu nakoma dakina
Har ya gama,shirin shi ban fito ba ina daki yaje ya tayar da mashin din shi, ko may yagani sai kuma ya sauko zuwa dakina ,
Kwance nake ina barci cikin wasu material mai adon baki da fari, dinkin dogon riga mai dogon hannu,
Sai naji yana jamin kafa na a hankali na farka daga barci idanuwa na da suke da nauyin barci ina kallon shi
Yana tsaye yau ma,sabbin tufafi ne a jikin shi, sky color,
Wanan barci fa haka har rana ya taka haka ? Baki fito ba sai faman barcin da kike yi,,
Ina kwana nace mai tare da yin mika ina kokarin dagowa daga kwanciyan danake,
Ni zan fita naga banganiki waje ba,shine na shigo na duba ki ko lafiya,
Yadda na aje cup din dana,saka kunu na idanuwan shi yakai sama yaga alaman ban karya ba,
Ko karyawa bakiyi bakina ta faman barci ko nace sai na tashi zan sha tea
Wani kallo yai min a tunanen shi ko shayin da suka,sha da amarya najewa gatse,
Nace ina son zuwa gidan musa na duba matar danaiwa karin ruwa yau sati daya ke nan,
Rai yabata yana cewa ban faye son yawan fitan nan ba fa kema kin sani ban son yawan shiga mutane sai mutum ya koyo wasu akida na daban,
Nidai ban yi magana ba ina sauraren shi kawai muryan Sadiya ce ke fadin ina nan waje fa tsaye but naga ya juya batare da ya tsaya mun karasa maganan mu ba yafita yana cewa sai ya dawo ,
Sai zuwa wani lokaci naji tayar da mashin din shi alaman sun dan tsaya da ita ne daga kofa,
Can na mike nafito don na dauraye cup din da zan sha tea da spoon a hannu na,
Wani kallo tai min tare da jan tsuki ta shige dakin ta na zauna ina kada tea Umma ta shigo da kifi danye wai a gyara ayi miyq dashi,
Nasan Umma tai hakane don ta burge Sadiya tayi muna miya mai dadi,
Umma nikan sai dai a gyara in ma har zanyi miya dashi don ina tsoron kada ya soke min hannu,
Murmushi nayi don jin may tace nasan dai baza,a ce nafito na gyara ba don bani ce dagirki ba,
Dole Asmau Umma ta,sa ta gyara kifin tana ta faman mita ita haka kawai za,a sakata aiki,
Iyye to may kike nufi dama saidai a dafa a baki kici komay kike nufi ni wallahi ba yar Agwai bace da kuka raina,
Cafdijam nace ashe akwai magana a gidan nan don Umma bata hada diyan ta da kowa ba, a duniya,
Miya kan a fuska ga miya amma gishiri bai bari akai shi a baki don zai iya yanke makoshi,
Ranan nan akabar abinci ba wanda ya iya kai ko loma a bakin shi,
Miya na wanda nakan dumama abina tunda safe suna daki na diban ma mama hafsi nakai mata a boye mukaci da breadi makasha ruwa muna jin diyan Umma suna jininin yunwa,
Washegari karan bugun kofan da Umma keyi na,Sadiya ya ne ya farka dani daga barci naji tana cewa ka tashi kaje ka samu jam,i duk kwanakin nan baka zuwa sallah asuba,,
Shiru banji an bude kofan ba sai bayan kamar minti talatin da wani abu aka bude kofan dakin lokacin ma ina ganin an karasa sallah ko,
Aiko ya na fitowa Umma tafara magana yanzu kai sallah asuba da ake raba alheri wa bayin Allah shine kake kokarin sakaci dashi har baka iya fitowa kasamu sallah a cikin jam,i,
Hmm ikon Allah wai mutum yai lokacin shi kuma ya hana wasu yin nasu sadiya ce ke fadin haka dai lokacin da tazo gap da inda Umma take tsaye, don ta jita,
Sakwarkwatai Umma tayi tabi ta da idanu kawai da mamaki abinda ya fito daga bakin ta,
****** ********** ******
Har kwana hudun da ake na bazawara ko uku ya cika banga Hamza yana zancen dawo dakina na nidai ido kawai na sa mai,
Har saida Sadiya tai sati daya suna tare da dashi babu wanda ya ce masu uffan a gidan,
A bangare na babu wani alaman batarai danayi a fili sai dai a cikin zuciya abin yan bata min rai sosai,
Wanda nake zaune gidan don shi bai san daraja na ba don haka nake ganin gara kawai ma nabar gidan
