Sarautar Mata

Chapter 63 of 94

akwai wani abu a kasan ran abokiyar zaman ta,sai dai mutum yai ta kokarin boyewa don kada kafitar a fili sunan ka yafita,
Don duk wace nata,yafi zafi har ta baiyyana kishin ta a,fili sunan tane yakan yifice a,duniya koda kuwa itace ake cuta sai kiga gaskiyarta ya dushe an bata mata suna da zafin kishi ke gareta,
Allah ubangiji yasa mufi karfin zuciyar mu akan duk kishiyar da zamu zauna da ita aduniyan nan,
Ina gidan zarah har zuwa wani lokaci tare da ita da mama sai yan barka dake zuwa yi mata murnan samun karuwa,
Ina kallon irin yadda kishiyoyinta suke ta faman yin dawainiya da ita a gidan duk da nasan cewa ta kasa tana kasan zukatan su dannewa kawai sukayi,
Zakice ai babu wani zancen kishi a cikin ransu a kanta suna matukar farin ciki ne da haihuwan nata,
Wanda a gaskiya zancen ba haka yake ba don ko wacen su sai da ta nuna bacin ran irin yadda Alhaji Bala ke rawan kafan haihuwan zara a fili,
Amma a fili suna nuna sunfi kowa farin ciki da,wanan haihuwan kishi ke nan na tsanaki sai kin daure zaki iya hadewa,

Na is gida a gajiye saboda tafiyan kafa danayi daga gidan zarah zuwa namu gidan akwai dan tazara amma haka na daure nai wanan tafiyan don na san watsake jikina,
Bayan na dan huta sai na kwabe nafito nafara dan aiyukan dake a gabana,
Umma da tafito waje don tasha iska take tambayana yaya masu jegon su ke nadan tsaya a cikin fara,a nace,
Umma baki ga dan ba gudan babba dashi wallahi zaki ce ba zarah ce ta haifi wanan yaron ba don girma,
Tau ijin tana cin abinci tana kula da kanta nace Umma kin manta cewa mama na can ai mama bata yarda komai daya dace mama tanayi a gurin,
Allah sarki zarah yau tazama uwa itama kamar kowa yau,
Muryan Sadiya ce daga bayan mu take cewa ai dole ta haifi yaro babba tunda mahaifin shi yana kokarin ganin ya bata hakkin ta taci tasha mai kyau yadda ya kamata,,.
Azatona zancen arzikine sai najuya a dan murmushi nake cewa ai abin ke dai badaga nan ba baiwane kawai
Tace ijiki ba mutum ya kwana ya tashi babu wani cimakar kwarai da,zai sa jikin mutum yaginu, da kyau,
Sai anan nafahinci inda zacen ta ya dosa don haka nikan na juya na nufi gurin nawa harkan nabarta nan tana zuba tana cewa,
Irin wanan abinda aka dauko ko haihuwa mutum yayi ai saida gaske zai samu abinda zaici wa cikin shi balle wani dan abin maski da zai dora sama,
Mama tace tau Allah dai ya sauke kowan ku lafiya yan kuda na kwana mu shine fatan mu yanzu,
Umma ta gajar ce zancen Sadiya da fadin haka don tasan inda ta dosa ga maganar ta,
Ga haihuwa anyi sai dai babu abin kashin kuyan a hannu don haka duk sun shiga a cikin wani yanayi na damuwa don rashin sanin taka maimai abin yi,
Barci na nake irin na masu ciki hankali na,a kwancd saidai zuwa dare nakan dan tashi barci yadan gagareni har zuwa asuba sai kuma shedan yadan rudeni na koma da kyat nakan tashi nai sallah kada asuba ta,wuce ni,
A hankali yau ma na bude idanuwa na dake da nauyin barci a cikin su,
Muryan Hanza nake ji daga bayana kamar yana magana da wani, naji yana fadin
O Allah ga bawankanan Allah kaikasan halin danake ciki a wanan rayuwan
Ya Allah kada ka bari muyi kunya akan wanan al,amari Allah kai muna mafita ta hanyar alherin ka,
Shiru naji yayi duk d idanuwa biyu ban nu mashi alamar cewa idanuwa na biyu ba a lokacin,
Zan iya cewa yai barci amma faskiya a zahiri idanuwan shi biyu ne ba barci yakeyi ba,
Don ina jin lokacin da yakai kwance bayan yagama addu,oin shi idanuwan shi suka a kaina gurin da nake kwance yayin da yake karare min kallon cikin mamaki, irin halina don a sanaiyar dayai min ni mutum ce maihakuri da dauri ga kuma uwaba sanin ya kamat,
Amma gaba daya duk na canza mai tinanen shi a lokaci daya na,sake gaba daya duk da dai ba,wani rashin mutunci ko jittuwane babu a tsakanin mi ba,
Amma kuma bai taba tunanen cewa zan uya bijirewa bukatar shi har na tsawon lokaci irin haka ba batare da na tausaya mai ba,
Lalai mata abar su akan kishi don duk danace dokan likita nake bi yasan harda wani dalilina na,daban,
Sai faman juyi yake a saman gado shi daya yana jin kansa tankar wani dan maraya mara galihu,
Idanuwan shi suna a kaina gurin da nake kwance a kasa saman ledan dakina daya sha guga sai kyali yakeyi don guga,
Bina da kallo yayi tun daga kafana har zuwa kai tare da sauke wani irin nufashi yana maigirgiza kai a hankali ya furta why Aisha why doing dis to me ?
Mikan da naji yayi da karfi tare da lankwsa hannayen shi saida sukai kara inajin su har inda nake ,
Cikin dakewa nake sauraren shi daga inda nake a kwance duk tausayin shi ya kamani ji nake kamar na tashi nasamay shi narugumi abina
Amma kuma sai na,karasa dauriya da dakewa a,cikin zuciyata batare dana mike na samay shi ba,
Har gari ya karasa waye muna a haka kowa da abinda ke acikin ranshi,

