Showing 18001 words to 21000 words out of 299981 words
wasun su harda dage sukeyi don su gani da kyau,
Hamza dai yana tsaye daga bakin shagin shi a cikin dakiyar zuciya kamar ya kurma ihu don bakin ciki,
Yace zai koma ta duka gab dashi sina magana kamar masu yin kiss abinda ya kara tayar wa Hamza da hankali kenan
Yaga bazai iya karasa kallon wanan cin fuskan ba ya,shige dan rubaben shagon shi ya zauna, rayuwan shi a bace,
Daga haka sukayi bankwana da Mansur bayan sun gama,aje magana akan yadda zasu hadu da dare,
Yara ta samu suka kwashe mata kayan zuwa cikin gida su,,
Kannin Hamza da akai komai a gaban idanuwan shi da zancen da su abokan Hamza din keyi ya,shige gida kaf ya zaiyana wa mahaifiyar su kamai tiryan tiryan,
Rayuwan Umma Rabi yai matukar baci inda ta hau fada da bambamin cewa ana cin amqnan dan ta da son yaudaran shi,
Tasha alwashin idan yamma yayi zata ahiga gidan gurin mahaifiyar Kubura ta,fada mata don su tsawata mata, in ma har basu sani bane,
****** ********* ******
Da yamma malam Mudi ya dawo daga kasuwa kauye da ya tafi ci don haka a gajiye yadawo gida,
Bai wani tsaya ba don lokacin sallah magriba da ya gaba to yai haraman zuwa sallah,
Acan ya samu wani ya fada mai cewa idan fa bai saka ido ga zancen Kubura ba zata saka shi a kunya,
Tiryan tiryan mutumin ke fada wa Malam Mudi duk irin abinda ya sani akan kubura din,
Umma Rabi tashigo gidan a cikin mutunci inda tai arraba da Kubura a zaune saman kushin din uwarta tana cin apple ,
Arayuwan Umma Rabi tace tabbass haka zancen yake ashe ba karya bane,
Don haka tafara zuwa gurin su Atika da Fatima suka gaisa tadan kara jajantawa ummi din da jikin ta,
Acan dakin mahaifitan Kubura wace ta samu zaune a kasa saman salaya ga kanyan marmari nan tana kasawa da alaman abokan zamanta zata aikawa, dashi,,
Suna gaisawa mama Saude tai wani hade rai tun anan Umma Rabi ta fahici da akwai magana,
Dan shiru ya biyo baya a dakin sai can Umma Rabi tace ummm, dama gurin ki nazo Saude tace to ai gani a gatsale,
Umma Rabi tace dama a kan zancen yaran nan ne shine nazo na fada maki cewa ya kamata ace kin tsawata wa Kubura don baidace ace tana kula wasu samarin ba haka, bayan tana da matsaya a kan ta,
Jin tai shiru yasa Mama Saude dagowa tana cewa kin gama tace eh, dama abinda ya kawoni ke nan kawai, don Allah ai mata fada Saude, kin san halin kurciya,
Ban gane tana kula wasu samarin ba da kikace, ?
Ta dan gyara zama tace eh mana bai dace ace kuma tana tsayawa hira da maza a kofan gidan nan da rana tsaka kuma a gaban Hamza din,
Shi Hamza din an daura mata aure ne dashi ko kuwa wai ?
Dakata Malama bazan tauyewa diyata incin taba na hanata cin kurciyan ta akan wani dan ki can,
Yarinyata,Allura cikin ruwa ce mai rabo ka dauka don haka sai kije idan dan ki yana iya shiga cikin takaran mane ma,sai ya,shiga in har rabon shi ce sai ayi dashi
O lalai k8ce min duk abinda Kubura takeyi da,sanin ki takeyin shi ashe ?
