Showing 186001 words to 189000 words out of 299981 words

Chapter 63 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17624

mace don tai mashi gyara kayan ka,
Ranan da akace mutumi yadawo tunda farar safiya ya,sallama masu da tashin hankali dan kudin da ya,samu a gurin Sadiya ya bawa mutumin amma,sai yace wai sam bazai karba
Yana kokarin tara masu mutane a kofan gida sai ga Mama Hafsi ta kasa kyalewa ta fito da kudi a hannun ta ta mika mai, kudin ya kama dubu ashirin da biyar saura rabi ke nan,
Mutumin yai hakkuri ya tafi yana dan zage zagen shi don shi yace bai san kaddara ba,
Shikuma Hamza kaddarace taja shi don bai taba sana,a da wanan mutumin ba,sai wanan karo da kudin ya hada,su na ledan da ya,saya ya,dura kayan shi a ciki,
Yau za,a ji labarin barayi gobe za,aji labarin su sai shiru kake ji babu wanda yaji su don su basu ko kasan sun ketara da kayan kasar Benin republic sun sayar har motar gaba daya a can,,,,

****** ********* ******
Tun ina saka yar damuwa a rai akan cikin dake a jikina har takai na gaji na,bar sa,wani bacin rai a,tare dani,
Ga kulawan da nake samu a gurin gwagona wanda yasa nayi kiba nayi wani irin bulbul dani, saboda duk wani abin da ya dace abawa mai ciki shi take kokarin kawo min,
Agaskiya banda abinda zan fada akan iyayyena don suna iya kokatin su dani sosai a zaman da nake a gurin su,
Zaune muke a dakin mu gwagona tana kada zaren ta irin da mutanen kauye keyi don sana,a sai take ce min ,
Ikon Allah wai jiya da mahaiginki nai mafarki Indo shine abin ya tsaya min a rai yana matukar damuna wallahi,
Din na ganshi a cikin wani yanayi wanda bazan iya gane ko yana mace ba ko a raye,
Gurin da na ganshi a tsaye abin ban ko iya musalin shi sai murmushi yake min nace mai ashe kana raye yace min yana nan yadai yi nisa ne damu kawai,
Nace gwago aida Sadaka kikayi kafin ki fadi mafarkin na ki don kinga shi sadaka yana mayar da sheri alheri haka kuma,wata katanface babba ga bawa,
Mafarki anfiso kayi sadaka kafin ka,fadi don kawar da shedan acikin sa da kwankwanto,
Tace aikuwa ina da dan guntun dawa a dakin nan bari na kaiwa Gude makauniya sadakan shi,
Gwago sadaka anfison mutum yayi shi da dafafen abin ci ko kosai ko masa ko kulikuli ko ayya ko gyada ko sugar da,dai sauran su,
Anfison mutum yai sadaka,da abu dafafe wanda zakawa yana ci yana jin dadi kai kuma Allah yana maka saukin al,amarinka a take,
Gwago tace aiko ina da,sauran tuwo a dakin nan da,kulin kuli kuli bari na rabawa yaran shi a waje,
Gwagona tana fita daga dakin na nisa tare da cewa ikon Allah ko may ya raba,shi da gida haka ya shiga duniya tsawon lokaci haka,
Don dai a gaskiya gidan su a kwai rufin asiri suna noma suna kiwo suna da gonaki da yawa gasu kuma yan kasuwa ne su,,
Amma ya tsalake yan uwan shi da kowa nashi ya shiga duniya ba wanda yasan idan yake ko a raye ko a mace,,
A gaskiya Ummina ma tayi hakkurin zama a cikin kauye irin wanan gaskiya ba yadda za,ayi ta zauna a haka,
Mutum adauko shi daga birni a kawo shi kauye irin haka bawani abinjin dadi ko kadan acikin sa,
Kyawo dai ace andauko mutum daga kauye an kawo shi birni zama ba daga birni akai mutum kauye ba,
Kauyen da ba ruwa ba wuta, babu wani abinjin dadi a gari ko wani dan abin marmari babu ba abinci mai dadi ko kamshi sam,
Gaskiya dolene Ummi ta tayar da hankalinta tabar wanan garin ta koma gurin diyan ta, da tabaro a Jega, su yayana Audi,
Muryan gwagona ce tadawo take cewa indo kin kuwa ga kamar kada nai sadakan nan sai naji wani irin sakat a cikin raina duk kuncin da nake ji da farko kamar an zare min shi yanzu,
Gwago ai Allah da Annabinsa sunyi gaskiya gurin taimakawa musulmai akan al,amarorin muna yau da kullun,
Komai yazo muna a bauyyane sai dai idan mutum bai bi tafarkin Allah ya juya zuwa,shirka shine zai yi wahala, a rayuwan shi,