Ganin irin yadda al,amarin sunan zara yake batun bada ruwa a,gari yasani rufe ido batare dana tuna komaiba nafitar da buhu biyu daga cikin abinda ke aje a gurina na nace suyi sha,anin bukin dashi idan an samu sai abiyani,
Ranan nasha godiya a guri Umma fiye da tsanmanina don har dakina take tana min godiya,
Bayan an sayar akadan yi yan abubuwan da suka dace na suna dasu anyi buki lafiya an watse lafiya,
Yanzu kowa ya zaunu a gida don zarah ma tana gida andawo da ita wai shan ruwan zafi,
Duk da mijin baiso ta tafi ko ina ba amma umma ta matsa wai a dawo mata da diyar ta a gaban ta ta duba abinta,
Mama Hafsi ta nuna mata cewa zata iya zuwa safe da yamma ta duba lafiyan ta amma fir Umma taki yarda da,zancen ta,
Hakan yasa kowa gane cewa wani hikima ce ta son yaudaran mijinnata don akama ce mai kawo kawo,
Sam Umma ta manta da,zancen cewa a gidan ta,akwai masu ciki haihuwan fari dake shirin haihuwa, duk da,dai sadiya bana farko bane ta taba haihuwa a baya sai da cikin yakai wata biyar tai barin cikin, sanadiyar faduwar mashin da tayi tasamu miscarriage,
Sai kuma yanzu data samu ciki a gidan Hamza shine karo na biyu dayin cikin ta,
Dawowan Zarah gida ya kara tayar da,wani fitina don sadiya ta nuna ba yarda da irin yadda akewa Zarah tallen miyan ta daban a,matsayin ta na maijego wai tunda mijin ta ke sayo abin miyan wani lokaci,
Ni duk abinda sukeyi ba,bakona bane don haka ban daga kai na kalle su ba,sai dai nai ta abindake a gabana,

