Sarautar Mata

Chapter 62 of 94

har iyayyen shi babu ragowa akan su,
Dafarko tanayi Umma najin dadi ashe abin zai dawo har a kanta itama,
Takance ke yar agwai taimakonki nakeyi don kinga yanzu inna haihu sai kawai ki dinga goya min Baby nikuma bada dadewa ba sai na kara sambado maku wani,
Darawa sukan yi kawai suna jin dadi wai Sadiya ta samu ciki, duk da bai daukan wanan zancen a lokacin don idan yai magana Umma takance ina ya fito,
Yau gashi bata,barkowa ba agidan kowa tanawa shedana son ran ta,
Kamar kada Aisha ta dawo da ciki sai bala,in ya karu mata kullun yanzu a cikin tashin hankali take a gidan,
Wai shi muna,fuki ne yasan matar shi nada ciki amma yaki fada mata tunfarko ya boye mata zancen,
Sulaiman Abokin shi ne da suke hira duk yamma a kofan gidan sune yakecewa,
Mijin Aisha angon Sadiya tunanen may kakeyine haka tundazu ana magana bakace uffan ba,
Dariyan yake yaiwa Sulaiman din tare da dunkule hannayen shi guri guda a,saman kirjin shi cikin dan murmusawa,
Yake cewa ina tunanen wani mutum ne abokin sana,a ta mutumin kirki dashi wallahi,
Aiko gaskiya kayi kokari ka jona dashi don mutumin arkizi ba,a sakaci dashi,
Zancen sulaiman ya tsaya mashi a rai sosai sai yake tunanen duk yadda zaiyi ya gyara tsakanin shi da Aisha sai yayi kafin abin yafi karfin zaton shi,

Nafito daga daki daure da zani agaba na sai dan karamin towel dana dan yafa akaina zuwa kafada na,
Ina duke a bakin randa ina zuba ruwa a bucket don na,watsa kafin maggariba yayi,
Sai ga Hamza yashigo dauke da buta a hannun shi da alama ruwan alwala zai diban masu a waje,
Cikin wata murya mai taushi da laushi nake ce ma Sannu da zuwa tare da karban butar daga hannunwan shi,
Ya karba min yana mamaki a cikin rashi don dazun da yashigo ko kallo bai isheni ba amma,yanzu sai gashi cikin mamakin shi na karba mai a mutunce tankar babu komai a tsakanin mu
Karban butar nayi na zuba mai ruwan tare da kokari mika mashi ,
Daidai wanan lokacin ne Sadiya ta fito da, dakinta tana cewa nagan ku muna fukai banza kawai wai kuna ci min amana ku fake ga zuba ruwa a roba kuna cewa wai taimako,
Ke dauki bucket din ki ki tafi inda zaki wanan yar fitina tafara jidalinta ke nan,
Haka zakace mana munafuki kawai rawa kan da kakeyi dan kaga ta,dawowa da dan abin duniya,
Har yafita yayin da take tsaye tana masifa ita kaida,a gurin,
Kai ke dai wanan yarinyar wallahi kin faye masifa ace mutum.kullun sai mutum yai masifa a raguwan shi na,safe daban na yama daban,
Kibawa kan ki lafiya kawai yafi amma wanan irin rayuwan bai ma ki kyau ba wallahi,
Rufe min bakikin ki tsohuwar munafuka kawai ai dakece ake hada bakin duk abinda akeyi a boye,
Cikin mamaki Umma ta bude bakin ta tana cewa Sadiya nice kuma mufuka yau gidan nan,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE


