Showing 180001 words to 183000 words out of 299981 words

Chapter 61 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17705

irin zaman takewan gidan na dasu Allah ya kare ku daga duk wani sherin shedan daka iya hada ku fitina agidan nan kowa ya,amsa da,Ameen baba,
Ya juya gurin Hamza yace ka,roki mahaifiyar ka gafara don ka ga,haske a rayuwan ka,
Ya mike yana cewa ni nabar ku lafiya,
Godiya,suka fara mai har ya,fara tafiya,sai ya ja ya dakata yana cewa wai ina ita,wanan yarinyan ban gan ta ba tunda na,shigo,
Jibrin ne ya bashi ansa da cewa ta tafi garin su yau sati biyu ke nan da,tafiyan ta,
A lokacin Hamza yadago kai ya dubi dakina wanda yake a rufe da padluck yana tunanen yaune fa ya kamata ace nadawo don sati biyu ke nan ashe,
Baba yace Allah sarki Allah yadawo muna da ita, lafiya yarinyan tana da hankali sosai wallahi

****** ********** ******
Washegari Sadiya ta,sa habaici a cikin gida cewa oho dai gani nan bari nan tsakanin ta da Hamza dai sai mutuwa,
Ko bata da,kirki dai dole a zauna da ita tunda mijinta yana son ya don wasu banza basu son ta ita ko ajikin ta tunda ba zaman su takeyi ba,
Ba wanda yabi ta kan ta don duk sunji maganan da Baba yai masu a,daren jiya,
Da kwana biyu ciwon baya ya kama Umma gashi dole ta dan gi wasu aiyuka da kanta don ko kallo bata ishi Sadiya ba,
Dole zarah ce tazo daga gidan ta taiwa sister dinta,su Asmau fadan cewa gasu a gida har uwar su zata zauna tana ganin bakin ciki irin haka,
Shi ke nan don Aisha bata,gida sai su su kasa zama su taimakawa umma sai dai itace zata dafa ta wanke iyakar su ci kawai,
Mama Hafsi tace ai basu da laifi don laifin yaya ne da ta koya masu tun farko ai bazataga bacin rai ba,
Sai dai ace yar mutane ne zata zauna taita masu komai su suna zaune yanzu ai gashi ankawo wacce ko kallo basu isheta ba,
Zarah tacd ai yanzu dai kowa yaga ranan ita Aisha din don wallahi idan tana nan duk wanan abin bazai faru ba,
Nan dai tai masu fada dole aka,raba masu aikin da kowa zai yi a gidan,
Hamza ya,sayo wa Umma magani din tasha ta dan samu sauki tare da robb ta shafa a,gurin,
Aiko take sadiya ta hade rai wai tana son ya,sayo mata fruits ta gyara, bakin ta tun jiya yaki sayowa yana cewa baida kudi,
Amma ai gashi ya,sayowa Umma magani yanzu ina ya samu kudin da ya,sayo maganin dashi,
Ba,wani ya,fadawa Umma ba ita,da kanta taji zancen da,suke saboda kusa da, dakin su yake,
Ikon Allah inji Umma don tasan cewa Allah ya hada ta da mara kirkin yarinya,
Gashi tana jin ana mata yaya jiki amma ko tace mata sannu Umma bata,samu ba,daga gare ta,
Dole sai da Hamza ya,sayo fruits din sannan aka zauna lafiya a gidan ita dashi,
Zarah wace ke kallon ikon Allah tace yanzu kan kin kai ga irin sarakuwar da kike so yar bana tunda kin ce Aish yar kauye ce yar tsiya da,sauran su,
Duk da abin yai dan sanyi saboda mama ta je ta samu mama Sa,a akan tajawa yarta kunne don abinda take a gidan yai yawa sosai,
Yau gashi sai aci dafa duka da dare don dole saboda tace ita bata iya wahalan tuka wa kowa tuwo da cikin ta,
Bayan kwana biyu da Umma ta samu sauki tadan fito waje ta zauna don ta,sha iska,
Sadiya tana daki tasa wakan hausa remix sai faman bin wakan take tanayi tana rawan ta,
Hamza wanda ya dawo da leda wani yaron makwabta yana bayan shi dauke da leda yaron yakai ledan gurin da Umma take zaune,
Sadiya ta dago labule tacewa yaron cikin tsawa kai kawo ledan nan nan,
Umma ta dago ksi tace mata ni nada sakon a,sayo min dan ganye ne don na dan gyara bakina dashi,
Ai baice min naki bane don haka nace akawo min don ban yarda ni da miji na ai min isa dashi don ni wallahi wanan mulkin ba a kawo min shi,
Fitowa yayi daga daki yana cewa ke sadiya ki shiga hankalinki fa don bazan yarda da wanan irin cin fuskan da kike min ba,
Mahaifiyata ce zata zama abin wullakantawan ki koda yaushe tace ita ce taba,da sako to maye kuma na jinini haka,
Umma tace kyale ta babana akai mata ledan sai ta gyara ta juyo cikin yatsunan fuska take cewa adai bar maki ke k8 gyara ,
Aiko yai cikin ta kamar zai dake ta,ranan taga masifan shi saida mama tashigo tace ya kyaleta tunda yasan tana da lalura a jikin ta,
Kofan gida yya koma ya zauna yai tagumi yana tunanen yaushe wai Aisha zata dawo,
Kewan ta ne ya kamashi yarinya mai hakkuri duk abinda akai mata zata iya shanyewa ta hade a ranta batare da wani yasan anyi shi ba a gidan gashi yanzu dan tafiyan ta komai ya kara rikicewa a gidan dama ance mugu kariyan na gari ashe kuwa haka hausan yake,


