Showing 174001 words to 177000 words out of 299981 words

Chapter 59 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17663

haka,
Ai ba a wasa da ciwo balle ciwon maran da tace irin haka, yana yawan damuwan ta,
Ya na kokarin tura hannun shi a aljihun rigar shi yake cewa yanzu karbi wanan ki bata tayi hakkuri da shi taje asibiti a fara duba lafiyan jikin ta a gani,,
Sun dan dauki lokaci a tare suna hira akan zance rayuwan auren na da Hamza ban ma san sunayi ba don ni barci na kawai nake ta kwasa saboda dama can ina da bashin barci a idanuwana
Fitan maigidan nata tai dan guntun tsuki tare da yin tir da halin wasu maza da basu da tausayi a kan mata su sun dauka mace kamar hullace zakayi iya amfani da ita a lokacin da kai ra,ayin ta,
Da zaran ka gama da ita,sai abubuwa su dinga tafiya a,slow ta tuna ranan da Hamza ya fara kawoni gidan su gwanin ban sha,awa kamar zai lashe ni,
Gashi duk wanda ya gan mu a lokacin yasan cewa mun dace da junan mu sosai dan auren yayi muna matching saboda akwai dan tazara a tsakanin mu ni dashi,
Amma ita wanan da yake cewa wai amarya za,a iyacewa sa,an juna suke da junan su a gurin haihuwa amma wai shine har yake rawan kafa a kan ta,
Lekawa tayi ta tagan ta inda ta hangoni kwance dunkule a saman kujera na dunkule waje daya ina ta sharban barci a hakanan,
Girgiza kanta tayi ta juya zuwa kitchen don duba girkin da ta dora tana cewa haka kawai an dagwara wa yar mutane damuwar da ba nata ba akai,
Duk hakkurin irin na yarinyar nan sai da yau aka kai iyakarta wanda dama so ake aga iyarkata a gidan,
Yanzu badon Allah yasa tai dabaran zuwa nan gidan ba da Allah kadai yasan abinda zai iya faruwa da ita,
Ga yarinya mai hakuri ladabi tsabta addini sanin yakamata, zakace ba karamar yarinya bace da,wanan halin ,duk an kuntata mata tabi ta ramay ta bushe a tsaye kamar wace ake miya da ita,

****** ********** ******
Tafe yake a,saman mashin din shi yana dauke da ledan da,ya,sayo cefanen kayan miya a cikin sa,
Yana aje mashin din ya dauki ledan ya karasa dashi cikin gida tun daga nesa ya hango kofan dakin Aisha kamar a rufe yake,
Bai kara gaskantawa ba,sai da ya iso gap da kofan ya hango kofan a rufe har da makulli jikinsa,
Sadiya wace jin karan mashin din shi yasa ta fitowa dauke da buta don ganin may ya shigo gidan dashi a lokacin,
Don idan bata fito ba bazata ga may ya shigo dashi ba don dakin Umma zai shiga dashi,
Sai da ya aje kedan kayan cefanen yafito daga dakin tambaya yake yana duban kofan dakin dake a rufe yana fadin ,
Ita wanan ta fitane kofan ta yake a rufe ko yaya akayi ne wai ?
Au kai baka san da fitan ta bane dama nima na shigo gidan na samu kofan dakin a haka nake tambaya ina ta tafi,
Wani iri yaji a lokacin don gaskiya ban taba fita gidan ba bada izinin sa ba,
Shiru yayi yana,tunane a zuciyar shi to ina Aisha ta, tafi batare da sanin sa ba haka, yau,
Muryan Sadiya ce ke cewa nadai ji lokacin da takewa mama Hafsi salama da zata fita,
Yanzu ai ta isane don shi har zata fita batare da umurni ba kamar matar bariki,
Batare da ya tankawa kowansu ba ya shiga dakin Sadiya yadan, zauna jim na tsawon wani dan lokaci sai gashi yafito,
Tana tambayan shi ina zai tafi da wanan ranan haka sai yake ce mata muyi da wani abokina zai zo ya samay ni a wanan lokacin,
Amsan da ya bata yadan kwantar mata da hankali don yasan cewa ta tambayane don taji idan ne man Aisha zai tafi, yi,
Shiko yana fita ya hango yaran gidan mu a kofan gida suna wasa yake tambayan su da cewa kai Aisha tana cikin gidan nan ne?
Yaron yadago kai yace wa anty yar agwai kake tambaya yace eh aciki bata rai,
Bata shigo ba don yanzu na shiga gida babu kowa a gidan mu sai su maman mu kawai ne a gidan,
Rai a bace yana jin daci a zuciyan shi ya koma cikin gida itako sadiya tana tambayan shi wai har bakon yazo ne yace wai yazo ya,wuce ina cikin gida,
Kwance yake amma yana sauraren ko zaiji dawowa na har akai sallah azahar baiji shigowana ba gidan,