Na nufi gurin iyayyena zaifi wanan zaman da yake shirin jefani ciki da kurciyana,
Mama Hafsi ne da taga har yau yana shirin kara kwana wurin Sadiya ta samu Ibrahim a,waje take fada mai halin da ake ciki don tana gudun tai magana ya zama fitina,
Hamza ya dawo da mashin din shi dauke da dan ledan da yakan riko ya shige da shi dakin Sadiya,
Yaya amma dai yau Uwargida ce keda girki ko don dai amarya ta gama kwanakin ta tun kwana uku da suka wuce amma baka koma dakin yar uwar ta ba,
Tsayawa Hamza yayi yana kallon Ibrahim din yake cewa dama idan an auri bazawara kwana nawa ake a gurin ta ne,
Ibrahim yace kwana uku ko hudu mana akewa bazawara budurwace kwana bakwai,
Yakalli dan uwan nashi yace wallahi Ibrahim ban san da haka ba kuma sai na dauka ko ita Humaira ta kyale ne kawai don ita wanan din ta san gidan sosai,
Yace to gaskiya yaya baka kyauta ba daga kai har su umma dake cikin gidan nan suna gani ana zaluntar diyan mutane don kawai hakkurin ta,
Kaji tsoron Allah wallahi ka kauce wa cin amana don gudun sabawa Allah,
Ubangiji zai yi fushi dakai akan wanan abin da kuka aikata
Banyi zaton zakayi saurin mantawa da irin halarcin da wanan yarinyar Aisha tai muna ba alokacin da muke bukatan taimako ta fitar da mu a kunya,
Ta zauna da mu cikin irin halin rayuwan matsatsin da muke acikin wanan gidan, yanzu don ka auri diyar kawar Umma shine za a hada kai har dakai a cutawa yar mutane
Shiru Hamza yayi yana tunane don bai taba tunanen Ibrahim nada kaifin hankalin irin haka ba,
Yaji dadin tunasar dashi da dan uwan nashi yayi sosai ya kuma gode mai da ya fitar dashi daga halakan daya tashi fadawa,
Yace cikin nuna damuwa a fuskan shi nagode Ibrahim insha Allahu zan kiyaye kamar yadda kace Allah ya bada iko inji Ibrahim din yabashi amsa,
Yana shiga cikin gida su Umma suna zaune a,waje da yaranta ga kida da ke tashi na yan wasan hausa daga dakin Sadiya muryan ta tana marming din wankan har waje,
Wani haushi ne ya kumay mashi zuciya tana jin muryan shi tai wuf tafito waje sai kawai taga yasha kwana zuwa dakina,
Ina duke a gaban fridge dina ina gyaran ruwan dake cikin sa, sai naji ya riko ni ta kunkuru na,
Nadago don nasan shine kawai zai iya min ta,sakani yi kwana biyu,
Yanzu Humaira kin min adalci ke nan a rayuwan mu saboda Allah ashe kwanan wacan yarinyan ya kare amma,shine ke baki fada min ba kika barni a duhu haka,
Kawai sai ma na,rasa may zan ce mai don zancen banza naji yana fadi shi da,yai aure bai san yadda akeyi ba yake nufi ko may
Ko kuwa sallon yaudare irin na maz yazo min da shi haka
Cikin kuka nace dan Allah ya hamza in har kasan baka bukatanane a gidan nan ka,sallamay ni kawai na koma gidan mu don wullakancin ya isa hakana,
Wani tsawa ya daka min tare da nuna ni da yar yatsar shi yana cewa, ina gargadin ki da kada na karajin kin furta kalman rabuwa a tsakanin mu
Idan ba haka ba ranki zai baci sosai a gidan nan banyi auren da har kike zaton zan maki wulakanci ba,
Don haka ki shiga hankalin ki ledan dake hannun shi na kayan sayi na jika makoshi ya miko min ya juya yana fadin ki karbi girkin ki yau din nan don anan zan kwana,
Ya fice yabarni tsaye ina mai binshi da kallon mamaki adake ka,a hanaka kuka ke nan,,,
Dakin Sadiya ya shiga inda ta bishi da harara tankar bai fahince ta ba sai ya basar da ita kawai ya fara kwasan kayan bukatan shi,
Kasa kannewa tayi tace dear ban fahince kaba namay ke nan shima ya tambaya batare da ya juyo ya kalle ta ba naga kana wani kwasan kaya kaman mai barin gari,
Bagari zan bari ba dakin dai zan bari zuwa dayan dakin kuma,
Amma dai sai nake gani kamar da sauran time aiko, ko dai har ka gaji dani ne wai, ?