Gwagona tace ai shi nake fadawa wasu yaya akan zancen Halidu don abinda ban mamaki ace daga dan tsantsami mutun ya tafi yabar gida har tsawon wani lokaci irin haka,
Ba ma wanda ya sani ko ya mutu ko yana raye don babu wanda zaice ya taba ganin shi, tunda yatafi,
Dan tsantsami ne na baki ya hada su da yaya Sale, akan gona shine asuban farko ya sulale yabar garin nan har yau ba mai cewa ga inda yake,
Gashi duk cikin mu yafimu zumunci ga kyauta, da son yin alheri har ga,wanda bai sani ba,
Matarshi ta farko ta,rasu a,gurin haihuwa ya jima ba aure shine da innar ki tazo ganin gida lokacin tana zawarci sai ya nemay ta bataso ba don zaman nan kauye amma sai iyayye suka fi karfinta aka daura dashi dayake akwai rabonki,
Amma auren nasu baiyi wani dadi ba don kokarin bata muna zumunci yayi shine ya zauna ba wani aure har zuwa lokacin da ya bar garin gabadaya,
Yanzu gashi kowa nason ganin shi babu dama mugun halin yaya yasa yaiwa dan uwan shi cin fuska a gaban mutane,
Shine yaji haushi zuciyar fulanin ta motsa mai yabar gida gaba daya don kunya wai,
Cikin zancen gwagona nadan tsunci amsoshin da nadade ina,son sanin su akan mahaifin nawa,
Ashe ma ba,dan duniya bane yadda su Ummi ke nufi wai ya tafi yawon duniya ne yabar gida,
Dalili ce tasa shi barin gida gaba daya gashi yanzu ba,a san inda yake ba ma gaba daya ko a,raye ko a mace,
Idan dai yana rayene Allah kadawi dashi gida cikin yan uwan shi inko yarigamu ne Allah ka,karbi bakuncin shi ka,haskaka mai makwancin sa,
Shiru shiru babu labarin zuwan kowa daga jega don haka gwago ta samu maza akan zance,
Wan mahaifina yace zuwa wani sati zai shirya ya je yaji may Hamza yake ciki da zancen aurena da shi da kuma cikin dake jikina,

****** ********* ******
Abubuwa duk sun taru sun rukice wa Hamza a lokaci daya gashi baida komai duk an kwashe shi tas,
Ga shi ba abinci a gida ga fitinan Sadiya sai abin da ya karu tsakanin shi da ita dama mutanen gida gaba daya,
Zancen zuwa ya,dawo da Aisha dake garin su ya tsaya mai a rai don shima a gaskiya yanzu rashinta a tare dashi ya kai mai ko ina,
Gashi ko kudin motan da zai je sokoto baida su balle har ya karasa kauyen mu gurin iyayyena,
Yanzu kunyan Baba Mudi yake matukar ji don yai mai alkawari bai cika ba hakan yana nufin cewa bai ra,ayin Aisha a ranshi ke nan,
Kwana yake da tashi da zancen a,cikin rayuwan shi ya rasa yadda zai yi da kan shi,
Ranan da abin ya ishe shi gashi sun kwana suna fitina,da,Sadiya baiyi barci ba ya yanke shawaran cewa ya,samu aminin shi mansur kawai da zancen tunda babu yadda zai yi,
Don haka washegari tunda safe ya shirya sai gidan Mansur yai mashi sallaman cewa ace shine ke sallama mashi,
Koda hindatu ta fada mai bai gaskanta zancen taba sai da yafito yasamu cewa Hamza din ne dai da kan shi,
Yai mashi iso da,su shigo daga cikin gida su zauna a falon shi,
Hindatu tana kitchen a lokacin irin yadda ta gaidashi sai baiji dadi a,ran shi ba sam ita ko dama da,gaiyya tai mashi haka din,
Cijin dan tsawalla suka kara gaisawa da Mansur din sai Mansur din ne yake tambayan shi cewa lafiya dai ko yafan shi da,safe hakan nan don ya,dade rabon shi da gidan gaba daya,
Cikin dan, shakka da kuma kunya yake cewa wallahi zancen Humaira ne gashi ina son zuwa garin su don na,dubata ko lafiya takai har warhakan nan a can,
Ga kuma abubuwa duk sun tsaya min a lokaci guda don ko kudin motan zuwa sokoto banda shi Wallahi,
Shiru Mansur yayi tare da dan furzar da iska daga bakin shi ya san harka ce ta aure idan bai taimaka mashi ba zancen zai lalace ne gaba daya,
Don haka,sai da yadan ja mai gas sannan yake cewa yanzu hankalinka yadawo akan ta ke nan ko da har kake kokarin zuwa dubata,
