Showing 171001 words to 174000 words out of 299981 words
Sadiya ta kure volume din shi har karshe da alamar rawa takeyi a dakin,
Fita yayi daga gidan baidawo ba,sai da lokacin cin abincin rana yayi sanan ya shigo gidan bai dade ba ya kara fita,
Hakana nai kwana biyu na kullun da wanda,Sadiya zatai fada dashi ayi cin mutunci ran hamza ya baci kawai,
Wai ita niyarta kada yaji dadin zama a dakina ta bata mashi rai kawai, har ya fita ba zan gane ma komai ba daga gare shi
****** ********* ******
A haka muka kai har wata uku da Sadiya a cikin tashin hankali, take da mitanen gidan da suka kawo ta babu sauki ko kadan a tsakanin su,.
Shidai Hamza ba mutum bane mai yawan zama a gari, don haka wani abin har aci a sude bai ma san anyi shi ba a gidan
Sadiya ta samu uwar ta da karya da gaskiya ta fada mata cewa shi ne abinda Umma ke mata a gidan ita da yaran ta,
Uwar ta harzuka sosai inda take shiga ba nan take fita ba wai ita bubu mai wullakan ta mata yar ta kan aure,
Da Hamza ya dawo gari ta aika aka kiramata shi tai mashi tas cewa bazata yatda da abinda Umma kewa yarta ba don dama tana da labar8n irin mugun halin da takewa sarakuwar ta shine yanzu take kokarin kawo halin gurrin diyar ta, tau ita baxata dauki wanan ba,
Shi taba mata ba Umma Rabi ba don haka ya rike mata diya da kyau in ba haka ba za,a ji su sosai,
Saboda kunyan ta da kuma nauyin ta da yake ji ya kasa mayar mata da amsa sai dai yace mata za,a gyara insha Allahu,
Wani sabon sallon iskan ci da rainin wayo Sadiya ta dauko a gidan yanzu zata iya shiga girki amma bazata girkawa kowa komai ba,
Sai dai kowa ya nemi abinda zaici a cikin sa don yunwa, saboda tace ita ba kuku bace mijinta ne dolen taiwa girki ba wasu kattai ba can,
Kuma in baya gari babu wanda zan wa girki ya zauna yaci banza don ni ba yar ga aiki bace,
Idan Sadiya batayi girki ba Umma takan so ta sani wai dole sai nayi girkin mama ce ta kashe wanan wutan tace babu hujja don kowa da kudin cefanen shi a hannun shi ai sai suyi hakkuri har lokacin da taga dama tai masu,
Hakana muke ta zama ba wani dadi a tsakani da Sadiya wace ta dauki kishin duniya ta dagwara wa zuciyar ta a kaina,
Na kai mata ko ina a cikin gidan nan bata kaunan taji wani abu da ya dangance ni ko kadan,
Koda baki akayi idan taga bakinane bazata gaisa dasu ba har su bargida nan,
Ita kokarinta shine ta daiga na bar mata gida don wullakanci da rainin hankali ba wanda bata gwada yi min koda kuwa yana gidan ne sai yai magana wani lokaci ya tsawata mata,,
Ganin da nayi bata da mutunci fiye da yadda nasan ta a baya yasa na dauki mataki a kanta ban yarda wani abu ko kadan ya hadani da ita baruwana da harkanta ko kadan,
Duk da rashin mutuncin da takewa Umma da yaranta zaka gan su kan su ahade da ita da zaran sunga ina daga cikin daki ko na fita yanzu za,a dasa gulmata ana zagina,,
Lokaci sai na Hamza normal din shi amma kuma wani sain sana ga duk ya canza ya koma min wani zaki sai fada zamuyi tayi har yatafi,
Daga baya dai sai na fahinci akwai matsala ta kowani hanya ta gurin Kishiya da kuma gurin ita Umma,
Don zai ita zuwa natare shi na,am ,nam amma dazaran ya kebe da Umma ko Sadiya yanzu duk annurin da yashigo daahi zai gushe zai yi kicin kicin da fuska kamar an mai sakon mutuwa
Taufa har ya tashi bazan gane mai ba sai dai naga ana ta bushasha da kishiya da kuma mutanen gida tun Ibrahim yana tsawata mashi da hakan har takai baiji dole yakawo ido ya sa mai don yaga yai nisa da yawa sosai uanzi Sadiya ce yar gaban goshi,,
Barkan ku da ahan ruwa yan uwa barkan mu da warhaka Allah yasa mu dace da rahamomin sa na wanan watan mai albarka, Allahuma Ameen,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYABA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,
