Showing 183001 words to 186000 words out of 299981 words

Chapter 62 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17693

yin haka yanzu sai dai ayi hakkuri akan zai dauki mataki akan al,amarin za a gyara komai,
Amma sai mahaifiyar Sadiya din ta iya nuna cewa sai dai mama hafsi tabar gidan don bazata yarda yar ta,ta zauna da ita gida daya ba bata kaunar ta,
Hamza dai hakkuri yake bayarwa cikin kwantar da kai yana cewa ayi hakkuri zai dauki mataki in Allah ya yarda,
Andawo mai da,Sadiya a daren don ita kanta ta fadawa mahaifiyarta a mayar da ita saboda,bazata yarda ta kwana gidan su ba kada a juya mata kan shi idan bata kusa,
Ba kunya washe gari ya nunawa mama cewa wai zata iya komawa garin su da ta,fito don shi zaman lafiya yake bukata a tare da iyalin shi,
Mama Hafsi take ce mai ya kwantar da hankalin shi, don
Itama tafi bukatan tabar masu gidan su tunda bai san darajan iyayyen shi ba ita bazata zauna tana kallon yadda yake wullakanta mahaifiyan shi a gaban ta ba,
Sai da Ibrahim yafito daga daki yanuna mashi cewa shima fa namijine cikin nuna,shi yake cewa babu inda mama zata indai don wanan munafukar matar takace, wace ta shigo don ta watsa muna gidan mu,
Yau gashi matar ka ta kwarai saboda mugun halin da ta sakata, tai tafiyan ta gurin iyayyen ta sun rike abinsu can,
Kana nan kana hauka akan wannan mara mutuncin matar taka wacce bata da kirki har kake wani zakewa akanta,
But Sadiya tadago labulen dakin ta fara surfawa Ibrahim zagi ta uwa ta uba tana aibanta shi da mugun kalamai, daga baki ta,
Umma dake ta hakkuri tana, hadewa don kada a ji muryan ta zancen bata san lokacin da tace ke ar, da halinki sadiya baki da mutunci ko kadan wanan mugun kalami irin haka ga dan uwan mijiki baki ko jin kunya ko nauyi,
Haba ai sai ta juya a kan Umma tana fadin dama duk bakin ku a hade yake nasani babu mai kaunata don ba don Allah kika yarda da,zancen auren mu ba,saida mamana tasan yadda ta shiga ta fita tafi karfin ki,
Don haka ni bazan kyale kowa ba a cikin ku aure ne da Hamza nayi sai mutuwa, babu yadda zakuyi dani,,
Duk wata bakar tsohuwa da bata san kama, mutuncin ta ba nima bazan ji kunyan ta ba daga yau,
Baki bude galala Umma take kallon Sadiya tana sauraren ta duk mamakin kalaman ta akanta ya cika ta,
Sadiya taci gaba da fadin dama nasan ki gurin son kai da nuna son diyan ki din haka idan kin shigar mashi ne an sayar maki sai mu kara dake,
Ni ba yar Agwai bace da kuka raina keda duyan ki kuke takata a duk lokacin da kukaga daman yi mata rashin mutunci, sai kuyi,
Sai hamza ne wanda yafito daga bandaki yake cewa ke ke ashe bance kada naji bakin ki a gidan nan ba kuma,
Ina bata tsaya sauraren shi ba,sai daga harshe take tana fadawa Umma da danta abinda duk yazo mata a,bakin ta lokacin,
Suna shiga daki mama hafsi tanisa tare da cewa, ki ga irin bala,in da kika kwasowa kanki da hannunki,
Lokacin da na nuna maki rashin dacewan haka, kikace ina bakin ciki da karuwan danki a fili, yanzu wa gari ya waya ?
Washegari da safe Baba Mudi yasa aka sallamawa Hamza inda yafito yana ganin Baba ne duk sai ta dan dabuce dan kunya da nauyin da ya kamashi,
