Showing 177001 words to 180000 words out of 299981 words

Chapter 60 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17670

ko gwago Talatu tana nan,
Da hannu suka nuna min wani bukka ginan laka mai tabbaibayin haki a saman dakin can na,nufa tare da yaran nan yan albarka biye da kaya a bayana,
Gwagona ta fito don yin wani abu dauke da roba a hannun ta sai ganina tayi a gaban ta, cikin mamaki dauke a fuskan ta tace shin Idon ta naka gani ko mafalkina nakai,
Cikin murmusawa tare da,sauke kayan dake a kan yaran da muke tare nace nita Gwago,
Mun samay ku lafiya tace keta tahe bamu da labari,lale marhabin da zuwan ,
Yaran zasu tafi nace su dakata, na bude wani leda na dauko sabulu da clean na basu suka tafi suna murna,
Daki aka, shiga min da kayana,suna haba haba da zuwana nan matan gidan suka fara shigowa daya bayan daya suna min sannu da zuwa,
Gwago Talatu tana fada masu cewa ni diyar Abu ne kanin ta da suka haifa da Ummi na,
Sai mamaki suke su na kallona nan naji wata tana fadin ai ni tun shigowar ta naga kama don kamar ta ya baci dana mahaifinta,
Kafin wani lokaci an kawo min abinci tuwon dawa surfafe da miyar kuka sai kamshin man shanu ke tashi ,
Ban tsaya wani tsandaba tunda nima sunan ina birni ne kawai na ci abincina saida na koshi dam,
Sai dare iyayyena maza suka dawo daga kasuwan nin da suka tafi ci, tun safe, wasu kuma daji suka tafi aiki, gona,kin su,
Suma an gabatar masu dani a matsayin diyar dan uwansu da basu san ni ba, yau gashi nakawo kaina a gurin su, da kaina,
An fada min sunayen su an kuma nuna min matan su da ma wasu yaran su,
Sai na fahinci a,bayanin gwago mahaifina shine karamin su a,dakin su don su biyar ne dakin su mahaifiyar su ta,bar su a gidan,
Sauran mutanen gidan duk yayyensu ne sun takwas sai dayan dakin mai mutum bakwai,
Nisawa nayi nace amma gwago ashe yawa ke gareku haka tace ai wasun su sun rasu wasu kuma sun fita daga gidan suna wani guri zaune,
Washe gari aka fara kaini gidajen yan uwa muna gaisawa dasu suna nana cewwa ba su sanni ba nima din dai ban san su ba,
Tun ranan da nazo nikewa gwagona duk wani hidima dana samu tana wa kanta irin su shara wanki har da, diban ruwa don amfanin mu,
Sai dai ban yarda na zauna da kazanta ba don da zaran nagama aiyukana zanyi wanka na gyara jikina tas ba zakace nai wani aikin wahala ba,
Wani lokaci nakan fita na taya su aikin girki muyi tare dasu wanan halin nawa ya ja min kwancinyan hankali da,farin jini ga kowa na gidan,
Don kin san shi bakauye bai son bakon shi da girman kai ko daukan kai da jin cewa ni wani ne nafiki ko nafika wayewa, yanzu zakiga kun fara kai ruwa rana dasu,
Basu girki da rana sai dai asha kunu da masa ko hura sai ganye idan an samu, da yamma ne za,a girka abinci kowa yaci,
Ranan da na cika sati daya da zuwa garin su babana suke tambayana yaushe zan koma nake cewa kila zan kai wata daya ko biyu don mijina baya gari ya tafi kurmi gurin sa,na,a,
Sunji dadin jin cewa zan kwana biyu a gurin su don haka suka sake jikin su ,
Da yamma ina taya su inna aikin girki sai naji sunyi cirko cirko suna magana a cikin jimamay cewa wai wata ke fama tun daren jiya take rusunne har ana zancen zuwa da ita asibiti,
Kamar na kyalesu sai dai na tambaya ko wacece suke ce min ai matar wani dan babana ne dake can farkon uguwa inda yai ginan shi,
A hankali nace da zan ganta aida na duba masu ita nagani sai take cewa
Ke har fa Yunusa likita ankira ya dubata yace a kaita asibitin illela a agani don abin yafi karfin shi, bazai iya ba,
Nace namiji aka kira ya duba mace mai haihuwa sai suke ce minbai shine likita don shine yaje yai karatu a birni,
Tsam na tsamay hannuna daga cikin ruwan da nake tatse masu kamun kokon su,
Jakar da,na,zuba magani na aciki da sauran tarkacen aikina danake bukata nace wa wata diyar wani babana da take gida zaune mijinta ya rasu, tana zawarci da ta rakani, gidan naga mara lafiyan,
Mutane ne gidan ancika fuskan kowan su babu dadin gani don basu a cikin dadin rai sai faman shawara ake yadda za,a tafi birni da ita,