Ranan da yamma ina zaune daga kofa na iba yan kullin kayan sana a ta,
Umma daga inda take a zaune ta kura min ido kallona take a cikin natsuwa, yadda nake aikina a hankali kwance, take kallona cikin tunane,
Mamaki take yadda duk irin musgunawan da suke min ban damu ban kuma,sa a,raina komai ba,
Sadiya wace fitowan ta ke nan daga dakin ta ta hangoni ina aikina ta tsaya daga kofa daidai lokacin da zan shiga daki da kayan dana kulla din na,saka a cikin fridge di na,
Ke yar Agwai ki duba dakin ki ko cup dina yana ciki ki miko min don ban gan shi ba tun jiya,
Haushin irin yadda ta kira sunana ne ya kamani don haka naki karba ma kiran da take min,
Yar Agwai ko kin zama kurma ne ana magana kin wani kyale mutane haka,
Ke dakata taji an fadi daga bayan ta muryan Hamza ne wanda ya shigo gidan ba tare da mashin din shi ba, don haka bata san da zuwan shi ba ,
Daga yau sai yau ban son naji kin kara kiranta da,wanan sunan banzan a gidan nan,
Ta,wani gi mashi wani irin mugun kallo irin na marasa kunyan mata,
Tace toh ai sunan ta ne kuma dole akirata dashi ta amsa kai mayye naka na fada,
Yace bako a gidan nan ba wallahi idan baki iya kiranta da sunan ta da Allah ya bata akan ki to ki kirata da Aishan ta zaifi,
Yanzu akan nakirata da yar agwai kake kokarin yi min cin mutunci irin haka don ka nuna mata kana giyon bayan ta ,
Yace eh a kan shi kuwa idan kuma kince kartane kikara kiranta dashi kiga yadda zan bata maki rai,
Lalai kako nuna min yau kana bayan matar ka may kake kokarin cewa wanan yar sadakan kana nufin tafini daraja a gurin ka ko may,
Ya juyo a hasale ya kara cewa da idanuwan shi da suka rine sukai ja kindai ji abinda na fada,
Kai kubar wanan zancen ya isa hakana ban son a fara karamin magana ajashi har yai tsawo,
Nidai ina dakina lokacin shi kuma dakin Sadiya yake don haka sai ya nufi can,
A can din ma ba barin fitinan sukayi haka sukaci gsba da,sa, in sa muna jin su a tsakar gida Sadiya tana fadin wai ua goyi bayana ,
Yake cewa ba zancen goyon bayan ta bane raini ne da wullakanci ban so tunda kin san sunan ta may zai hanaki kiranta da sunan ta sai wani sunan banza can ,
Kodan kin ga tana hakkuri da kauda kai ga duk wani al,amari shiyasa har raini zai kai ga haka,
A gaskiya cikin ran Sadiya tai matukar jin tsoron yadda Hamza yau ya koma halin mai anihin sunan watau Hamzan gaskiya don babu wargi a idanuwan shi ko kadan,
Daurewa dai tayi tana bashi amsa cikin dakewan zuciya don itama ta dan turza mai, kada yaga gazawan ta,
Haka suka karaci tsiyan su ba wanda ya basu hakkuri suka gaji sukai shiru,
Wanan tsiyan bai hanasu kwana tare ba don da safe sai ga shi dauke da buta yafito wanka,
Muna kicibis dashi yai kamar ya dan daburce ni dai na kauce mai na,ci gaba da abinda nakeyi ina fadin jarabbaben banza kawai,
Can tafito tana wani kasaita da isa wai ita matar so bayan tafito daga wankan bata shiga daki ba sai ta tsaya daga waje tana wani tsefe ruwa a gahin kanta wai don kowa ya gan ta,tai wankan tsarki,
Kwanonin da muka ci abinci nida mama na kwaso zuwa gurin wanke wanke nabi ta gabanta tana gani na, ta wani girgiza kan ta,,
Tankar ban fahinci may takeyi ba sai aiyukana nake ta gaji ta dauko buta ta tsuguna wai tana kara alawa,
Ana zaton wuta a makera sai gashi a masaka ni ban damu ba amma Umma ta kasa hakkuri tai magana,
Wanan ai aikin banza ne mutum ya makara da,sallah har rana ya yi ja da,fitowa shine har zai tsaya wani heleken banza wa mutane,,,
Kamar zata bada amsa sai kuma ta ja bakinta tai shiru kawai tare da shigewa dakin ta,