****** ********* ******
A cikin dare ina barci na dinga jin hayaniya yana dan tashi a gidan nabude idanuwa na dakyat don barci nake a lokacin mai dadi,
Dana,saurara dakyau sai nake jin muryan su mamane harda muryan mahaifiyar Sadiya a cikin su,
Da kyat na tashi na bude kofana sai nakejin muryoyinsu zancen na kuda naji sunayi,
Ganin na bude kofana shi kuma Hamza a lokacin naga ya shigo gida da saurin shi, yana ce masu ya tafi gurin makwabcin mu don asamu mota amma yace wai motar babu mai acikin ta,
Yanzu yaya za,ayi kenan ga yarinya tana ta,wahala haka tun karfe hudu na yamma bata haihu ba,
Abinda ba,asani ba na juya na koma dakina don nima dai nayi nauyi sosai a lokacin,
Ban kwantaba na zauna a saman kujera na ina iya tsiyakayo maganan su daga inda nake zaune,
Yadda nakejin nishinta har dakina sai tabani tausayi sosai, gani da abubuwan da ya kamata nai mata amma kuma kishiya ce ba halin na taimaka mata,
Nishin da naji yai yawa uwar na mata,fasa wai ta nisa kwarai tasa nafito nace mama ta daina mugun yunkurin nishi don kada ta samu matsala,
Sadiya tanajin muryana ta daga murya tana fadin Aisha don Allah kizo ki taimaka min kada na mutu ba,a,samu motan kaini asibiti ba,
Uwar tace baki da hankaline da zakice kishiya ta karban maki haihuwa,
Daki na koma abina don jin abinda uwarta tace min sai faman fada take mata wai ashe bata da,wayyo,
Sakata nasawa kofana,saidai gaskiya ban samu yin wani barcin kirki ba don tausayin ta, da nake ji,
Barci barawo nasamu ya dan daukeni zuwa asuba naji ana ta buga min kofa da karfi da sauri na budd kofa mahaifiyar sadiya ce da mama suke tsaye a kofana,
Mama take cewa don Allah nazo na duba,Sadiya tana a cikin wani hali,
Na,rasa yadda zan yi do gaskiya nace bazan taba taba don ina gudun abinda ka iya zuwa ya dawo,
Fita nayi zuwa kofan ta,wanda zance na mata yaushe rabon da naje dakin Sadiya koda kuwa kofan tane,
Kayane kamar dakin tsohuwa ko ina sai doyin tsamin dauda da dakin keyi,
Mama da mahaifiyar ta naiwa kwatancen yadda zasu taimaka mata na fake da cewa ni bazan iya ba don bana jin dadi,
Ina daga kofa nake basu directions ba adauki lokaci mai tsawo ba,sai tai wani nishi maikarfi sai ga da yafito,
Ikon Allah muna ta,wahala tun dazun ashe ga abu da saukia gida,
Gaba dayan su bazu kula da cewa yaron baiyi kukaba,sai faman cewa suke namiji ne gashi gudan babba dashi,
Nace mama ku yanke mai cibi don ya samu yadan huta ko,
Saboda yasha wuya kuma gashi baiyi kuka ba nan hankalin su gaba daya yadawo ga zance na rezan ma Sadiya bata dashi sai gurin Zarah aka,samu sabon reza,
Yaro yaki kuka har tsawon wani lokaci nace gaskiya su kaishi asibiti da sauri don a duba lafiyan shi,
Yaron yana hannun Umma, sai numfashi yake sama sama wani iri saboda wahalar da ya sha a ciki,
Ruwan wanka na,dora masu sai mamace tazo ta karbe ni tana cewa jeki huta kinji Aisha kema ai ba lafiyane dake ba,
Tunda,safe suka tafi asibiti sai gasu sundawo suna cewa wai anbasu gado saboda yaron baida lafiya