Kwarai kuwa sukaji muryan malam mudi wanda ya shigo gida rai a bace shima yazo da zancen da aka fada mai a,massalaci don yayi bincike sai gashi yaji da kunnuwan shi abinda Mama Saude din take fada, da bakin ta,
Nan akafara musayar harshe akan zancen tsakani Baba Mudi da mama Saude mahaifiyar Kubura,
Umma Rabi ta bargidan a cikin bacin rai da mamaki uwa kamar Saude ace wai ta zabawa yarta abinda ranta ke so,
Har takai kofa take jin malam Mudi yana cewa koda,Kubura zata mutu ne sai ya aura mata Hamza ,
Ita kuma mama Saude tace wallahi yar ta bazata yi aure gidan wahala,ba,
Ita a wahalce yarta a wahalce wazai kama wani a cikin su,
Wanan zancen yai matukar tayar wa Umma Rabi da hankali sosai, inda,ta bar gida duk da Atika na mata sai da,safe,,
****** ********* ******
Wanan zancen wasa wasa ya fara karfi a tsakanin mama Saude da baba Mudi,
Amma duk wanan fitinan bai sa jikin Kubura rai sanyi ba akan fitinan iyayyen nata,
Don ita sam yanzu yadda idon ta ya bude bata jin zata iya auren Hamza, don baiyi mata ba,
Bai daga cikin tsarin irin mazajen da take so ko sha,awan mallaka,
Don haka ta sha,alwashi a ranta cewa bazata taba yarda da zancen auren Hamzan da mahaifinta ke son ya tursasa mata ba,
Wanan fitinan yasa gaba daya gidan ya koma ba,wani armashi don duk mutannen gidan suna a cikin damuwan wanan futinan da,akeyi,
Magana wasa wasa har ta kai ga magabantan su sunzo an zauna dasu akan zance baba ya kafe akan sai ya aura mata Hamza,din,
Yanzu duk inda Kubura zata fita an kafa mata,dokar cewa dole sai da,daya daga cikin yaran gidan a tare da ita,
Sanin da tayi cewa yaran Atika zasu iya fadan duk wani abinda sukaga tayi yasa ta yanke cewa ta dinga fita da Aisha kawai don tasan idan tace kada ta fada bazata fada din ba,
Don haka yau taiwa baban karyan cewa suna son zuwa gidan Anty Sadiya babban yarta da suke daki daya,
Baba yake tambayan ta ko da,zata fita take cewa da yar AGWAI zata fita, dan shiru yayi sai kuma yace kada su dade a can din yafita,
Tunda zasu fita Fatima taiwa yar ta fadan cewa ta iya kanta kuma ta kama bakinta ga duk abinda ta gani don karshen ta akanta laifi zai dawo idan har tazo tafadi wani zance akan Kubura din,
Aisha tace wa mahaifiyar ta tau insha Allahu Ummi bazan kasance mai hadin hasumi ba,,,
Wasu yan kodadun kayan ta ta,saka ta sukafita duk da ita Kubura bato ace tafita da mai irin wanan shigar ba,
Dole ba yadda ta iya,dole suka,fita a hankan don shine rufin asirin ta,
Sai da tajata zuwa inda zasu hadu da Mansur din ta inda suna a cikin mota a zaune har suka gama abinda suke tafuto suka nufi gidan Anty Sadiyan su,
Ko a gidan yar uwar tasu Aisha bata zauna a daki ba daga waje ta,dawi tadan zauna tana jiran su,
Bayan fitowan su zasu tafigidane Anty Sadiya ta rako su take cewa ,
Shikam baba may yasa wai ya nace a kan zancen wanqn Hamzan da ya matsa haka ne wai,
Ai yanzu shi kamshi Hamza din yasan cewa kin wuce ajin sa,
Ya dauki yar AGwai ya bashi mana don itace daidai da wanan din, saboda yar talauci ce kamar shi,
Sai suka saka dariya har da tafawa a,tsakanin su kamar wasu kawaye can,
Daga, can gurin da take tsaye dan nisa kadan dasu tana iya jiyo hiran nasu da irin zagin da,suke wa mahaifin nasu cewa ya tara gida da mata da yara ana ta,wahala,
Har suka dawo kan zagin mahaifiyar ta da cewa wai taga guri harda daukan ciki yanzu mai ga cikin nan yana,wahal da ita babu mai taimakon ta,
Sai da,sukayi gulman su suka gaji sannan sukayi sallama da ita,
Kubura tace ke dallah tashi mu tafi kinji kin zama,wa mutun kamar wata,sojan gona,
Aisha da take sauraren su ta,sauke doguwar ajiyar zuciya taiwa sadiya sai anjima suka kama hanya, gida,
****** ********** ******
Hamza kan iyanzu ya kusa kammala karatun shi na diploma da yake yi, inda kuma yake ta har kokin shi,
Zance kubura dashi ya lafa don an dakatar da zancen baba ne dai yasha alwashi cewa sai yai mata auren nan komai abinta,
Wajen goma sha dayan dare kowa ya,samu mafaka ya kwanta suna barci a dakin Mahaifiyar ta taji kamar ana kiran sunan ta a marki,