Duk abinda ke wakana a tsakanin Umma da,Sadiya ko kallon ba su isheni ba, banyi har aci a,sude don kan su, akeji saboda kaikaine ya koma a kan mashekiya
Don nice akaso aiwa wanan hadin kan aimin cin fuska yadda rai yaso,
Sai Allah ya kareni daga duk wani sheri da kule,kulen da aika yi akaina,
Matsala ta tsakani nada maigida na ne ban damu da,zancen su ba ni sam,
Don da,zaran na karbi girki mun shiga cikin rikici ke nan da,shi akan wai gudun shi nakeyi,
Sam yaki gane kaina tun da na dawo acikin ya,dan samu rangwamay ke nan akan fadar da mama tai min,
Yau ma kamar kullun ina zaune a bakin gado na na zuba uban tagumi fuskana babu sasauci a cikin sa,
Babu abinda nake tunane sai irin wanan rayuwan da na tsunci kai na a cikin gidan Hamza,
Tambayan da a kullun nakeyiwa kaina shine a haka zan zauna naita zama har na haihu abinda zan haifa ya tsunci kan sa cikin irin wanan rayuwan,
Jin an taba kofa dakina yasani saurin dago kaina duk da nasan cewa ba kowa bane sai Hamza,
Shigowa dakin yayi da,sallaman shi na dan dago kai tare da dan tsura mashi idanu,
Gaba daya naga duk ya canza min a fuska ya sauya min duk ya ramay yai baki ga,sutura,duk sun yi wani motsu motsu,
Sannu a hankali yakai zaune daga gefena kadan yana mai sauke ajiyar zuciya,
Cikin sanyin murya yafara min magana da cewa,
Aisha wanan zaman banzan danakeyi a rayuwa ta ya fara isata ace mutum ya zauna ba wani sana,a da yakeyi dan kudi na,shigo mai na rufin asiri
Sai da kullun mutum ya yini zaune a lalace ba wani abin yi a gaban shi,
Gashi banda wani dan uwa ko jigo da zan iya tunkaran shi don ya taimaka min
Cikin dan tausasa murya nace niko a ganina may zai hana kafara dan aikin karfi kana samun dan canji, don kaga girman kai shine ke cutuwar dan arewa,
Shiru yayi tare da dan furzar da iska daga bakin shi a hankali,
Yace in sha Allahu zan gwada hakan ko zan dan samu nayi nayi,,
Can kuma sai yadan tausa muryan shi yana cewa,
Ni abin ma duk yai min yawa wallahi a waje ba dadi gida ma ba,dadi mutun da iyalinsa suna gudun shi balle na,waje,
Nace cikin daure fuskana saboda na gane may yake nufi, haba, dai yaya ya kamata ace iyanzu ka fahince ni fa,
Bafa zan yarda na karya dokan likita ba don idan wahala,ya cika dani babu mai kula da al,amarina balle ya taimaka min, da ko zuwa asibiti ne balle gurin likita,
Hmmm Aisha Humaira ya kamata ace yanzu k8n hakkura da,abinda ya faru a baya tsakani da ke bawai ki rike zancen haka ba,a ranki,
Wallahi, Kinji na,yi maki rantsuwar muslmi zankiye duk wani hakkin ki da bacin ranki da,ya rataya a kaina da yardan Allah,
Cikin dan daga murya da ban tabayi mai ba nake cewa bana bukatar rantsuwar ka don ni lafiyata yafi min ko a yanzu
Don ko cikin dagani har kai bawai mun san da zuwan shi bane don da na riga kowa kin yarda da,shigan shi a jikina tunda ba,a kaunar hada zuria dani a gidan nan,
Don haka wallahi ba zan saurareka ba don kuwa ni baka da abinda zaka fada min ,
Duk irin halarcin da nai a gidan nan a,rayuwata rana daya aka nuna min cewa niba yar mutunci bace a gurin ku,
Tun dana fara magana kan shi yana kasa sadde bai tankamin ba sai can naji ya sauke ajiyan zuciya tare da shafan kan shi a hankali,
Yadago jajayen idanuwan shi yana cewa mai yazafi haka Humaira dakike fadar wanan magana?
Na kara cewa a hasale rashin kaunar da ka iya,rufe idanuwan ka,kanuna min a fili shi ya jawo hakan,
Yace naji zan dai kyale ki ne don lalurar dake a jikin ki kawai amma in bashi ba,ai bakifi karfina,ba,wallahi,
Wani irin azaban radadin soyayyar Humaira yake jin yana taso mashi yana,sukar masa kahon zuciyar shi ,
Mikewa,yayi rai a bace komai duk ya rikice mashi a lokaci guda sai yake cewa, naji nasan yanzu baki bukata na,a,rayuwan ki ko kadan akan abinda ya faru a baya tsakanin mu
Wanda ke kin san cewa hakan bayina bane kawai akasine aka samu a tsakanin mu,
Wani irin kallon na,watsa mai mai nuna tsana a fili
Murmushi mai nuna takaici yayi cikin kada kan shi, yana tafiya yake cewa watarana zaki fahinci cewa ni ba makiyin ki bane ai,
Ya dan kai hannun shi da,wasa yana son ya lakatar min hancina cikin sauri na gwauce ina cewa wallahi kada ka fara na fada maka,
Yayi yar dariyar yake tare da cewa Allah ya kyauta yafita yabar dakin ran shi a bace,,
Ganin da nayi ya bar min dakin yasani rakashi da hararan takaici nace a fili je ka karata can da matar ka kunfi kusa ai,
Muddin ina tuna irin kuntata min da Hamza yayi a gidan banga ranan da zaiyi fari a,gareni ba
Da irin wanan tunanen ne har naji an soma kiran sallah magariba haka yasani mikewa zuwa yin alwala,
Shiko yana fita kofar gida ya koma ya zauna tare da soma tunanen duniya,
Sadiya ta,shigo gidan ahi ta,bata mashi zaman lafiya da matar shi mai kaunar shi a,rayuwa,