Sai wajajen karfe biyu Anty ta shigo dakin tana aje kayan abincin da ta sa min a kusa da inda nake kwance,
Motsinta danaji yasani farkawa gami da dan bude idanuwa na da su kai min nauyi saboda barcin da nayi,
Kin farka injin Anty Hindatu take ce min da taga ina motsawa, na karasa bude ido da salati a bakina ina fadin ashe nayi barci ne dai haka da yawa tace cikin murmushi kin kai kusan awa uku da wani abu kina barci fa,
Ki tashi kici abinci kiyi sallah sai ki koma gida har yayan ki ma ya shigo ya,samay ki kina barci,
Nace da sauri cikin dago kai ina kallon yaya mansur ya shigo ashe tace eh a daidai lokacin da take kokarin zama saman daya daga cikin kijerun dakin,
A gaskiya baiji dafin abinda Hamza yake maki ba sai dai yace kiyi hakkuri zai samu lokaci su zauna dashi,
Nace ai da ya bar shi kawai idan an kwana biyu tafiyana zanyi kawai naje na huta anty,
Yanzu kici abinci sai ki shirya ki koma dakin,ki ga kudi nan yabar wai abaki kije asibiti don kudin basu da,wani yawa,sosai,
Idanuwa ne suka ciciko da hawaye don tausayin kaina nake cewa cikin murya mai rauni,
Har da wani dawai niya bayan wanan mutuncin da kukai min kun mayar dani tankar wata yar uwar ku ta jini, haka
Hindatu tace kai haba Aisha ake yanzu yar uwar muce ta jiki don Allah yariga da ta hadamu ko da ke,
Zan fara sanar tawa kuka tace cikin daure fuska dakata da wanan kukan naki Aisha maye na kuka dubu goma ne fa kawai ya baki don baida kudi yace a hannun shi,
Cikin zaro ido tare da tambayan ta da,sauri nace har dubu goma anty shine ba yawa,
Wanda ya ajeni ko dari daya ya kasa bani naje a duba lafiyata sai kawai na,sake kuka sai danayi ya isheni,
Na mike na shiga bandaki don inyi alwala tace min shiga kiyi wanka dayani sai kiji dadin yin sallah kici abinci,
Ban mussa ba don dama ina bukatan jin sanyi a jikina don haka na,watso ruwan koda nafito nasamu wasu sabbin tufafi a saman gadon ya ta aje min na dinkin dogon riga nawasu material masu kyau sabbi wai ta dinka amma sunyi mata kadan,
Nasa sai dinkin yai min das a jikina kurciyana yafito tsam a cikin kayan na zauna naci abinci sama sama itako tana akan bakin ta tana bani shawaran cewa,
Idan na koma kada na nuna wani bacin rai din idan muyi sa,in sa dashi zai su ji dadi ne don dama ana jiran ajimu ne dashi,
Munyi sallama tana nanata min cewa nayi kokari na tafi ganin likita don nasan abinda ke damuna,
Ban tafi gida ba,sai da na tsaya wani kayon chemist na BLB nai masu bayanin yadda naje ji suka ban magani na kashe dubu biyu da dari hudu na hau mashi zuwa gida, dauke da leda na dake dauke da tarkacen kayana aciki,
Hamza ya fito don fita waje fuskan shi kicin kinci a daure sai mukai kicibis dashi,
Ina kika shigane haka tun da safe ba wanda yasan inda kika tafi,
Na sunkuyar da kaina kasa nace mashi natafi asibiti ne don marana ya damay ni da ciwo sosai da dare ban samu yin barci ba,
Idon shi a kan ledan da ke a hannun inda ya hango maganin da na,sayo
Ban ji dadi yadda zaki fita gida batare da sanin kowa ba har tsawon wani lokaci haka,
Nace cikin sanyin murya babu kowa ne a kusa lokacin kuma maran ya matsa min da ciwo natafi can kuma sai na samu layi da yawa,
Baice min uffan ba,ya dan rabani ya wuce wani haushine ya kumay min zuciyata,
Dafa kan da zan yi na hango idanuwan Sadiya da,Asamau a kan mu suna tsaye suna kallon mu,
Asmau ce take ce min ina kika shige haka tundazu ba wanda yasan kin fita,
Ina kokarin ciro key dina a yar post dina nake ce mata shi ai yasan na fita ya dai mantane kawai,
Ai dole ya matan tunda hasken zuciyar shi bata gidan duk yabi yawani damu mutane wai ta fita bai sani ba,
Sadiya ce take fadin haka a lokacin da take kokarin juya tashige dakin ta cikin haushi,
Allah nagods ma nace tare da fadin wai Anty hindatu Allah ya,saka maki da,alheri dama ance ta yaro kyau yake baya karko,