Badon komai ba don ya dade suna wasan buya da shi don sam bai yarda su hada hanya da baba din don nauyin shi yake ji sosai,
Baya ce mai bayan sun gaisa Hamza idan nauyin iyali ya hau kan mutum sai ya hada da hakkuri don kowa da halinai aka zama dashi,
Kaga mu maza idan munkayi sake har mace tayi galaba akan mu ba karamin kona mu sukai ba, akan iyayyen mu,
Don haka kayi aniyan gyarawa da mahaifiyan ka kada ka bari shedan ya rude ka akan uwar ka don mace shedaniya ce idan ba,a dace ba,
Hamza ya gane nufin Baba ke nan yaji hayaniyar da akai a gidan tun shekaran jiya,
Don haka kunya da nauyi suka kamashi don yanzu hankalinshi yadan fara dawowa yasan Sadiya shu,uma ce sai dai babu yadda zai yi saboda gashi aure ya hada kuma har da rabo a tsakani,
Shi kuma gaskiya yanzu yana son haihuwa sosai don tun Umma na fadi bai dauka har yanzu abin ya shiga ran shi sosai,
Godiya ta sakeyi wa baba yana cewa ya gode insha Allahu za,a gyara da yardan Allah,
Sai kuma yaji abinda yake nokewa akan shi Baba ya sako zancen da cewa,
Kayi kokari katai ka taho da matanka don nasan cewa akwai dalilin da yasa takai har wanan lokacin a can,
Amma in katai koma manene zakaji don nasan iyayyen ta mutanen kirkine sosai, baza su rike ta har zuwa wanan lokacin ba haka kawai,
Yace cikin ladabi in Allah yaso Baba zan tafi idan na dawo daga tafiyan da zan yi,
Allah yaba da ikon zuwa inji ba yace shike nan ni zan tafi kasuwan Kalgo don yau na taka ci,
Yaiwa Baba a dawo lafiya ya juya zuwa gida yana tunanen zancen su da Baba shi dai gaskiya dattijon nan yana ganin mutuncin shi don mutum ne wanda yasan ya kamata,
Duk ya ya bashi diya a lokacin da ya ke da bukatan taimako yazo ya kasa rike mai ita yadda ya dace baisa yagan shi zai fada a masifa ba ya ki fada mai gaskiya,
Sai kuna zuciyan shi take ce mai itama Aisha may zai sa ta tafi ta wuce lokacin da ya bata ta dawo taje tai zaman ta, har wanan lokaci haka a gurin iyayyen ta,
Wanan dalilin da zogin ganin yana da wata mace a tare dashi yasa shi shareta kawai yana gani ai in tagaji zata dawo da kan ta tun da ba fada sukayi ba lafiya kalau suka rabu da ita don shi da kan shi ya kaita har tashan mota da zata wuce,
Indan da tana nan yasan duk wanan fitinan daya ki ci yaki karewa tsakani su Umma da Sadiya da baza,ayi shi haka ba,
Yawan cin fadan duk akan aikin gida ne don Sadiya raguwace har ta karshe bata son motsa jikin ta ko kadan
Sai dai gurin kwanane kawai take da kuzari da lakka bayan haka bata iya komai a gida ba don ko girkin tayi haka zaici shi ba,dadi, tun bai saba ba har yanzu yasaba haka yake hafiyan abin shi,
Amma dai koma may ye ya tsayar da ita idan yadawo zaiyi kokari yatafi yagani da kan shi kamar yadda yai wa baba alkawari,
Dama can Mansur ya matsama akan cewa ya tafi yadawo da matar shi don wallahi idan ya bari Aisha ta kurce mai sai yayi daya sanin rabuwa da ita daga,baya don wanan da yake gani kamar wata matar arziki babu komai na alheri a tare da uta sai tsiya don tin ba,aje ko ina ba tafara tarwatsa mai kwanciyan hankalin shi,
Sai yake ganin don Aisha tana tare da matar mansur ne yake fada mai hakana bai ganin kirkin sadiya din,
Haka yasa yanzu bai son ma su zauna dafa shi sai mansur din don kada ya kawo mai zancen Aisha,