A hankali ta fara bude idanuwanta inda take jin muryan Ummi a cikin wani irin yanayi tana ce mata ta miko mata kujera daga waje,
Ba shiri Aisha tamike ta cire sakatan dakin da,sauri tafita sai gadmta dauke da kauwar kujerar zama,
Nan ta dire wa Ummi kujerar a gaban ta, tajuya a cikin kuka,sai da uwar ta daka mata tsawa akan kada ta tara mata mutanr fa,
Dole Aisha tai shiru daga karshe dataga bazata iya sauraran halin da Ummi take ciki, don haka tafito zuwa wahe ita kadai a,tsakar gida tadan rakube a gefe guda,
Sai zuwa can taji kukan jariri zubur Aisha tamike ta shiga dakin a cikin dan rudewa,
Sai sannu takewa mahaifiyar tata dakuma kojatin kallon yaron dake yashe a kasa yana tsala ihu kamar mai shedawa duniya ya iso,
Ummi may zan taimaka maki dashi yanzu nune tai mata da hannu data dauko reza da zannuwa a gurin da ta boye su,
Da sauri Aisha ta nufi gurin dukawar ta taji uwar na,wani sabon nishi cikin rashi kuzari,
Don Allah Ummi kada k8 mutu ki barni Aisha taje fadi daga gurin da take,
Yar jaririyar ta guda ce ta karkare fadowa duniya sai wani kuka take tsalawa sosai,
Fatima ta umurci Aisha da ta tafi gurin mama saude ta sheda nata ta haihu,
Yan mintin suka shigo dakin a tare" da mama Saude da Atika nan aka shigamaram barka da, arziki tare da kammala duk wani abinda haihuwa ta kumsa,
Kafin wani lokaci sun yi komai duk sun gyara gidan yadda ya kamat,
Ranan Aisha batayi barci ba don farin ciki da takeyi ganin cewa, Allahya sauki mahaifiyar ta lafiya yau,
Washegari gida ya tashi da murna da farin cikin ganin sun sami karuwa,
Sai yan uwa da,abokan arziki suka fara tururuwan shigowa yin barkan haihuwa,
Tun wanan lokacin Aisha tazama wata busy girl bata da lokacin kanta ko kadan,
A cikin wanan haline kuma ta fara tsanan tawa Aisha tare da takurawa rayuwanta dana ta urin aikace aikacen don ta koma kamar wata basaraka a gidan ,
Saboda mahaufiyar ta tana goyon bayan ta akan zancen ta,sosai yanzu haka yasa kowa a gidan bai shiga shirgita,
Sai dagwa dagwa suke da ita don a samu a rabu lafiya kawai,
Aisha tana,dakin su tana gyara wa uwar ta daki Kubura ta kwada mata kira wai tazo ta kwashi wankin ta,tai mata,
Daga inda Ummi take zaune tallabe da yar diyar ta ta cewa Aisha akull nafa k8n tafi gurin wankin nan sai na bata maki rai yau a gidan nan,
Shiru shiru Aisha bata futo ba daga dakin yasaka Kubura zuwa ta,wani hankada masu kofan dakin tana cewa
Wai Aisha bake ce nake kira ki kwashi wanki ki min ba zaki wani shige daki ki kyale ni,
Tau sannu mara kunya diyar sarkin santal bul bazata wanke maki ba ke aiki may kike da bazaki wanke abinki ba,
Au tace cikin jefawa Ummi din wani kallon rashin kunya ashe kece kika hanata ke nan fitowa,
Ummi tace eh don ko na isa da ita to idan ba,a,son tai wani abu a gidan ta koma gidan ubanta mana,
Da,sauri Ummi ta dago kai tana karewa Kubura din kallo acikin mamaki,
Juyawa Kubura din tayi tana mai tafita tana sake mugun magana kan cewa aikuwa sun kulla agidan nan da Ummi da yarta don sai tabar mata gudan uban su,,,,
👑SARAUTAR MATA👑
0⃣8⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
RABBI LA TADHARNI FARDAN WA ANTA KHAYR AL-WARITHIN,,,
YA UBANGINA KADA KA BARNI MAKADAICIN ALHALIN KUWA KAINE MAFI ALHERIN MASU ALHERI,,,
Ranan haka muka wuni zugun zugun a gidan ba wani dadi rai alhalin tun bayan daurin aure bamu ga baba a gidan,
Ba wani bukin da akeyi kamar yadda mutane sukayi zaton yi don uwar mai buki bata da shirin buki,
Sai dai yan uwan baba sun dan taka rawa gurin ganin cewa, sun hada dan kudi sunyiwa mutanen dake nan dahuwar dafa dukar shikafa,
Ummi suna daki da yar uwar ta acikin jimamay abinda zai fito daga gurin mutanen da,suka kira da yan uwa na wai iyayyena,
Mutanen da,sam basu damu dani ba a matsayin yar su,
Don ni da farko ma nayi zaton cewa ko banda ubane don ganin irin yadda ake tsangwama min a,gidan Baba Mudi mijin uwata,
Alhalin gashi shine uban yayena da kuma kanne na