Da nabita nawa shawaran dana yanke da yau anji mu a gidan nan anyi min dariya,
Ban bi ta kan abincin su ba don dama ba aimin tayi ba naci gaba da harkokina tare da shan maganin da aka bani a kemis,
Alhamdullahi zance don gaskiya naji ciwon yai matukar lafa min don na daina jin shi kamar baya, can,
Da dare ya shigo dakina ya bayan yai komai kamar yadda ya,saba yi zai kwanta naji ya ce min
Daga yau na fada maki kada ki kara fita gidan nan batare da sani ba don bazan dauki wanan ba a raina,
Nace amma na fada maka zancen yadda nake ji a jikina kaki ka,saya min koda dan paracitamal nasha,
Amma gabana ka fita zuwa sayawa Sadiya maganin ciwon kai yaya kake son yi da raina so kake na zauna haka ciwo yana cina a gida ba magani,
Sai na sa kuka irin mai tayar da hankali ina fadin nidai kagaji dani dama can ba wai ina cikin ranka bane
Ni banda kowa a gidan nan sai Allah sai kai sai ko mama hafsi wace ke dan nuna min kulawanta a kaina,
Kai din kuma yanzu ka dauko min wullakanci a gaban kowa yadda ranka yaso, idan ban fita na nemo magani ba mutuwa kake son na zauna nayi kuna kallona har kukai ga yadda kuke so,
Shiru yayi can yace bana ki kaiki asibiti bane bari nayi nadan samu kudi a hannuna sai muje asibitin,,
Ban tanka mashi ba shima bai kara magana ba don ganin yadda nake kuka,
Washegari bai fitaba da,wuri don yana son gyara min zuciya, ina jin yadda Sadiya take daga muryan ta don kawai yaji motsinta yafito daga dakin,
Duk da ba komai muke adakin ba ina zaune na tsure shi da idanuwa bai fito ba saida yai mashi dadi ya fito daga dakin yai wanka yafita
Kwana biyu mun dan sake jiki kamar ba komai a raina wanan sakewan da Sadiya taga tai kaman zata kama da wuta don taga kamar ina a cikin farin ciki ne, a gidan ita,
Sannu a hankali nadan hada kudin tafiyana inda na samu zuwa gurin Ummi na fada mata,shirin da nakeyi na tafiya zuwa gurin dangin mahaifina a sokoto,
Ummi bataji dadin hakan ba amma kuma sai daga baya take cewa hakan nada kyau tunda suna iya kokarin su a kaina,
Itama mama Rahana nasamay ta da zancen inda tai amanna da wanan shirin nawa da yi min fatan alheri a kan hakan da zan yi,
Sai bayan kwana biyu ranan da nake da girki nai mashi magana akan ina son zuwa sokoto na duba yan uwana,
Yace yana,son sanin dalilin tafiyan da zan yi nake ce mai wan mahaifina da ya rasu nake son naje nai masu gaisuwa sai kuma na gaida sauran dangina na can,
Shiru yayi kamar mai nazari azatona zan sha wahala gurin yardan shi sai naji yace kwana nawa zakiyi idan kin tafi,
Nace zan yi kwana goma ko sati biyu idan an yardan min da haka din ,
Ba matsala zaki iya sati biyu sai ki dawo idan kin shirya sai ki fada min lokacin da zaki wuce don na sani,
Nace ni ai ko gobe ne kace zan iya tafiya don a shirye nake ko yanzu,
Au ashe ma har kin gama shirinki ni ban sani ba nace a,a ni bawai na shirya bane naga ba wani dogon shiri ne zan yi ba ai,
Ya zuba min ido yana kallona yake cewa ki bari ranan Jumma,a mai zuwa saiki tafi Allah ya kaimu nace mai,
Nan nafara shiri na ba,wanda ya,sani a gidan sai dai kafin na wuce nake jin wai cikine da sadiya ashe sai shafwaba taje wa mutane suko duk sun mutu a kan ta,
Duk da naji wani abu a raina lokacin da na samu labatin ciki amma sai na daure naba kaina hakkuri don ban son na zama mai hassada da iyin Allah,
Habaici ko da magana na,shagube a bakin Umma,sai abinda ya karu nai kamar ban fahinta,ba,
Abakin Hamza sukaji zancen cewa zan je sokoto gurin mahaifana don an min rasuwa,
Umma cewa tayi bana an tuna ana da yan uwa ke nan ashe zasu bakuwan yayama ai karo karo a sallamo bakuwa dashi,
Nidai ranan Jumma tunda safe na shirya saida na shiga gurin Ummi nai sallama dasu na kuma fadawa baba mudi yana tasamin albarkan cewa na kyauta da zanje na dubosu,
Nai sallama da kowa na kama hanyan zuwa sokoto ni kadai a kato na farko da zan tafi gidan iyayyena mahaifana,