Zan dakata anan sai bayan sallah idan Allah ya kaimu sai muci gaba mu kara jin yadda abubuwan suka kaya tsakanin Hamza da iyalin shi
Dafatan zamu sha ruwa lafiya Allah ya sadamu da rahamomin sa Allah yasa muna a cikin yantattatun bayinsa,
Ayi sallah lafiya yan uwa musulmai kada ku manta kusani ga,addu,oin ku don Allah,,,,,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU

IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,


Wasa,wasa watana daya da kwanaki a gatin mu sai a lokacin ne iyayyena suka fahinci cewa akwai matsala a tare dani,
Dafarko sunji dadin zamana irin yadda nake kula da harkan lafiyan yan garin gida da,waje,
Sai daga,baya da,suka,ji ban zancen tafiya ko kadan sai suka,fara tunanen ko akwai matsala a tare da nine,
Ban boye masu ba,alokacin da,suka tuntube ni na,fayyace masu komai nan wani wan mahaifina mai saurin fushi yace aikuwa bazan koma ba,muddin bashi ya kawo kafan sho cikin garin nan ba ,
Sai yasan cewa ke ma ya ce kamar kowa kina da gatan ki, don bai dauke ki a gaban mu ba,shiyasa suke ganin kamar baki da gata ko,
Wanan zancen yasa na kara sake jikina acikin yan uwa ina ta harkokin gabana batare da na,sa wani damuwa akan zancen ba a raina,
Al,amari na kiwon lafiya take mutum ke samun alheri daga wanan fannin, don haka ba karamin alheri na,samu ba a dan zaman da nayi,
Suna jin dadina nima inajin dadin don zaka ce a cikin su na tashi tun farko saboda yadda na sake jikina dasu tundai idan har ance mutum dan uwan haihuwa nane ,
Ranan da nazo garin idan baki manta na,fada maki akwai wasu yara da,suka daukan min kaya zuwa cikin gidan mu har na basu kyautan clean da,sabulu saboda taimakona da suka yi,
Wanan kyautan da nai masu yajawo min hanyan alheri sosai a gurin mahaifiyan yaran,
Don ba karamin dadi kyautan yai mata ita,aganin ta na yaba da yaranta da har nai masu alheri,irin haka,
Sai ga matar har gida tazo mi godiya nima da aka kwana biyu na tafi har gidan su mun jima da ita duk da ba hira mukeyi ba sai hakan yai mata dadi sosai, daga haka muka saba da Yarbuga, sunan matan ke nan,
Sanu sanu har shakuwa mai karfi yashiga tsakanin mu duk da ita ma,a gidan yawa take zaune tare da,sarakanta da matan yannin mijin ta,
Duk da ba,a garin mijina nake ba hakan bai hanani kula da duk wani hakkin auren Hamza da ke a kaina ba,
Mussan man gurin shiga na da kuma yadda nake mu,amulla da mutane gurin kama mutunci na,
Kunsan yan kauye da son ganin bakuwar mace tun dai da suka,ga na kwana biyu a garin sai suke zaton kila dai ni bazawara ce ko kuma budurwa,
Sau da yawa akan tuntubi yan gidan mu akan zance na sai suke fada masu cewa da aurena mijina yai tafiyane shine na dawo gida har zuwa lokacin da zai dawo sai na koma, dakina,