Ranan haka Hamza ya yini yana rawan kafa akan Sadiya ita ko sai wani nuna isa da gadara takewa mutanen gida ita a,dole ga matar so a gurin miji,
Abin yana matukar bata min rai irin yadda yake nuna mata fifiko a fili a gaban kowan,
Washegari kuwa wajajen karfe goma na,safe nafito a cikin shirina na nu fi kofan mama nake ce mata zan tafi uguwa tabar abinda take ta leko tana ce min yau za a uguwa ne nai murmushi nace eh amma ba dadewa zanyi ba,
Na nufi kofan dakin Umma yana a rufe har zan fita sai nai shawaran na kulle kofan dakina kawai,
Na ja kofan dakin na rufotare da,sa padluck na rufi na fita zuwa gidan mu ina gap da zan shiga gidan namu sai nai wani tunen cewa Ummi tana fama da kan ta zan kai mata wani bakin ciki a cikin kishiyoyi masu jira suji gwam,
Take na canza shawara na juya na nufi gidan Anty Hindatu tare da kokarin tare mai yar mashin,
A cikin wani irin yanayi na fada gidan saboda irin yadda naita tunane ina saman mashin, kafin na iso,
Ko Sallama ba irin wanda na saba yi ba idan na zo mata na yau daban yake da na kullun,
Tana zaune a kasan ties din dakin ta ga cup din da ta sha hura mai sanyi da kankara daga gefen ta, sai plate din da taci indomie a dayan gefen nata,
Ina shiga dakin sai ta bini da idanuwan mamaki lokaci daya taga duk na canza mata a fuska,
Zubewa nayi saman daya daga cikin kushin din dake dakin cikin muryan kuka nake mata ina kwana,
Ta dago kan ta tana kara yi ma yanayi na kallon mamaki, tare da saurin gyara zaman ta da kyau,
Idanuwan ta kyam a akan fuskana tana kokarin nazarin yanayi na tare da,son tambayana ko lafiya,
Kamar jira nake tace Aisha yau kuwa lafiya kike haka sai kawai na barke mata da wani irin kuka mai tsuma zuciyan mai jinta,
Wani irin gululun bakin ciki ne yazo mata a makoshi don ta,san cewa yau da magana ke nan don yadda ta sanni da hakkuri amna yau ta ganni a haka,
Wani irin sanyayan ajiyan zuciya ta sauke tare da mikewa zuwa inda nake zaune tazo ga kujeran dake kusa da,wanda nake zaune ta zauna,
Cikin sanyi murya ta iya bude baki da kyat don tausayi na tana cewa ,
Ki natsu Aisha muyi magana don wanan kukan bawai zai maki mafanin abinda ke damun ki bane,
Aisha nasan cewa kin yarda danine shiya sa kikazo guri don komay je damun ki nasan ba karamar damuwa bace tafito dake har kika shiga irin wanan yanayin damuwar, haka,
Duk maganan da take min acikin nuna damuwar ta gare ni bai sa na dakatar da hawaye da sheshekan kukan danake yi ba mai tsuma zuciya,
Dafani ta dan yi kadan tana,fadin Aisha wanan kukan da kike yi ai wani sabon damuwa ne kika korin jawowa kan ki, wanda zai iya maki illa ko jawo maki wani nakasar rayuwa, don haka kibar kukan nan muji mai ke faruwa,
Na yi kokarin ganin na,dakatar da,kunkan danake amma,sai dai ina zuciyata ya kasa daina bacin ran da take tare dashi,
Tsayin dan lokaci muna zaune a haka ina rera kukana, tana zaune daga gefena tana kallo na acikin tausaya har tsawon wani dan lokaci
Kaina yana kife a makarin kujera nadan samu na,sasauta kukan bayan nayi mai issata yadda nake so tana zaune tana kallona don tasan yin kukan shine dan samu sanyin zuciyata,
Nadago kai tare da cewa cikin muryan kuka Antu Hamza so yake yakashe ni a gidan nan wallahi,
Duk irin hakuri da nake kokari yake suga,karshe na kawai,
Anty na,rasa yadda zanyi duk wani shawaran da kuka,bani ke da,su Ummi ina kokarin ganin cewa na yishi don kawai a zauna lafiya,
Amma yanzu abubuwan da suke bullo min dashi yafi karfin tunane na wallahi sai a gurin mama nake dan samun sauki a gidan
Ita kuma mama bawai wani power ne da ita yanzu ba a gidan don saboda Sadiya Umma bata ragawa yar uwar ta ko kadan,
Nace cikin wani sanyin murya yanzu anty don Allah ace kwana kusan tara ina fama da wani irin ciwaon mara mai wahal dani a gidan na fada mashi amma sai yai banza da,al,amarin,