Cikin jin nauyi da kunya yake cewa ba hakana bane, kawai dama ina da niyan idan na,dawo daga tafiyan da nayi na karshe sai na tafi garin shine kuma wanan kaddaran ya,faru dani a hanya,
Hmmm kawai mansur ya ce bawai ya yarda da,zancen Hanza din band,
Sai cewa Hamza yayi dama ai nabarta ne don kowa a gidan ya gama fahintar gaskiya kafin na,dawo da ita,
Yanzu ita wanan da Umma ta ce na,auro ita ce ta gari ai gashi tana,nuna mata halin ta, tunda Humaira bata da amanan su bagashi nan yana fita a tsakanin su ba,
Cloud you believe cewa Umma da kan ta shekaran jiya saida tai min zancen cewa wai ya zancen Humaira ne ake ciki,
Yace nabata amsa da cewa sai na samu sarari zan tafi garin ,
Ashe wanan yar arigido din tana,kusa shine tashiga fitina wai in dai Humaira zata dawo ne sai dai na sake ta don ita bazata kara zama da ita ba a matsayin kishiya kuma,
Muryan Hindatu sukaji kawai tsagal tana cewa eyyeh yar raini wayyo wallahi saidai ita ta fita tabar gidan amma kamar Aisha ta dawo tagama ko,
Ai tsakanin ka da Aisha wallahi sai Allah dama ai munbari ne muga iya gudun ku tunda kunce,wai mu bamu iyaba ga,wacce ta iya ankawo,
Banda cikn may zama da Sadiya ya karaka dashi duniyan nan wanan mai farar kafan tsiya haka,?
Duk auren ta ya mayar dakai wani iri kakoma kamar wani tsoho ba hamza ba can
Dariya kawai hamza keyi ita ko Hindu sai zazaga mai masifa takeyi shiko yana ta faman murmushi kawai,
Mansur ne yace mata to ku raga mashi hakana mana tunda yayi saranda ai shike nan ko,
Wallahi, abin akwai wulakanci a ciki ace yarinya tana ta hadiyan hakkuri gurin mahaifiyar ka da yan uwanka da gurinka kawai take jin dan sayi shine kai kuma,fon ka auro wanan mai bussashen idon zakawani juya mata baya,
Ai haihuwan da kake wa rawan kafan za ai maka a gida na Allah don bai manta da kowa ba ko ita Aishan yaga dama yana iya bata duk sanda yaso,
Cikin sanyin murya yake cewa tau yanzu dai don Allah dai ayi hakkuri anyi kuskure insha Allahu za,a gyara, gaba,
Oho dai mu wallahi munfi karfi aceza,a wulakanta mu ko a,yarda mu don ko yanzu mun nunawa mutun bafa dole bane zama da mutun don anga muna hakkuri shine ake kokarin takamu yadda aka,so,
Kudai yi hakkuri dan Allah insha Allahu bazaa kara ba nan gaba,
Da kyat mansur ya,samu ta fita daga falon don ta,barsu su karasa zancen su,
Sun aje magana da cewa karshen sati zasu shiga garin mu da yardan Allah dai lokacin da babana yake cewa ranan litani zai shigo jega,don yaji ba,asin zancen mu,
Daga haka sukai sallama Hamza yana wa Mansur godiya don yasan duk cikin garin nan shika dai ne mai kaunar shi tsakani da Allah,
Sai dai maganganun Hindatu sunyi matukar tsayawa Hamza arai don yasan duk abinda yaji a bakinta akan shi nake zaune nima don bakin mu daya da ita,
Hindatu ta san komai akan tafiyana kyale su kawai tayi shida mansur din don a tunanen shi mansur baisan komai ba ke nan,
Shi fa ba wai qani fifita Sadiya yake a kaina ba,saboda cikin dake a jikin tane kawai yake dan kokarin shi akanta,
Kuma ita,Sadiya mace ce mai masifan son kwana da miji don hakane yake kokarin biye mata,a zauna lafiya kada Umma tace yai laifi,
To amma may yarage Aisha din dashi da ake ganin rashin adalcin shi a kan ta hakane wai,
Amma yanzu abinda zaiyi shine zai kokarta yaga inda keda matsala sai yagyara don baison a kirashi da,rashi adalci kuma,

****** ******** ******
Ina kwance ina barci a,saman gadon karan gwagona,wanda tunda nazo a,sama nake kwana ita kuma tana kasa saman tabarman roba,
A cikin barcin da nakeyi nake jin muryan Inna tana fadin wasu bakine su kazo wai sun na neman ,Indo amma dai ina ganin kamar mijinta ne,
Mijin ta,shin daga ina,sunka ce suke ?
Wai da Jega suke, inna taba da amsa,,
Ke walleh shina duk yadda ankayi suna sunka taho,?