Nake cewa bayan mun gaisa a can na,samu gwagona na ko zan iya ganin mara lafiyan kafin a,wuce da ita,
Gwagona tace may zakiyi mata Ido, likita ma yace atai da ita can cikin gari aiki za ai mata,
Ganin na dage cewa zan dubata yasa sukace a bari na shiga gurin mara lafiyan na,fara dubata,
Tana cikin wani irin condition wanda ba,a,aon mai ciki ta kai a lokacin don bata da jini a jikin ta ga kuma maleria ya kamata,
Nadan dubata da kyau naga yan matsalolin da suke damun jikinta don haihuwan ba,zai iya zuwa mata a lokacin ba sai ta dan watsake tukun na,
Tausayin mutanen muna kauye naji irin yadda ake ta masu abu a cikin duhu ba tare da sanin gaskiyan al,amari ba,
Nakira mijinta da,wasu daga cikin iyayyenta nai masu bayani wasu sun yarda wasu basu yarda ba da zancen gaba daya,
Don ba kudi suka yarda dacewa a gwada shawarana a,gani nai mata allura nabata yan kwayoyi na kara duba lafiyan cikin ta,
Nace ya samo mata maganin karin jini abata don ta samu karfin a jikin ta amma sai yace min ai baida kudi nafitar da dari biyu nace a,sayo min sprite da tumatir din leda na hada na bata ta shanye su dukka,
Sai ga mai na kuda takai kwance sai barci nafito mutane su kabini da idanuwa caaa nakoma gida, nabar su nan,
Sai zuwa,magariba na koma gidan nasamay ta ta farka daga barci nace abata wani abu mai dan ruwa tasha koda koko ne ko shayi don tayi losing din afatay din ta bazata iya cin abinci ba mai nauyi sai harshen ta ya,warware tukunna,
Tana sha sai wani irin zufa take karyo wa wanda ya nuna ta samu lafiya a jikin ta lokacin nai masu sallama na,dawo gida,
Haba zance sai yafara yadawa ai wata,bakuwar likita tazo gidan Liman tsoho tunda safe wata,mata ce ta tayar damu wai na,duba mata lafiyan yaron ta yaki samun karfin jikin shi,
Tun wanan lokacin na zama wata mai kula da lafiyan yan uwa da abokan arziki
Da yake kauye ne sai gashi wanan Yunusa likita yai karana a gidan mai gari cewa na, zo gari ina son cutawa mutane ban da takardan kare karatu irin nasa,
Sai da magana tai magana koda ya fitar da nashi aka,duba nawa sai akaga ai nafishi ilimi sosai shi course kawai ma ya yi ba karatu ba,
Nakuma basu hakkuri da cewa ni yan uwana nake dubawa bawai sana,a nazo yiba agatin don bazan dade ba zan koma,
Nan ake fadawa maigari koni diyar waye a cikin garin yace Allah sarki yarinya kinyi kokari da kikazo duba yan uwanki Allah kuma ya baiyana muna inda mahaifinki yake idan yana raye, kowa ya,amsa da,Allahuma Ameen,
Ranan da na ce matat dan uwana zata haihu sai gashi cikin yardan Allah ta sauka lafiya inda na karbi haihuwan ta,
Sai dai na lura da ina,shakan karnin jinin nan duk sai naji jikina ya sake ba shiri nai mata abinda zanyi na koma gida a gagauce na ta shega amai dole na sha magani don ina gani nima maleria ne ya kamani,
Da safe a cikin ikon Allah ya tashi wasai dani sai dai ban son shakar karnin haihuwan da a ji wanda acan baya ba haka nakeji ba, idan ina karban haihuwa sai nake cewa watakila ita wanan nata jinin yana da karfine sosai,
Alheri sosai nake samu akan wanan harkan hankalina kwance don tun ina tunanen gida hat yanzu na,saba da mutanen garin ban tunanen komai kuma again,

****** ********** ******
Karfe sha biyun rana ko abin karyawa ba,ayi ba agidan tana daki kwance abinta,
Mama Hafsi tun da ta gane cewa za,ayi tsiya a gidan sai ta kwashi kayan sayarwan ta zuwa cikin uguwa,
Umma wace ta dawo da zuman ta karya tun a gurin wanke wanke ta hango kaya kwanoni kuda nabi yooo,
Gurin da na,saba aje mata abin karyawan ta tanufa sai dai babu komai sai sauran tuwon jiya dake acikin wani kwano duk ya bushe yayi bawa ga kuda na bin su yooo,
Daga inda take tafara kiran Sadiya Sadiya Sadiya ,
Sadiya wace take kwance tana ta kwasan barcin ta hankali a kwance taji iri kiran da Umma ke mata ta farka a gigice tana cewa lafiya wai haka,
Ta bude labulen dakin ta tana cewa a,a wanan ir8n kira haka kamar wani tashin hankali,
Ni wallahi ban son idan ina barci a dinga tayardani ban tashiba sai kaina ya dinga ciwo daga yau kada a kara tayar dani idan ina kwance,
Baki a bude Umma tace Sadiya kan ki dayw kuwa ?