Ni kadai ce Allah bai nufa nafito daga tsatson shi ba,
Sanadiyar fitar da mama tayi a gidan bayan haihuwan yaya Audi,
Na fara fahintar hakan ne don ganin irin tarin damuwar da mahaifiyata take shiga a kaina a gidan,
Nayi zaton cewa Baba shine mahaifina amma saboda irin bakin cikinnda yake yawan cusa wa mahaifiyata dani agidan yasa na soma fahinta cewa bashine mahaifina ba tun ina karama,
Abu na biyu shine irin yadda Baba ya dauki son duniya ya,dora a kan yan dakin su Kubura duk da dai namu diyan daki maza ne,
Gashi da azahiri zaka zaci duk diyan gudan bugu daya yake masu a kan so,
Amma idan ka tsaya sosai ka natsu sai kagano tarin kin jini da yakewa diyan mahaifiya na,
Dan abu kadan zasu yi kaga kyara da hanttara daga gare shi, kodan kuskure kadan ne yanzu za,a jishi dasu har ya hada da uwar mu,
Sai da idan ka shiga gidan zaka ga matan gidan suna normal life din su a tare ne tankar babu k8shi a tsakanin su ,
Hakan ma diyan su komai a tare sukeyi komai babu wari a tsakani nice kawai suke nunawa wari a gidan babu boyo ko shayi,
Fitar mahaifiya ta agidan yadda mama Rahana ke fada min tace ya faru ne ga hadin kan ds matan gidan sukai mata wanda matsi yai yawa har takai yan uwan Ummi sun bukaci da yasauwaka mata a lokacin ,
Bayan komawan Ummi garin su sokoto ne tana cika idda ta,auri wani dan uwansu saidai shi bafillacen daji ne yana zaune a gari yana yar sanaan dabbobi,
Sai kuma zaman ba,a kai ko ina ba ya,watse saboda rayuwan ta yana gurin "ya"yan ta da ta bari a gidan Baba Mudi,
Wata uku ta kashe auren tafito ashe da akwai rabon ciki a jikinta gashi har ta cika idda ana batun komawa gidan malam Mudi sai ciki ya,baiyyana don haka aka dakata dole sai da ta haihu da yar jaririyar ta ta tare a gidan wanda tun a lokacin take ta samun wani kalubalen rayuwa daga maigidan dama abokan zaman ta dakeyi a boye,
Suma abokan zaman sun gwanmace dawowan Fatima gidan ne akan sabon auren da yaso ya kara a lokacin,
Don haka zaman nasu ya kara zama na kwarai babu mai tsangwama,wa wani daga cikin su a,fili sai dai kishin boye wanda baa rasa ba can,
Wani ikon Allah gaba daya gidan malam mudi babu yaro mai hazaka irin Aisha din,
Duk wani karatun da zatayi, zaka,ga tazo na daya a gurin amma duk da hakan babu yabon da take samu, daga gurin maigidan sai ma ya gune cewa andai batane kawai ba,wani ilimi da tafi su dashi,
Haka rayuwan Aisha ya kasance a gidan da dadi ba dadi, har zuwa wanan ranan da Aisha ta taimakawa Baba tafitar dashi daga kunya,
****** ********** ******
Gidan su Hamzs babu wani abinda suka gudanar akan zancen don basu ji komai daga gurin Baba ba,
Suna sauraren dawowan shi don anzo ance baya gida tun da safe,
Ashe shi baba tanufi sokoto ne gidan iyayyen Aisha din ya,sanar dasu irin yadda abu ya kaya,,
Da,farko kanin mahaifiyar Aisha ya dauka suka tafi can garin gurin yan uwan mahaifin yariyar don shi uban yanzu bai kusa ya kara gaba ko,,
Bayan an fito, daga massalaci suka zauna dasu inda a cikin girmamawa da mutuntawa suka karbe shi don ya rike masu jinin su a gurin shi,
Nan Baba ya,fara koro masu da bayani abinda yake tafe dashi tare da sheda masu cewa yazo ya basu hakkuri a bissa kuskuren da yayi na rashi sanar da,su
Har ya shige gaba ya,daura wa yarsu aure ba tare da sanin su ba,
Sunnuna rashin jin dadin sanar dasu da ba,ayi ba amma kuma sunyi mashi godiya da nuna cewa yana da hakki a kan yarinyar ai tunda shine ya tayar da ita, a gurin shi,
Nan suka cecmai idan lokacin da yarinya zata tare a gidan mijin ta yayi ya sanar dasu zasu shigo gurin bukin , tare da abinda Allah ya hore masu,
Wani irin sanyi malam Mudi yaji na samu mutane masu saukin kai, ya kara,masu godiya yabar su suna mai godiya, sumq din, akan rikon yar su da yayi har da aurar da ita,
Sun hado shi da dan tsaraban kauye cewa yakaiwa iyalin shi agida ai masu godiya,
Ba karamin farin ciki Baba ya,dawo dashi da ruggan mu gurin iyayyena,
Sai da dare ne ya samu iyayyen Hamza suka dan tattauna dasu yana mai basu hakuri akan sauyin da suka