A hankali na bude idanuwa na dake lumshe saboda nauyin barcin da nakeyi ina jin zancen su kamar a mafarki,
Don gaba daya na,fitar da,rai ga zuwan shi garin mu asalima dai ina ga kamar har mun rabu ko,
Saidai, bakin cikina shine wanan cikin nashi dake ajikina shine kawai bacin raina,
Don ban son wani alaka ya,shiga tsakani na,dashi gaba daya na,ma manta da cewa na taba auren shi, a rayuwana gaba daya,
Sai dai kashh wanan cikin da Allah ya bani a lokacin da zuciya take a cikin kunci bai sani jin dadin sa,ba,
Kukai masu tabarma muryan gwagona ne ke tashi da kuma sauran matan uban naina dake sintiri a tsakar gidan mu,
A hankali na mike zaune a hankali daga kwanciyar da nake ina mai kura masu idanuwa na don gani yadda duk suka rude da zuwan su ,
Mutumin da bai rike masu amana diyar su ba kamar yadda,sukai mai halarci da farko,
Abinci aka fara gabatar masu dashi tare da fura danono mai kauri sun sha furan sosai fiye da abincin
Sannan suka,fara ganin iyayyena maza suka zauna dasu dan su tatauna akan zancen mu,
Mansur ne yafara magana yana mai basu hakkurin rashin zuwan su da wuri sai kuma matsalar kaddaran da ya,fadawa shi hamza din wanda ya kara jawo masu delay din zuwa,da,wuri,
Nan suka,dauki salati kowa,da irin nashi kabbaran suna mamakin irin yadda za,ace, wai ansace mota har kayan dake cikinsa baki daya kai irin wanan zamani haka babu tausayi ga mutane ko kadan,
Dole jin wanan zancen yasa su Baba suka tausaya mashi, suka kasa cewa wani abu akan abinda suka kullayi mashi sa farko,
Amma duk da gaka,saida Baba Sale yai mashi nasiha akan jin tsoeon Allah dakuma rike amna da hakkin aure,
Inda yake cewa Hamza ya gode wa Allah da ya bashi mata mai mutunci kirki ladabi da,sanin ya kamata, kaman ba karamar yarinya ba a,dan zaman da mukayi da ita mun fahinci halaiyanta tunda tazo garin nan bata,taba ketare maganan mu ko fada dawani ba a gidan nan,
Wanan gaskiyane baba halintane wallahi don duk zaman mu da ita wallahi bani mijinta ba har mutanen gida da muke zaune dasu ba may cewa Humaira tai mashi wani abu sai dai kawai zama irin na mata na yau da kullun,
To dan Allah a tsare gaba don bawai ba mu son ta bane kaga mun barta can kawai don uwar ta da kuma mijin ta da muka ga ya dauki nauyin yaran mukewa wanan halarci amma a hakikanin gaskiya baso mubaka ita ba takoma gurin ka ,
Don kagan ni nan wallahi a jibi nake da niyan zuwa mu kashe wanan auren naku,
Cikin sauri Hamza yace don Allah Baba kuyi hakkuri insha Allahu ba asakewa,
Baba yace ai wanan cikin dake a jikin ta yasa kaga ban dauki wani mataki ba tun zuwan ta,
Cikin wani irin mamaki da tsoro Hamza ya ce ciki Baba ?
Mansur ma da,sauri yace ikon Allah cikine ga Aisha din ?
Ciki har ana batun haihuwan shi kenan kuma baku san da zancen shi ba ke nan ko ?
Gyara zama Hamza yayi gumi yana karyo mishi cikin jin nauyi da kunya yake dan cewa
Wallahi Baba bamu san tana da ciki ba don ko mahaifiya na ina ganin basu sani ba don banji kowa yana fadi ba,
Magana,su Baba keyi da Mansur amma shi hankalinshi yana ga tunanen cewa,
Ita Humaira wata irin yarinya ce da zurfin ciki irin haka ciki a jikin ta har ya girma amma ba wanda tafadawa tana ganin irin yadda ake dauki da murnan samun cikin Sadiya a gidan amma tai shiru,
Yana son yaga yaya ta koma da ciki ajikin ta yason yaga yadda jikin ta zai koma yadda ciki zai zauna a jikin Humaira,
Daga karshe aka basu ison cewa su shiga ciki suga gwagona da nake wurin ta,
Daga cikin dakin gwago aka shimfida masu tabarma suka zauna kamar yadda sarakai keyi idan sun zo gaisuwa,
Sun gaisa acikin mutunci itama dai hakkuri suka bata sai take dan masu nasiha akan rikon amana da zaman aure,
Hamza sai raba ido yake yaga ko ta ina zai ganni na fito don yaga yadda na koma,
Matan gidan mu sai tururuwan zuwa suke suna gaishesu da zuwa don kawai su gan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login