****** ********* ******
Rigar da nake sakawa normal a jikina yau shine yaki sizing din jikina dole ina son yin adon jumma,a dashi na cire shi na sakewani,
Gwagona dake zaune daga wajen daki idanuwan ta akaina naji tana fadin anya Indo ba zargina ne zai zama gaskiya ba kuwa,
Da,sauri na jaye madubin da nake kallon ina mai duban gwagona nace gwago zargin may kike ne kuma,
Tace ciki a jikin ki mana don gaskiya idan har ba idona ne ke min gizo ba zan iya cewa ciki ne dake Indo,
Cikin dan langabe kaina na marairaice nake cewa haba gwago kada ki sa gaba faduwa mana ki daina wanan zancen kada wasu suji ki a zaci cewa da gaskene zargin ki a kaina
Ai, gaskiya take fadi don ba wanda baisan cewa kina da ciki ba,a gidan nan,
Cikin sauri muka juya inda Inno take shigowa dauke da kwaryan gari da lariya a cikin sa ,
Innalillahi na,samu furtawa don jin mugun kazafin da ake shirin min da rana tsaka,
Nace haba mama Inna wani irin ciki kuma ni da yau rabona da mijina kusan wata uku ke nan ta yaya zan yi ciki ba miji tare dani,
Ciki kan ai da abinki kinka taho, garin ga,
Cikin da yanzu yakai wata shidda da yan kai zakice wai wani abu,
Shin ko gwagon kina bakin son tasan da zancen cikin wai kika,wani dan boye boye haka, ?
Lalaikan Inno walle sai yanzu idon yaggane min zahiri cikina kuwa gashi har ya girma haka,
Amma dai yarinyar ga ke, shammace ni wallahi a,a ankayi ban ankara ba da lalura a jikin ki tun wuri,
Kesan munafukin ciki na da ita gashi kuma cikin farina shi yassa ba aganewa don har ma sai ta haihu mutane basu sani ba,
Amma ko ai jikin ta duk ya nuna,alamar ciki tu dauri naso na hwada maki amma,sai najja bakina nai shiru ka acce min na faye surutun tsiya,
Dauri Inno amm, ai da ke sani kifada min wallahi don wanga abu duk ya bashe ni walleh,
A hankali nakai zaune daga inda nake tsaye a bakin gadon karan gwagona na dake dakin ina mai fadin,
Innalillahi wa,inna alaihin raji,un
Shi ciki fa kinkace ajikina mama Inno tace shin wai kina nufin baki san komai ba ko ,a a ?
Nace a han kali cikin dago kaina da fuskana daya canza a lokaci daya,
Walleh, gwago ban san cewa akwai ciki ajikina ba nidai abinda nissani shina ciwon maran da nai tayi kafin na taho nan niya, kaman zan mutuwa in dare yayi,,
Daga haka na fada tunane cewa in ko ciki ne har wata shidda to tun shigowan sadiya gidan ba,a dade ba na samay cikin ke nan,
Hawayen bacin rai naji suna silalowa daga idanuwa a hankali, wanda nai bakin ciki dajin wanan mugun labari a wanan ranan,
Haihuwa da Hamza mutumin da bai san mutunci naba bai san zafina sai takura da gallazawa kawai,
Muryan su gwago naji suna fadin amma ai su iyayyen shi sun san cewa kina da cikin ko ?
Sai a lokacin nadan dawo cikin hankali na dan girgiza kai ina cewa ban tsan mani ba gwago don da mama ta fada min ko kowa bai fada min ba,,
Ranan haka na,wuni a cikin bacin rai ina da nasanin samun wanan cikin a gidan Hamza da nayi,
Mutumin da yanzu nafi tsanar shi da kowa a duniya saboda rashin rike amana da,bai,da shi a,rayuwa,
Don idan da da amana da bai wullakantani ba haka a idon duniya, kowa yagani saboda irin halarcin da nai mai a baya,
Gwagona bata bari an kwana ba ta samu iyayyena maza da zancen cikin dake gareni don ita tunda nace gidan mijina basu da labari kada su zo su ja zancen suce ba cikin su bane abin ya zama wani sabon tashin hankali kuma,
Amma sai dayan Baba na yace ai al,amarin da sauki don kinga watan nin cikin ya zarta na zuwan ta nan gurin mu,
Yanzu mu sauri zuwan shi idan har bai zo din ba zywa wani dan lokaci kafin ta haihu sai mu tuntube su da zancen don yasan da ajiyan shi a nan,
A haka kabar zancen cewa idan basu zo ba za a samau su da zancen cikin aji daga bakin su,