Yau ma kamar kullun bayan nagama duk wani aikin dana saba yiwa gwago a,shiyan mu da kuma dakin kwanan mu,
Sai na shiga wanka nafito na gyara jikina duk da ba wani kwalliya nayi ba ina kokarin saka hijjab a kaina ne gwago ta shigo dakin take kallo na a cikin mamaki,
Fita zakiyi ne Indo gwago ce mai tambaya na ganin ina,shirin fita zuwa unguwa,
Nace gwago gida malam kabiru zan tafi na duba jikin wanan yaron dana karawa ruwa jiya,
Gwago tace hakane amma dai Indo kikara kula da kanki duk da nasan kina yi to amma, kikara akan wanda kikeyi a baya,
Don kin san mutane yanzu sai a hankali don ganin da suke maki haka a gida suna daukan cewa ke bazawara ce,
Da,sauri na juyo ina fadin nashiga uku gwago kallon da mutane ke min ke nan a she,
Tace aikin san maza da zaran sun kyalla idon su ga bakuwar mace zaki ga abin ya,zama masu tankar gasa a gari,
Shine dan gidan hakimi ya turo wurin babanki wai suna kamun kafa idan har mijinki ya,sake ki ne,
Innalilla wa,inna alaihim rajjiun nasamu furtawa tare da kaiwa zaune, daga tsayen da nake ina cewa na shiga uku gwago kada fa fushin Allah ya hau kaina,
Tace ki kwantar da hankalinki Indo don kowa ya,shede ki da kamun kai a garin nan don har ma kin fi matan su tsare dokan aure din ke ga sock ga hijjab gudan babba da kike sakawa a jikin ki,
Don haka tashi kije Allab ya tsare ki yakare ki ga,duk wani mugun abinda ka kawo maki illa a rayuwan ki ,
Na ansa da hankali da fadan Ameen gwago amma gaskiya zan daina fita cikin gari yanzu sai da dare na,dinga fita,
Dariya gwago tayi tace ai baki tsira,ba ko a haka din don wani sabon sheri za a dauka a dagwara maki a ka,
Don haka fita da rana ya fiye maki fitan daren da kike gani shine saukin ki a,rayuwa, alheri,
Badon naso ba haka na daure nafita zuwa duba yaron da nakewa treating don naga yadda lafiyan ta,shi take,
Zamu dawo nabiya gurin aminiyata maman saudat muka dan gaisa sama,sama da ita nake fada mata zancen da mukayi da gwagona don haka zata rage gani na gidan ta don tsaron mutuncina,,
Take cewa ai haka maza suke ko ita ai akwai wani kanin mijinta baiyi auren fari ba ya matsa mata,wai tai min magana yana sona da,aure,
Cikin sauri nace wa iyazu billahi amma dai mutane basu da,akidar arziki saboda son zuciya zasu mayar dani bazawarar karfi da yaji,
Tun daga wanan danan na daina fita kamar farko idan ma kazo ne na duba ma mara lafiya zan tsaya a gida sai dai ka kawo yaron na fita na duba shi inga abinda ke damun mutum, iya kofan gidan mu kawai, ban zuwa gidan kowa kuma,,
Ganin haka yasa,gwagona kara tausaya min don tasan cewa ba karamin hakkuri da sanin ya kamata nake dashi ba , saboda ganin yadda a lokaci daya na kama kaina, ga komai don gudun zargin mutanen duniya akaina,