Alhamdullah don yanzu abubuwa sun dan daidaita a tsakani da maigidan amma babu zancen kasan cewa tare da maigida a tsakanin mu don ban bada fuskan yin haka ba
Saboda na fada mai ban daukan wanan akidar a tsakanin mu yanzu,
Duk iya irin wayyon su na maza yai min amma bai samu kaina ta wanan harkan ba,
Karshe ma,sai cewa yake wai ina gudun shine shiya kawo haka a tsakanin mu sai dai na nuna mai cewa saboda ciwon maran da ke samuna yasa likita ya fada min na,tsare kaina,
Hakan yasa ni samun sassauci akan bibiyata da yake yawan yi kan zance guda,

****** ********* ******
Natsuwa ta soma zuwa wa yaya Hamza don shawaran da na bashi na yadan fara buga buga shi yabi,
Matsalar sho gudane shine fitinar Sadiya gashi ba dama ya dauki wani mataki a kanta don tana da tsohon ciki a jikin ta,
Sai dai yanzu da cikin ta ya girma ta dan rage fitina sai dai sa ido daga zaune take yaba bakar magana ga kowa a gidan ,
Harkokina nake normal duk da ina cikin lalura amma ina dan sana,ana danakeyi don gujewa zaman banza,
Kamar yadda kowa ke fada min cewa naci faba da hakkuri hakan nakeyi,
Don al,amarin ubangji haka yake, wani lokacin sai yayi maka abinda zakaita bakin ciki akan shi saboda wauta da rashin hakkuri irin na mu na dan adam don rashin sanin abinda yake boye a,gurin Allah,
Sai daga baya sannu a hankali zakagane ai wanan abin shine alheri da a kullun kake roko gare ka ,
Don haka yanzu da na,samu natsuwar hankali a gida sai na fahinci cewa shigowan Sadiya a cikin mu wani hikima ne na ubangiji rashin ganewa ne yasani tayar da hankalina da farko a kan zaman ta,
Don ni kadai nasan irin zaman ukubar danayi tare dasu Umma da yaranta a baya,
Rayuwa nayi a gidan irin na bauta banda yancin kaina ko kadan a gurin umma,
Nakan ta rokon Allah da yakawo min agajin da zan samu sasauci akan zaman aurena a gidan Hamza na samu saukin al,amari,
Batare da wata fitina ko hayaniya tsakani na dasu ba ta jajibo wa kanta auren Sadiya agidan wanda yanzu shine sanadin samun saukin duk wani yawan fitinansu da,sa ido a kaina,
Sai gashi da yin auren ba,aje ko ina ba zaman yaki dadi a tsakan su ni kuma na samu nawa yancin ta sanadin hakan
Don haka duk halin da bawa ya,samu kanshi da mu tashi muna ta kishi irin na hauka a tsakani gara ki san yadda kika kama kanki ta hanyar hakkuri da dan basarwa har Allah ya kawo adadin abin,