Barkan mu da shan ruwa yan uwa da fatan samun rahaman ubangiji a tarw da mu,
Kutayani addu,a dafatan samun nasara arayuwan mu baki daya,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,


Nasamu saura mutum biyu motar sokoto ta cika shi da kan shi ya kai ni tasha a,saman mashin din sa,
Don har nafito da kayana inawa mutane sai na dawo sai gashi yafito daga dakin Sadiya yana sa aninaiyar rigan shi tare da, gyara kwalar rigan shi,
Inda na aje kumshin kayan da,zanyi tafiya dasu ya nufa ya dauka ya daure su a bayan mashin din shi ya dauko, min yar troler din da kayana,suke a cikin sa ya aza a gaban mashi na hau baya muka fita sadiya ko lekowa batayi ba da zan fita,
Amma a lokacin da yake daki na tsaya daga kofa nai masu zan tafi Allah ya,sada mu da alherin sa,
Amma hakan nai sa tai min magana ba ta na ciki taki fitowa daga dakin nata muyi sallama, da ita,
Ina shiga motan ko minti biyar ba ayiba saiga wata mata da yaran ta ita ma ta zo sai motar tai batun tashi,
Ya zaro dubu daya,daga aljihun shi yace nai kufin mota dashi nai mashi godiya na shiga motan baya mu mata biyu da maza biyu muka zauna, a makure, motar ta,daga,,,
Tafiya muke yayin da nake tunanen irin yadda zamana da mutanen gidan mijina yake gudana mutanen da zance nake rayuwa da su yanzu,
Na gyara zama ina tausayawa kaina irin yadda duk kyautatawan da nake masu agidan basugane min sai ma kara samin kiyayyan da suke a kan samun sadiya wace ke zaman ci masu mutunci amma basu gani, hakan,
Mota tana sauka sai na tuna yadda mama Rahana tace min sai nake tambayan ko za,a samu motan zuwa kauyen mu,
Aka nuna min gurin da motacin da zasu kaini Illela, ko da mun isa illela kuma sai na samu mashin din da zan hau ya kaini Burkusuma,
Ranan haka na yini a hanya sai yamma lissa na isa garin ina ta mamaki kuma banga laifin Ummi ba da taki zama a garin ta kashe auren ta da mahaifina da dan ruwan cikina,
Wanda yafito garin jega da sokoto za a dauka akai wanan surkumin kauyen aure ace yai rayuwa acikin jeji irin haka,
Na tambayi gidan Liman Lawal tsoho kamar yadda mama Rahana tai min kwatancen idan naje garin,
Gidane irin na kauye ginar shigifa na jan laka katangar gidan ma jar lakace akayi da ita duk yaddan darje baida wani tsawo sosai,
Har gap da kofan shiga gidan mai mashin din ya,saukeni tare da kayan da nai tsaraba dasu,
Ina tsaye sai ga wasu yara sun fito daga cikin gidan dauke da kwano wai suna tallar bakuru,
Nace don Allah kuzo ku taimaka min na,shiga da kayan nan ciki ba mussu yaran kauye suka zo da sauri suka kama min muka shiga cikin gidan da kayana
Matan gidan suna a guri daya suna aikin girkin dare kamar yadda matan kauye suke yin aikin su a hade guri daya,
Nashigo masu da sallama duk idanuwan su ca akaina suna min kallon mamaki gaba dayan su don basu taba sani na ba,
Nagaishe su da aiki tare da masu ya gida da kuma lafiyan kowa,
Wata baka ta daura dan kwali waware bakinta ja take cewa boyar Allah daga ina haka ?
Murmushi na dan sake har sai da dimple dina ya dan lutsa kadan nace don Allah

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login