Gashi yanzu Alhamdullahi don na samu alheri fiye da tsanmani maikaratu a kauyen mu don nima ban tsan mani abin har yakai haka ba,
Don duk wanda naiwa aiki yaji dadi zakiga sun kawo min hatsi mai tarin yawa sun bani, a madadin kudi,
Shine gwagona ta samo daki daba kowa a gidan tana tara min wai idan zan koma sai na koma dashi gida,
Masara gyaro da dawa,da maiwa buhu buhu aka dinke min su gaba dayan su,
Naso a,sayar dasu a,can amma gwagona tace wai ai idan mutum yazo gida bai koma da amfanin gona ba tankar yan uwan shi matsiyata ne, ni gashi Allah yai min baiwa mai tarin yawa zance wai asayar kada ta,sake jin hakan ,
Dole naja bakina na tsuke nai shiru gudun kada ran ta ya baci a saboda ni,

Hamza ya,shirya kamar kullun yai sallama da mutanen gida ya kama hanya zuwa kurmi kai kaya kamar yadda yasaba yi,
Sai dai kafin ya tafi dole yabar dan abin da za,a dinga amfani dashi wadattace kafin ya dawo don gudun fitina,
Saboda,wancan tafiyan da yayi na karshe yadawo ya,samu korafin cewa wai Sadiya ta kwashe kayan abinci takai wa mahaifiyarta a gidan su,
Da kyat ya,samu ya kashe wanan wutan don Umma ta hau sosai cewa anbarsu da yunwa kuma basu san inda abinci ya shiga ba,
Ranan harda yabon Aisha yaji tayi take cewa tunda suke da Aisha ko gishirin su bata taba,dauka ta,bayar a makwabta ba,
Da kyat yasamu ya shawo kan zance har aka kashe wutan maganan don Sadiya tace sai dai a raba girki a tsakanin ta,da,su Umma don bazata iya ba ita,


Kuyi hakkuri dashi baida yawa insga Allahu zaku dinga jina na gode da kulawan ku a,gare ni tan uwa da fatan anyi sallah lafiya

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU






,IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,


Tsatsaye suke saman hanya da bakaken kayan su, don su, satan su na daban ne,
Motar kayan abinci suke sata daga motar har abincin da aka dauko su batar dasu zuwa wani kasan na daban,
Cikin tashin hankali na cikin motar suka fito don ganin bindigan da aka nuna masu,
Nan suka arta cikin daji suka bar kayan nasu da komai aguri kowa yana neman ceton rayuwan shi,
Daga ciki harda Hamza cikin masu gudun fanfalakin neman taimakon centon rayukan su sai daji suke ta bazawa dagudu acikin duhun dare,
Washegari suka tsinci kawunan su a kauyukan yarbawa da basu ko jin hausa a bakin su,
Da taimakon Allah suka samu suka dawo arewa hurjanjan dasu cikin tashin hankali,
Kafin wani lokaci labari duk ya karade ko ina kowa da irin yadda yake bada nasa labarin gurin mayarwa,
Ranan gidan su Umma Rabi sunga tashin hankali ba kadan ba mutane sai shigowa suke yi yin jaja da Allah ya tsare gaba,
Hamza ya shiga tashin hankali mara musali a lokacin haka yasa Umma dan fara shiga da fice gurin nema mashi taimakon don ya dawo a cikin natsuwan shi duk da ya na fada mata cewa normal yake damuwa ce kawai ke damun shi,
Tunane ke mai yawa na yaya zai samu wasu kudi nan gaba don yanzu bashi da komai atare da shi,
Gashi har da kudin mutane da yadan hada zuwa wanan tafiyan kuma mai kudin ba musulmi bane baida yarda da kaddara,
Wanan ne damuwar Hamza har ya shiga wasu hali na tashin hankali,
Bayan kaman sati biyu da samun wanan matsalar mutumin dake binsa dubu Hamsi yafara mashi sallama a gida,
Hankalin kowa ya tashi don mutumin yana ikirarin cewa, zaiyi karan hamza a gurin hukuma don a karban mai kudin shi,
Alkawari yai mai cewa ya dawo bayan kwana biyu zai kokarta ya,sama mai koda kadan ne ya bashi,
Hakan yasa mutumin yin hakkuri ya,tafi a cikin fushi da sharadin zaidawo nan da kwana biyu din,
Hamza hankalin shi ya kara tashi sosai yarasa ina,zai sa kanshi don tashin hankali,
Gashi yanzu ba,wani shiri suke da,mansur ba kamar farko balle ya,tafi neman taimako a gurin shi,
Sama sama suke akan yasha mai magana akan ya,dawo da matar shi yana basarwa don shi baiga dalilin da zanje na zauna garin mu ba,wani dalili maikarfi,
Kuma iyayyena na can suka kyale ni yaiwa mama Rahana magana tace sunfita iko dani babu inda zata ita,
Wanan dalilin yakara sa shi yin fushi tare da kafewa akan bazai tafi ko ina ba ita kuma Sadiya tana kara,zugashi yana hawa dokin karya,
Da rarashi da komai Hamza ya,samu Sadiya ta ara mai dubu goma sha biyu wanda take samu daga gare shi a baya take tarawa wai itama zata sai fridge dashi don taga duk da,ban gida mama tana sana,a da fridge dina tana tara min kudin,
Yaso ya tambayi mama amma yana tunanen irin rashin mutuncin daya shuka mata na cewa wai ta bar gidan don ba zai zauna da ita tana saka mashi mata a gaba ba,
Wanan kunyan da nauyi yanzu yake nadaman da,yasani da baiwa mama wanan aika aikan ba akan Sadiya,
Duk abindake gudana mama tankar bata,san abinda ke faruwa ba a gidan share kowa tayi kawai, tana kallon su,
Don duk kokarin da tayi dasu a,baya Hamza ya nuna mata bai gode ba saboda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login