Ni kike fadawa wanan magana haka ba ko jin kunya ,
Kunyan may fa don na,fada maki abinda ban so ban kuma ra,ayin ana min shi,
Eyy lalai kuwa kin kai ashe baki da kunya ban sani ba haka ,
Dama shine, dalilin kiran to ban girka ba don bashi nazo yi ba dama ta juya ta,shige daki ta gyara saitin fankan ta na kasa don ya bata iska da kyau,
Umma tana tsaye sororo cikin mamaki tace a ranta ashe haka yarinyar nan take batada kunya ko kadan a rayuwan ta,
Ga yunwan da,take ji dole ta nufi gurin murhu ta fara hasa,wuta don tasan cewa, har da yaranta dole su ji yinwa don sun saba karyawa duk safe da dumamay tuwo ko koko da kosai,
Tana can tana tunane ta tabo wutw da hannunta da,sauri tafara yarfar da hannunwanta don zafi daidai lokacin Ibrahim ya,shigo gidan yana ganin abinda ya faru yake cewa Umma lafiya ?
May zakiyi a gaban murhu kuma yanzu da wanan uwar ranan haka ?
Rai bace ga,zafin wutan da ta taba yana kona mata rai taceczan nema munw abin karyawa ne,
A,a ita Sadiya bazata fito tayi ba,sai ke tace tace batw jin dadi shiyasa nafito ni nayi,
Duk wanda ya shigo ya tambaye ta,amsa daya take basu shi dai ibrahim bai yarda ba yasan halin tsiyan sadiya ne ya motsa mata,
Sai ma fita da yayi a gidan don bai iya ganin takaici yace a ran shi,
Harshi uban tafiyan Hamza yashigo ya,samu ummu tana kashe kunu a gaban murhu tana gamawa ta mayar da,wutan abinci sama,
Can sai ga,Sadiya da cup din ta bata jira ma Umma ta zuba mata ba,sai ta,shiga diban kokon da kan ta,
Umma tana futowa taganta a duke agaban roban kunu tana diban kokon da kanta,
Ikon Allah wai yaya hakane kuma da zakizo kina diban baki ko iya jiran na,zuba maki,
Wanda ta diba sai ta mayar ta nufi daki da cup dina hannun ta,
Tana,shiga daki Hamza dake kwance yaganta da cup tazo ta zauna a tunzure gaban shi tana huci yake cewa wai may nene kuma,
Sai kuka tafara cewa harda abinci kuma za aimin iyaka dashi don kawai anga banda lafiya ban dafa ba,
Rai bace yafita yana cewa haba Umma yanzu kuma don bata da lafiya shine kunun mw baza,a bata tasha ba sai a hana ta duk da lalurar dake a jikin ta, kuma,
Ikon Allah ita Sadiyan tace ma na hanata kokon ko kuma kai,
Yace ai shike nan bari na fita na,samo mata dan abinda zata ci kada ta zauna da yunwa a jikin ta, yai mata illa,
Sai kawai yafita yana cewa gaskiya ni ba ai min adalci a gidan nan duk kokarin da nakeyi sai an muguntawa iyalina,,
Umma tabi Hamza da kallon mamaki akan Sadiya da itace ta nema mashi auren ta yake mayar mata da magana agaban sauran diyan ta,
Jin yafita yasa Sadiya fitowa da buta a hannun ta tana wani fisge fisgen kai, da tafiyan gadara wai ita an cuta mata a gidan mijinta yai cin mutunci,
Yadawo dauke da leda mai take away a cikin sa yawuce dashi daki duk suka bishi da idanuwa
Can bayan ta gama ci sai ta jefo ledan take away din ta tsakar gida miyar agusi ne da sakwara taci, sai ledan pure water mai sanyi da gwagwanin multina,
Ranan Ummatakai matukar hasala,da Hamza duk yadda,taso taboye bacin ran ta abin ya,faskara,dan sai da ta nuna mai hasalan ta a fili,
Sai taga dama zatai masu girki ko shi sai idan Hamza ya lalashe ta don ya gaji da,sayo abincin kasuwa kullun,
Umma tana ganin ikon Allah ranan Sadiya tsaye tayi tace ita bazata karbi abin girki a gurin Umma ba don ba Umma take aure ba dole kayan girki yadawo gurin ta daga ranan,