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


Gaba daya hankalin kowa,a gidan a tashe yakd saboda wanan haihuwan da akayi,
Sai dai kuma,gashi an samu karuwa,amma kum,yaron baizo da lafiya ba a jikin shi,
Babu wanda ya zauna a gida don hankalin su ya na a gurin yaro mara lafiya, da uwar sa,
Ina zaune a kofan dakina na saman tabarman dana shimfida a kofar dakina don daki a kwai zafi sosai a cikin sa,
Kafafuwana da suka hau suka kumbura sunyi sutum sutum dasu,
Gyara zama nayi cikin kara jingina baya na da bangon da nake zaune a gefen shi,
Tausayin kaina ya kamani don ba bu wanda ya,damu da damuwana agidan kowa hankalin shi na kan haihuwan da akai masu sai farin ciki sukeyi, abinsu,
Ibrahim wanda tun safe ban gan shi ba,a gida ya,shigo da,alama bai kwana a gida ba dawowan shi ke nan a lokacin,
Har zai shiga dakin mahaifiyar su sai kuma yadan dawo baya yana dan kare min kallo ya ke cewa madam yaya akayi ne wai,?
Dan murmushi nayi tare da,gyara,zamana nasan har kullun duk cikin diyan Umma babu mai kaunana yadda Ibrahim yake matukar nuna,mi kullawan akoda yai she,
Cikin murmushi nake cewa sai yanzu aka,dawo kenan yace wallahi kin san aikin mu sai a cikin dare muke tashi mu fara kwaba flower don kada mu makara,
Yana shiga dakin shi sai ga Hamza ya shigo gidan da ganin fuskan shi kasan cewa yana a cikin matukar damuwa
Sannu da zuwa nai mashi tare da dan yunkurin mikewa,zaune da kyau nayi don na fuskan ce shi,.
Tambayan shi nayi cewa yaya jikin yaron sai yake ce min cikin dan canza fuska mai nuna damuwan mutum da cewan da,sauki a takaice,
Murya mai nuna damuwa a fili yadan ce a kasalance magani aka rubuta na,sayo na,samu na,sayo wasu wasu kuma ban samu sayan su ba tukun,
Shiru na dan yi zuwa wani dan lokaci ina zancen zuci don nasan yau duk inda zai shiga neman kudi a garin nan ya shiga don yai fari a gurin Sadiya in ba haka ba su sa kafan wando guda dashi da ita,
A sake na dan dago kaina nake cewa a zubo ma abinci ne kadan ci ko ? na nuna kamar ba abinda ya damay ni a zuciya na hakana,
Idon shibda suka dan kada sukai ja ya dago ya kara kallona yake cewa ashe kin samu girka abincin ne,
A,sake batare da na bashi amsa ba nake cewa na,asibiti ga ya can idan ka tashi sai a kai masu nasu don rana ya soma yi ko,
Na mike da kyat na zubo mai abinci a plate don nasan ba zama zaiyi ba balle na kawo mai a kulu,
Na tafi de bo mai ruwan sha ya kalli abincin ya,wani sauke ajiyan zuciya tare da godiya a ranshi don yasan cewa in badon Allah ya hada shi da nice ba yau da,bai san yadda zai yi ba,
Don inda Sadiya ce yadda bai bata, ko kwandala tayi girki ba,sai dai na,asibitin su mutum don baza tayi ba, wani bacin rai da,ahi kadai yasan dalilin shi yazo mai a rai abinda ya haddasa mai, bacin rai ya dan runtse idanuwan shi a hankali,
Har zuwa lokacin da nakawo mai ruwan idanuwan shi suna a lumshe bai bude su ba sai da yaji motsina ya dan bude lumsassun idanuwan shi da,suka kada sukai jawur,,
Ya sauke su a kaina cikin dan sake ajiyan zuciya, yake cewa wallahi duk abubuwan sun daure min gaba daya duk na zagaye garin nan amma ban samu wanda zai taima min ba da ko kwandala koda da sunan rance ne,
Allah ya kyauta nace tare da mikewa nabar gurin cikin dan tafiyana da nake yi da kyat, irin ta masu tsohon ciki,
Bin bayana yayi da kallon yadda yaga ina tafiya da kyat kuma a,hakan nayi muna girkin gida,
Ya shiga asibiti da kulla Sadiya tana hango shi ta,fara cewa ji shi dan Allah yanzu haka matar shi ce tai girkin don rufin asiri ya wani dauko ya nufo mutane dashi,
Tun dazun ance a,kawo magani amma,shiru kake ji ba,wani motsi tun safe sai yanzu ya,shigo wa mutane, da gadara aljihu babu ko kwabo,
Wata matar makwabatar su da tazo duba,su take cewa haba Sadiya mijinki ne fa na,sunna kikewa wanan zari haka gaskiya hakan baiyi ba,
Daidai lokacin ya iso gare su yana gaida su ya aje kayan abinci daga gefen su kadan
Gurin da yaron yake kwance yana mayar da numfashi sama sama ya,dan tsaya har tsowon wani lokaci yana kallon yaron , cikin tausaya mashi,
Muryan Sadiya ce tas shi juyowa tana fadin har yanzu ba,a,sayo maganin bane don nurse din ta,zo dazun tana tambayan mu ko an sayo,
Ledan da ya,aje gefe tare da,abinci ya,dauko yake cewa ga,wanda aka,samu,
Ke nan ba,a samu ba gaba daya ke nan gaakiya ni wanan al,amarin ya fa fara isata ace mutum kamar shi yafi kowa,shiga talauci komai mutim bai iya kata bus akan shi,
Tunda,abin ya,ishe ki ai sai kiyi maganin abi ko yafada cikin dan juyawa a,fusace ya fita daga dakin,
Yana fita daga,dakin ta jawo kulan abincin da yashigo dashi tana cewa bari naga yar sherin may ta,dafa muna ne wai,
Tana bude kulan tayi tozali da tuwon shimkafa da miyan taushe sai kifin da nai amfani da su a ciki,
Aka zuba mata tashiga ci tana ta,surutun tsiya kamar ba dantane a cikin wani hali ba na rashin lafiya irin haka,