Jiya ina jin wai Sadiya tana ciwon kai acikin daren nan yafita zuwa sayo mata magani,
Ire iren cin fuskan da suka kamaci wanan agidan su nake yawan fuskan ta a kullun
Na koma dani da banza duk daya a gidan gurin shi da yan yan uwan shi har mahaifiyar shi,
Don Allah Anty ki fada min may Anty may zanyi wanda zan kwaci kaina daga wanan masifan daya bullo min kuma,
Ni da na yanke shawaran cewa nabar mashi gidan shi kawai duk da nasan cewa zama a gurin Ummina wani sabin tashin hankaline a gare ta to amma anty hakan zai fi min sauki gara na koma can sokoto gurin dangin mahaifina zaifi min sauki wallahi,
Cikin sauri ina kai nan na ji Anty tace kada kifara zancen barin gida don wata banzan Sadiya Aisha,
Duk abubuwan da kikaga yana faruwa a gidan na,dan lokaci ne don ramin karya kurarece wanan abin bazai dore ba,
Idan kin kara hakkuri komai zai zo ya,wuce tankar ba a yi shi ba a gidan,
Nace cikin sake hawaye anty wallahi, ni banga alamar wanan abin zai kai karshe ba don kullun da,sabon fitinar da suke bullo min da shi a gidan amma ina hakkurewa,
Gani ban iya fadawa kowa halin da nake ciki don nasan kishiyoyin Ummi ne zasu fara yi min gwai, don shine ko ita Ummi ban iya fadawa halin da nake ciki a gidan,
Girgiza kai Anti tayi tana cewa kada ki fara ki fada mata komai ki kara dai daurewa na dan wani lokaci kiyi hakkuri mugani,
Ke dai ki kara rungumar addu,a ki sanyayawa zuciyar ki komai ki kara kawar da kanki a kansu,
Insha Allahu addu,a ita makamin muminine, babu abin da yafi karfin Allah,
Shawara daya ce da zan iya baki shine ki dan yi tafiya zuwa gurin yan uwan mahaifinki din da kikace don ki dan basu wuri
Insha Allahu dagawan ki gidan zai kara saka su kowa ya fahinci halaiyar dan uwa don yanzu ance mugu kariyan na gari,,
Don haka ba yanzu ba idan an kwana biyu zaki iya shirya tafiya ki zuwa sokoto din,,
Wayan tane akakira don haka sai ta dakatar da maganan da mukeyi take wayan ta,
Hakane ban san lokacin da barci yai awon gaba dani ba ganin barci ya daukeni yasa ta mikewa tabarni don ta fahinci barcin ma ban samun yin shi a,wadace,
A waje maigidanta ya samay ta zaune fuskanta kawai ya isar mai da sakon bata a,cikin dadin rai tambayan ta yake cikin nuna kulawan shi da,damuwa a gare ta,
Nan take mai bayanin abinda nazo dashi tare da sake zance akan dalilin da yasa matan yanzu suke gudun kishiya ke nan,
Don a yanzu in ba Allah ya gyaraba duk wace zata shigo ita gurin ta shine ta ture macen da zata samu a gida,
Don a,ganin ta tunda kekin yi lokacin ki da,miji ai yanzu turned dinta,dole ke uwar gida ki bar mata miji kwatakwata don ke angama dake take gani tunda har miji ya kara auro to to bai kaunar ki ko ra,ayin ki ne,
Tace cikin bacin rai tare da nuna damuwa karara a,fuskan ta ke cewa yanzu don Allah honey har nawa Aisha take da,za,a ce wai hamza yana kokarin jefa rayuwan ta a,cikin wahala irin haka,
Yarinyar da ,bata ko kai shekara Shirin da wani abuba akewa,wanan irin rayuwa haka,
Ganin yadda ta dage take sababi da abokin shi kuma yaron shi duk da yasan cewa Hamza din baida gaskiya yasa shi cewa yanzu ina Aisha din take ta nuna mai daki su ya dan taka daga tagan su ya hango ni kwance nadan kifa kai a kushin ina barci shima tausayina ne ya kamashi ya dawo inda Hindatun take zaune ya zauna daga gefen ta a hankali yana fadin cewa,
Yanzu kinga dole ne mu taimaka mata don ta tafi asibiti a diba lafiyan ta, sai kuma ki tambaye ta idan akwai wani abinda za,a taimaka mata zaki iya dubawa idan muna dashi sai a bata tayi hakkuri, don shi Hamza na,rasa gane may nene matsalarshi da zaidinga gallazawa yarinyar mutane