****** ********* ******
Mun wayi gari da labarin haihuwan Zarah wanda kowa a gidan farin ciki yake,
Mama bata tsaya ba ta nufi gidan da yan komatsai irin wanda uwa take kaiwa yarta idan ta haihu,
Kamar su roban wanka na yaro da uwa sabulu wanda akewa hadin kamshi kala kala, da yan sauran tarkace irin na,al,ada,
Zan ita cewa tun bayan dawowana daga gida wanan ne karo na biyu dana fita daga gidan zuwa uguwa,
Na,shirya a cikin yar atamfana zani da riga masu ruwan grey color da farin zane,
Na kawo hijjab dina na dagwara a saman kayan tare da jawo kofan dakina ina kokarin kulle kofan ne Hamza ya shigo gidan,
Ranan yana dakin Sadiya ne don haka ban tsaya ga abinda nakeyi ba sai muryan shi da nakeji daga bayana yana fadin,
Zaki fita ke nan na dan juyo ina cewa eh ina son zuwa kafin rana yai min a hanya don da kafa nake son zuwa,saboda na mike kafana,
Kada ki rufe idon shi a kan kofana danake kokatin kullewa,yace ina son daukan wani abu a dakin,
Hakan yasani bude kofan tare da dan jaye jikina don ya shiga daga ciki,
Bayan shigan shi sai na dan bi bayan shi zuwa cikin dakin da ya shiga din, na samay shi a tsaye yana ce min
Kinyi matukar kyau Humaira cikin nan ya yi maki matukar kyau sosai a jikin ki,
Sai dai kassh ana min rowan na gana da dan tayina saboda wani hujja na likita wanda ba gaskiya bane hakan,
Anya Humaira baki tinanen cewa kina shiga hakkina da yawa a gidan nan,
Mutum da matarshi amma baida daman ya tabata ace mai zai aikata zunubi ne
Cikin natsuwa nace mai wanan ne dama abinda zaka dauka din ko kuwa,
Murmushi yayi tare da kokarin jawoni zuwa jikin shi,
Da sauri na dan gwauce daga rugumar da yai niyar yimin tare da cewa kada ka manta da cewa banice da hakkin kaba yau,
Koma nice din wanan abin bazai yi a tsakanin mu ba don ni lafiyata tafi min komai,
Yar murmushi ce ta subuce mai da sauri ya dan jaye min don bani hanya na fice daga dakin,
Tsaye na samu Sadiya kamar zakanya tana mai kallona cikin nazarin ko da,akwai abinda ya faru a tsakanin mu dashi,
Nakecewa yar wahala sai kitayi don kece da wahala ni wanan bai damayni ba yanzu,
Dakin Umma na nufa don nasallamayta cewa zan tafi a daidai lokacin da lokacin da ya fito da wani leda a hannun shi,
Kamar bai fahinci mai Sadiya take nufi a ranta ba, ya wani sha toka fuskan shi a daure babu annuri,
Ganin ya fita na koma na rufo kofa dakina a cikin zazzakar muryana mai tare da wani sanadarin dake sanya mai sauraron ta rudani,
Saina dawo zan tafi barka a gidan Zarah na ce mata batare dana tsaya jin mai zatace min ba
Sadiya tana jin abinda na fada ta wani dan tabe bakinta tana cewa wanan matsalar ki ce don baki zama kowa agurin su,
Tankar banji taba sai fitan danayi abina sai jin muryan ta nayi tanacewa Hamza dakai nake magana,
Nafita ina murmushi don nasan kaidin kishine kawai don kada mu fita tare dashi agidan tai wanan magana,