Ban samu shiga gurin su ba,sai da akai sallah azahar na,shirya na tafi dubo su a lokaci Umma ta,dawo gida ita da zarah,
Tun daga nesa nake jiyo muryoyin su suna hira cikin dariya ita da matan uguwar su da,sukazo duban ta,
Tana hagone ta wani juyawa ta bada baya yayin da na karaso nai ma matan da ke zaune ina,wuni,
Sadiya bata juyo inda nake ba nake tambayan matan da na samu a dakin nake ya jikin yaron suka amsa min da,da sauki,
Idanuwana akan yaron ina kallon yadda yake mayar da numfashi da,sauri da,sauri,
Tausayin yaron ya kamani irin yadda naga yanayin shi nasan yaron yana jin jiki akwai abinda ke damun shi,
Tsayin lokaci idanuwa akan yaro ban san lokacin da tausayi yasa cewa ya kuwa samu yin kukan,
Har yanzu baiyi ba amma insha Allahu zai yi ai, tunda lafiya tana shigan shi a hankali muryan mama,Sa,a mahaifiyar Sadiya ke fadin haka,
Tsayin lokaci suna ta hiran su Sadiya tankar bata,san da tsayina a gurin ba,
Ina tsaye ina kallon wasu sun shigo ambasu yaron su dauka ni kuwa an hana min daukan shi don ina kishiya yar a,dawa,
Inan tsaye dai ba,a bani ko gurin zama ba, Sai ga,wata nurse tazo tana fadin don Allah su rage yawa a,dakin don sun cika mutane da surutu , da yawa,
Zan juya nima na fita Hamza ya shigo yana cewa ashe kin samu fitowa nazaci bazaki iya zuwa ba ai yadda na ganki dazun ai, yana kokarin mika ledan da ya,shigo dashi a hannun shi,
Murmushi nayi nake cewa na lalabo nazo na duba su na koma,ai ba,dadewa zanyi ba,
Wanan ai basu cika ba abinda aka ce guda shiddane zaka kawo kwali biyu kawai,
Su na samu kuma bazanyi sata ba don kiji dadi ko ?
Nurse ki duba min wanan maganin da ya,sayo don ba duka ya kawo ba sai nurse din takaraso tana dan duba maganin tace gaskiya sai ka,karo sauran zaifi don wanan kawai ai bazaiyi amfani ba,
Caraf nace ai duk antibiotics ne zasu iya amfana da amfara,shan su kafin sauran su zo don su fara yi mai aiki, sai na,fadi

Download complete TXT · Novel page