Yace ba gajiya nayi dake ba Sadiya bana son na fada cikin sabon Allah ne kwai don itama tana da hakki a kaina kamar yadda kema yanzu kike da hakki a akaina,
Tace au kana nufin ke nan daya muke da ita ko da har zaka wani hadani da wanan mara galihun, matar taka,
Hamza ya juyo da sauri yana kallon ta yace a idanuwan ki take hakana ni agurina mace mafi daraja gareni,
Yanzi musali idan kece nai wa iri haka yaya zakiji a ran ki nasan bazaki ji dadi ba don haka naje son na kwatanta adalci a kan ku baki daya,
Hmmm aikama kasan wallahi ba daya muke ba ni da ita don mata suna suka tara aciki dole a kwai zarah,
Yace to gaskiya ni har uanzu Humaira ce zarah ta don ban hadata da kowa daga haka yafice daga dakin dauke da wasu kayan bukatoci nashi a hannuwa shi,
Hakika maganganun Hamza a kanta sun matukar bata haushi so sai batayi tsanmani duk irin dafuwan da tasha har Hanza zai iya bude baki tun yanzu ya tuna da wata humairacan,
Tace wai Humaira kamar wata matar azo agani yarinya karama ta ishi mutane da a guri,
Ashe muna fuki duk wanan ihun da satin da yake min duk karya ne nida ina zaton abubuwan dana ci da wanda na sha ne duk suka gigita min shi a she muna fukinkuwan dadi ne kawai yakeyi baifita hankalin shi ba,
Hmm,ummm aiki kona gabana ja don wanan yar iskan ni bazan zauna da ita ba ta hanani jim dadi mijina,
Yanzu yadda na saba da wanan rugumar nashi kwana biyu ace wai haka zan kwanta babu wani shafa ko tsotso sai ni da pillow kawai,
Gaskiya da sake Umma zan fara zuwa na samu kafin na fadawa mamana abinda ake ciki ta tashi min tsaye,
Yana fita naga kuka ba zai min ba take zancen Hindatu ya fado min a rai da take ce min duk ranan da mijina yagama kwanakin shi a dakin amarya zai dawo dakina na tabbatar nai mashi tanadi mai kyau, wanda zan tare shi yasan nima mace ce mai daraja da kima,
Idanuwana na kai gurin da na boye wasu abubuwan da tai min tanadi tace ance in kana da kyau kara da wanka,
Kafin na mike sai gashi dakin dauke kayan aji su boxer din shi touch light, redio da su brush,
Ya samu guri ya aje su ya ce min ga kudin cefane na saiyo abinda babu shi a gidan, nayi girkin dare,
Ranan Sadiya kamar zatayi hauka don duk tabi ta tayar da hankalin ta sosai agidan don har zuwa tayi cikin dare wurin Umma takai karan Hamza
Bayan Umma ta gama sauraren take ce wa yanzu so kike na mara maki baya dana ya kaice duk mu taru mu hallaka gaba,dayan mu,
Wata irin zuciya Sadiya tayi tace oho ashe dama muna funtar mu kikayi kina ra,ayin matan shi amma sai kika nina muna ke baruwan ki da ita,
Haka tafita daga dakin tana bakar magana ni wallahi idan tsoho baiji kunyan hawan jakiba jaki baijin kunyar yarda tsoho muje zuwa indai nice,
Sai kamshi ke tashi daga dakina gado yasha gyara ledan kasa sai kyali yake yi ni kaina dakin ya ban sha,awa irin yadda dakin ya dauki gyara,
Bawai ina jin dadi bane acikin raina cewa zai dawo gare ni nai wanan gyaran kwai dai nayi ne don kwato inci na kamr yadda kowa ke min nasihan na zage nayi abinda zan kyautata,mai fiye da da can baya, ,
Abincin sa yana daki kamar yadda naga Sadiya ta tsiri aje mai adaki ba kamar yadda Umma ta hana ni kai masa dakin mu ba a baya,