Tafiya nake a hankali har nakai gidan su zarah din dake cike da jama,a yan zuwa barka,
Na samu mama hafsi agidan itace mai kula da zarah da yaron ta,
Taimin sannu da zuwa tare da bani gurin zamana zauna alokavin zarah wace tafito daga bayi take cewa ,a,a maraba da matar yayana,
Cikin murnushi nake cewa matar yayan ku tana can gida zaune,
Ni yar uwarkuce don haka ku daina zolayata haka da,wanan sunan,
Dariya zarah dake kaiwa zaune takeyi tace rufa muna asiri da wanan bakar anobar matar
Ni ai Sadiya takai min ko ina agidan nan Aisha wallahi da ace ina da iko da zan fitar da ita aida yanzu zamanta da ta a cikin gidan mu, ya kare,
Ledar dake a hannuna na kayan jariri da zanin daukan yan barka na mika ma mama ina cewa asawa jariri ba yawa
Godiya sukeyi tare da kokarin warware ledan don ganin abinda ke a cikin ledan,
Nakarbi jariri daga hannun mama ina dan murmushi tare da cewa masha Allahu
Allah ya raya muna yasa dadin musulmi ne wanan baby haka maigirma zarah kinyi kokari wallahi,
Murmushi tayi tare dan dan zuba ruwan zafi a cijin wani cup ta kawo kunu mai zafi ta zuba kawai ta dan fara kurbawa a hankali,
Itace ke sha nice daga gefe nake dan rutse idanuwana a hankali don jjin zafin nakeji kamar nice mai shan ruwan,
A take naga ta wani hada gumi a fuskanta zuwa wuya nadan kalleta a cikin murmushi nace sannu,
Itama murmushin ta mayar tare da dan share zufan tana cewa aikema kina saman hanya Aisha,
Gidan an samu karuwa alokaci daya Umma dake ta cewa wai anki a haihu gashi da,Allah zai bayar sai yakawo muna duk a lokaci guda ,
Ikon Allah dama ai gajin hakkuri ne irin namu na dan adam ana sa Allah dole ne bai tashi ba
Yanzu bagashi gurin neman kiba an samo rama ba may auren Sadiya ya kawo wa yaya a rayuwanta banda zubar da mutunci a idon duniya,
Ina dadin ka zauna matar danka tana maka rashin mutinci a bainan jama a harda batin nakasa ta,
Lokacin danake fada mata illar abinda take kokarin jawowa kanta zuwa tayi tafadawa Sa,a suka zo gidan sukai min rashin mutunci shine har yau ba mu gaisawa da Sa,a ko mayawa goma zatayi gidan nan ba ruwana da ita,
Kin san tashin yarinyar nan kin san kuma halin uwar ta amma har ki yarda ki hada zuria da ita don rashi sanin ciwon kai,
Zarah tace ai yanzu yafita a tsakanin su nima kaina saida nai laifi a gurin Umma don nace kada tayi wanan hadin da take sonyi zai iya kawo masu matsalar amintakan su,
Amma Umma ta rufe ido tai min tas akan shi harda fushi tayi dani saida Alhaji yakaini na roketa gafara,
Yanzu gashi za,a hada zuria dasu kinga ai dole ayi hakkuri da zaman ta tunda ina zata,
Zarah ta,amsawa mama dacewa nima zancen da shi yaya Hamza yake min ke nan yace bazai iya rabuwa da mace mai ciki ba haka don shima yana gudun aiwa diyan shi ko kannen shi watarana,
Don na kawar da zancen don sam ban ma son naji zancen Sadiya da Hamza din sai cewa nayi amma a,asibiti kika haihu ko tace dolema Aisha ina zan iya haihuwan wanan yaro agida,
Nan muka nausa a hiran yadda ta sha wuya wurin haihuwa duk inajin tsoron hiran yafiye min jin zancen Sadiya da sukeyi,
Don ni kwata kwata ban son zancen ta a raina saboda irin wanan zancen yana bata min rai sosai,
Don gaskiya kishiya koda wace kuke zaman lafiya ce sa ita dole

Download complete TXT · Novel page