****** ********** ******
Tafe yake a,saman mashin din shi amma zuciya shi cike take damuwa dake tare dashi,
Saboda duk kwana kin nan ya,rasa abinda ke damun zuciyan shi wanda ba komai bane ya kara haddasa mai wannan yawan damuwa sai rashin kwanciyan hankalin da,bai samu a tsakanin matar shi da yan uwan shi har ma da mahaifiyar shi wani lokaci,
Duk itace sillar wanan auren sai kuma ya kasance yanzu abin daga baya babu dadi a tsakanin su,
Wanda yake ganin hakan duk laifin Umma ce wacce bata sararawa matar tashi duk da tasan cewa tana dauke da lalura a jikin ta,
Amma baisa su daga mata kafa,ba,su barta da halinta duk yasan cewa ita ma Sadiya ba a baya ba gurin takkalar magana, agidan,
Don kullun idan zaiji fitina daga itace zancen fitinan zaifara fitowa, amma sai ya take gaskiya wai, don kada ranta ya baci ya shafi dan dake a cikin cikin ta,
Tunda shi haihuwa yake so yanzu kamar zai tashi sama ya fadawa Allah, akan yana son ganin gudan jinin shi a duniya shima,
Ga Sadiya wacce ta kura mai ido don taga yadda zaiyi da ledan hannun shi, don ganin su Umma a,tsakar gida yayi,
Ga kuma su Umma da mama,da,sauran yan uwan shi duk idon su a kan ledan,
Cikin dakewan zuciya ya wuce su ya mika mata ledan yayin da yai murya kasa kasa yana cewa ta dan san mai ya ba,su Umma koda kwara biyu ne su ci,
Duk suna kallon abinda ke faruwa a gaban su take cewa wanan dan abinda baida yawa zai ce sai yabawa wasu sun ci,
Mama Hafsi batasan lokacin da take cewa ba amma dai ke wanan yarinyar baki da mĂștunci yanzu wanda,zai bawa mahaifiyar tashi kikewa wanan tsiwar ba kunya agaban kowa,
Ki dai ji tsoron Allah don kema uwace watarana zaki haifa ne ai maki duk yadda ki kaiwa wata,
Haba mama Hamza ya tare zancen da sauri a cikin bata rai yana fadin wanan ai mugun fatane kawai akewa mutum amma don Allah dan wanan zancen ai bakai ace an tsaya wanan zance haka ba,
Cikin mamakin shi duk wanda ke gurin yake kallon shi yadda ya murje ido yanawa mama hafsi tsawa akan matar shi,
Matar da tun suna kanana take faman dawai niya dasu a duniya ta dauke su tankar diyan da ta haifa da cikin ta,
Cikin mamaki shi mama take kallon shi ida ta iya bude baki da kyat tace Hamza kan ka daya kuwa don wanan yarinyar mara mutunci yau har idon ka ya rufe kana fada min magana iya son ranka,
Mama idan dai ba wani fitina kike nema ba a gidan nan banga dalilin yin wanan magana ba don dan wanan abin dana kawo mata don tana marmari kawai shine har abinda ya tsone ido, kuma,
Mama zatai magana Umma wace take zaune kamar ruwa ya cita tace barshi hafsi ,
Idon tani ce ya kawo mata abinda ma yafi wanan agidan nan bazan kara mai magana ba,
Sadiya ce ta saka wani irin kuka ta mike da ledan a hannun ta zuwa dakin ta tana cewa ita gidan su zata tafi don dai kowa ya tsane ta agidan ,
Ba yau ba tasan cewa mama hafsi bata kaunar ta akan Aisha take gwada mata kiyayya tau ita zata bar masu gidan bazata zauna da,su ba sai dai idan yana son ta ya nema mata wani gida ta zauna,
Ya juya idan iyayyen nashi suke yana fadin kin gani mama yau kun kai ga yadda kuke so
Ni ba zan yarda a rabani da mata ta ba muna zaman lafiya kowa a gidan nan ya tsane ta ba mai kaunan ta,
Ya bi Sadiya daki wace, take cewa cikin sabo hijjab din ta tana shirin barin gidan cikin kuka,
Zan bar gidan sai ku zauna da,wacce kuke kaunan zama da ita kullun Sadiya ce mai laifi,
Hamza yana cewa nace ki dawo babu inda zaki tafi don dani kike zama bada wani wani ba agidan,
Amma haka bai sa ta tsaya ba fuuu tabar gidan da kukan ta zuwa gidan su cikin kukan kissa da kisisina,
Hamza din yabi bayan ta a gigice yana lalashin ta yana bata magana akan ta dawo wai zai dauki mataki,
Suna fita mama ta juya inda Umma take tana fadin cewa yaya kinga irin annobar da kika jawo wa kanki a gidan nan,
Yarinya karama da irin wannan makircin manyan mata haka kamar wata uwar mata,
Umma tace ai da ki kyale su hafsi don duk abinda ake ina gani kyalesu kawai nake yi don ban son yawan fitina,
Yaya,bazan kyale ba don kona yaron nan yarinyar nan ke son yi a gidan nan,
Yana zaune da matar arzikin shi yar mutunci amma kikai ruwa kikai tsaki akan sai ya kara,aure wai Aisha bata da kirki,
Yau ga irin abinda kika daukowa,kanki a,gidan ruwan dafa kanki da kanki wanan makiran yarinyar idan ba,a yi da gaske ba,sai ta rabashi da kowa a gidan nan
Yanzu gashi yarinyar nan daga zuwa ganin gida wata biyu da dan kai iyayyen ta sun rike ta a can ,
Nan kuma babu wanda ya bi bayan ta a ga may ke faruwa da ita da,sunan sati biyu gashi har yau bata dawo garin nan ba,
Ibrahim ke tsaye wanda ya,shigo gidan don ganin fitan Sadiya da kuka dan uwan shi yana bin bayan ta a cikin tashi hankali yana son ya tambaya ko may ke faruwa sai kuma ya samu mama hafsi tana mayar da magana,
Can Hamza ya shigo gida rai a bace nan yake cewa cikin bacin rai shi gaskiya ba zai yarda a kashe mai aure ba don yana son matar shi,

Sai da yamma iyayyen Sadiya,suka kira akan cewa lalai sai ya canzawa Sadiya gurin zama tunda ba,a kaunar ta a gidan,.
Nan ya nuna masu cewa gaskiya baida zarahin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login