Bayan yadawo masallaci ya shigo gida sun gaisa da su Umma ya mike zuwa dakin mu nan yasamu abincin saman da center table na aje mai komai a guri daya gwanin ban sha,awan tallaka bawan Allah,
Ya,na shiga ya kwabe kayan jikin shi daga,shi sai dogon wandon dake jikin shi, ya zauna don yaci abinci,
Gefen shi kadan nadawo na,zauna don ko hakan sai da na tursasa rayuwana yabar min daci,
Yana cin abincin kamar mai yunwa abaya sai daya kusa cinyewa saura kadan mukajiyo muryan Sadiya tana fadin,
Idan ban iya girki ba ai sai ki fito ke kiyi ko kuma wace ta iya taita maki kullun,
Tsuki naji yaja tare da dan girgiza kan shi ni dai tankar ban gan shi ba,
Mikewa nayi ina fadin in kaima ruwan wanka ne yanzu cikin kada kai ya bani amsa, da cewa eh, nakai mai ruwan,
Ni kaina nasan da cewa akwai canji sosai ga Hamza don ya canza gaba daya ya zama wani dan duniya yanzu,
Sai dai duk ta hanyan da ya bullo min yasamu nima nakai gurin don haka bani kadai ce yabar wa mamaki ba harda shi na barshi da mamakina sosai,
Washegari da safe tun kan nafito na gyara jikina nafito naiwa mutanen gida ina kwana tare da nifar gurin girkin mu,
Na aza girki nadawo na gyara dakina tare da sharo kofana har zuwa na mama hafsi da nake makwabtaka da ita,
Sai da na gama komai na koma daki na,shige tare da sake labule don Hamza din yana ciki kwance yana barcin safe abinda bai saba yi min ba yanzu shi yake yi,,
Can ina zaune daki ahiko batcin shi yake saman gado yayin da,Sadiya take dakin tatana faman leke ta labule ko ya fito daga dakin nawa saboda takalman shi dake aje a kofan daki zata gane yana nan ko baya nan,
Ummata fito tana cewa kai, kai kai wanan mugun sharan kuma fa haka waye yai muna shara a gida tsabbare tsabbare, a kabar min kofa na,
Ta daga kai ta kallo kofan dakin mu ni da mama tagan shi a,share tas yana sheki da shi duk na gyara gurin na kawar da duk wasu komatsai a kofan namu,
Nice nayishi ba kowa ba ina yatanki da bazasu share maki kofa sai nice boyar su zan fito na share masu guri,
Tsaye sororo Umma tayi tana kallon inda Sadiya take tsaye daga kofan dakin ta rike da labulen kofa a hannun ta,
Sadiya nice kike kokarin fadawa magana ina fadi kina fadi a tsakar gida haka ?
Eyyeh Sadiya ni ce har zakice wai na samo yarana su share min kofan dakina,
Sadiya tace Umma ta yaya ma zan maki shara bayan ga yaran zaune tare dake gandan gandan a gaban ki,
Muryan Sadiya dayaji yasashi farkawa daga,barci yana fadin subbahanallahi,
Mikewa yayi zibur zuwa waje baida ko riga ajikin shi wanda hakan yai matukar batawa Sadiya rai don tana ganin tun safe kilama muna kwance tare makale da junan mu,
Wanan wani irin rashin mutunci ne kike sa,in sa da mahaifiyana daga shigowan ki gida zaki fara yiwa mutane rashin mutunci haka,
Kai kyaleta nace maka ban son jin wani magana kuma maganan ya isa haka na,
Amma Umma ta yaya zan kyaleta tana maki haka a gaban muna gani
Mama tace wai batace kawuce ba kada zancen yai tsawo katafi mana kawai zai fi ai,
Rai bace yadawo daki bai dadeba nakai mairuwan wanka nafitar mai da sabon man shafi mai kanshi ya shafa bai ma,damu da tambayan ina na,samo shi ba,
Yana cikin shiri ya karan redio na tashi daga dakin