Umma kamar zatayi hauka don ta hango Sadiya zata raba ta da dan ta gaba daya idan tai sake,
Ga aiki yanzu kamar zai kashe ta agidan komai sadiya bata yi wai ita mai ciki ce sai abinda take so zata ci,
Shagwaba sai yadda tayi da kowa a gidan shiko gogan baijin kunya gaban kowa,sai faman tarairatan ta yake kamar zai goya ta a bayan shi,
Yanzun ma ko fita ya,daina yi sosai koda yaushe suna tare sai bakin jaraba da,sukeyi dare da,rana, a daki,
Tafiya ya kamshi dole ya tafi baxon yaso zuwa ba kwanan shi biyar a can yadawo,
Yasamu Sadiya tayi kaca kaca da mutanen gidan nan ya hau sababi da yan uwan har yakai ya kira baba Madu kan azauna a sulhunta,su,
Bayan amayar da jawabi ir8n rashin mutuncin da Sadiya takewa Umma har yakai yaranta Jibrin da Ibrahim sun ki yarda sunyi niyar lankada mata dan karen duka,sai da ta gudu zuwa gidan su,
Shine ita kuma mahaifiyarta ta fito zuwa gidan da nata masifan na aka rikice har mama,Sa,a tana cewa
Watau abinda takewa Yar Agwai shine yakawo a kan yar ta to ita gaskiya bazata iya dauka wanan cin fuskan ba wa yar ta, don ita yarta tana da gatan ta,
Ibrahim yace oho dama,ashe don bata da gata yasa kika dauko yar iskan yarki kika cinnawa mutane mugun abu ,
Umma ta hana shi magana ta koreshi daga gidan don kada magan tai nisa sosai,
Nan dai tace Sadiya ta koma ta shiga dakinta babu wanda ya isa ya kore ta a gidan tunda ba su ke auren ta ba,
Bayan fitan mama sa,a da,tawagarta ne mama hafsi tace ni dama nasan ai za a rina don badon Allah akai wanan hadin ba tun farko,
Anyine don aciwa yar mutanr mutunci yanzu kuma sai gashi ganwo ya juye da kaya akai,
Aisha dai ta huta ai kwana biyu yanzu za,agani mai mutunci a cikin su
Ba wanda ya tanka mata don ran kowa a bace yake a gidan saida yadawo ne su Sadiya da uwarta suka kwashi karya da gaskiya zuka fada mashi shiko ya hau ya zauna yana tawa mutane yankan kauna,
Baba Madu yace haba Hamza yau ina hankalin ka yatafi da har kabari mace zata hadaka da mahaifiyar ka haka da yan uwan ka
Sai lokacin ya dan sadda kan shi a kasa saboda ya dan dawo hankalin shi,
Baba yace Hamza kada ka manta da irin dawainiyar da wanan boyar Allah tayi da ku a baya yanzu lokaci yayi da zata ji dadi a,gare ku,
Musan man ma kai da da kowa ke yaba irin hankalin ka da kokarin ka, ga mahaifiyar ka da yan uwanka har da ma mu iyayyen naka,
Ga mata yar arziki maikirki da mutunci da Allah ya hada ka da ita tun farko,
Sai yanzu ne da rana tsaka zaka bata duk wanan alherin naka akan wata mace bakuwa
Baba Sadiya ba bakuwa bace don ita yar gida ce don diyar aminiyar Umma ce,
Koma,wacece bata nuna muna cewa ita ta gida ce ba don da batabar mahaifiyar ka tana aiki da kanta ba kuma tana ci mata mutunci,
Duk inda yafito don ya kare Sadiya,sai baba Madu ya nuna mai rashin dacewan haka a gare shi har dai baba ya ce kai Hamza barin fada maka ba,a kyauta ba,
Kayi gagawan bawa mahaifiyar ka hakkuri akan wanan zancen kuma a gyara,
Ke kuma Rabi na dawo a kan ki kin san halin yaran yanzu kokai ka haifi abinka,sai kai hakkuri dasu don haka ki dinga kawar da idon ki akan matan yayan ki don yaran yanzu basu da mutunci,
Don kinga a kwai banbancin rayuwa a,tsakani ita waccan ta farkon da,wanan da kika hada da hannun ki don haka sai kinyi hakkuri sosai akan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login